❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : ANISH Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i ' Wannan labarin kirkiro shi na yi , duk yadda ya yi kama da labarin wata ko wani babu hannu na a ciki , ban yarda ba wani ya sauya min ko da kalma daya ce da ga cikin aiki na , yadda mu ka fara shi cikin Amincin Allah ina fatan mu ida shi a haka ' ❤ Wannan page naku ne massoya na ❤ Allah ya bar mu tare forever and ever BOOK 1 ……………………………📚✍✍ ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ [01/08/2024] PAGE 1 ❤🔥 BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM * NIGERIA ( KANO STATE ) * NEW ROAD Wata kyakyawar yarinya ce ta ke tafiya a hankali saman titi ta na tafe ta Na wassa , a shekaru ba za ta wuce 14 years ba Kyakyawar ce gaskia jinin haussa Fulani , skin din ta chocolate , ta na da shape kamar coca cola duk da karancin shekarun ta breast din ta a cike ya ke kuma a tsatsaye ga M Skuma hips , ta na dara daren idanu barare kal kamar madara , kwayar idanun ta black ce har wani kyali ta ke , ga dogon hanci mai kyau , ga dan karamin bakin ta , lips din ta pink colour yarinyar ta hadu kamar ita ta yi kan ta Sanye ta ke cikin wando dark brown da riga zuwa guyiwa egg white , ta daura dan karamin hijab zuwa kirji shi ma egg white, ta na rataye da Bag yar karama a baya , ga Dukan allamu da ga school ta ke Ta na tafe ta na wasu juye² ta na yar waka da ga gani kassan har yanzu ta na dawainiya da yarinta Sai da ta karasso bakin hanya za ta tsalaka titi ta tsaya ta na dube dube Cen ta hango wani makaho a daya gefen titin , ya na sanye da bakin glass ya na rike da sandar shi ya na tafiya cikin konciyar hankali Makahon kyakyawan gaske ne , fari kal da shi me zubin larabawa , ya na sanye da wandon jeans baki da riga fara , kafar shi na sanye cikin boot bakake su ma , ya hadu over , ya na da dogon hanci da dan karamin baki lips din red colour kamar jini na sama ya yi wani shape kamar heart , ga wani kontancen saje a gefe da gefen fuskar shi , gashin kan shi baki kirin da shi so smooth ya zubo mishi bayan keya sai wasu sirarren da su ka zubo mishi a gaban goshi , ya na da tsayi ga murdaden jiki kamar dan dambe , damtsen shi a murde su ke kamar za su fassa hannun rigar , ga wani kyakyawan gashi konce luff saman hannayan shi , idan ka kare face din shi kallo da kyau ya na da wani dan karamin zane baki geffen wuyan shi na dama amma gashin shi ya rufe shi ba a iya ganin shi da kyau , zannen ya fito kamar CROWN an dasa misi wata SWORD a tsakiya Tun da ta hango shi ta saki wani kyawatencen murmushi Da sauri ta kali damar ta , ta kali hagun ta , ta ga babu motoci sannan ta fara tafiya da dan sauri ta tsalaka titi Da gudu ta bi bayan shi Sai da ta zo dab da shi ta tsaya geffen shi ,cikin wata kyakyawar murya mai dadi ta ce " Yaya Zayd " Bai ce da ita komai ba su ka ci gaba da tafiya a jere Sai da su ka yi nisa cikin tafiyar su sannan ta kale shi ta ce " Yaya Zayd gida za ke je ko kuma wajen Abba za ka wuce " Jinjina mata kai ba tare da ya ce mata komai ba Haka su ka ci gaba da tafiya ta na zuba mishi surutu shi kuma ya na sauraron ta , sai in ta yi mishi tambaya sai ya girgiza mata kai ko ya jingina mata Sai da su ka iso bakin kofar wani gida , gida ne madaidaici an mishi shafen siminti da kofar gidan Light green, gida ne irin na ma su hali dan bai yi kama da gidan wadan da ci da sha ke yi musu wuya Su na isowa kofar gidan su ka tsaya a tare kamar ya san sun iso Juyo wa ta yi ta kaleshi ta ce " Yaya Zayd ni zan shiga ciki nagode da rakiya " ta kai karchen ta na murmushi Jinjina mata kai kawai ya yi , ya fara takawa ya yi gaba abun sa Ya na barin wajen ita ma ta juya ta shiga cikin gidan ta na sallama Wata mace ce ta zaune tsakiyar gidan saman tabarma , ta na tsintsar wake A hankali ta dago kan ta kali kofar shigowa ta na amsa sallamar , ta na ganin yarinyar ta saki dan karamin murmushi ta ce " Inaya har ki dawo , ina ki ka baro Nesrine " Takowa yarinyar ta yi ta zo geffen ta ta zauna ta cire jakar ta ta ajiye gefe sannan ta kama tray din hannun ta ta na fadin " mun riga su fitowa shi ya sa na tafowa ta " Murmushi matar ta yi kafin ta ce " shikenan tashi ki je ki cire kayan ki , ki watsa ruwa kin debo rana " Jinjina mata kai ta yi kafin ta ce " toh mama , amma bara na ida tsintse waken sai na tafi " Matse fuska mama ta yi ta kai hannu ta karbi tray din ta na fadin " Inaya tashi ki je na ce ko " Dan murmushi ta yi kafin ta kai dan lips din ta saitin kumatun ta, ta sumbata kafin ta mike ta dauki jakar ta ta wuce dakin da ke fuskantar su Ta na shiga dakin mama ta ji ana sallama Murmushi ta saki ta na amsa sallamar kafin ta ce " Nesrine ina ki ka tsaya haka " Wata kyakyawar budurwa ce ta shigo cikin gidan ta na sanye da uniform din school irin da Inaya, skin din ta chocolate ita ma kamanin ta sak irin na Inaya ba dan ta fi ta dan jiki ba da shekaru sai ayi musu daukar Twins , a killa a shekaru ta kai 17 zuwa 18 Geffen mama ta zo ta zauna ta kontar da kan ta saman kafadar ta sannan ta lumshe idanun ta ta ce " mama ni fa na gaji da zuwa makarantar nan, dubi duk jiki na ciwo " " karbi nan ja'ira kawai, in baki je makarantar ba ki yi mi ko aure ki ke so na yi miki, shikenan zan ce ma Zayd ya ka kudin sadakin ki tun da na lura ya na son ki " mama ta fada ta na ajiye tray din geffen ta , sannan ta yi kokarin tashi Da sauri Nesrine ta ce " a'a wlh mama, me zan yi da makaho kuma kurma, ai ba maza su ka kare duniya ba " Dariya maman ta yi ta na shirin magana su ka jiyo muryar Inaya ta na fadin " Ai ko cikin mazan yaya Zayd na daban ne , ba dan Nakassar da Allah ya jarabe shi da ita, da wlh ko yar aikin shi baki kai matsayin zama ba " ta kai karchen ta murguna mata baki Hararrar ta Nesrine ta yi kafin ta kali mama ta ce " mama kun gani ko, ita fa ta ke tsokana ta sai in na dake ta, ku ga laifi na " " Ni ai gaskia na fada, kin san dama an ce gaskia daci gare ta " ta fada ta kama hanyar toilet " mamaaaaa" Nesrine ta fada ta na jan sunnan Kallon ta mama ta yi kafin ta ce " kin ga ko kar ki kuskura ki daura hannu saman ta kin san halin baban na ku da Abdoul ba su son abun da ya taba autar su dan haka kyale ta , ai kuma laifin ki ne kin fi kowa sanin yadda ta ke ji da Zayd shi ne za ki wani bata mishi sunna " Kumbure fuska ta yi ta na fadin " amma mama haka zan zuba mata ido ta min magana yadda ta ga dama na fa girme ta sh........" Mama ta katse ta de cewa " to sai ki kama girman ki ko ki kyale ta " Ta na gama fadar haka ta juya ta shiga kitchen Tsaki Nesrine ta yi kafin ta mike ta dauki jakar ta, ta wuce dakin da Inaya ta fito Daki ne dan madaidaici sai yar katifar su da ke karchen dakin, da closet din kayan su ya na fuskantar katifar sai yar karamar dressing mirror Ta na shiga ta Fada saman gadon ta yi rub da ciki ko hijabin jikin ta ba ta cire ba A hankali ta fara sakin kuka kassa kassa ( ko kukan me ta ke oho 🤔🤷‍♀️) Ta na cikin kukan nata Inaya ta shigo dakin ta na sanye da hijab zuwa guyiwa Ta na jin shigowar ta ta yi saurin kauda kan ta gefe ta saka kanta tsakanin pillow ta na goge hawayen ta A hankali Inaya ta ke takowa cikin dakin ta na dan wake waken ta , ta wuce wajen closet din su ta bude ta dauki wata gown mara nauyi launin blue ta saka sannan ta dauki hijabin ta ta saka ta dauki daddumar ta, ta koma bakin gadon ta shinfida Kallon Nesrine ta yi kafin ta ce " Nesrine tashi ki je ki yi Alwalla lokacin sallat ya yi " Shiru Nesrine ba ta amsa mata ba, ko motsi ba ta yi ba Dan tsaki Inaya ta ja ta na kunbure fuska ta ce " kar ki tashi in kin ga dama " Ta na gama fadar haka ta fara gabatar da sallar ta Nesrine ta na jin ta fara sallat ta yi sauri ta mike ta koma gaban closet ta tsaya ta bawa Inaya baya Da sauri sauri ta cire hijabin jikin ta ta cire uniform din ta ta daura wata towel fara sannan ta saka hijabin ta , ta yi sauri ta fice dakin ta wuce toilet After some minutes ta shigo cikin dakin Lokacin har Inaya ta Kamala sallar ta , ta na zaune saman gadon su ta jingina a bayan gadon ta na rike da littafin ta ta na karantawa Da sallama ta shigo dakin ta na sunkuyar da kai Ba ta ce da Inaya komai ba ta wuce wajen closet din su , itama ta saka gown irin ta Inaya sai dai ta ta launin Red ce Bayan ta saka rigar ta dauki hijab ita ma ta saka ta dauki daddumar ta Inda Inaya ta shinfida ta ta , nan ta shinfida ita ma sannan ta gabatar da sallar ta Ta na tsaka da sallar ta mama ta shigo dakin ta na sallama Dago kan ta Inaya ta yi ta na amsa mata sallamar ta " Yawwa Inaya, dan Allah tasso ki je kiyo min cepane yaran nan sun koma sangayar su " ta na gama fadar haka ta sa kai ta juya Da sauri Inaya ta diro da ga saman gadon ta na murmushi dan dama na son fita amma ba hali A hanzarce ta saka hijabin ta, ta saka dan takalmin ta ta fito A harabar gidan ta isko mama cikin yar runfar da ke bakin kofar dakin ta , ta na zaune saman yar karamar kujera Gaban ta ta karaso ta tsuguna ta na fadin " gani mama " Dan murmushi mama ta yi kafin ta ce " to malama an ji za a fita shi ne ki ka tasso da sauri ko " Sunkuyar da kai ta yi ta na murmushi dan mama ta gano ta Dubu dayan da ke cikin hannun ta, ta mika mata ta ce " shikenan karbi ki sayo min albassa da timatir na dari biyar biyar ki yi sauri kin ga fa rana ta yi kar ki tsaya wannan shirmen na ki " Yar dariya ta yi kafin ta ce " mama ni fa ba na tsaya wa shirme kin ga kullum sai na riga Nesrine isowa gida " Ta na gama fadar haka ta tashi ta nufi hanyar fita gidan Da kallo mama ta bi ta har ta fita gidan sannan ta ce " kai ni wannan yarinyar Allah ka shirya min ita, a ce ki na girma ki na cin kassa " Inaya kuma ta na fita gidan ta fara wake waken da ta saba yi A hankali ta ke tafiyar har ta karaso wajen wata bishiya Cen ta hango wani datijo zaune kassan inuwar bishiyar ga wasu kananan yara zagaye da shi su na rike da allo su na karatu Tun da ta hango shi ta saki wani kyawatencen murmushi ta fara takowa da sauri ta tinkaro bishiyar ta na sallama A hankali ya dago kai ya na amsa mata sallamar ta Wani dan murmushi ya saki kadan kafin ya ce " Auta me kuma ki ke yi nan " Riko hanayan ta baya ta yi ta na yar jujuyawa cikin shagwaba ta ce " mama ce ta aike ni cepane " " shikenan yi sauri ki je, kin ga rana ta yi " ya fada ya na kokarin mike wa tsaye Jinjina mishi kai kawai ta yi ta na murmushi ta wucewar ta Ta na barin wajen ya kali yaran ya ce da su " ku ci gaba da karatu ina zuwa " " Toh malam " su ka fada a tare A hankali ya ke tafiyar shi ya na sanye da manyan kaya , ka na ganin ka san wannan datijon ya na cike da haiba da mutunci Ya yi tafiya wajen minti biyar kafin ya iso gidan da Inaya ta fito Bakin shi da sallama ya shigo cikin gidan Mama ta na zaune inda Inaya ta baro ta ba ta motsa ba Ta na ganin shi ta saki murmushi ta ce " sannu da zuwa Abban Abdoul " Jinjina mata kai ya yi kafin ya ce " Amina ba na ce miki ki bar barin yarin yar nan ta na fita ba " Sunkuyar da kai mama ta yi kafin ta ce " yi hakouri malam Nesrine ce ta na sallat shi ne na aike ta " " Amina da sai ki bari ta Kamala, kin fi kowa sanin hatsarin da ke bibiyar Inaya cikin rayuwar ta tun shigowar ta duniya me a ba mu fuskanta ba , a dalilin ta mu ka baro Kaduna saboda barazanar da a ke mana , yanzu in su ka samu labarin mu na nan kin san fa baza mu tsira ba , ni ko makarantar da su ke zuwa dan kin matsa ne na hakura na bar ta, ta na tafiya , ba dan Zayd ya na bibiyar ta ba ban san abun da zai faru da ita ba , dan Allah ki bar barin ta na fita wlh bazan iya jure rashin ta ba " ya fada cikin rauni zuciya ( GA DUKAN ALLAMU AKWAI WANI BOYAYEN AL'AMARI A TATARE DA AHALIN GA 🤔🤔 ) Wasu hawaye ne su ka zubo mata ta cikin zafin zuciya ta ce " yanzu dan Allah malam haka za mu ida rayuwar mu kullum mu na gudu , mi mu ka yi musu da za su ringa bibiyar mu haka , kawai dan ka hana ma d'an su auren Inaya shi ne su ke neman su kashe mana ita, meye laifin ta a cikin wannan abun yarinya karama su na neman su lalata mana rayuwar ta " ta kai karchen kuka na kubce mata Da sauri ta juya ta koma cikin dakin ta Ajiyar zuciya Abba ya sauke kafin ya bi bayan ta shi ma ya shiga dakin ya na sallama Bakin gadon ya isko ta zaune ta na kukan ta Geffen ta ya je ya zauna ya kai hannu shi bayan ta ya na dan bubugawa ya ce " kiyi hakuri Amina, in sha Allah ba abun da zai faru da ita dan na mallaka ta a hannun wanda zai kulla min da ita fiye da mu " Dago kai ta yi ta kale shi cikin kuka ta ce " ban gane ba malam, wa ka mallakawa ita kuma me ka ke nufi " Hannun shi ya kai ya goge hawayen ta sannan ya mike tsaye ya ce " in sha Allah in lokaci ya yi za ki san komai " Ya na gama fadar haka ya juya ya bar dakin Ya na fitowa harabar gidan Inaya ta shigo ta na sallama hannun ta rike da leda baka sai murmushi ta ke gwanin ban sha'awa Ya na ganin ta ya saki murmushi shi ya ce " Auta har kin dawo " Jinjina mishi kai kawai ta yi ta ci gaba da takawa ta shiga kitchen Ta na shiga shi ma ya fara takawa ya nufi hanyar fita gidan Ya na fitowa waje ya isko Zayd ya na tsaye bakin kofar gidan ya jingina da bangon gidan ya na rike da sandar shi ya dan daga kan shi ya na kallon gaban shi Abba na ganin shi ya saki murmushi ya ce " A Zayd ashe tare ku ke " Jinjina mishi kai Zayd ya yi sannan ya juya ya fara takawa Murmushi Abba ya yi ya girgiza kan shi ya bi bayan shi su ka ci gaba da tafiya a tare Sai da su ka karaso kofar wani gida dan nesa kadan da na Abba su ka tsaya a tare sannan Abba ya kale shi ya ce " Zayd za ka zo cin abincin da dadare dai ko na ga jiya ba ka zo ba " Girgiza mishi kai kawai ba ta tare da ya ce komai ba Dan murmushi Abba ya yi kafin ya ce " haba Zayd wai in ka na tare da ni din ma sai ka yi min kurmancin na ka " Dan karamin murmushi geffen fuska ya yi kafin ya yi magana cikin wata zazzakar murya cike da nitsuwa ya ce " uncle ba na jin dadin maganar ne , so ku bar matsa min ina magana please " ya fada cikin wata kwarbabiyar haoussa kamar wanda ke koyo ( WAIT ! WAIT ! WAIT ! BAN GANE BA KENAN DAMA BA KURMA BA NE KO YA NE WANNAN ZANCEN YAKE 😳😳😳😳😳 ) Jinjina kan shi Abba ya yi kafin ya ce " ba komai, amma fa mu na jiran ka yau kar ka zauna ba ka zo ba " ya na gama fadar haka ya yi gaba ya ci gaba da tafiyar shi Ya na fara tafiya shi ma Zayd ya juya ya nufi kofar gidan ya na sa hannu shi cikin aljihu Sai da ya karaso kofar gidan ya tsaya ya ciro wasu keys da ga cikin aljihun shi ya bude kofar sannan ya shiga ya na medo kofar Gida ne mai kyau dai'dai me hali amma fa ya fi na Abba Girma da kyau A hankali ya ke takowa ya nufi terrace din gaban shi ya Haye Nan ma ya sa key ya bude kofar shiga falon Masha Allah duk da falon karami ne amma ya hadu , an saka mike wasu sofas red colour , buyi two seaters, daya three seater sai guda one seater , a tsakiyar su kuma wata yar karamar table ce ta glass sai wasu remote da ke saman ta Da ka shigo bangaran dama ka na fuskantar wata yar karamar dining room mai dauke da dining table karama mai kujeru guda hudu Sai wata yar drawer da ke karshen dining room din ta na dauke da kayan breakfast kamar su madara sugar coffee da sauren su Bangaran hagu kuma wata door ce wadda za ta sada ka kitchen din Bayan sofa mai three seater wani corridor ne mai dauke da wasu door guda biyu wanda ina kwaytata zaton bedroom ne Bai tsaya bin ta falon ba ya wuce kai tsaye corridor din Door ta karshe ya nufa ya kama handle din kofar ya murda ya shiga ciki ya rufo kofar SAI MUN HADU GOBE 🤘 KAR KU MANTA KU NA TARE DA ALKALAMIN ANISH , WANNAN SO MA TABI NE ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : ANISH Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i BOOK 1 ……………………………📚✍✍ [05/08/2024] ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ PAGE 2 ❤🔥 After some minutes ya fito sanye da wandon three cuter black colour da t-shirt fara mara nauyi , babu takalmi a kafar shi , ya na sanye da bakaken glass kamar kullum Takowa ya ke cike da izza da kwarjini , hannun shi na rike da wata dankareriar waya kirar Iphone 13 pro max mai launin Gold sai shining ta ke kamar zinaryar gaske A hankali ya shigo falon ya nufi sofa three seaters ya Haye ya konta Bayan ya konta ya daura hannun shi daya saman forehead din shi, dayan kuma ya fara latsa wayar shi ( A IYA SANI NA DAI MAKAHO BA YA LATSA WAYAR SHI HAKA 🤔🤔 ) Bai fi ten minutes ba da konciyar shi wani kyakyawan matashi ya shigo falon ya na sallama hannun shi rike da ledodin restaurant Ko motsawa Zayd bai yi ba , ko sallamar shi cen kassan makoshi ya amsa mishi ita Dan karamin murmushi saurayin ya yi kafin ya tako ya zauna saman sofa two seaters da ke geffen wadda Zayd ke konce sannan ya ajiye ledodin hannun shi saman table " Nawfel ga abinci ka nan " ya fada ya na kallon shi ta wutsiyar ido A dubu dari Zayd ya mike zaune ya matse fuska ya nuna saurayin da dan yatsa cikin turanci ya ce " kar na sake jin ka kira ni da wannan sunnan Diya idan ba haka ba " Dariya sosai saurayin ya yi shi ma da turanci ya ce " In haka ne ni ma ka daina kira na da Diya , ni fa yanzu suna na Moussa " ya kai karshen ya na kashe mishi ido guda Dan tsaki Zayd ya ja kafin ya ajiye wayar shi gefe ya matso bakin sofar , ya kai hannu ya janyo table din gaban shi sannan ya bude ledodin da Diya wato Moussa ya kawo mishi Moussa kuma kallon shi ya ke ya na murmushi har sai da ya ga ya fara cin abincin sannan ya ce " Amir wai ka na da labarin......... " Bai karasa maganar shi ba Zayd ya daga mishi hannu akan ya isa haka " Haba Amir yanzu haka za mu ci gaba da zama yanzu wajen shekara hudu kenan , ba ka kewar Al-Amira Tesnim da Malikat ka na tunanin halin da su ke ciki , ko kuma ka manta da Malik " Shiru Zayd ya yi bai ce komai , ya ci gaba da cin abincin shi Sai da ya ida sannan ya mike tsaye ya nufi dining room ya bude fridge ya dauki gorar ruwa guda ya dawo ya zauna inda ya tashi sannan ya bude ta ya fara sha Jinjina kan shi Moussa ya yi cikin ranshi ya ce " Gaskia kam jinin sarauta ba wassa ba ne , ko da ba cikin masarautar ya ke ba " " Amir wai yanzu haka za mu ci gaba da wannan zaman , ka san halin da masarauta ke ciki , kar fa ka manta jinin mayakka ne kai , bai kama ta a ce ka baro filin yakin ka ba " Moussa ya fada cikin raunin murya Sai da Ya ida shan ruwan shi sannan ya mike ya nufi corridor ya na fadin " ai ka san hanyar komawa ni ban tare ka ba " Ya na gama fadar haka ya shige corridor ya shiga bedroom din da ya fito Jinjina kan shi kawai moussa ya yi ya na murmushi ya ce " ni anya ba diyar malan din nan ya fara so ba , ka san dama an ce soyayya ke meda sarki bawa " ya kai karshen ya na bushewa da dariya Sai da ya yi dariyar shi iya son ran shi sannan ya mike ya dauki ledodin saman table ya kai kitchen sannan ya dawo ya nufi corridor ya shiga dayan bedroom da ke kussan wanda Zayd ya shiga * Misalin karfe 8 na dare * Gidan su Inaya Zaune su ke cikin harabar gidan saman tabbarma su na sanye da hijab dark blue har kassa , ko wace ta na rike da littafi Malan na gaban su zaune ya na karatun kur'ani , su kuma sun sunkuyar da kai su na sauraron shi Mama kuma ta na zaune geffen shi ita ma ta na sanye da hijab amma fari Su na a haka wani dan matashin saurayi ya fito da ga cikin dakin da ke fuskantar na su Inaya Ya hadu ba laifi skin din shi chocolate kamar ta Inaya amma ta Inaya ta fi dan haske Ya na da dogon hanci da kontancen saje , ya na da dara daren idanu brown colour , ya na da dan tsayi da mudewar jiki amma ba sosai ba a shekaru ba zai wuce 26 ba amma ya tare kassunba ga kwarjini Sanye ya ke da wando three cuter Fari da shirt red kamar jini ya na rike da waya kirar Tecno pop 6 Bai bi ta kan mutanan gidan da ke zaune kussan kofar dakin shi ba ya sa kai ya fice da ga gidan Malan na kallon shi ta kassan ido amma bai ce da shi komai ba , sai da ya ida karatun shi saman ya dago kai ya kali su Inaya ya ce " Auta, ina ga za mu tsaya a nan gobe sai mu ci gaba " Jinjina mishi kai su ka yi a tare ba su ce komai ba , su ka mike su ka shiga dakin su dan su ajiye littafan su Bayan mintina goma Inaya ta fara fitowa ta na sanye da doguwar riga irin ta barci da dan guntun kyale ta ya yafa a kan ta Ta na fitowa ta ji ana sallama Cak ta tsaya ta na kallon kofar gidan kafin ta amsa sallamar Wani dan karamin murmushi ta saki ganin waye ke tare da yayan na ta Da gudu ta je ta fada jikin yayan ta ta na fadin " yaya Abdoul kenan yaya Zayd ka je nemowa " ta fada ta na kallon Zayd ta geffen ido Raba jikin ta ta yi da na Abdoul sannan ta ce " sannu da zuwa yaya Zayd " Jinjina mata kai kawai ya yi bai ce komai ba Duk abun da su ke Malan ya na kallon su amma bai ce komai ba sai ma murmushi da ya ke " malan Zayd ku karaso mana " malam ya fada cikin zolaya Yar dariya Inaya ta yi ta riko hannun Abdoul, shi kuma ya riko hannun Zayd su ka fara takawa a jere Saman tabbarma da malam ke zaune su ka karaso Saki hannun ta Abdoul ya yi sannan ya ce ma Zayd su zauna A tare suka zauna geffen Malam su ka sa Zayd a tsakiya Ta na ganin sun zauna ta juya ta fara takawa ta nufi hanyar kitchen dan ta taimaka wa mama Kamar an ce ya dago kai ya kali gaban shi Ya na dagowa idanun shi ba su sauka ko ina ba sai saman hips din ta , gashi rigar da ta ke sanye yar shara shara ce a na ganin shape din ta Sai da ya ji zuciyar shi ta buga a dubu dari ya sunkuyar da kan shi dan ya yi arba da abun da ya fi karfin shi Malam da Abdoul sarai su ka lura da shi, dan Abdoul har kumshe dariya ya ke Dan murmushi Malam ya yi kafin ya matso cikin rada ya ce " Zayd in ka shirya ni ban da matsala ka zo ka dauki matar ka ta tare a dakin ka " Dago kai ya yi ya kali malam ya na zaro idanu duk da su na cikin bakin glass Yar dariya malam ya yi dan dama tsokanar shi ya ke son yi Shi ma Abdoul yar dariya ya yi kafin ya daura hannun shi saman kafadar Zayd ya ce " Bro ka yi sauri fa dan kar ayi maka wufff da ita " Dan tsaki Zayd ya ja ya na kauda kan shi gefe Dai'dai lokacin da Inaya je fitowa da ga kitchen ta na rike da tray Da sauri ya kauda kan shi dayan geffen cikin ranshi ya na fara danasanin abun da ya yi shekarun da su ka wuce Gaban su ta zo ta ajiye tray din sannan ta mike ta juya ta koma dakin su Ta na barin wajen Abdoul ya kai hannu ya janye tray din na sama , ya dauki spoon ya mika ma Zayd da malam sannan ya ce musu bismillah A tare su ka fara cin abincin , har su ka Kamala ba wanda ya ce ma dan uwan shi wani abu Sai da su ka ida mama ta zo ta gyara wajen ta kawo musu jug na ruwa da glass biyu , su ka sha sannan Zayd ya ce da Abdoul ya raka shi gida Sai da ya tsokane shi sannan su ka tashi su ka bar gidan a tare Ya na fita Inaya ta fito da ga dakin su Ta na ganin malam zaune shi kadai Da sauri ta karaso wajen shi ta ce " Abba yaya Zayd har ya tafi " ta kai karshen ta na kallon wajen kofar gidan Dan murmushi yayi kafin ya mata nuni da gefen shi Ba musu ta tako ta zauna geffen shi ta na sunkuyar da kai ta fara wassa da yatsun ta Hannu shi ya daura saman kan ta kafin ya ce " Auta , fada min gaskia , ki na son Zayd " A razane ta dago kai ta kaleshi ta na zaro idanu, ta ma rasa amsar da za ta bashi Daga mata gera yayi kafin ya ce " ba ki ba ni amsa ba " Da sauri ta ce " a'a Abba ba ni son shi , kawai dai na dauke shi a matsayin yaya na , kuma ai ku ku ka ce na dauke shi tamkar yaya Abdoul " ta fada cikin shagwaba " kennan ba ki son yayan ki Abdoul " Da sauri ta ce mishi " ina son shi mana " Dan karamin murmushi ya yi kafin ya janye hannun shi da ga saman kan ta ya ce " to shi Zayd me ya sa ba ki son shi , ko ba yayan ki ba ne ?" " ai shi da yaya Abdoul ba daya ba ne , ba zan iya cewa ina son shi kamar yadda na ke son yaya Abdoul " " kamar ya kenan ? " Turo dan bakin nan nata ta yi cike da shagwaba ta ce " Abba ni ma ban sani ba , ni na ma tafiya ta barci na ke ji " ta na gama fadar haka ta tashi da sauri ta koma cikin dakin su Ya na kallon ta har ta shiga dakin su , sannan ya saki murmushi ya na girgiza kan shi , ita dai har yanzu ta na fama da yarinta , da ga yanayin maganar ta kadai ya isa ka gane Bangaran Inaya kuma ta na shiga dakin su ta fada saman gadon su ta yi rub da ciki Bugun ta a baya Nesrine ta yi kafin ta ce " ke dan Allah malama yi a hankali kar ki kare mana gado " Dago kai Inaya ta yi ta zauna ta na kallon ta Dan turo baki tayi cikin shagwaba ta ce " kin ga ko ki daina bugu na ko in fada ma Abba " " ina ruwa na tashi muje na raka ki ma " ta fada ta na meda kallon ta saman book din hannun ta Marairaice fuska Inaya ta yi kafin ta ce " Nesrine, wai Abba tambaya ta ya yi in ina son yaya Zayd " ta kai karshen kamar ta yi kuka Dago kai Nesrine ta yi ta kale ta da kyau kafin ta bushe da wata shegiyar dariya har da dafe ciki Marairaice fuska Inaya ta yi kamar ta yi kuka ta ce " haba Nesrine ya zan yi miki magana ki yi zaune ki na yi min dariya " Dan tsagaita dariyar ta Nesrine ta yi kafin ta ce " Yau ni tambayar Abba ce ta bani dariya , yo mi ne abun so cikin wannan abun , mutumin da ba ya magana , ba ya gani wa zai iya zama da shi ai ni ko sadaka a ke bani shi wlh ba ni so " ta kai karshen ta na sake bushewa da dariya Hararrar ta Inaya ta yi kafin ta ce " kin ga matsala ta da ke wlh ba a iya magana da ke " " yo ai wannan ba magana ba ce zancen gaskia wa zai iya son Zayd, ba dan kyawon shi ba ai ko kallo bai isa wani ba " " wai ke me ya sa ki ke yawwan cin zarafin mutane, me ya yi miki, kullum sai kin kaskantar da shi , ko dan kin ga ba ya da kowa ba ya da idon gani , ba ya da bakin magana ko dan bashi da kudi , kin je makaranta ki yi karatun kur'ani ki san Allah ba ya son mai kaskantar na kassa da shi , yanzu in kin wayi gari kin koma kurma ko makafniya ki na tunanin wani zai so ki ne , Ka zamto mai furta abin alkhairi fiye dana sharri. Domin furta sharri yakan haddasa damuwa , na alkhairi kuwa ya kan sanya walwala da farin ciki. Kasani cewa mara godiyar Allah basa cigaba. Hakama mai furta sharri , wlh Nesrine ki ji tsoron duniya wannan jiji da kai da ki ka dauko ba na familyn mu ba ne , ba mu gado wannan ba gwara tun wuri ki tambayi kan ki ina ki ka dauko su " " ke dan Allah malama ya isa dan kawai na tabo wani banza cen shi ne za ki yi zaune ki na min fada kamar wata uwa ta , ai ba karya na yi ba dan ko ke da kan ki da ki ke protecting din shi ba son shi ki ke ba dan haka ki bani lfy sakara kawai , kamata ya yi ki tafi massalaci ki dauki speaker ki ringa yi musu wa'azi ko ba komi kin samu lada no sens " ta kai karshen ta na saukowa da ga saman gadon ta fice da ga dakin da kallo Inaya ta rakata har sai da ta fita sannan ta ce a fili " wlh karya ki ke, duk abun da zai sa mace ta so namiji yaya Zayd ya malake shi , dan ya ma fi sauran mazan wlh ko cikin dubu za ki duba da wuya ki samu kamar yaya Zayd " ta kai karshen hawaye na zubo mata Da sauri ta koma ta yi rub da ciki ta fara kuka kassa kassa * Zayd Tafiya su ke saman hanya shi da Abdoul, sai zuba ya ke mishi amma shi kuma ko kalma daya bai ce da shi ba " Zayd wai minene cikeken sunan ka " Abdoul ya tambaye shi Cak ya tsaya da tafya ya na kallon gaban shi kamar ya ga wani abu ya kassa gaba ya kassa baya A hankali ya medo da kallon shi kan Abdoul ya zuba mishi ido mai ce komai Ganin ya yi shiru kuma ya tsaya ya na kallon shi ya sa Abdoul cewa " ko sunnan na ka ma ka manta " Jinjina mishi kai Zayd kafin ya fara takawa ya yi gaba Dan murmushi Abdoul ya yi kafin ya ce " to tun da ka san hanya ni zan koma gida " ya fada ya na daga mishi murya Bai ce mishi komai ya ci gaba da tafiyar shi Ganin bai ce komai ba ya sa Abdoul juyawa ya koma gida Shi ma Zayd hanyar gidan shi ya kama Bai fi minti biyu ba ya iso gida Da sallama bakin shi ya shigo falon gidan nan ya isko Moussa ya na zaune saman sofa da ga shi sai short da singlet ya na latsa wayar shi Dago kai ya yi ya na amsa mishi sallamar shi kafin ya ce " Amir wai ina ka tsaya ne haka tun dazu ni ke jira ka " A hankali ya sa hannu ya zame glass din idanun shi Allahuma barik ashe ba banza ba ya ke saka glass ba , ko ni sai da na yaba kyawon idanun shi Ya na da dara daran idanu Farare kal kamar madara Launin idanun shi Hazel mai bala'in kyau , har wani green ya ke yi , sai shining ya ke abun har ya ba ka tsoro kamar idanun mage cikin dare haka su ke Karasowa ya yi cikin falon ya ajiye glass din saman table sannan ya zauna Saman sofa jingina bayan shi a jikin forehead din sofar ya daga kan shi sama ya lumshe idanun shi Duk abun da ya ke Moussa ya na kallon shi amma bai ce da shi komai ba dan ya san abokin na shi ba karamin miskili ba ne ba bazan ba a ka kassa gano shi ba kurma ba ne Ajiye wayar shi Moussa ya yi saman table kafin ya matso bakin sofar ya kai hannu shi ya dafe cinyar Zayd Medo kan shi ya yi a hankali sannan ya bude idanun shi ya daga mishi gera allamar minene ? " Amir wai me ya ke damun ka ne , duk ka bi ka sauya kamar ba Nawfel din da na sani ba , kamar ba magajin Malik , ko dai ka fada soyayya ne " ya kai karshen ya na kashe mishi ido guda Dan tsaki Zayd ya ja kafin ya kauda kan shi gefe kafin ya ce " Diya dan Allah ka bar kira na da wannan su nan, wannan sunnan ya goge da ga cikin rayuwa ta tun lokacin da mu ka shigo garin nan " " in haka ne ka daina kira na da Diya ni ma , yanzu Amir baza ka koma ka karbi mulkin ka ba " Da sauri ya katse shi da cewa " ai Malik bai mutu ba , har yanzu ya na kan mulki kuma ko ya mutu ba ni son mulkin, a kan shi a ka nemi halaka ni dan haka su je na bar musu kayan su , na ga ai kaima yarima mai jiran gado ne me ya sa baza ka koma masarautar ku ba ka karbi mulkin ta ba " Yar dariya Moussa ya yi ya na dauke hannun shi da ga saman cinyar Zayd sannan ya ce " haba kai ma Amir ta ya zan karbi mulki bayan ni ne na uku babban yayan mu na raye zan ce na karbi mulki ? shi ya sa na baro musu kayan su , ni fa mulki sam ba ya cikin tsarin rayuwa ta ba yadda za ka yi an haifo ka cikin jinin sarauta dole ka hakura " Mikewa tsaye Zayd ya yi ya bar falon Har zai shiga corridor ya tsaya ba tare da ya juyo ba ya ce " ka na da labarin Amira da Malikat ? " Dan murmushi Moussa ya yi kafin ya ce " kar ka damu su na cikin koshin lafya " Jinjina kan shi kawai ya yi sannan ya fara takawa ya shiga corridor din ya shiga bedroom din shi Ya na shiga shi ma Moussa ya mike ya koma bedroom dinshi shi ma * Washe gari * AMINU KANO COLLEGE OF EDUCATION *Nesrine Zaune ta ke kassan wata bishiya cikin harabar college din ta na rike da wani book ta na karatu Kamar da ga sama ta ji an zabce mata book din ta A dubu dari ta dago kai , wata irin mumunar faduwa gaban ta ya yi lokacin da ta yi arba da wanda ya zabce mata book din ta Wasu samari ne guda biyu su na tsaye gaban ta Wanda ke rike da littafin ta ya fi dayan tsayi kadan ya kuma fi shi haske a shekaru zai kai 25 haka ya na da dogon hanci da kananan idanu ya dan tara gashin kai Ya na sanye da crazy jeans blue da t-shirt blue ita ma Daya kuma ya na da dan duhu kadan amma kamanin su daya sai dai wannan bai tara gashin kai ba, idanun shi kuma brown colour ne , kuma ya na da saje , lips din shi kuma sun dan yi pink kadan a shekaru ba Zai wuce 23 years ba Shi kuma ya na sanye da jeans baki da t-shirt white color Wanda ke rike da book din ta ya fara magana ya ce " baby wai ba na ce da ke ba ki ringa samu na a wajen parking space lokacin break ba " Wasu yawu Nesrine ta hadiye murya na kerma ta ce " yi hakuri Hafiz bazan sake ba " Geffen ta ya zo ya zauna ya na mika mata book din ta ya ce " ba komai baby nan din ma ya na da dadin zama sai dai da mutane dayawa shi ya sa na ce ki ringa tarda ni parking space " Ta na shirin magana ta ji Muryar Inaya ta na yi musu sallama A tsorace ta dago kai ta kale ta Inaya kuma ta yi zaton classmate din nesrine ne sai ba ta ka komai a ran ta ba ta kali yar uwarta ta ce " Nesrine dan Allah in kin tashi tafya gida ki jira ni " Ta na gama fadar haka ta juya da gudu ta bar wajen kamar ta ga wani abun tsoro Tun da ta iso wajen saurayin da ke tsaye ya tsare ta da idanu sai kallon ta ya ke ya na hadiye yawu Sai da ta bar wajen ya na kallon ta har ta kure wa kallon shi sannan ya dawo da kallon shi kan hafiz ya ce " bro wacece wacen yarinyar ta hadu fa, she look so innocent " Dum Nesrine ta ji gaban ta ya fadi dan ta san in Moctar ya lakewa Inaya ta shi ga uku cikin college din nan dan sai ya azabtar da ita shi ma ba karamin mugu ba ne ga mugun son mata , dama dama Hafiz a kan shi Ta yi nisa cikin tunanin ta sai ji ta yi an daura hannu saman cinyar ta A razane ta dawo cikin hayacin ta, ta na kallon hannun hafiz da ke saman cinyar ta " lfy baby ina tambayar ki kin yi shiru " ya fada ya na leko face din ta " minene ? " ta fada cen kassan makoshi Dan murmushi yayi kafin ya ce " who is she , ko sister din ki ce " Da sauri ta ce " a'a kawai saman hanya na hadu da ita " " okay meye sunnan ta " ya tambayeta ya na tsare ta da ido Wasu yawu ta hadiye kafin ta ce " ban sani ba " Lips din ta har kerma su ke yi Ba ta gama rufe bakin ta ba , ta ji Tass saukar mari a face din ta Da sauri ta kai hannu ta saman kumatun ta ta na dafe wajen wasu hawaye na zubo mata Mike wa tsaye ya yi cikin bacin rai ya daga mata murya ya ce " ni za ki raina wa hankali ke har kin isa ki min karya " Ya na gama fadar haka ya kai hannu ya shake ta ya hada kan ta da bishiyar cikin tsawa ya ce " meye sunnan ta na ce miki " Cikin kuka ta ce mishi " Maryam sunnan ta Maryam " da kyair kalmar ta karshe ta fito dan ba karamar shaga ya yi mata ba Ganin ya na neman ya kashe ta ya sa Moctar kai hannun shi ya dafa kafadar shi ya ce " bro sake ta kar ta mutu " Da sauri ya janye hannun shi da ga wuyan ta , ya ja baya kadan kafin ya ce " nan gaba ki san irin amsar da za ki ba ni in na tambaye ki " ya na gama fadar haka ya juya ya bar wajen Bin bayan shi Moctar ya yi su ka bar wajen Su na barin wajen ta fadi kassa ta konta ta na sauke kuka mai cin rai Sai da ta share wajen good 30 minutes ta na kukan sannan ta mike a hankali ta na jan kafa ta nufi toilet din mata ta wanke face din ta sannan ta dawo ta dauki school bag din ta ta tafi class ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : ANISH Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ PAGE 3 ❤🔥 * After some hours Tafiya su ke saman titi a jere , Nesrine ta yi nisa cikin tunanin ta , ita kuma Inaya sai wassan nin ta ta ke kamar karamar yarinya Su na tsaka da tafiyar su wata mota fara kirar Mercedes ta tsaya a gaban su ta tare musu hanyar wuce Dum Nesrine ta ji gaban ta ya fadi dan ta san ko wanene Inaya kuma ta yi tsaye ta na kallon motar dan ita ba ta san ko su waye ba Su na tsaye a hakan su ka ga an bude kofofin gaban na motar Hafiz da Moctar su ka fito Gaban su ka zo su tsaye sannan Moctar ya ce " yan mata ku zo mu rage muku hanya mana " Dan murmushi Inaya ta yi sannan ta riko hannun Nesrine ta ce " mun gode amma mun iso gidan ai " ta kai karshen ta na rabawa ta geffen su za ta wuce Da sauri Moctar ya sha gaban su ya ce " haba yan mata taimako ne fa " " babu komai mun gode gidan mu fa cen karshen layin ne , ka ga kuma ba ni son Abban mu ya kan ki zai mana fada " Ba ta gama rufe bakin ta ba ta tsinci Muryar Hafiz ya na fadin " ke Nesi wuce cikin motar nan na kai ku gida " Wasu yawu Nesrine ta hadiye ta na tsoron ta shiga motar in malam ya gan ta zai yi mata fada, in kuma ta ki ta san halin Hafiz yanzu zai yi mata Dukan mutuwa kuma ba izinin ramawa, kawai sai ta tsaya ta na faman muzurai Ta yi nisa cikin tunanin ta sai tsintar Muryar Abdoul su ka yi ya na fadin " Nesrine me ku ke yi a nan ? " A razane ta juyo ta na kallon shi zuciya na duka uku uku Ya ko tsare da wadanan dara daren idanun shi " yaya Abdoul dama classmate din su Nesrine ne su ka ce wai su rage mana hanya shi ne na ce musu mun ma iso gida amma su ka ki yarda " Inaya ta fada babu ko tsoro " shikenan ba komai wuce ko tafi gida yanzu " Tun bai rufe bakin shi ba Nesrine ta kamo hannun Inaya ta raba ta geffen Moctar da sauri ta bar wajen Su na barin wajen Abdoul ya juyawar shi shi ma ya yi tafiyar shi su ka bar Hafiz da Moctar tsaye a wajen Bayan Abdoul ya bar wajen Moctar ya kali Hafiz da ke ta hura hanci ya ce " kai dan malam rage wannan fushin na ka, ga shi yanzu sun tafiyar su ba tare da mun ga gidan su ba " Dan tsaki Hafiz ya ja sannan ya juya ya fara takawa ya na fadin " ai mun hadu school " " kai malam kar ka manta ba college din ba mu ke , yawwan zuwan mu cen ya janyo mana matsala " Geffen driver Hafiz ya bude ya shiga Ya na ganin ya shiga motar shi ma ya bude geffen mai zaman banza ya shiga Bayan ya shiga Hafiz ya tada motar su ka bar wajen da mugun gudu Duk abun da ya faru a kan idon Zayd , dan ya na biye da su Inaya amma su ba su gan shi ba , ya na shirin ya je ya yi ma su Hafiz Dukan tsiya ya ga Abdoul ya shawo kwanar ya nufi su Inaya kawai sai ya yi tsayiwar shi sai da ya ga tafiyar su sannan ya juya ya kama hanyar komawa gidan shi Bangaran Inaya kuma , sai da su ka isa cikin gidan babu wanda ta ce da yar uwarta wani abu Sai da suka shiga cikin bedroom din su sannan Inaya ta kwace hannun ta da karfi ta dan ja baya ta na kallon Nesrine ta ce " wai me ya same ki Nesrine kin ga yadda saurayin cen ya yi miki tsawa kuma ki ka kassa ce mishi wani abu " Cire hijabin ta Nesrine ta yi ta ajiye saman sannan ta zauna geffen gadon ta dago kai ta kali Inaya ta ce " Inaya ke karama ce baza ki gane ba amma wlh ki raba hanya da samarin nan ko cikin school in ki ka gan su ki tsere ki buya dan wlh ba mutanan kirki ba ne " ta na gama fadar haka ta tashi ta fice da ga dakin Inaya dai ta na tsaye ta na kallon ta har ta ida maganar ta ta tashi ta bar dakin ba ta ce mata komai ba Nesrine kuma bayan ta fita kai tsaye toilet ta shiga Maimakon ta yi wanka sai ta jingina a jikin bangon toilet din ta aza kuka Cikin kukan nata ta ke fadin " ya Allah na roke ka raba ni da Hafiz , ya Allah ko ba ka raba ni da shi ba kar ka bari ya kusan ci yar uwata , ban San me na yi mishi a duniya ba ya ke neman ya cutar da ni , na shiga uku ni Nesrine , RAMATOU kin cuce ni kin hada ni da bala'i da na sani bazan taba yarda da abotar ki ba, Allah ya isa tsakani na da ke " Haka ta yi ta dimimuwan ta har ta gaji ta yi shiru sannan ta yi wanka ta fito ta koma bedroom din su Ta na shiga ta tarda Inaya har ta yi barci dan gajiya * Misalin karfe 5 na yamma * Inaya Zaune ta ke bakin kofar gidan su saman wasu duwatsu ta na faman wassa ita kadai kamar karamar yarinya Tun da ga nesa ya hango ta zaune ta cikin bakin glass din shi Ya na tare shi da Moussa, ya na sanye da wandon jeans baki da t-shirt dark blue , shi kuma Moussa jallabiya ce fara ya ke sanye da Lokacin da Moussa ya gan ta ya saki murmushi ya kali Zayd ya ce " Amir ga fa babyn ka cen ta na wassa " " ina ga yarinyar nan ta na da matsala a kwakwolwar ta gaskia " ya fada mishi cen kassa kassa ta yadda shi da Moussa kawai su ka ji abun da ya fada Jinjina mishi kai Moussa ya yi dan ya lura yanayin ta bai yi kama da masu cikakiyar lafya ba a shekarun ta Haka su ka ci gaba da tafiyar su har su ka karaso inda ta ke zaune su ka yi mata sallama A hankali ta dago kan ta, ta na amsa musu sallamar su kafin ta ce " ina wuni yaya Moussa " Dan murmushi Moussa ya yi kafin ya ce " lafya lau babyn malam , ko dai in ce babyn Zayd " Dan zaro idanu ta yi ta na kallon Moussa sannan ta kali Zayd da ya tsareta da ido Turo dan bakin nan nata ta yi gaba ta shagwabe fuska sannan ta ce " a'a ni babyn malam ce ni na ma tafiya ta wajen Abba " ta kai karshen ta na mikewa ta fara tafiya Da sauri Moussa ya ce " to tsaya mu raka ki mu ma cen za mu je " Da sauri Zayd ya kale shi dan ya lura Moussa na neman ya kwabo mishi ruwa Jinjina mishi kai kawai ta yi ta ci gaba da tafiyar ta Su kuma juya su ka bi bayan ta, ba yadda Zayd ya iya dole ya hakura ya bi bayan shi su ka tafi Tun da su ka kamo hanya ya ke kallon ta ta cikin glass Ita kuma sai wasu juye'juye ta ke ta na halba kafa ta na wassa yadda kassan me shekara biyar haka ta ke Shi kuma Zayd wannan abun da ta ke ya na yawwan tuno mishi da kanwar shi dan ita ma haka ta ke da rawan kai Kawai sai ya tsinci kan shi ya na jin wani bakon yanayi , cikin zuciyar shi ya ce " she is so cute and innocente why malam zai aura min ita da karancin shekarun ta haka , ya kamata na tambaye shi dalilin shi na yin hakan " Sai magana ya ke cikin zuciyar shi har su ka karaso sangayar Malam bai sani ba, sai da Moussa ya kai hannu ya taba shi ya na fadin " Amir ba ka ji ne malam na gaida ka ? " A dan razane ya juyo ya kali Moussa sannan ya meda kallon shi kan Malam da ke zaune saman tabbarma sanye da manyan kaya ga Inaya geffen shi ta rungume shi ta na murmushi Dan murmushi malam ya yi kafin ya ce " malam Zayd tunanin mi ka ke haka " Girgiza mishi kai kawai Zayd ya yi allamun ba komai sannan ya dawo da kallon shi kan Moussa ya mishi allamun su tafi Jinjina mishi kai ya yi sannan ya kali malam ya ce " malam za mu wuce sai mun dawo " Dan murmushi malam ya yi ya ce " shikenan Allah kiyaye hanya , Auta baza ki raka su ba " ya fada ya na medo da kallon shi kan Inaya da ke konce a jikin shi kamar baby Cikin shagwaba ta ce " Abba yanzu fa su ka rako ni , sannan kuma na sake rakiyar su , ni gaskia babu inda zan je " Malam na shirin magana ya ga Zayd ya kama hannun Moussa ya ja shi su ka bar wurin Ta na kallon su ta kassan ido har su ka bar wajen sannan ta mike da ga jikin malam ta ce " Abba , yaya Zayd sunnan shi ne hakan na gaskia ko " Jinjina mata kai malam ya yi ya na son ya ji abun da za ta cewa " to amma Abba me ya sa yaya Moussa ke kiran shi da Amir , Amir ai ya nufin yarima " ta fada ta na kallon malam Shi kuma malam juya kan shi ya yi ya kali su Zayd da su ka yi nisa cikin tafiyar su Ba tare da ya juyo ba ya ce " ni ma ban sani ba, halan sunnan da ya ke kiran shi ne da shi lokacin su na kanana kin San ba dole sai dan sarki ba a ke kira da Amir " Cikin ranshi kuma ya na tambayar kanshi shin wanene assalin Zayd din da su ka sani ( TOOOO ! MU MA DAI MU NA SON MIJI WAYE AINAHIN ZAYD DIN NAN 🙄 ) Haka ta zauna wajen malam ta na ta zuba mishi shagwaba shi kuma ya na biye mata sai da su ka ga magriba ta gaba to sannan su ka tashi su ka koma gida a tare , ta na rike da hannun shi ta na wassa da shi ( Ita dai wannan yarinyar da wuya ta zauna ba ta motsi 😑😑 ) Bayan sun koma gida , da kanta ta debo ma malam ruwa cikin buta ya yi Alwalla sannan ya tafi mosque Bayan ya fita ita ma debo ruwa ta yi Alwalla ta koma bedroom din su dan ta yi sallat Ta na shiga dakin ta tarda Nesrine ta na zaune saman dadduma ta daga hannayan ta sama ta na adu'a Dauko daddumar ta Inaya ta yi ta zo ta shinfida geffen Nesrine sannan ta tada sallar ta Ba su tashi da ga kan daddumar sai da su ka hada da sallar isha su ka yi a tare Bayan sun ida Nesrine ta mike ta nade daddumar ta ta mayar da ita wajen ta sannan ta fito da ga dakin Ta na fitowa ta ji sallamar Abdoul Dum ta ji gaban ta ya buga dan ta san da wuya ya kyale ta bai mata fada ba Kamar ko ta sani da sauri ta juya za ta koma dakin su ya kira sunan ta Wasu yawu ta hadiye a hankali ta juyo ta ce " na'am " Takowa ya yi ya zo gaban ta ya tsaya sannan ya ce " su waye samarin nan da na gan ku a tare " Sunkuyar da kai ta yi , Cikin in'ina ta ce " ni ma ban san su ba kawai sun tseda mu ne saman hanya wai mu je su rage mana hanya " Jinjina kan shi ya yi sannan ya ce " shikenan nan gaba kar ku sake tsaya wa ko sun muku magana ku kyale su " " to yaya Abdoul " ta fada ba tare da ta dago kai ba dan tsoron ta ke ji ya wanke ta da mari Shi kuma tsaya wa ya yi ya kare mata kallo da kyau ya ga yadda ta ke ta rawar jiki kamar ya ce zai dake ta Sai da ya dan jima a haka sannan ya juya ba tare da ya ce komai ba ya shiga bedroom din shi Ita kuma ta na jin ya fara takawa ta dago kai ta ga ya nufi dakin shi ta sauke ajiyar zuciya har da dafe saitin zuciyar ta ta na jan nunfashi a hankali Sai da ta nitsu da kyau sannan ta kama hanyar kitchen ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : ANISH Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i BOOK 1 ……………………………📚✍✍ ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ PAGE 4 ❤🔥 Da sallama a bakin ta ta shigo kitchen din, nan ta isko mama gaban murhu, har ta gaba girki Dan juyo wa mama ta yi ta kali Nesrine sannan ta ce " lafya idanun ki duk sun kumbura haka ? " Ta na shirin magana ta tsinci muryar Inaya ta na fadin " kuka ta yi shi ya sa su ka kunbura " A tare duk su ka jiyo su ka kale ta Ta na tsaye bakin kofar kitchen din ta na sanye da doguwar riga mara nauyi ta saka dan karamin hijab zuwa kirji Hararrar ta Nesrine ta yi kafin ta ce " tooo malama miye ruwan ki a ciki ? " Hannayan ta duka biyu Inaya ta sa ta rike kugun ta, ta ce " da ruwana , sai dai ki yi abun da za ki yi " ta kai karshen ta na murguna mata baki Da sauri Nesrine ta dauki wani plate ta juya za ta bugawa Inaya Da gudu Inaya ta juya ta bar kitchen din ta na kara Ita ma Nesrine bayan ta ta bi da gudu ta na fadin " yau sai na yi maganin ki mara kunya kawai " Inaya kuma ido a rufe ta yi da gudu za ta bar gidan Har ta kai bakin kofa ba ta sani ba, kawai sai ji ta yi ta bugi wani abu da karfi ta yi baya za ta fadi ta na sakin kara mai karfi, wanda ya sanya shi toshe kunnuwan shi da duka hannayan shi biyu Cak Nesrine ta tsaya ta na kallon su ta na zaro idanu Malam ne da Zayd su ka shigo gidan sai da su ka yi sallama amma Inaya ba ta ji su ba , har sai da ta bugi kirjin Zayd da karfi Shi kuma ya kassa taro ta dan ya na tsoron ya taro ta wani ya lura da hakan ya yi mishi wata magana da za ta bata mishi rai shi ya sa ya kyale ta ta fadi Inaya kuma ta na faduwa kan ta ya bugu dum ga kassa har sai kassar ta dan girgiza Da gudu Nesrine ta saki plate din hannun ta ta nufo ta da gudu ta na fadin " Inaya, Inaya , Inaya " kamar ta yi kuka Shi ma malam da ke tsaye geffen Zayd da gudu ya yi kan ta ya talabo ta ya na kiran sunan ta Ina ita ko jin su ba ta yi sai kuka ta ke kamar karamar yarinya Ganin yadda su ka bi su ka rude ya sa shi kauda kan shi gefe ya saki dan siririn tsaki A hankali ya fara takowa inda ta ke konce ta na kuka Dukowa ya yi gaban ta, ya sanya hannayan shi duka biyu ya dauke ta cak kamar baby ya mike tsaye sannan ya nufi tabbarma da ya gani a shinfide kussan dakin Abdoul Da sauri malam ya bi bayan shi , ita kuma Nesrine ta tsaya ta na kare mishi kallo cikin ran ta, ta na tunanin ya akayi ya san tabbarma ta na cen wajen , mutumin da ba shi gani Malam kuwa bai kawo komai a ran shi ba dan ya san akwaye makafi dayawa da su ke aiki kamar ma su idanu ba mamaki ya hadace inda su ke zama kullum shi ya sa ya nufi wajen kai tsaye ( HAKAN NA NUFIN MALAM YA SAN ZAYD BA KURMA BA NE AMMA BAI SAN SHI BA MAKAHO BA NE 🤔 ) Sai da ya karaso wajen tabbarma sannan ya kontar da ita a wajen ya koma gefe ya zauna , ita kuma har yanzu kuka ta ke kamar baby ba ta ma san an dauke ta ba Ya na kontar da ita malam ya karaso wajen ya zauna geffen ta ya talabo kan ta ya zaunar da ita ya rungume ta ya na fadin " ya isa haka auta daina na kukan nan haka kar ki janyo wa kan ki ciwo " A hankali ta fara rage sautin kukan ta ta na hadiyar zuciya Ta na a haka ta ji an tabo mata kafar ta Ta na konce a jikin malam din ta dago kan ta ta kale shi Ya na ganin ta dago kan ta ya kai hannayan shi biyu ya rike kunnuwan shi ya dan sunkuyar da kai allamun ya na bata hakuri Wata yar karamar dariya ta yi cikin kukan nata sai da dan dimple din ta na geffen dama ya banyana karan farko kenan da na gan shi kuma gashi ba karamin kyau ya na kara mata ba A hankali ya dago kan shi ya na kallon ta ta cikin glass din shi, abun har dariya ya so ya bashi yadda ta ke dariya ta na kuka lokaci guda " Shikenan auta ya wuce ko ? " malam ya fada ya na kai hannun shi ya goge mata hawayen ta Jinjina mishi kai ta kafin ta kai hannun ta bayan kanta ta ce " Abba wajen zafi ya ke min " ta kai karshen cikin shagwaba Dan murmushi malam ya yi kafin ya ce " babu komai auta na zai wuce tashi ki je daki, ki konta " Da to ta amsa mishi sannan ta fara kokarin mike wa da ga jikin shi Da sauri Nesrine da ke tsaye waje guda tun dazu ta na kallon su , ta karaso wajen ta kamo hannun Inaya ta taimaka mata ta mike tsaye su ka nufi cikin daki su Su na shiga cikin dakin Inaya ta Haye saman gadon ta yi rub da ciki ta na sauke nunfashi a hankali ta lumshe idanun ta Ita kuma Nesrine ta juya ta baro dakin ta tafi kitchen dan ta taimaka wa mama Ta na shiga malam ya kali Zayd ya ce " Zayd me ya sa ba ka taro ta ba, yanzu da ta ji ciwo fa, dama ta na da tabo a kan ta na dauka shi ne ya motsa yadda na ga ta na kukan nan " Kallon shi Zayd ya yi cikin sanyi murya ya ce " sorry uncle ban gan ta ba ne kai ma kai sani , amma wane tabo ne wannan ? " ya tambaya ya na son ya ji karin bayani Ya na shirin magana Abdoul ya fito da ga dakin shi ya na sanye da jallabiya brown mai dogayen hannu ya karaso geffen su ya zauna ya na yi musu sallama A tare su ka amsa sallamar ta shi amma ta kadai a ka ji , dan Zayd in ba kallon bakin shi ka yi ba baza ka gane ya amsa ba Sai da ya zauna sannan ya ce "malam, na ji wani ya yi kara, cikin gidan nan ne ? " Dan murmushi malam ya yi kafin ya ce " ba komai, auta ce ta dan fadi amma ba ta ji ciwo ba " Jinjina kan shi kawai Abdoul ya yi ba tare da ya ce komai Su na a haka Nesrine ta fito da ga kitchen ta na rike da plate ta shiga dakin su Ta na shiga mama ta fito da ga kitchen din ta na rike da tray madaidaici ta karaso wajen su malam ta yi musu sallama ta ajiye tray din gaban su , sannan ta koma kitchen ta dauko musu jug na ruwa da glass biyu ta ka ta ajiye musu sannan ta wuce dakin ta Ta na shiga dakin Abdoul ya bude musu tray din ya mika ma kowane spoon guda sannan ya ce musu bismillah Kamar yadda su ka saba haka wannan karan ma haka su ka ci Sai da su ka Kamala ba wanda ya ce ma wani ufan , sannan Abdul ya zuba mishi ruwa ya riko hannun shi ya daura cup din a sama godiya zayd ya yi mishi sannan ya kai cup din a baki Ya na tsaka da shan ruwan Inaya ta fito da ga dakin su ta na dafe kai da hannu guda ta na dan lumshe idanu kamar mai jin barci A tare duka su ka dago kai su na kallon ta ba wanda ya ce da ita komai Ta na tsaka da tafiyar ta ta ji wani mugun jiri ya debe ta ta yi fuuuuu baya ta tafi za ta fadi Da sauri Abdoul ya yi kokarin tashi dan ya taro ta amma sai dai mi ? Tun kafin ya mike ya ga Zayd ya mike a dubu dari ya nufe ta , taku biyu kawai ya yi ya riko hannun ta ya janyo ta da karfi , ta fado saman fafadar kirjin shi Baki sake Abdoul da malam ke kallon shi sannan su juyo su kali juna su na son su yi magana amma maganar ta kassam fitowa Basu Ankara ba sai kawai ganin su ka ya dauke ta cak ya komo inda ya tashi ya kontar da ita, sannan ya kai hannu ya dauki glass din ruwa ya zuba kadan a hannun shi ya yarfa mata a fuska A hankali ta ware idanun ta ta na karanto kalmar shahada Ajiyar zuciya malam ya sauke ya na lumshe idanun shi a hankali sannan ya bude ya kali Abdoul ya ce " Abdoul meda ta dakin su " Da to ya amsa mishi sannan ya mike tsaye ya kai hannu ya dauke ta cak kamar baby ya nufi bedroom din su da ita Ya na barin wajen malam ya kali Zayd ya ce " Zayd na san kai ba kurma ba ne amma yau abun da na gani makaho bazai iya yin hakan ba " Shiru Zayd ya yi ya na sauraron shi amma ya kassa bude baki ya yi magana yau dai asirin shi na shirin tonuwa Dafa kafadar shi malam ya yi kafin ya ce " Zayd ni fa na yarda da kai, dalilin da ya sa na aura maka Inaya nassan ka na da kyakyawar zuciya amma ban San assalin ka ba kuma bazan ce ka fada min har sai randa ka yi ninya amma zan so in sani meyassa ka ke karyar wadanan nakassa al'halin ka na cikin koshin lafya ? " Malam na gama fadar haka Abdoul ya fito da ga cikin dakin su Inaya ya dawo inda ya tashi ya zauna Ya na zama Zayd ya ce " Ni ban taba ce muku ni kurma ne ko kuma makaho ku ne ku ka yi hassashen ku a haka a sani na dai ba wanda ya taba yi min wannan tambayar " Dan zaro idanu malam ya yi dan fa maganar Zayd ba karya ba ce dan tun lokacin da su ka shigo garin kano su ka hadu da Zayd kullum shiru da shi ko an mishi magana sai dai ya girgiza kai ko ya jingina da haka har su ka yi tunanin ko shi kurma ne , gashi kullum ya na sanye da bakin glass wani lokaci ya na rike da sanda kamar makaho dalilin da ya sa su ke tunanin shi kurma ne kuma makaho Kallon shi da kyau Abdoul ya yi kafin ya ce " Zayd ka na nufin yanzu ka na iya gani na " Sai da ya dauki lokaci kafin ya ce " of cours ina iya ganin ka, ka na sanye da jallabiya brown mai dogayen hannu , ni fa ba ni son yawwan magana dan Allah ku daina saka ni dole sai na bude baki na yi magana zan iya fadar abun da zai bata muku rai baki daya " ya fada kai a sunkuye Jinjina kan shi Abdoul ya yi kafin ya ce " don Allah Zayd zan so na ga idanun ka ko da so guda ne ka ga yanzu four years kullum ina ganin ka da glass wannan karan ina so na gan su " Dago kan shi ya yi a hankali ya na kallon Abdoul ta cikin glass din shi kafin ya sa hannu a hankali ya zame glass din shi A tare zuciyar malam da Abdoul su ka buga da su ka ci karo da wadanan hazel eyes na Zayd ga shi ko ya na fuskantar lamps din wajen sai idanun shi su ka yi reflecting hasken lamps din sai su ka yi wani kyali na musaman su ka zama kamar idanun mage , tsakani da Allah har ni sai da na ji tsoro Da sauri Abdoul ya ce " don Allah meda glass din ka wlh sai da na ji tsoro " A hankali ya sunkuyar da kai ya Meda glass din shi sannan ya dago kai ya kali Abdoul ya ce " yanzu dai baza ka ce ba ka taba ganin idanu na ba " " ni ko na gan so , ai wadanan ko a mafarki na gan su sai na gane su " ya kai karshen ya na yar karamar dariya Malam dai ya yi sumar zaune ya rasa wane irin mutun ne Zayd , sam bai yi kama da mutanan Nigeria ba karewar zancen bai ma yi kama da mutanan Africa ba ki daya Haka su ka ci gaba da hirar su wadda yawancin Abdoul da malam ke yin ta shi Zayd ya na zaune kamar gunki Sai wajen karfe 10 na dare sannan ya mike zai koma gida, Abdoul ya dan raka shi kadan kafin ya komawar shi gida Bayan ya koma gida bai tsaya bin ta kan Moussa ba kai tsaye ya wuce bedroom din shi ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : ANISH Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i BOOK 1 ……………………………📚✍✍ [09/08/2024] ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ PAGE 5 ❤🔥 ▪ Washe gari Yau ta kama week-end ce Inaya da Nesrine ba su tafi college ba, sai misalin karfe 9 na safe Nesrine ta farka da ga barci Inaya kuma sai wajen karfe 10 ta farka , da wani mugun ciwon kai ta farka da ga barcin ta amma sai ta shanye Ta mike ta fito dakin ta shiga toilet ta yi wanka sannan ta fito ta shirya cikin wando jeans baki da doguwar riga zuwa guyiwa pink colour ta saka dan karamin hijab zuwa kirji sai tashin kamshi ta ke Kai tsaye kitchen ta nufa dan ta taya mama girki ita da Nesrine tun da yau week-end A tare su ka yi dafuwar su cikin konciyar hankali su na hirar su har misalin karfe 12 na safe sannan su ka Kamala Bayan sun ida Inaya na shirin shiga dakin ta ta tsinci Muryar malam ya na fadin " Auta dan Allah dauki abincin Zayd ki kai mishi " ya fada ya na ida shigowa cikin gidan Dan murmushi ta yi sannan ta ce mishi to ta juya ta koma kitchen Dama mama ta fida mishi na shi cikin wani kwano ta ajiye gefe dama sun saba fida mishi abincin rana kullum wani yaro da ke sangayar malam ke zowa ya kai mishi wannan karan ne na farko da za ta kai mishi da kan ta Shi ma malam da gangan ya ce ta kai mishi , Allah kaɗai ya san manufar shi ta yin hakan Jim kadan ta fito rike da wani dan basket a hannun ta, ta fita gidan, a lokacin har malam ya shiga dakin shi A hankali ta ke tafiya saman hanya ta na kallon kassa kamar mai tunanin wani abu Sai da ta karaso kofar gidan sannan ta dago kai, ta kai hannu ta tura kofar ta shiga ta na sallama Wannan karan farko da ta shigo gidan shi , Ta sha ruwan mamaki ganin yanayin gidan, har da wata babbar mota fara ta tambayi kanta ta ina motar ta shigo , in ta shigo ai fitar ba za ta yi wuya ba kuma ita kofa daya ta gani kuma karama ce Da wannan tunanin ta ci gaba da takawa har ta isa terrace din gaban ta Ta kai hannu ta bubuga kofar, sau daya Shiru ba a bude ba sai ta sake bugawa karo na biyu Wannan karan bai fi one minute ba ta ga kofar ta bude Sai ga Moussa ya na tsaye rike da kofar ya na sanye da wando three cuter da t-shirt ya na shan iska Sallama ta yi mishi ta gaishe da shi cikin fara'a sannan ta mika mishi basket din hannun ta ta ce ga abincin su in ji malam Dan murmushi yayi kafin ya dan ja gefe kadan ya ce " bismillah shigo mana dama yunwa na ke ji idan mun ida sai ki koma da basket din ki ko ? " Jinjina mishi kai ta yi ta na murmushi kafin ta sa kafa ta shiga falon ta na sallama *Zayd Ya na zaune saman sofa da ke fuskantar kofar shigowa, ya na sanye da jallabiya fara mai kananan hannu, ya na sanye da wadanan glass din na shi baki, ya jinjina a bayan sofar ya daga kai sama ya lumshe idanu duk da su na cikin glass Ya ji sallamar ta amma ko motsi bai yi bare ya amsa mata A hankali ta karaso cikin falon ta na bin shi da kallo gaskia ya yi mata kyau Ta na cikin dube duben ta ta tsinci Muryar moussa ya na fadin " ko kin dawo nan da zama ? " Girgiza mishi kai ta yi ta na murmushi sannan ta karasa ta ajiye basket din hannun ta saman table ta ce " ina wuni yaya Zayd " Shiru bai amsa mata ba ko motsi bai yi ba Amma sarai ya ji ta Da sauri Moussa ya ce " barci ya ke " dan ya kare dan uwan shi Murmushi ta yi sannan ta koma bakin sofar da ke wajen kofar shigowa ta zauna kassa saman carpet Karasowa Moussa ya yi ya zauna saman sofar da Zayd ke zaune, ya kai hannu ya janyo table din gaban shi ya kai hannu ya ciro kwanonin da ke ciki da plate guda ya fara serving din kan shi ya fara ci ya na yi mata hira ta na amsa mishi a kai a kai Duk abun da su ke Zayd na sauraron su dan ba barci ya ke ba kawai dai ya lumshe idanun shi bare kuma su na cikin bakin glass Sai da ya Kamala cin abincin tass ya cinye komai sannan ya meda kayan cikin basket ya tashi ya je dining room ya bude fridge ya dauko gorar ruwa guda sannan ya dawo inda ya tashi ya zauna ya bude ya sha ruwan Sai da ya ida sannan ya koma ya jingina a bayan sofar ya lumshe idanun ya bude a hankali ya kali Inaya ya ce " Gaskia abincin nan ya yi dadi " Shiru ta yi ta kurewa waje guda ido babu ko kiftawa " Inaya tunanin mi ki ke " ya tambayeta ya na kallon ta Nan ma shiru ba ta motsa ba Tasowa ya yi da ga jikin sofar ya kai hannu ya dan bubuga cinyar Zayd A hankali ya ware idanun shi ya taso da jikin sofar shi ma ya kali Moussa " duba ka ga, ko tunani me ta ke ? " Moussa ya fada ya na nuna mishi Inaya A hankali ya juyo kan shi ya kale ta Ta yi zugum waje guda kamar wadda ta suma Mikewa tsaye ya yi ya koma saman sofar da ke bayan ta ya zauna ya kai hannun shi ya dafa kafadar ta A razane ta dawo cikin hayacin ta , ta na sakin kara ta kai hannayan ta ta toshe kunnuwan ta ta na fadin " Ku kyale ni , ku kyale , kar ku tabani , wayo Abba na, aaaaaaaaaaaa " A rude ya sauko kassa ya riko ta da hannayan shi biyu, shi ma Moussa da sauri ya tasso ya koma gaban ta ya tsuguna ya na fadin " Inaya lafya me ya faru " Ina sam ba ta jin shi ta toshe kunnuwan ta , ta na sakin kara kamar mai aljanu Da karfi Zayd ya sa hannayan shi duka biyu ya riko nata ya yanye su da karfi ya sauke su ya riko a bayan ta sannan ya kali Moussa ba tare da ya ce komai ba Kamar ya san abun da ya ke nufi sai ya Jinjina mishi kai sannan ya fara karanto ayatul kursi'u dan a tunanin shi aljanu ne gare ta Kamar da gaske ya na fara karanta, ta fara samun nitsuwa ta na kallon shi ta na sauke ajiyar zuciya a hankali ta lumshe idanun ta ta fada jikin Zayd Sai da ya karanta ajatul kursi sau biyar sannan ya bari ya kali Zayd ya ce " Amir ba dai aljanu ne da ita ba ? " Girgiza mishi kai Zayd ya yi ba tare da ya ce komai ba ya na rungume da ita Ya na sauraron yadda ta ke sauke ajiyar zuciya a jere idanu a lumshe Sai da ta ji ta nitsu sannan ta bude idanun ta, ta mike da ga jikin Zayd ta na kallon Moussa Dan murmushi ta saki kafin ta mike tsaye ta ce " yaya Moussa ni zan koma gida " " shikenan muje na raka ki " ya fada ya na mikewa tsaye ya dauki basket din saman table ya riko hannun ta ya ce mu tafi Ba musu ta bi bayan shi su ka bar falon Shi ma Zayd mike wa ya yi ya bi bayan su a hankali dan nesa kadan da su Sai da su ka iso bakin kofar gidan sannan ya saki hannun ta ya mika mata basket din ta ya ce ta shiga Karbar basket din ta yi sannan ta ce mishi sai an jima ta shige gidan su Har ya juya zai bar wajen Cak ya tsaya ya na kallon Zayd da ke tsaye bayan shi cike da mamaki " yaushe ya biyo mu kuma ? " ya tambayi kanshi Ya na shirin magana Zayd ya riga shi cewa " shiga ka yi min magana da uncle " Ba musu ya juya ya shiga gidan ya na sallama shi kuma ya tsaya nan ya na jiran su Jim kadan Moussa ya fito , malam na bayan shi Sallama malam ya yi mishi sannan ya bashi hannu su ka yi musbaha Sai da su ka gaisa sannan Zayd ya ce " Uncle ina son muyi wata magana " " ina sauraron ka, mi ka ke son muyi magana a kai ? " Malam ya fada ya na tsare shi da ido Ajiyar zuciya Zayd ya yi kafin ya ce " uncle zan so ka fada min dalilin da ya sa ka aura min yarinyar nan tsawon shekara biyu duk lokacin da na tambaye ka ba ka ba ni amsa , a yau ina son na sani " Nan take yanayin face din malam ta sauya ya rasa amsar da zai ba shi Ga kuma Zayd ya tsare shi da ido har ga Allah bai shiriya fada wa Zayd wannan sirrin ba Wasu yawu malam ya hadiye kafin ya ce " Zayd ba zan iya fada maka ba a yanzu , idan lokacin ya yi za ka gane komai " " shikenan next week zan zo na dauki matata zan gano abun da ake boye min da kai na " ya na gama fadar haka ya juya ya bar wajen ya na taku cike da izza (TO FA NA MULKIN SUN FARA TASHI 🤣 🥀 ) Yanayin da ya yi maganar shi Ba karamin kwarjini ya yi wa malam ba kawai ya tsaya ya na kallon shi ya rasa me zai ce Kallon shi Moussa ya yi sannan ya ce mishi " malam zan tafi " sannan ya juya shi ma ya fara takawa ya bar wajen Jinjina kan shi malam ya yi sannan ya fara takawa dama ya fito zai je mosque ya jiyo sallamar Moussa Bayan sallar isha Inaya A hankali ta ke fitowa da ga cikin dakin su Ta na sanye da gown pink colour mara nauyi da hijab pink shi ma zuwa guyiwa A hankali ta ke takowa cike da nitsuwa ta nufi kitchen Har ta kai kofar kitchen ta jiyo mama na magana sama sama da karfi A hankali ta juyo ta nufi kofar dakin mama dan a tunanin ta ita ka dai ce ko da ita ta ke magana ba ta ji da kyau ba Har kai kofar dakin ta bude baki za ta yi sallama ta ji Muryar malam ya na fadin " abun da ki ka ji Amina, auta dai na aurar da ita tun shekara biyu da su ka wuce kuma yanzu mijin ta ya ce ya na son ta koma gidan shi " Dumm ta ji gaban ya buga da karfi nan take idanun ta su ka kawo ruwa Ta na a haka ta jiyo muryar mama ta na fadin " Malam Inaya fa duk shekarun ta nawa , in da ma a ce Nesrine ce....... " Da sauri malam ya katse ta da cewa " Amina , Inaya fa ba yarinya ba ce , gwara na san ta na gidan mijin ta hankali na zai fi konciya " " yanzu me Inaya ta sani a kan aure " " Shin wai me ki ke jin tsoro a kai , ki kontar da hankalin ki ba abun da zai faru da ita " Duk maganar nan da su ke a kunnen Inaya Lips din ta har kerma su ke ta bude baki ta na fadin " a....a....aure ni kuma ? A'a a'a " ta fada ta na girgiza kai da gudu ta juya ta bar wajen Maimakon ta koma bedroom din su , sai ta bar gidan baki ɗaya Gudu ta ke da iya karfin ido a rufe Da karfi ta bangaje kofar gidan shi ta shiga ta nufi wajen motar da ke cikin gidan ta buya a baya ta Zube saman guyiwowin ta ta aza kuka da iya karfin ta kamar wata mahaukaciya Ba ta fi ten minutes da shigowar ta wajen Moussa da Zayd su ka fito da ga cikin falon Su na sanye da jeans baki da t-shirt amma ta Zayd fara ce ta Moussa kuma blue Su na tsaka da tafiyar su su ka jiyo kukan mutun Cak su ka tsaya a tare su na kallon juna su na zaro idanu A hankali su ka fara bin wajen da kallo ba su ga kowa ba Cen Moussa ya ce " ko dai aljanu ne ke wannan kukan ? " Girgiza mishi kai Zayd ya yi kafin ya fara takawa a hankali ya nufi motar shi ( WATA SABUA MAKAHO DA TUKA MOTA 🤣✌) ya na kara nufo motar sautin kukan na karuwa A hankali ya fara zagayen motar har ya iso inda ta ke Ta na zaune ta cusa kan ta tsakanin cinyoyin ta sai kuka ta ke kamar ba gobe A hankali ya tako ya zo geffen ta ya zauna shi ma sannan ya kai hannu ya dafa kafadar ta , Moussa kuma ya na tsaye gaban su A hankali ta dago kan ta cikin kukan nata fuskar ta duk ta yi jaga'jaga da hawaye har da majina Ta na ɗaura ido saman shi ta ji wani kukan ya zo mata ta kara sautin kukan ta ta na meda kan ta tsakanin cinyoyin ta Da sauri Moussa ya ce " Inaya lafiya ki ke irin wannan kukan wani abu ya faru ne ? " Ki dagi kai ba ta yi ba bare ta amsa mishi asali ma ita ko jin shi ba ta yi ba , ta na ta kukan ta , Allah kadai ya san abun da ta ke yi wa irin wannan kukan Tsugunawa gaban ta Moussa ya yi duk ya bi ya rude ya na fadin " Babyn malam don Allah ki daina kukan nan ki fada min abun da ke faruwa , kar ki janyo wa kan ki illa " Shi dai malam Zayd ya na zaune gefe ya zuba musu ido ta cikin glass din shi kamar ya na son ya karance wani abu Tabi shi Moussa ya yi ya na fadin " Amir please ka yi mata magana , may be ta saurare ka , ka ga ni ta ki yi min magana " Gyada mishi kai Zayd ya yi kafin ya kai hannun shi a hankali ya dan bubuga shoulder din ta Slowly ta dago da kan ta , ta kale shi dama jira ya ke sai ya yi mata allamun " minene ki na kuka ? " da hannu TO A NAN ZAN DASSA AYA SAI MUN HADU GOBE✌✌✌✌ KAR KU MANTA KU NA TARE DA ALKALAMIN ANISH ❤ ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : ANISH Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP 👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/IrsjzfoHUHBJzdgRtskPcY BOOK 1 ……………………………📚✍✍ [11/08/2024] ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ PAGE 6 ❤🔥 Da hannu ya mata allamun " minene ki na kuka haka ? " Cikin wata disashashiyar murya ta ce " yaya Zayd wai Abba ya yi min aure " Da sauri Moussa ya ce " to mine matsalar ba ki na son wadan a ka aura miki ba " Medo da kallon ta ta yi kan Moussa cikin kukan ta ce " yaya Moussa ni fa ina da wanda na ke so , kuma ni ban ma san wanda Abba ya aura min , ni ko ma wanene ba na son shi , dan Allah yaya Moussa ka je ka same shi ka ce ya raba auren nan wlh ba ni son shi " ta kai karshen ta na meda kan tsakanin cinyoyin ta Dan satar kallon Zayd ya yi ta kassan ido kafin ya ce " shikenan babyn malam , ya isa haka dainan kukan nan , yanzu fada min wa ne wannan wanda ki ke so " Da sauri ta dago kai ta ce " ni fa yaya ..........." kut maganar ta yanke ta zaro idanu ta na kallon Moussa Shi dai Zayd ya na zaune ya zuba mata ido ya na jiran ya ji sauran maganar in da gaske akwai wanda su ke soyayya to zai sake ta ya aura mata wanda ta ke so da kan shi Ganin ta yi shiru ta tsaya sai kallon Moussa ta ke sai ya kai dan yatsun shi saitin face din ta ya kyasta mata Sai da ta dan razane sannan ta medo da kallon ta kan shi Tambayar ta ya yi minene Girgiza mishi kawai sannan ta meda shi tsakanin cinyoyin ta amma ba kuka ta ke ba wannan karan Kallon Moussa ya yi sannan ya daga mishi gera guda Jinjina mishi kai Moussa ya yi sannan ya sunkuyo gaban ta ya ce " shikenan yanzu tashi mu koma gida ko " Ba tare da ta dago kai ba ta ce " ni wlh ba inda zan je " Ya na shirin magana Zayd ya daga mishi hannu ya na girgiza mishi kai Mikewa tsaye moussa ya yi ya dan ja baya kadan Shi ma Zayd mike wa tsaye ya yi sannan ya fara takawa ya nufi kofar fita ya bar gidan Ta na jin ya fara takawa ta dago kai a hankali ta na kallon shi ta wutsiyar ido Sai da ta ga ya fita gidan sannan ta sake sakin wani sabon kukan ( yarinyar nan da a gaba na ta ke sai na wanka mata biyar 😑😑😑 ) Juyawa Moussa ya yi zai bar wajen sai ya dawo ya ce mata " tashi ki shiga cikin gidan tun da baza ki koma cen gidan ku ba " Ya na gama fadar haka ya sa kai ya fice shi ma Cen ya hango Zayd har ya yi nisa da tafiyar shi Da sauri ya fara takawa har ya kamo shi dai'dai ya karaso kofar gidan su Inaya Su na karasowa wajen Abdoul da malam su ka fito da sauri kamar sun ga wani abun gudu Da sauri Moussa ya taro su ya na cewa " Abdoul ina za ku je haka da sauri wani abu ya faru " Abdoul na shirin magana malam ya riga shi cewa " Inaya ce ba ta cikin gidan nan ban San inda ta yi ba " Dan murmushi Moussa ya yi kafin ya ce " ku kontar da hankalin ku , yanzu nan mu ka baro ta gidan mu, kar ku damu ba abun da ya same ta " wata nanauyar Ajiyar zuciya malam da Abdoul su ka sauke a tare " uncle kun san da yarinyar nan ta na da wanda ta ke so " su ka tsinci Muryar Zayd ya na fada Kallon juna Abdoul da malam su ka yi kafin su kali Zayd har su na hada baki wajen cewa " ita da kanta ta fada maka hakan ? " Jinjina musu kai a hankali ya yi bai ce komai ba Dan murmushi malam ya yi sannan ya ce " yo ai wannan ba matsala ba ce dan..... " Da sauri Zayd ya katse shi da cewa " kamar ya ba matsala ba ce ? no uncle tun da ta na da wanda ta ke so ni zan nemo shi in aura mata shi da kai na , baza ta ji dadin zama da mutuman da ba ta so , a karancin shekarun nan na ta bai kama ta ta shiga cikin irin wannan kunci ba , dama ni ta yi min karama sosai " bai jira amsar malam ba ya juya ya bar wajen Sai da ya bar wajen sannan malam ya kali Moussa ya ce " wai maganar me ya ke yi ne haka ? " Dan karamin murmushi Moussa ya yi kafin ya ce " wai zai saki babyn malam tun da ta ce ta na da wanda ta ke so ya aura mata shi , ku kyale shi yayi ta neman kan shi har ya gaji , zan koma gida sai da safe " ya juya ya bar wajen Da sauri Abdoul ya yi shirin bin bayan shi, amma malam ya riko hannun shi ya ce " nassan auta ce za ka je daukowa kyale ta, da safe ta dawo da kan ta " Jinjina mishi kai Abdoul ya yi sannan ya juya ya koma cikin gidan malam ya bi bayan shi Da sallama su ka shigo cikin gidan a tare Da sauri Nesrine da ke konce ta tada kai da cinyar mama ta na kuka, ta tasso ta tarbo malam cikin kukan ta ke cewa " Abba ina Inaya ta yi ne " Dan murmushi yayi kafin ya ce " kontar da hankalin ki, ta na gidan mijin ta " Dan zaro idanu ta yi ta na maimaita kalmar miji cikin ranta Ta geffen ta malam ya raba ya wuce ya karaso inda mama ke zaune shi ma ya zauna Shi kuma Abdoul ya wuce bedroom din shi Ya na zama Nesrine ta juyo da sauri ta nufo malam ta zo gaban shi ta tsaya ta ce " Abba wane mijin kuma, Abba Inaya fa shekarun ta 14 ina ta kai aure ko period fa ba ta fara ba " duk cikin kukan ta ke mishi wannan maganar ta ma manta da mahaifin ta ta ke magana Malam na shirin magana mama ta riga shi cewa " yanzu dan Allah malam ina Inaya ta isa aure me ma ta sani a kai , ka hada ta da wanda ba mu san shi ba , wanda ba son shi ta ke ba yanzu in ya je ya cutar mana da ita da wane za muji malam bibiyar da ake mana ko wannan " ta kai karshen ta na sakin kuka Da sauri Nesrine ta karaso wajen ta ta Zube saman guyiwowin ta ta rungume mama ita ma ta na sakin kuka ( shi kukan kawai dan an yi mata aure ne 🤔🤔????? ) " yanzu Amina ya ki ke son na yi kin fi son na saka ido wancen yaron ya gano inda muke ya zo ya dauke mana ita, kuma na fada miki auren ya yi wajen shekara biyu yanzu , kuma ta na son mijin na ta , dan ni da kai na na tambaye ta in ta na son shi , ku yanzu a tunanin ku in Sudais ya gano inda muke ba sai ta fi shiga cikin matsa la ba dan Allah ku kontar da hankalin ba abun da zai faru da ita " ya kai karshen ya na kai hannun shi saman kafadar mama A hankali mama ta dago da ga jikin Nesrine ta kali malam ta ce " shikenan na ji abun ka fada amma ba ka fada min wanene wanda ka aura mata " Jinjina kan shi ya yi kadan sannan ya ce " ba kowa ba ne face Zayd " A dubu dari Nesrine ta mike tsaye ta na fadin " Zayd ???? " da karfi ta na zaro idanu, yanzu mutumin da ko hanya ba ta fatan ta hada su wai shi ne mijin kanwar ta, mutumin da ko gani ba ya yi kamm akwai ta " e Zayd , wanda ke zowa gidan nan wanda ku ke ma kallon makaho da kurma shi din dai " malam ya fada ya na kallon ta Cikin bacin rai mama ta ce " haba malam, wannan makaho ta ya zai iya kare mana yarinyar mu , ko shi ta kan shi ya ke , ya zai kula da ita, inda ma abokin shi Moussa ne da sauki amma Zayd ? " Mikewa tsaye malam ya yi cikin bacin rai ya ce " bara ku ji aure dai an riga da an aura kuma ba zai sake ta ba in kun ga dama ku karbe shi in kun ki ku ta matsewa " Ya na gama fadar haka ya kama hanyar dakin shi ya shige ya bar su nan zaune Juya wa ita ma Nesrine ta yi ta koma dakin ta da gudu ta na sakin sabon kuka Ita ma mama ta juya ta koma dakin ta zuciya ba dadi Duk abun da su ke Abdoul na jin su amma ya yi banza da su ya yi konciyar shi Zayd Bayan ya koma gida kai tsaye bedroom din shi ya wuce, ga Dukan allamu ya manta da Inaya da ke cikin gidan Shi ma Moussa ya na shigo wa ya wuce kai tsaye cikin falo A tunanin shi ta na nan amma da ya shigo ya ga ba kowa a cikin falon Da sauri ya juya ya fita falon ya koma wajen da su ka baro ta Ta na nan kamar yadda ya baro ta , amma ta daina kuka sai ajiyar zuciya ta ke saukewa a hankali allamun ta yi barci Dan murmushi yayi kafin ya juya ya koma cikin gidan a hankali Kai tsaye bedroom din Zayd ya wuce Sai da ya yi mishi knocking sannan ya shiga dakin ya na sallama Ya na zaune saman gadon shi ya jingina a bayan gadon ga computer a gaban shi , ya cire wadanan glass din na shi na gado Karasowa wajen shi Moussa ya yi ya tsaya gaban shi ya ce " Amir don Allah je ka dauko babyn malam ta yi barci a wajen motar " Ba tare da ya dago kai ba ya ce " kai me ya hana ka dauko ta ? " Hararrar shi Moussa ya yi kafin ya ce " Amir ban San rainin sens ka fi kowa sani ba muharama ta ba ce bazan iya dauko ta ba , dan haka malam tashi ka je ka dauko matar ka " Dago kai Zayd ya yi ya wurga ma Moussa wani mugun kallo Shi Moussa dariya ma abun ya bashi dama da gangan ya ki dauko ta , ya zo ya tada shi ya je ya dauko ta Wani file da ke geffen shi Zayd ya doko ya tila wa Moussa Da sauri Moussa ya kwace gefe ya na dariya ya ce " to malam da ga taimako na ga dai matar ka ce ba tawa ba in ka ga dama ka bar ta a cen ta mutu " Ya na gama fadar haka ya juya ya fice dakin ya shiga bedroom din shi ya na dariya Dan kauda kai gefe Zayd ya yi ya na jan tsaki a fili ya ce " wlh sai na yi maganin ka, jarabbabe kawai " Ya na gama fadar haka ya ajiye computer din geffen shi sannan ya sauko da ga saman gadon ya fito dakin Kai tsaye parking space ya nufa inda su ka baro ta Ya na zuwa bai tsaya wani dogon tunani ba ya sa hannayan shi biyu ya dauke ta cak kamar baby ya koma cikin gidan da ita Maimakon ya wuce bedroom din shi da ita sai ya kontar da ita saman doguwar sofa sannan ya juya ya koma bedroom din shi ya ci gaba da aikin shi ▪Washe gari ▪Inaya Washe gari ba ta farka da ga barcin wahalar ta ba sai wajen karfe 10 na safe, ko da ta farka ta ga ba motsin kowa a cikin gidan allamun sun fita Jin hakan ya sa ta mikewa ta fara takawa ta bar falon ta fito harabar gidan Abun mamaki babu motar nan a cikin gidan, to ta ina ta fita ? (Ko ni wannan tambayar ta tsaya min a rai , ta ina motar nan ke shigowa bare har ta fita ) Ganin ba ta da me ba ta amsa kawai sai ta sa kai ta bar gidan baki daya ta koma gidan su A hankali ta ke tafiya kamar wadda a ka zarewa lakar jiki har ta karaso gidan su Bakin ta dauke da sallama ta shigo gidan A hankali mama ta dago kan ta, ta amsa mata sallamar ta Ganin ita ce ya sa mama sakin wani dan murmushi ta ce " Auta zo nan ina son magana da ke " Ba musu ta tako a hankali ta zo geffen mama ta zauna ta na sunkuyar da kai ta na gaishe ta Sai da mama ta amsa mata gaisuwar ta sannan ta ce " Auta a ina ki ka kwana ? " Ba tare da ta dago kai ba ta ce " gidan su yaya Moussa " ta fada a takaice Jinjina kan ta mama ta yi kafin ta ce " Auta fada min gaskia ki na son Zayd a yadda ya ke hakan ? " Sai da ta dan doki lokacin kafin ta dago kan ta slowly ta ce " shin mama ko ina son shi ai yanzu lokaci ya kure, Abba ya aura min wani cen daban wanda ban sani ba , ba na kuma so , ni gaskiya ba a yi min adalci ba " ta kai karshen kuka na kubce mata Ta tashi da gudu ta shige dakin su Mama sai kiran ta take amma ina sam ba ta jin ta Dama tambayar da ta yi mata dan ta tabbatar da abun da malam ya ce ne na Inaya na son mijin ta, gashi ta tabbatar amma ta lura ita Inaya ba ta san waye mijin na ta ba , ta so ta fada mata ta ki tsaya wa Jinjina kanta kawai mama ta yi ta ci gaba da yanke kayan lambun da ke gaban ta NI MA NA DAUKI TAKARDU NA , NA BI BAYAN INAYA 😴😴😴😴😴😴😴 SAI MUN HADU GOBE KAR KU MANTA KU NA TARE DA ALKALAMIN MEERAH ✌️✌️❤️ SANNAN A TAIMAKA MIN DA SHARING FISABILLILAHI 🙏🙏🙏💖💖💖 ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH A.K.A ANISH Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP 👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/IrsjzfoHUHBJzdgRtskPcY TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP CHANEL 👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i BOOK 1 ……………………………📚✍✍ [12/08/2024] ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ PAGE 7 ❤🔥 Bayan ta shiga bedroom din su , kai tsaye saman gadon ta Haye ta yi rub da ciki ta na sakin sabon kukan Ta na shiga bedroom din su Nesrine ta shigo gidan ta na sallama hannun ta rike wasu ledodi allamun mama ta aike ta cepane , amma duk yanayin face din ta babu alamun fara'a a cikin Inda mama ke zaune ta karaso ta zauna ta na ajiye ledodin gaban ta sannan ta ce " mama wai har yanzu Inaya ba ta dawo ba ? " Murmushi mama ta yi kafin ta ce " hmmmm ta dawo ta na cikin dakin ku " Da sauri Nesrine ta mike ta nufi dakin su da gudu Kallon ta mama ta yi ta saki wani dan karamin murmushi ta ce " ke ma Allah ya ka miki mijin auren in rabu da wannan shirman naki " Nesrine kuma ta shiga dakin su ba bu ko sallama ta hango Inaya konce saman gado ta yi rub da ciki sai kuka ta ke A hankali ta tako ta karaso bakin gadon ta zauna ta kai hannu ta, ta dan bubugi kafar Inaya Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta juya a hankali ta mike zaune ta kai hannu ta dauki pillow din ta , ta rungume shi a kirjin ta ta na kallon Nesrine Dan murmushi Nesrine ta yi kafin ta kai hannu kan face din ta , ta goge mata hawayen ta sannan ta ce " haba sister di na, na miye kuka kuma ? " Hadiyar zuciya Inaya ta yi kafin ta ce " Nesi wai fa ki na ji Abba aure ya yi min , ni fa wlh ina da wanda na ke so ba ni son wadan aka aura min " ta kai karshen ta na boye face din ta cikin pillow " sannu malama yanzu har kin San minene so ? " Nesrine ta fada cikin sigar zolaya Dago kan ta ta yi ta wurga mata hararra Yar dariya Nesrine ta yi kafin ta ce " shikenan yi hakuri ai ni dama sai da na fada miki , ba wadda za ta iya son wacen makaho ga shi kuma kurma am........." Ba ta ida maganar ta ba Inaya ta katse ta da cewa " wai dan Allah me ya yi miki a duniya da ki ka tsane shi haka, na ga bai taba shiga harkar ki ba , ko gaisuwa ba ta taba shiga tsakanin ku ba amma kin dauki tsanar duniyar nan kin daura mishi, in ke baki son shi toh wlh akwaye ma su son shi dayawa a duniya ciki har da ni " Ta na gama fadar haka ta tila pillow din hannun ta gefe sannan ta diro da ga saman gadon ta fice dakin Ta na fita Nesrine ta rike habar ta ta ce " yanzu fa ta ce ba ta son shi amma wai shi har da kare shi yanzu ko a tunanin ta ita kadai ke iya cewa ta na son shi ko ba ta son shi " Dan tsaki ta ja sannan ta mike ta fito dakin Ta dawo inda mama ke zaune ta zauna ta na tsuke fuska ta ce " wai wannan yarinyar minene matsalar ta , yanzu fa ta ce ba ta son yaya Zayd, yanzu kuma za ta sake cewa ta na son shi " Yar dariya mama ta yi kafin ta ce " kyale ta haba ina ga ba ta san da shi ne Abba ya aura mata " Kauda kai gefe Nesrine ta yi ta na tsaki ta ce " yanzu dan Allah mama haka za mu zuba ido mu na kallo Abba ya bawa wacen makahon auren Inaya, yanzu da wane ido zai kula da ita , da wane bakin zai yi mata magana ni fa gaskia ban yarda da hakan ba " " toh Nesrine ya za ki yi na ga ba ki da izinin raba auren nan , ko kin ki, ko kin so Inaya matar Zayd ce , ni gwara ZAYD din ma da wancen dan iskan Sudais , ko ba komi ya na da tarbiya da kyawawen halaye kuma nakassar shi bai sa ya zama rago ba, ki na gani tun safe ya ke fita ya tafi aiki duk da baya gani da kan shi ya ke neman abincin shi, to me ya fi wannan ka ci halal din ka , ko wa ya na maka shedar mutumin gwarai, bara ki ji , ni wlh ko da ya fi makaho da kurma, zan aura mishi Inaya dan na san zai kula da ita duk da ba mu San assalin shi ba shekara hudun nan da mu ka yi da shi ya isa ka gane shi wane irin mutun ne " " hmmmm yanzu kennan mama kin yarda da auren nan, autar ta mu guda za a dauka a bawa kurma, makaho wanda bai ma san da me ta ke kama ba " Yar dariya mama ta yi kafin ta ce " to ina ruwan Allah da wannan ai zuciyar mutun ya kamata ki duba , sai ki ga mutun kamar shi ya yi kan shi dan kyau amma zuciyar a bushe ta ke kamar kafiran farko, amma sai ki ga wanda bashi da kyau ya na da zuciya mai kyau tsarkakiya, ke yanzu a ganin ki Zayd bai fi Inaya kyau ba kuma a hakan ya yarda ya aure ta , duk da bai gan ta ba kin ga wannan auren na su ya ishe ki ishara Allah ba ya barci , kaddara ce kawai ta hada su , amma ba dan haka ba ni na san inda zayd na da cikakiyar lafya wlh ko inda ya taka ba ki kai ki taka ba " Nesrine na shirin magana Inaya ta fito da toilet, ta wuce bedroom din su ko kallon inda su mama su ke ba ta yi ba Dan zaro mama ta yi ta na girgiza kai sannan ta ce ma Nesrine " kin ga tashi ni ki yi min aiki na " Da to Nesrine ta amsa mata sannan ta tashi ta shiga kitchen A takaice ranar yau Inaya a cikin bedroom din su ta yi ta, ko harabar gidan ba ta leko ba, abinci ma sai Nesrine ta kai mata daki su ci , abu guda ke fido ta sallat , Zayd kuma yau tun safe da su ka bar gidan shi da Moussa har bayan sallar isha ba su dawo ba Washe gari Yau ta kama ranar monday, tun karfe 6 Nesrine da Inaya su ka tashi su ka yi duk wani aiki na gidan sannan su ka shirya sai karfe 7:30 su ka bar gidan su ka kama hanyar college Tun bisa hanya Nesrine ke yi ma Inaya magana amma ta kyale ta ko kallon ta ba ta yi ba Sai da abun ya bawa Nesrine haushi ta daina mata magana ma Har sai da su ka iso AMINU KANO COLLEGE OF EDUCATION sannan ko wace ta wuce class din ta 11pm Zaune ta ke cikin cafeteria din school din , ta na rike da book , ga bottle drinks nan a gaban ta saman table ta na karatun ta cikin konciyar hankali Ta na a haka wasu yan mata guda biyu su ka zo table din ta su na mata sallama Ko dago kai ba ta yi ba ta kale su amma ta amsa musu sallamar su cen kassan makoshi shi ma dan ya zama dole a matsayin ta na musulma Dayar na mini skert da yar t-shirt colour din uniform din college din babu hijab a jikin ta sai wani dan karamin veil da ta nada a kan ta , ta yi simple make up Dayar kuma ta na sanye da uniform din ta kamar na Nesrine wato wando da riga zuwa guyiwa da hijab zuwa kirji , ta na rike da hand bag guda biyu Wadda ke sanye da mini skert din ta ja chair din da ke fuskantar ta Nesrine ta zauna sannan ta kai hannu ta karbe book din hannun ta ta na fadin " me ki ke karantawa ne haka ? " Hararrar ta Nesrine ta yi kafin ta mike tsaye ta tatare kayan ta sannan ta mika wa yarinyar hannu ta ce " ban Book di na don Allah zan koma class " Mikewa tsaye yarinyar ta yi ta ce " haba Nesi me ya yi zafi haka " " kin ga Ramatou ki ban book di na, sannan kuma sunana Nesrine ba Nesi ba " Dayar yarinyar da ke tsaye ta ce " tooo ! Me ya yi zafi haka ? " Cikin fushi Nesrine ta kale ta ta ce " kin ga Halima ban sanyo da ke ba " Dariya yarinyar da ta kira da RAMATOU ta yi kafin ta ce " yanzu wannan fushin Nesi duk dan Hafiz ya miki fada ne jiya ? " Dawo da kallon ta kan RAMATOU ta yi sannan ta ce " kin ga ko wlh tun wuri ki ce mishi ya fita da ga harka ta , ba ni son shi , in kuma ya matsa na sa yaya na ya yi mishi dan banzan duka " Dariya RAMATOU ta yi har da dafe ciki sannan ta ce " to sai mi in kin fada mishi me zai yi , wlh ko karar shi ya kai gaban yan sanda ba abun da za ayi mishi dan haka tun wuri gwara ki karbi soyayyar shi, ni ban ma ga abun so cikin dirty girl irin ki ba , ni ko abotar da mu ke kawai dan ki na temakamin ne ina samun good grades ba dan haka ba ko kallo ba ki ishe ni ba , ke ba ki san yan mata nawa ne ke biyar yaya na ba da sunnan soyayya amma ya ki dan ya ce ya na son ki shi ne za ki wani ja mishi aji, yar rainin sens kawai, sannan ki ji yaya Moctar ya ga kanwar ki kuma ya ce ya na son ta , na fada mishi gaskiyar sunnan ta da kuma karyar da kika yi mishi na cewa hanya ce kawai ta hada ku wlh idan ki ka matsawa Inaya ta ce ba ta son shi " ta kai karshen ta na kyasta mata dan yatsun ta saitin fuskar ta Cike da izza ta ce " to wlh ki kuka da kan ki " Ta na gama fadar haka ta tila mata book din ta a fuska sannan ta juya ta bar cafeteria din Halima na biye da bayan ta Su na barin wajen Nesrine ta koma ta zauna ta daura kan ta saman table din sannan ta saki kuka kassa kassa Sai da a ka koma cikin class sannan ta tashi ta fara shiga toilet ta wanke face din ta sannan ta wuce class Nassan kowa ya na son ya ji wanene Hafiz , to nima ina son ji 😂✌ Hafiz dai babban d'a ne ga governor din Kano, Moctar na bi mishi sannan Ramatou sai autar su Nabila , a shekaru zai kai 25 , Moctar kuma 21 , Ramatou 19 years sai Nabila da baza ta wuce 15 years ba Tun bayan mahaifin shi ya zama governor wata izza da jiji da kai su ka saukar mishi Duk abun da ya gani ya ce ya na so to sai ya same shi ko da ta karfi ce Ga shi ba ya da mutunci ko kadan mahaifin nashi ma in ya bata mishi rai sai ya mishi kaca'kaca dan ba raga mishi ya ke ba Tun haifuwar Nabila mahaifiyar su ta rasu , mahaifin na su ya sake aure har wajen sau uku Amma duk wadda ya auro ba ta one month ta ke barin gidan sakamakon Dukan tsiyar da Hafiz ke yi musu Mahaifin shi na sane amma ya ki yi mishi magana dan ya san ba karamin aikin Hafiz ne ba shi ma ya rufe shi da duka Shi ya sa ya ja bakin shi ya yi shirin ya zuba mishi ido dan ya fi karfin shi Duk wata badakala sa ya ke yi mahaifin shi na sane , sannu sannu har ya fara janyo Moctar cikin badakalar ta shi Kullum su ne tafiya nightclub, ga shan giya da kayan maye À takaice ba abun da ba su sha, sai dai ba su taba kusantar mace ba da sunnan Zina Karewar zancen Nesrine da Inaya su ne mata na farko da su ka gani su ka ji su na son su Yadda a ka yi Hafiz ya hadu da Nesrine Wata rana ce driver din Ramatou bai zo daukar ta ba sai ta kira Moctar a kan ya zo ya dauke ta A lokacin su na tare da Hafiz Da su ka iso school din , su na tsaye bakin gate ita da Nesrine Tun da Hafiz ya daura ido saman ta ya ji ya na son ta Sai bayan sun koma gida ne ya ke tambayar RAMATOU wacece wanan yarinyar da su ke tare Nan ta fada mishi wacece Nesrine sai dai ba ta fada mishi ba ta na da kanwa Goben shi tun karfe 7 ya je bakin gate fin school din ya jiran ta Amma wani ikon Allah ranar nan Nesrine ba ta zo school ba Sai da ya gama tsayuwar shi ya gaji sannan ya koma gida , Goben shi ma haka ya dawo school din Wannan karan ta zo amma ta na baya dan Inaya ta riga ta fitowa shi ya sa bai gane Inaya kanwar ta ba ce Babu ko sallama ya kira ta cike da girman kai Kallo guda ta yi mishi ta gane yayan Ramatou ne dalilin da ya sa ta fara sakin mishi fuska Sannu sannu ta fara ganin halayan shi na gaskiya Kullum sai ya zo college din su dan ya gan ta Wata rana har waya mai tsada ya kama ta amma ta ki karba Haka kuma ba karamin bata mishi rai ya yi ba har ya tsinka mata mari cikin fushi sannan ya bata wayar da karfi ya ce zai kire ta Inda ya ajiye wayar nan ta bar ta ta yi tafiyar ta ko wa ya dauke ta oho ! Washe gari bayan ta zo school ya isko ta ya ke tambayar ta ina wayar da ya bata Nan ta mishi karyar wai Mamar ta ta gan ta kuma ta amshe ta Bai yi mata magana ba kawai ya bar school din , sai da ya yi wajen sati bai zo ba Nan Ramatou ta zo ta hura mata kunne a kan Hafiz tsakani da Allah ya ke son ta ta daure ta ringa kula shi ko ya ji dadi Abotar da ke tsakanin su ya sa ta yarda da zancen ta, dan ko ba komi yayan ta ne bai kamata ta wulakan tashi haka ba Sannu sannu ta fara kula shi har ta fada soyayyar shi Amma shi kuma ya na nan kamar dai kullum, bai sauya ba sam dan wani lokaci in ta bata mishi har marin ta ya ke wai a haka wai ya na son ta ( ni dai na ce humm) Babu irin gift din da bai kama ta ba amma ko wane lokaci sai dai ta yar da shi tsakar hanya ko kuma ta bar shi nan inda ya bata shi Sannu har soyayyar da ke mishi har ta fita zuciyar ta dan a ganin ta, Hafiz ba al'heri ba ne a rayuwar ta shi ya sa yanzu ta daina kula shi, shi kuma hakan ba karamin zafi ya ke mishi ba TO KUN DAI JI WANENE HAFIZ DA KUMA ABUN DA KE TSAKANIN SHI DA NESRINE ✌ ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : ANISH Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP 👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/IrsjzfoHUHBJzdgRtskPcY BOOK 1 ……………………………📚✍✍ [13/08/2024] ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ PAGE 8 ❤🔥 ▪Zayd Zaune ya ke cikin motar su wajen mai zaman banza ya na rike da wayar shi ya na latsa wa ya na sanye da tracksuit sky blue colour ya na sanye da wadanan bakin glglass din nashi na gado Yayin da Moussa shi kuma ke tukin, ya na sanye da Jeans baki da t-shirt Red colour Su na a haka Moussa ya katse shirun na su da cewa " wai Amir ka fada ma babyn ka za ka yi tafiya ne ? " ya kai karshen ya na dan satar kallon shi ta wutsiyar ido Shiru bai amsa mishi ba ko dago kai bai yi ba ya ci gaba da aikin shi Dan murmushi geffen fuska Moussa ya yi sannan ya ce " Amir wai me ya sa ba ka kula yarinyar nan , ya kamata a ce yanzu ka fara yi mata magana tun da har za ta dawo tare da mu da zama " Ba tare da ya dago kai ba ya ce " meye ruwan ka a ciki ? " " babu kawai gani na yi bai dace abun da ka ke mata ba, ka ga fa kallon makaho da kurma ta ke maka ba ta san kai ainahin wanene ba, ba ta san kowa na ka ba, ko cikeken sunnan ka ba ta sani amma a haka ta ke son ka " A hankali Zayd ya dago kai ya kali Moussa ya ce " me ka ke son cewa ? " Yar karamar dariya Moussa ya yi kafin ya ce " lalle ma ka cika dan rainin sens, yanzu ka na son ka ce min duk soyayyar da ta ke maka ba ka ganin komai ? , lalle ma yau ka cika babban makaho " ya kai karshen ya na sake bushewa da dariya " wait ! Maganar me ka ke yi haka, wannan baby har ya san minene soyayya ? na ga ai gaban ka ta ce dakwai wanda ta ke so , ni wlh maganar ta sai da ta ban mamaki , a sani na dai ban taba ganin ta da wani yaron ba , sai dai a cikin college din su " ya kai karshen ya na medo da kallon shi kan wayar hannun shi ya ci gaba da aikin shi " humm wai kenan ba ka gane ba da sunnan ka ne ta so fada ba, dan ka na wajen ne ya sa ta yi shiru , kai a ganin ka duk abun nan da ta ke ma da sunnan makobtaka ne kawai, no Amir ! Wlh pure love ne ta ke yi maka, kallo guda za ka yi mata ka gane soyayyar ka a idanun ta, nassan wadanan bakin glass din ya hana ka gani, Amir kai ka ce min ka na son ka manta rayuwar ka ta baya , to wannan damar ka ce , ka karbi matar ka , and found your family " Shiru Zayd ya yi bai ce da shi komai ba amma cikin ranshi ya na tunanin kalmomin Zayd tabass wanda ke maka kallon makaho da kurma , kuma a hakan mutumin ya so ka ya tabbata soyayyar gaskia ya ke maka " no ! Gaskia she is to small for me , wannan ko dauko ta ba na tunanin za ta iya bare har a yi tunanin wata familyn, gaskia ban yarda da abun da Diya ke fada ba " ya fada cikin zuciyar shi Cen kuma wata zuciyar ta ce mishi " in ta tabbata yanzu kai ma ka na son ta ? " Da sauri ya girgiza kan shi ya ce " no ! Impossible i can't do that " Kallon shi Moussa ya yi kafin ya ce " what you can not do ? " Dago kai ya yi ya kali Moussa sannan ya ce " ba zan iya daukar ta a matsayin mata ta ba " sannan ya meda bayan ya jingina a bayan kujerar shi ya lumshe idanun shi " Why ? na ga ai matar ka ce da aure a tsakanin ku " " Diya ba za ka gane ba ne , ni fa ban san minene soyayya ba , ba na tunanin zan iya son yarinyar nan gaskia , she is to young , duk shekarun nata nawa su ke ? at least na yi biyun shekarun ta " Moussa bai ce mishi komai ba ya yi parking din motar su a geffen hanya ya na jin sun tsaya ya bude idanun shi a hankali ya kali Moussa ya ce " Why ka tseda motar ? " bai ba shi amsar tambayar shi ba ya ce " Amir , na san dalilin da ya sa ka ce ba za ka iya daukar ta a matsayin matar ka ba , har yanzu kallon yarinya ka ke yi mata , ka na tunanin ba za ta iya ba ka hakin ka na aure ba , please ka Meda wannan zancen gefe , yarinyar nan ta na son ka tsakani da Allah , na sani kai ma ka na son ta cikin zuciyar ka , kawai wannan izzar ta ka ce ta gidan sarauta ke hana ka yarda da ka na son ta kai ma " " I don't love her , ni dai na fada maka ba zan iya daukar ta a matsayin mata ba gaskia " ya kai karshen ya na lumshe idanun shi " Why ? ba ta da kyau ne ? .. " cikin nitsuwa Zayd ya katse shi da cewa " no , kai ma ka sani ta na da kyau , She is so cute musaman idan ta yi murmushi wannan dan dimple na ta ya fito " wani kyawatencen murmushi Moussa ya saki cikin zuciyar shi ya ce " Sannu da rainin sens kawai , yanzu har ka San da ta na da wani dimple ? , mu je zuwa za ka aiki na " a fili kuma ya ce " Kennan murmushin ta na burge ka " " Yeah sosai ma , Kamar Fitar rana haka murmushin ta ya ke , ko ba ka so dole sai ka kalla " ( Kai fa da allamun Malam Zayd ya fara fita hayacin shi 🤣🤣🤣🤣 ) ya na gama fadar haka ya jiyo Moussa ya bushe da wata shegiyar dariya a dubu dari Zayd ya bude idanun shi ya na kallon Moussa da ke ta dariyar shi har wasu hawaye su ka zubo mishi dan karamin tsaki Zayd ya yi kafin ya ce " ka ga malam idan ba za ka tada motar nan ba mu tafi fada min na sauka " dan tsagaita dariyar shi Moussa ya yi kafin ya ce " okay shikenan mu tafi , Mister Love " ya kai karshen ya na tada motar su ka bar wajen shi dai Zayd bai ce mishi komai ba ya meda idanun shi ya lumshe , ko me ya ke tunani oho ! Ta kassan ido Moussa ke kallon shi , har sai da zayd ya lumshe idanun shi , Daga kafadun shi Moussa ya yi irin ban damu ba cikin ranshi ya ce " in ta yi tsami ma ji " Haka su ka ci gaba da tafiyar su ba wanda ya ce ma wani ufan har su ka isa inda za su je ▪Inaya Konce ta ke saman bed din su ta na kallon ceiling ta daura hannu daya saman ciki dayan kuma saman gashin ta, ko tunanin mi ta ke oho ! Ta na a haka malam ya shigo dakin ya na sallama Ba tare da ta motsa ba ta amsa mishi sallamar shi kassa kassa Bakin gadon ya karaso ya zauna sannan ya kai hannun shi ya daura saman nata da ke saman cikin ta ya ce " auta, wai me ya ke damun ki ne tun shekaran jiya na lura yanayin duk ya sauya ko waje na da ki ke zuwa kin daina ko laifi na yi miki ? " A hankali ta janye hannun ta , sannan ta juya ta bashi baya sai ta ce " Abba me ya sa za ku min aure ba tare da na sani ba, nassan ku na ikon yin hakan amma Abba ni ba ni son wanda a ka aura min , gaskia Abba a raba auren nan " " dalilin da ya sa wacen ranar na tambaye ki in kina son shi , amma ba ki ba ni amsa ba ki ka tashi ki ka tafiyar ki " " ni Abba ba ku tambaye ni in ina son shi ba , " " to shikenan yanzu bara na sake tambayar ki , ki na son Zayd ? " Da sauri ta ce " ina son shi , duk da ban san meye so ba amma har cikin raina na ke jin shi , amma gashi yanzu kun raba mu har abada Abba ya zan yi na cire son shi a cikin raina " ta kai karshen kamar ta yi kuka Dan murmushi yayi kafin ya ce " to ai ba sai kin cire son shi ba a ran ki " " Abba ya zan je gidan wani ina son wani kuma, ni gaskia Abba ba ni son wanda a ka aura min , ko da ba za ku yarda na auri yaya Zayd dan Allah Abba kar ku aura min wanda ba ni so " " na ga yanzu ki ka ce ki na son shi ya kuma za ki juya zancen " Kuka ta saki ta fara harba kafafun ta kamar karamar yarinya ta ce " ni Abba ba shi ba na ce na ke so " Yar karamar dariya malam ya yi dama da gangan ya ke jan mata rai Sai da ya ida dariyar shi sannan ya ce " to shikenan wanene ki ka ce ki na so ? " " yaya Zayd " ta fada cikin kukan nata Hannun shi ya kai saman kafadar ta sannan ya ce " yo ai ni ma shi ni ke cewa, shi ne wanda na aura miki , amma tunda ba ki so zan kira shi in ce ba ki son auren " ya kai karshen ya na janye hannun shi da ga saman kafadar ta ya mike ya zai bar dakin Har ya kai bakin kofar ya jiyo Muryar ta ta na fadin " da gaske Abba yaya Zayd ku ka aura min ? " A hankali ya juyo ya na kallon ta Ta na zaune tsakiyar gadon ta na kallon shi idanun cike da hawaye Jinjina mata kai ya yi sannan ya sa kai ya fice dakin Wani irin sanyi ne ta ji cikin zuciyar ta lokaci guda ba ta san lokacin da wani kyakyawan murmushi ya kubce mata ba har da wata yar karamar dariya Ta dauko pillow ta boye fuskar ta, ta na dariya ta koma ta konta ▪After one week ▪Misalin karfe 5 na yamma ▪Inaya Zaune ta cikin falon gidan ta buga uban tagumi kamar ta yi kuka ita kadai cikin gidan Ta na a haka ta ji a na sallama A hankali ta dago kan ta, ta amsa sallamar Zayd ne da Moussa su ka shigo gidan ko wane ya na rike da ledodi Ta na ganin su ta saki murmushi ta ce " sannu da dawowa " Moussa ne ya amsa mata ya na murmushi ya na takowa ya ajiye ledodin hannun shi saman sofa sannan ya zauna saman sofar da ke fuskantar ta ta Shi ma Zayd takowa ya yi ya ajiye ledodin hannun shi saman table sannan ya zauna geffen Moussa ya jingina a bayan sofar ya daga kai ya lumshe idanu shi ta cikin glass din shi Murmushi ta yi kafin ta mike ta nufi dining table ta bude fridge ta dauko jug na ruwa ta ajiye saman tray da glass biyu Sannan ta dauko tray ta komo falo , ta ajiye shi saman table ta zuba ruwan cikin glass ta mika wa Moussa Karba ya yi ya na murmushi ya yi mata godiya Har ta dauki guda glass za ta zubama Zayd Moussa ya yi saurin cewa " bari ba sai kin zuba mishi ba azumi ya ke " Dago kai ta yi ta kaleshi sannan ta saki dan karamin murmushi sannan ta mike ta koma saman sofar da ta tasso ta na sunkuyar da kai Ta na zama ko , Zayd ya mike tsaye ya nufi corridor ya shiga bedroom din shi Da kallo su ka raka shi ita da Moussa har sai da ya shiga bedroom din shi sannan ta kali Moussa ta ce " yaya Moussa ina ganin yaya Zayd ba ya so na " Dan murmushi yayi kafin ya ce " haba babyn malam ya isa ma ya ce ba ya son ki kawai aiki ne ya yi mana yawa kwanan nan shi ya sa ki ka ga ba ma yawwan zama gida " Jinjina mishi kai tayi sannan ta sunkuyar da kai ta fara wassa da dan yatsun ta Dan murmushi yayi kafin ya matso bakin sofar ya kai hannu ya dauki ledodin da su ka zo da su sannan ya mike ya tako gaban ta ya ajiye mata su sannan ya ce " Ga tsarabar ki nan, sannan ki shirya gobe za ki koma school " Da sauri ta dago kai ta kaleshi ta ce " yaya Moussa school fa ? Yaya Zayd ya yarda ? " Jinjina mata kai ya yi kafin ya ce " yes ya yarda mana shi da kan shi ya je ya sayo miki sabon uniform , da sauran abubuwan da za ki bukata " Da sauri ta mike tsaye ta na tsale ta na dariya kamar karamar yarinya Shi dai Moussa ya tsaya ya na kallon ta ya na murmushi " she is si innocente " ya fada cikin ranshi dai'dai lokacin da ya ke juya wa zai shiga corridor Har ya yi nisa ya tsinci Muryar ta ta na fadin " nagode yaya Moussa " Ba tare da ya juyo ba ya ce " ba ni ya kamata ki yi ma godiya ba " Ya na gama fadar haka ya ci gaba da takawa ya nufi bedroom din Zayd Bai mishi knocking ba kawai ya wuce bedroom din kai tsaye ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH❤💫 Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP CHANEL 👇👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP 👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/IrsjzfoHUHBJzdgRtskPcY BOOK 1 ……………………………📚✍✍ [14/08/2024] ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ PAGE 9 ❤🔥 ▪Zayd zaune ya kebakin gadon shi ya na rike da wayar shi , ya na sanye da jeans navy blue , da T-shirt white color , amma ya cire bakin glass din shi ya na a haka Moussa ya shigo Dakin ya na sallama cen kassan makoshi ya amsa mishi sallamar shi , ko shi kan shi Moussa bai ji amsar ba Geffen shi Moussa ya tako ya zauna sannan ya ce " Amir ! " Ba tare da ya dago kan shi ba ya ce mishi " uhmm ? " " Amir na yi tunanin maganar da na yi maka za ka saurare ni , wai me ya sa duk abun da na fada maka in dai ba ka niya ba baza ka yi shi ba , yanzu sati guda da ka je gidan su yarinyar nan ka dauko ta amma ko kalma daya ba ka taba ce mata ba , ka ce min akwai binciken da ka ke son yi a kan ta, in ba ta zauna kusa da kai ba ta ya za ka yi binciken , Zayd wlh ba na jin dadin abun da ka ke mata , shin minene laifin ta a ciki, ka na ga karama ce sosai ko ba za ka iya soyayya da ita ba ka kula da ita a matsayin kanwar ka mana " Shi dai Zayd ko dago kai bai yi bare ya ce mishi wani abu ya na ci gaba da latsa wayar shi Sai da Moussa ya gaji da zubar shi sannan ya ce " Amir ni ina son in san dalilin da ya sa aka aura maka ita " Wannan karan sai da ya dago kai slowly ya kale shi kafin ya ce " a kan hakan ni ke bincike " Dan zaro idanu Moussa ya yi kafin ya ce " ban gane ba kawai malam zowa ya yi ya ce ka aure ta kai kuma ka yarda ? In da ba ka son ta na minene za ka yarda " Ajiye wayar hannun shi ya yi saman bedside drawer sannan ya juyo da kyau ya kali Moussa sannan ya ce mishi " ba haka ba ne , shekara biyu baya , lokacin ka tafi Abuja dibo company , dai'dai na fito da ga cikin gida na hadu da malam ya na tafiya da sauri ko kallon gaban shi ba ya yi, a haka har ya kai min karo ya yi baya zai fadi , bayan na taro shi ya na yi min godiya kuka ya kubce mishi har da hawaye ya shiga yi min wasu magaganun allamun ya fita cikin hayacin shi , na yi matukar mamaki ya babban mutun na kuka haka kamar karamin yaro , na so na ji dalilin kukan na shi , sai na ja hannun shi mu ka shigo gidan nan na zaunar da shi sannan da hannu na tambaye shi minene ya ke kuka nan ya ke ce min " Zayd kashe min auta ta za su yi yanzu shekara biyu ina boye ta amma ina ji a jiki na wannan karan sai sun gano mu ban San ya zan yi ba , ita ce farin ciki na , ba zan iya jure rashin ta ba Zayd na shiga uku na " ni sam ban gane abun da ya ke nufi, sai na tsaya ina kallon shi ina son in karanci abun da ya ke nufi, sai da ya ida kukan shi sannan ya riko hannu na ya ce min " don Allah Zayd ina son in roke ka wata Alfarma " jinjina mishi kai na yi , ina kallon shi ya mike tsaye ya dawo gaba na ya zube saman guyiwowin shi ya ce min " don Allah Zayd ina son ka auri Inaya " a rude na mike tsaye ina fadin " what aure ? " mikewa malam ya yi ya na zaro idanu ya na kallo na ya ce " Zayd, dama ka na magana ? " ban amsa mishi tambayar shi ba na ce " uncle yi hakuri gaskia babu aure a sha'anin rayuwa ta bare kuma wannan yarinya ta yi min kannanta " komawa ya yi ya zube saman guyiwowin shi ya riko kafafuna ya roke ni da na yarda na aure ta in ba haka ba komai zai iya faruwa da ita kuma duk abun da ya faru da ita da hannu na a ciki tun da na samu damar ceton rayuwar ta amma na ki duk ya bi ya kashe min jiki ba yadda zan yi na yarda , a ranar a ka aure na da ita, limamin massalaci ya zama waliyi na, shi kuma malam na ta , na biya sadaki a ka aura mana aure , duk lokacin da na tambayi malam dalilin da ya sa a ka aura min ita sai ya ce min in bari in lokacin ya yi zan sani , dalilin da ya sa na ce yanzu ta dawo gaba na na dinga ganin ta ko zan gano dalilin da ya sa malam ya aura min ita " ya kai karshen ya sauke ajiyar zuciya ya dan lumshe idanun shi dan ba karamar wuya ya sha ba wajen yin wannan maganar duka , ji ya yi kamar harshen shi zai fado kassa Jinjina kan shi Moussa ya yi kafin ya ce " yanzu me ka ke tunani a kai ? " " duk yadda a ka yi akwai wanda ke bibiyar rayuwar ta , ka manta ranar nan ta na zaune ta fara sakin kara kamar wadda a ka dauke da karfi , wai ba ka lura da wasu abubuwa da ta ke kamar mara hankali ni ina jin yarinyar nan aljanu gare ta ma " yar karamar Dariya Moussa ya yi kafin ya ce " O'O kenan ka na lure da duk wane abu da ta ke " " of course ba matata ba ce " ya fada a takaice ya na mike wa ya wuce toilet Da kallo Moussa ya raka shi har sai da shiga toilet sannan ya ce " matar ka ko , to za ka ga yadda zan yi wufff da ita dan rainin hankali " Sai da ya ida sambatun shi sannan ya mike ya fice ya koma bedroom din shi Bai jima da fita ba Zayd ya fito da ga cikin toilet ya yi Alwalla sannan ya nufi bedside drawer , ya dauki wayar shi ya sa cikin aljihu , ya kuma dauki wadanan bakake glass din shi ya saka sannan ya fito dakin kai tsaye corridor ya baro ya shigo falo Inaya na nan zaune saman sofa ta na kallon Tv Har ya yi gaba zai wuce ya tsaya cak a hankali ya juyo ya zuba mata ido Ta na zaune waje guda kamar kungi ko kifta ido ba ta yi Slowly ya tako ya tsaya gaban ta ya dan sunkuyo ya na kallon face din ta Ko motsi ba ta yi kamar wanda ya suma Yatsun shi biyu ya kai saitin face din ta ya kyasta mata Da karfi zuciyar ta ta buga Ta ja wani dogon nunfashi ta yi baya ta fadi konce saman sofar ta na nunfashi sama sama idanu a lumshe Shi duk ya bi ya rude ya rasa mai zaiyi ya tsaya kawai ya zuba mata idanu Sannu sannu har nunfashin ta ya fara dawowa dai'dai A hankali ta bude idanun ta ta na kallon ceiling din falon A haka Moussa ya fito ya same su Ya na ganin su a haka ya saki wani kyawatencen murmushi cikin ranshi ya ce " me kuma ka yi ma y'ar mutane ? " Ya na gama fadar haka ya karaso geffen Zayd ya tsaya ya kale shi ya ce " Amir lafya wani abu ka yi mata ? " Girgiza mishi kai Zayd ya yi ba tare da ya ce komai Medo da kallon shi kan Inaya ya yi kafin ya kira sunan ta a hankali " Na'am " ta amsa mishi ta na kallon ceiling din " me ya faru ne ? " ya tambayeta ya na lekon face din ta A hankali ta fara kokarin dagowa ta gyara zaman ta sannan ta ce " yaya Moussa ji na yi kamar an danne min zuciya, duk ta yi min nauyi " Murmushi kadan Moussa ya yi kafin ya ce " shikenan ba komai har yanzu ki na jin hakan ? " Girgiza mishi kai ta yi kafin ta dago kai a hankali Idanun ta ba su sauka ko ina ba sai cikin nashi, shi ma ita ya ke kallon ta cikin bakin glass din shi Da sauri ta sunkuyar da kan ta ta takure waje guda Kai a sunkuye ta ga ya miko mata hannu Da sauri ta dago kai ta kaleshi ta na son ta yi magana amma ta ki fitowa A hankali ta medo da kallon ta kan hannun shi kafin ta dago nata slowly ta daura a saman na shi Dum zuciyoyin su su ka buga lokacin guda , dalilin mi ? Oho su kadai su ka sani 🤣🤣🤣🤣🤣 Ta na daura hannun ta, ya janyo ta ta mike tsaye sannan ya juya su ka fara tafiya a hankali ya na rike da hannun ta Sai da su ka shiga bedroom din shi sannan ya saki hannun da hannu ya mata allamun " ki shiga ki yi Alwalla ki yi sallat sai ki konta " ( WAI DAMA ANA MAGANA DA HANNU 🤔🤔 ) Jinjina mishi kai tayi ba tare da ta ce komai ba Juya wa ya yi ya fara takawa har ya kai bakin kofar dakin ya tsinci Muryar ta, ta na fadin " a dawo lafya yaya Zayd ! " Jinjina mata kai kawai ya yi ba tare da ya juyo ba ya ci gaba da tafiyar shi Ya na fita ita ma ta juya ta shiga toilet din Shi kuma ya na fitowa ya tardo Moussa zaune saman sofa ya na latsa wayar shi Ya na ganin shi ya saki murmushi ya ce " na dauka , ka na cen ka na cin angoncin ka ka kyale ni nan " Dan tsaki ya ja ya ci gaba da takawar shi zai bar falon Dariya Moussa ya yi kafin ya mike ya bi bayan shi da sauri Su na fitowa harabar gidan Moussa ya kaleshi ya ce " Amir ka gano abun da ke damun ta ne ? " Sai da su ka fita gidan sannan ya ce " na gano nan gaba " Jinjina mishi kai kawai Moussa ya yi su ka ci gaba da tafiyar su har su ka isa mosque Basu dawo gidan ba sai bayan sallar isha, nan su ka isko ta gyara gidan tsab sai kamshin turare ya ke , har da abinci ta girka musu ta jera komai saman dining table Kallon Zayd Moussa ya na murmushi ya ce " kai da ke cewa mu wuce restaurant mu sayo abinci, madam har ta shirya mana ashe " Kauda kan shi gefe Zayd ya yi sannan ya ci gaba da takawa ya shiga corridor ya wuce bedroom din shi Nan ma wajen a gyare ya ke sai tashin turare ya ke , ta share ko ina ta goge ta canza mishi bedsheet Sai da ta gyara komai sannan ta yi wanka ta sauya kaya ta Haye bed din ta konta Dan karamin murmushin geffen fuska ya yi sannan ya juya ya bar mata dakin dan ba ya son tada ta Falo ya fito nan ya ga Moussa saman dining table sai cin abincin ya ke , kamar mai jin yunwa Chair din da ke fuskantar tashi ya ja ya zauna sannan ya fara serving din kan shi dan shi ma fa yunwar ya ke ji , ya na iya jure komai a duniya amma banda yunwa shi ya sa duk irin fushin da zai yi bazai yi fushi da abinci ba Bayan ya yi serving din kan shi ya deba a spoon ya kai baki Sai da ya dan zaro idanu lokacin da ya ji taste din abincin, ba karamin dadi ya yi mishi ba Duk abun da ya ke Moussa na kallon shi ta kassan ido, cikin ranshi ya ce " tukunna ma sannu sannu sai ta mamaye wannan zuciyar ta ka ta dutse " Haka su ka ci gaba da cin abincin ba wanda ya ce ma wani kala har sai da su ka ida su ka sha ruwa su ka daura da juice sannan Moussa ya riga shi cewa " Amir gaskia da ga yau na daina cin abincin restaurant baby na zai dinga girka min " Kallon shi da kyau Zayd ya yi kafin ya ce " wane baby kuma ? " Dariya sosai ya yi sannan ya mike tsaye ya tatare dishes din ya gyara wajen ya meda su kitchen sannan ya dawo ya wuce falo Sai da ya zauna sannan shi ma Zayd ya taso ya shigo falon ya zauna sai da ya zauna sannan Moussa ya ce mishi " ba za ka je wajen ta ba ne " wani irin kukan kura ne Zayd ya yi ya tashi da gudu ya nufi Moussa amma kafin ya karaso shi ma Moussa ya tashi da gudu ya nufi dining room ya na fadin " lafiya malam da ga tambaya " " Diya , wlh ka shige min hanci , wai ba zan iya yin rana guda ba , ba ka sa na yi magana ba , Har ka sa na zama perrot " Zayd ya fada ya na tsaye bakin dining room ya na kallon Moussa dariya sosai Moussa ya yi kafin ya ce " Laifi na ne ? ni fa kawai ina taimaka maka ne ka kula da matar ka " " i don't need your help , please let me , ka bar ni na ji da wannan jarabar da a ka gama ni da ita " " wait ! wait ! Amir ka na jin abun da ka ke fada kuwa , yanzu matar ta ka , ka ke kira da jaraba " Moussa ya fada cike da rudu wani iska mai zafi Zayd ya furza da ga bakin shi kafin ya juya a hankali ya koma falo ya zauna saman sofa ya jingina bayan shi a jikin forehead din sofar ya daga kai sama ya lumshe idanun shi a hankali Moussa ya tako shi ma ya karaso cikin falon ya zauna saman sofa , ya zauna ya na kallon Zayd a hankali ya ce mishi " Amir , na san abun da ke cikin ran ka , kar ka manta ni kadai ne abokin ka , ni kadai ne wanda ka ke shawara da shi , kuma ba zan ga laifin ka ba dan ka ce jaraba , na san ba ka cikin hayacin ka , ko ni a ka yi wa irin wannan abun sai na ce jaraba , amma wannan abun ba jaraba ba ce , kaddarar ka ce , yarinyar nan wlh ita ce kaddarar ka , na ji hausawa na cewa Matar mutun kabarin sa , dubi wace uwar duniya ka baro ka zo nan , kawai dan ka auri yarinyar ne , kawai ka karbi kaddarar ka hannu bibiyu , wlh za ka yi dadin rayuwar ka da ita " cikin nitsuwa Zayd ya katse shi da cewa " please keep quiet , ina son na yi barci " dan zaro idanu Moussa ya yi ya na kallon shi cikin zuciyar shi ya ce " iyeeeee , sannu su yarima , ba shakka ! za ka ga aiki na " da ga haka ba wanda ya ce ma wani ufan har sai da Moussa ya koma bedroom din shi ya bar Zayd nan a falon ▪Misalin karfe 12 na dare Ya na konce saman doguwar sofa ya daura hannun shi guda saman goshin dayan kuma saman ciki ya lumshe idanun shi Ya na a haka ya jiyo takun mutun, a hankali ya ware idanun shi dan dama ba barci ya ke ba kawai ya lumshe idanun shi ne A hankali ya dago kai ya kali saitin da ya ke jin takun mutun din Sai da ya dan zaro idanu ganin ta tsaye cikin wannan daren , ta na tafiya a hankali idanu a rufe Ya na kallon ta har ta shiga kitchen Da sauri ya mike ya bi bayan ta , ya na shiga kitchen din ya gan ta rike da wuka ta na motsa lips din ta kamar mai magana Dan zaro idanu yayi a dubu dari ya yi kan ta ya karbe wukar har sai da ta dan yanke shi , dan rumtse idanun kadan ya yi ya sake budewa a kan ta Ta na tsaye waje guda sai tangal tangal ta ke ido rufe " wai me ya ke damun yarinyar nan ' ya fada cikin zuciyar shi A hankali ya kai hannu ya dauke ta cak kamar baby ya juya ya baro kitchen din, kai tsaye bedroom din shi ya meda ta ya kontar da ita saman gadon sannan shi ma ya Haye ya konta ya na kallon ta , a haka har barci ya dauke shi ▪Washe gari Misalin karfe 4 ya safe ya farka da ga barcin shi Ya na bude idanu su ka sauka a kan ta , ta juyo su na fuskantar juna ta na sauke nunfashi a hankali Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya juya a hankali ya sauko kafafun shi kassa sannan ya mike tsaye ya nufi closet din kayan shi ya bude ya dauki kayan shi wandon jeans light blue da t-shirt fara sannan ya fice dakin Kai tsaye dakin Moussa ya wuce babu ko sallama ya shigo dakin kai tsaye ya wuce toilet Shi kuma Moussa sai kwana ya ke da ga shi sai short ko shigowar Zayd bai ji ba , sai da ya fara jin saukar ruwa sannan ya bude idanun a hankali ya na motsi Kallon kofar toilet din ya yi ya ga dakwai dan haske Murmushi kadan ya saki kafin ya fara karanto adu'ar tashi da ga barci ya mike zaune ............................. ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH❤🔥 Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP 👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/IrsjzfoHUHBJzdgRtskPcY TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP CHANEL 👇👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i BOOK 1 ……………………………📚✍✍ [15/08/2024] ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ PAGE 10 ❤🔥 After some minutes ya fito sanye da kayan da ya dauko da ga bedroom din shi Kallon shi da kyau Moussa ya yi kafin ya ce " ango ! Me kuma ya kawo ka toilet di na " Ko kallon shi Zayd bai yi ba ya sa kai ya fice bedroom din Ya na fita Moussa ya mike ya na dariya ya shiga toilet shi ma ▪Inaya Misalin karfe 6 ta farka da ga barcin ta Ta na bude ido ta fara bin dakin da kallo , Sai da ta dan dauki lokaci sannan ta mike zaune ta sauko kafafun ta kassa sannan ta mike tsaye ta fara takawa ta nufi toilet Bai fi five minutes ba da shigar ta toilet ya shigo dakin ya na sallama a tunanin shi ta farka Sai ya ga dakin ba kowa ga kuma karar ruwa Sai ya tako bakin gadon ya zauna ya kai hannu saman drawer ya dauki bakin glass din shi ya sa , ya sunkuyar da kan shi ya na kallon kassa kamar mai tunanin wani abu ▪AFTER SOME MINUTES Ya na zaune a haka ta fito da ga cikin toilet din ta na daure da towel a kirjin ta Ta na ganin shi ta saki murmushi , ba tare da ce mishi komai ba ta tako wajen trolley din ta ta bude ta dauki uniform din ta Har ta juya za ta koma toilet wata zuciyar ta ta ce mata " ina kuma za ki koma mutumin da ba gani ba ya ke " Daga kafadun ta ta yi ta na turo baki nan na ta gaba ta koma ta ajiye kayan na ta saman trolley Sannan ta kai hannu zame towel din jikin ta, ta koma naked Hum kamar an ce mishi Zayd dago kai haka ya dago kai dai'dai lokacin da ta saki towel din ta ya fadi kassa ta duka ta dauki pant din ta Da sauri ya rumtse idanun shi ya kauda kai gefe , tun da ya ke a rayuwar shi wannan ne karan farko da ya ga tsiraicin mace , sai da ya ji zuciyar shi ta buga, cikin ranshi ya ce " na shiga uku ni Nawfel ba ta ga da mutun ne cikin dakin ko ita ma ta koma makafniya " Inaya kuma Tsab ta shirya war ta cikin uniform din ta, ita ta ma manta da mutun a cikin dakin Sai da ta gama shiryawa sannan ta dauki towel din da ta yadda kassa ta meda shi toilet sannan ta fice dakin Duk takun ta ya na jin ta amma ya ki bude idanu ya na tsoron ya sake bude su ya yi arba da abun da ya fi karfin shi Sai da ya ji ta bude kofa ta fita sannan ya bude idanun shi slowly ya kali saitin kofar ya na ganin ta fice ya sauke wata ajiyar zuciya mai mai nauyi Inaya kuma bayan ta fita kitchen ta wuce dan ta shirya musu breakfast Sai wajen karfe 7 cib sannan ta baro kitchen din ta shirya musu komai saman dining table sannan ta koma bedroom din ta Ya na nan zaune inda ta bar shi ko motsi bai yi ba Bakin ta dauke da sallama ta shigo dakin Cen cikin zuciyar shi ya amsa mata A hankali ta tako gaban shi ta tsaya sannan ta Zube saman guyiwowin ta ta ce " ina kwana yaya Zayd " Jinjina mata kai kawai ya yi bai ce mata komai ba Murmushi ta yi kafin ta mike ta nufi trolley din ta, ta dauki hijabin ta ta saka ta dauki school bag din ta sannan ta dawo gaban shi dan nesa kadan ta ce " yaya Zayd zan biya wajen Nesrine sai mu ta fi tare " Jinjina mata kai ya yi kafin ya sa hannu shi cikin aljihun wandon shi ya ciro kudi yan dubu dubu sun kai ashirin sabi gal sannan ya mika mata Dan zaro idanu ta yi ta na kallon kudin ta na tunanin ina ya sami wadanan kudade duka Ganin har yanzu ba ta karba ba ya sa shi dago kai a hankali ya kale ta Da sauri ya rumtse idanun shi dan ya tino kallon da ya yi mata ta na naked Ita kuma ba ta lura ba da ya datse idanun shi ba dan ya na sanye da glass bakake Ajiyar zuciya ta sauke ta yi murmushi kafin ta ce " yaya Zayd ka barshi kawai " Girgiza mata kai ya yi ya mike tsaye ya tako a hankali gaban ta ya kara mika mata kudin Wannan karan ba yadda za ta yi sai da ta karba ta na yi mishi godiya sannan ta saka su cikin bag din ta Sai da ya ga ta sa kudin cikin jakar ta sannan ya juya ya fice Da sauri ta bi bayan shi ita ma ta fito dakin A nan falo su ka isko Moussa ya na zaune saman sofa ya na latsa wayar shi Ya na dago kai ya gan su ya saki dan murmushi ba karamin kyau su ka yi mishi ba , cike da Fara'a ya ce " baby na har kin fito ? " Sunkuyar da kai kassa ta yi ta na fadin " ina kwana yaya Moussa " " lafya lau baby na , da fatan wannan jarabbaben bai takura miki ba " ya kai karshen ya na medo da kallon shi kan Zayd da ya zauna saman sofa da ke fuskantar tashi Girgiza mishi kai tayi kafin ta ce " yaya Moussa na shirya muku breakfast din ku , ko ku na bukatar wani abu ne ? " Girgiza mata kai ya yi kafin ya ce " no baby hakan ma ya isa , sai kin dawo Allah kiyaye hanya " Da amine ta amsa mishi sannan ta fara takawa ta fita falon Ya na jin ta fita ya sa hannu ya janye glass din shi ya ajiye su geffen shi ya zubawa Moussa wadanan hazel eyes din shi Sarai Moussa ya lura da shi amma ya yi banza da shi ya tashi ya nufi dining room ya fara breakfast sai da Moussa ya Kamala breakfast din shi sannan ya dawo cikin parlourn ya zauna saman sofa geffen Zayd ya kale shi ya ce " wai ka san wani abu " a hankali Zayd ya girgiza mishi kai allamun a'a " dama na san ba za ka sani ba , na ji labarin cewa gimbiya RIANNA ta samu tambayar aure da ga Daular Ottoman " a dubu dari Zayd ya juyo ya kali Moussa cike da rudu ya ke fadin " wassa ka ke yi amma ko " a hankali Moussa ya girgiza mishi kai allamun a'a sannan ya daura da cewa " ba wassa na ke ba , amma ba ta yarda ba , maganar dai har yanzu ta na a wajen Malik tukunna bai yanke shawara ba " dauke kallon shi Zayd ya yi da ga saman Moussa shiru ya yi na dan wani lokaci kafin ya bude baki a hankali ya ce " Wanene ya nemi auren na ta ? " " ni ma ban sani ba , Samarin da ke cikin Daular Ottoman su na dayawa gaskia , ba mamaki sarkin da kan shi ke son auren ta " " dole akwai abun da su ka shirya ta hanyar auren nan " cikin ko in kula Moussa ya ce mishi " Ya wuce Mulkin saudiya su ke so " a hankali Zayd ya juyo da kan shi ya kali Moussa ya ce " kamar ya kennan " " Amir yi tunani mana , Gimbiya RIANNA ita ce babbar yarinyar Malik , yayar ka ce , Kuma kai kadai ne magajin Malik , yanzu ba ka tunanin duk ranar da Malik ya fadi ya mutu , al'halin ya rasa yaron shi tilo da zai gaje shi , wa zai hawa Mulkin saudiya ? dole Mijin Gimbiya RIANNA shi zai hawa , ka fi kowa sanin irin alakar da ke tsakanin Daular Saudiya da kuma Daular Ottoman , har yanzu ba wani jituwa a dakwai tsakanin su , kuma har yanzu Daular Ottoman na da kudurin nan na ta na hawa Mulkin Saudiya baki dayan ta " a hankali Zayd ya gyada kan shi dan fa maganar Moussa ba kariya ba ce " yanzu me ka ke tunani a kai ? " " me kuma na ke tunani , kawai ka koma Daular Saudiya , ka fada musu dama ba mutuwa ka yi ba , bayanar ka ita za ruguza duk wani makircin da su ke shirin kulawa ta hanyar auren nan " girgiza mishi kai Zayd ya yi kafin ya ce " sai dai ka yi hakuri amma Batun komawa Daular Saudiya ka bar shi kawai " " why ba za ka koma ba , Amir yanzu kennan ka hakura da ahalin ka , ba za su sake ganin ka ba ? " shiru shi dai Zayd ya yi bai ce mishi komai ya na kallon gaban shi Allah kadai ya san abun da ya ke tunani ganin yadda ya yi shiru bai ce komai ba ya sa Moussa sakin wani cool murmushi ya rage sautin Muryar shi ya ce " Ko dai ba za ka iya rabuwa da babyn ka ba " " Ba zan iya tafiya na bar ta ba gaskiya , kuma ba zan iya raba ta da ahalin ta ba , ba zan so ta ji kewar su ba kamar yadda na ke jin kewar nawa " Zayd ya fada ba tare da ya kali Moussa ja shi a tunanin shi cikin zuciyar shi ya yi wannan maganar kawai sai jiyo Muryar Moussa ya yi ya bushe da dariya a hankali Zayd ya juyo kai ya kale shi cike da rudu ya ce " lafiya ka ke dariya kai kadai ? " tsagaita dariyar shi Moussa ya yi ya na girgiza mishi kai ya ce " ba komai Mister Love " dan karamin tsaki Zayd ya yi kafin ya ce " minene kuma Mister love ? Diya ban san dalilin da ya sa kullum sai mun fara magana da kai sai ka kawo shirme a ciki " yar karamar dariya Moussa ya yi kafin ya ce " Sorry sorry...... " bai kai karshen maganar shi ba ya ga Zayd ya mike ya nufi corridor da sauri Moussa ya ce " a'a Mister love ina za ka je haka ? " ko sannu Zayd bai ce mishi ba ya sa kafa ya shige corridor din ya nufi bedroom din shi sai da ya shige corridor din sannan Moussa ya sake bushewa da dariya ya na fadin " wa ya ga Inaya da cikin Amir , ni dai na gani " ya na gama fadar haka ya sake bushewa da dariya shi kadai kamar zautace ▪Inaya Bayan ta fita gidan ta fara tafiyar ta cikin konciyar hankali , kai tsaye gidan su ta nufa Da sallama a bakin ta ta shigo cikin gidan Mama na zaune bakin kofar dakin ta , dai'dai lokacin da Nesrine ke fitowa da ga dakin su ta na sanye da uniform ita ma Ta na ganin Inaya ta saki wani kyawatencen murmushi da gudu ta je ta rungume ta ta na fadin " na yi kewar ki sosai " Rungume ta ita ma Inaya ta yi ta na murmushi Cen su ka tsinci Muryar mama ta na fadin " toh malama kin sake ta, ta zo ta gaishe ni ko ? " A tare su ka yi dariya su na raba jikin su da na juna sannan Nesrine ta riko hannun ta su ka nufi mama Ta na isa mama ta bude mata hanayan ta akan ta zo Ba musu ta fada jikin ta ta na murmushi ta ce " ina kwana mama ? " " lafya lau autar mama ya ki ke komai dai'dai ko " ta fada ta raba jikin ta da na Inaya Kallon ta da kyau mama ta yi cike da mamaki ta ce " ban gane ba school za ki koma tun wuri haka " Murmushi Inaya ta yi kafin ta ce " eh mama yaya Zayd da kan shi ya sayo min uniform ki na gani ? " ta kai karshen ta na juyawa Mama na shirin magana Nesrine ta riga ta cewa " wuce mu tafi don Allah kar mu yi late" " shikenan wuce ku tafi , sai kun dawo " mama ta fada ta na murmushi Hannu Nesrine Inaya ta kamo su ka juya ta ce " mu tafi " Jinjina mata kai Nesrine ta yi kafin ta juya su fara takawa su ka bar gidan A tare su ke tafiyar su cikin konciyar hankali su na tafe su na hira gwanin ban sha'awa Sai da su ka kawo bakin kofar college din , Inaya ta ga masu sayarda kayan marmari Da sauri ta saki hannun Nesrine ta nufi guda da ga cikin su Karasowa wajen Nesrine ta yi ta kai hannu ta daura a kafadar ta ta na fadin " to sarkin ciye² me kuma za ki saya " Kallon ta Inaya ta yi sannan ta ce " Apple mana , ina marmarin Apple sosai wlh dama ban tsaya breakfast ba " Ta kai karshen ta na meda kallon ta kan mai sayarwar ta ce da shi ya saka mata Apple shida ta na kai hannu cikin jakar ta, ta ciro kudin da Zayd ya bata Zaro idanu Nesrine ta yi ta na kallon kudin cike da mamaki ta ce " ke Inaya ina ki ka samu uban kudi haka ? " Ba tare da ta kaleta ba ta na kokarin ciro dubu biyu ta bawa mai sayarwa ta ce " yaya Zayd ne ya bani " ta kai karshen ta na karbar ledar Apple din ta juyo ta kali Nesrine ta ce " mu tafi ? " Ba musu su ka juya su ka shiga cikin college din su na tafe su na hira har sai da su ka kai bakin kofar class din su sannan su ka rabu ▪After some hours Zaune su ke saman chair a cikin cafeteria , Inaya sai faman cin Apple ta ke ,Nesrine kuma na kallon ta ta na murmushi har ga Allah ta yi kewar Yar uwarta sosai , tun tafiyar ta har yanzu ba ta samu ta yi barcin kirki ba , ta saba kullum sai ta rungume Inaya cikin barcin ta , yanzu kuma ba ta nan ita daya saman gadon sai dai ta yi ta juyi idan ta gaji ta rungume pillow Sai da ta kusa kamalawa ta dago kai ta kali Nesrine , murmushi kadan ta yi kafin ta mika mata Apple din hannun ta ta ce " za ki ci ne ? " Girgiza mata kai Nesrine ta yi ta na murmushi ta ce " a'a ci kayan ki babyn Zayd " Daga kafadun ta Inaya ta yi ta ci gaba da cin Apple din ta hankali konce , ita komai na ta irin na yara ne Sai da Nesrine ta ga ta Kamala sannan ta ce " Inaya zan so na tambaye ki wani abu " Jinjina mata kai Inaya ta yi ta na fadin " wane abu kuma ? " Ajiyar zuciya Nesrine ta sauke sannan ta ce " da gaske ki na son yaya Zayd , a yadda ya ke hakan ba ya magana kuma ba ya gani ? " Murmushi kadan Inaya ta yi kafin ta jinjina mata kai allamun e sannan ta daura da cewa " ina son shi a haka , kuma ai yanzu miji na ne , tsakanin shi da Allah ya ke tare da ni , ni ma tsakani da Allah na ke tare da shi , Ni ma ban san ya a ka yi na kamu da son shi haka , lokaci guda ya shiga cikin zuciya ta , kuma ba na fatan ya fita , ko bayan mutuwa ta , rashin ganin shi ko rashin maganar shi hakan ba zai sauya abun da ke cikin zuciya ta ba har abada " " why Inaya ? Ki duba duk mazan da ke cikin duniya , ki rasa wanda za ki so sai kurma kuma makaho , me na sama ya ci bare ya ba na kassa , da wane idon zai kula da ke , mutumin da ko magana ba ya yi miki , wai a haka za ki bude baki ki Ce ki na son shi , me ya mallaka da su sauran mazajen duniya ba su mallaka ba , da har soyayyar shi za ta rufe miki ido ki kasa ganin minene al'heri a gare ki , ko ke ma kin zama makafniya kamar shi ? " " wai Nesrine wa ya fada miki yaya Zayd kurma ne , ko kuma shi ya fada miki shi makaho ne " Inaya ta fada cikin bacin rai ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ (LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) BY : MEERAH ❤✌ Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMENTS SECTION 👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/IrsjzfoHUHBJzdgRtskPcY TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP CHANEL 👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ PAGE 11 ❤🔥 Dan zaro idanu Nesrine ta yi ta na kallon ta cike da tantama ta ce " wai Inaya me ya ke damun ki ne , inda ya na magana duk shekaru hudun nan da mu ka yi tare da shi me ya sa ko kalma daya ban ji ta fito da ga bakin shi ba , kennan a haka ku ke rayuwa cikin gidan na shi , kennan rayuwa da kurma na yi miki dadi ? " Mikewa tsaye Inaya ta yi ta dauki jakar ta ta na fadin " kin ga Nesrine ban san me ya sa ba ki son yaya Zayd ba, ni fa ina son shi a haka kuma duk abun da za ki fada bazai sa na daina son shi ba , ku duka kallon kurma da makaho ku ke yi mishi amma ai ni ina gane abun da ya ke fada kuma da makaftar tashi ya ke aiki , kin ga ya fi karfin a ce mishi makaho kin ga idan ba za ki fadi abun al'heri a kan yaya Zayd ba ki daina yi min magana " " Inaya yanzu saboda wancen banzan za ki fada min haka , minene shi a wajen ki , da ga na fada miki abun ya ke gaskiya " " Gaskiya guda ce , ina son shi a haka , wai shi makaho ko kurma ba shi da zuciya ne , kafin ki yi min wannan maganar ki je ki fadawa Abba , ai shi ya bawa yaya Zayd aure na , da bai yarda da shi ba , ba zai yarda ya aura mishi ni ba " marairaice fuska Nesrine ta yi ta na fadin " yanzu Inaya kin fi son wacen mutum a kai na , ni Nesi din ki , me Zayd din nan gare shi da har idanun ki za su rufe a kan soyayyar shi , me ya ke da shi , da sauran mazan duniya ba su da shi , dama zama da makafi na meda mutum makaho ? " a hankali Inaya ta girgiza mata kai cikin sanyin murya ta ce mata " a'a Nesrine ke ce dai makafniyar , har yanzu idanun ki sun kassa gwada miki , kyakyawar zuciyar yaya Zayd , Soyayya ta ita ce ya ke da , kuma har abada babu namijin da zai same ta , Nesi wai ya ki ka sauya lokaci guda haka ? a sani na ba haka ki ke ba , ba ki kaskantar da mutane kamar haka ko ma dai minene zan so ki sani , yaya Zayd dai miji na , kuma a hakan na ke son shi , a hakan zan zauna da shi , idan ki na jin haushin hakan ki kashe kan ki ki huta " ( TO FA YAU A TABO BABYN ZAYD 🤣🤣🤣🤣 ) Ta kai karshen ta na juyawa za ta bar wajen kawai sai ta ji ta bugi mutun Dan bayan kadan ta ja ta dago kai ta kaleshi ta ce " sorry " Murmushi kadan Moctar ya yi kafin ya ce " ba komai " Da sauri ta raba ta geffen shi za ta wuce Da sauri ya riko hannun ta ya ce " haba ina kuma za ki je , ni fa wajen ki na zo " Cikin bacin rai Inaya ta kwace hannun ta ta juya ta fara takawa za ta bar wajen Da sauri ya sha gaban ta ya ce " ba da ke na ke ba , za ki wuce ki kyale ni ? " Cikin bacin rai Inaya ta ce " ka ga malam ka ba ni hanya na wuce ni matar aure ce " Dariya Moctar ya yi har da dafe ciki Sai da ya tsagaita dariyar shi sannan ya ce " oh sannu madam to , shi ne za a yi biki ba'a gayace mu ba ? " ya kai karshen ya na kashe mata ido guda Dan tsaki Inaya ta ja kafin ta raba ta geffen shi ta wucewar ta Da kallo ya bi har sai da ta kurewa ganin shi sannan ya juyo ya kali inda Nesrine ke zaune Sai dai kuma me ? Babu ita babu mai kama da ita, tun lokacin da ya bata baya ta tatare kayan ta a hankali ta tsere dan ta sani tabass Moctar ya na tare da Hafiz , idan kuma Hafiz ya zo wajen ta san tabass ba zai kyale ta ba shi ya sa ta tsere Abun da ba ta sani ba Moctar shi kadai ya ke tafe , Hafiz bai san da cewa college din zai zo kawai ya ce mishi zai fita ne Tsaki kadan ya ja kafin ya fara takawa ya fice cafeteria din shi ma ▪Inaya Ta na barin wajen ta koma kai tsaye class din su ta koma dai'dai lokacin da prof din su zai shiga class din After some hours Bayan sun sauka da ga school ko wace ta wuce gida , Inaya kuma gidan mijin ta kai tsaye ta wuce dan yau fa Nesrine da Moctar sun tado mata na bacin ran ▪Zayd Su na zaune cikin falo shi da Moussa ko wane sai faman latsa wayar shi ya ke Su na zaune a haka Inaya ta shigo falon ta na sallama kassa kassa Dago kan shi Moussa ya yi ya na amsa mata sallamar ta da murmushi Ya na shirin yi mata magana ya ga ta wuce corridor kai tsaye ko gaida su ba ta yi ba Da kallo ya rakata har sai da ta shiga bedroom din Zayd sannan ya dawo da kallon shi kan Zayd ya ce " Amir ina ga yau wani ya tabo ran baby na " Slowly Zayd ya dago kan shi ya zubawa Moussa wadanan hazel eyes din shi ta cikin glass kafin ya ce " wai wanene babyn ka cikin gidan nan ? " Hararrar wassa Moussa ya yi mishi sannan ya ce " bayan wadda ka ke kira da matar ka wa ke cikin gidan nan, ita ce baby na mana, ka ga na ma tafi na rarrashi abu na " ya kai karshen ya na mikewa tsaye zai shiga corridor Da sauri Zayd ya riko hannun shi ya ce " kai Diya ban san rainin sens matar tawa ka ke kira da baby ? " Kwace hannun shi Moussa ya yi kafin ya ce " tun da kai ba ka so ni ina so wlh , ni wlh ka ci gaba da kyale ta ma , hakan ya yi min dadi , ko na samu son da ta ke yi maka ya dawo kai na , i really love her, i don't know how ko yaushe hakan ta faru i'm falling in love for her , ni da za ka min Alfarma ka sake ta na je na roki malam ya aura min ita tun da kai ba ka son ta " " Diya wai ka na jin abun da ka ke fada ne " " ka ga malam ni don Allah kyale ni , wai ba ka ga yadda baby na ta dawo ne gidan ko gaisuwar arziki ba ta yi min ba , ka ga ni na tafi rarrashin ta " ya kai karshen ya na juyawa ya shiga corridor ya nufi bedroom din Zayd Sumar zaune Zayd ya yi ya na jin abun da Moussa ya ke fada mishi nan take ya ji wani uban kishi ya taso mishi yanzu shi Moussa zai yanka a baya ya zagayo ya ce matar shi ya ke so kuma Da sauri ya girgiza kan shi ya ce " no ! No ! Impossible bazai yi yu ba " Ya na gama fadar haka ya mike tsaye da sauri ya shiga corridor kai tsaye ya wuce bedroom din shi cikin zafin nama ya bude kofar dakin ya shiga Cak ya tsaya bakin kofar ya na bin dakin da kallo , duk wajen a tirje ya ke , ga pillow duk an zubar da su kassa , an zare bedsheet an tila shi gefe guda Cen ya hango Inaya zaune a kassa ta saka kan ta tsakanin cinyoyin ta, ga jakar school din ta cen gefe ta tila ta Tsaya wa ya yi ya na bin dakin da kallo ya na son ya ga Moussa amma ita kadai ya gani Abun da bai sani ba shi dama Moussa wassa ne ya ke yi mishi dan ya san abokin shi da mugun kishi nan take zai fara bibiyar Inaya duk wane abu da za ta yi sai ya Ankara da shi , dalilin da ya sa ya ke yi mishi wannan abun amma shi gaskia ba son Inaya ya ke ba ko yanzu da ya shiga corridor din bedroom din shi ya shiga ba na Zayd ba A hankali ya fara takowa cikin dakin har ya karaso inda ta ke zaune shi ma ya zauna gaban ta ya yi irin zaman cin tuwo ya zuba mata idanu, da allamun ba kuka ta ke ba Sai da ya gaji da kallon ta sannan ya kai hannu shi ya kyasta mata dan yatsun shi biyu saitin kunnen ta Da sauri ta dago kan ta ta na kallon shi dan ita ba ta ji shigowar shi ba cikin dakin har lokacin da ya zauna gaban ta , duk ta yi nisa cikin tunanin ta Dan murmushi ta saki kafin ta gyara zaman ta, ta yi irin zaman da ya yi ta sunkuyar da kai ta riko tafin kafarta guda da hannayan ta duka biyu Ganin ba ta da niyar yi mishi magana ya sa ya kai hannu ya dago habar ta ya na kallon face din ta , sam babu digon hawaye a cikin idanun ta , to me ya faru kennan ? Ita kuma murmushi kadan ta saki kafin ta ce " yaya Zayd me ya faru ? " Janye hannun shi ya yi kafin ya girgiza mata kai sannan ya kai hannu ya nuna nata sannan ya mata allamu da hannu " me ya ke damun ki ? " Sunkuyar da kan ta yi kafin ta ce " yaya Zayd wlh Nesrine ta na yawwan takura min wai na auri kurma kuma makaho duk cikin mazan da ke cikin duniyar nan wai shi na zaba, ban San minene matsalar ta ba , ni na fada mata ina son ka a hakan amma ta ki jin magana har wasu classmate din ta ta fadawa yanzu duk sun bi sun takura min a school , ni wlh in ba ta bani lafya sai na fadawa Abba , shin minene matsalar in baka gani ko baka magana na ga kai ma mutun ne ka na da tsoron Allah , ka na sallat ka na azumi ka yarda da Allah da manzon sa , kuma ka na da zuciya mai kyau , amma ita duk ba ta ganin wannan , wlh ina jiye mata duniya ba ta san abun da zai faru da ita ba nan gaba , sam ba ta ganin darajar mutane , duk abin da na ke son na gwada mata ta ki gani amma a haka wai ta ke ce maka makaho al'halin ita a bata gani " Tun da ta fara magana ya tsare ta da idanu ya na kallon ta cikin ranshi kuma cewa ya ke " Moussa ya yi gaskia she is so innocente , her heart is so pure , ba ta jin tsoron fadin abun da ke cikin zuciyar ta , duk zaman da na yi a Nigeria ke ce mace ta farko da ta ce min ta na so na a matsayin makaho kuma kurma al'halin ba haka ba ne , ina ga zan yarda da maganar Moussa na amshi soyayyar ta , muyi sabuwar rayuwa nassan bazan samu wadda za ta zauna da ni tsakanin ta da Allah kamar ke ba " Ya na gama fadar haka ya mike tsaye ya juya ya fara takawa ya fice dakin tun da ya mike ta dago kai ta na kallon yadda ya ke tafiya cike da nitsuwa , ita ta rasa dalilin da ya sa komai na shi burge ta ya ke yi , haka kawai ta ci gaba da kallon shi har sai da ya fice sannan ta saki wani cool murmushi ta ce " ina son ka yaya Zayd , kai ma na san wata rana za ka bude baki ka ce ka na so na " ta na gama fadar haka ta tashi ta shiga gyaran dakin Zayd kuma Ya na fitowa falon ya isko Moussa ya na konce saman sofa ya na latsa wayar shi Ya na ganin Zayd ya fito ya mike zaune ya na murmushi ya ce " har ka ida rarrashin baby na " Ko kallon shi Zayd bai yi ba ya sa kai ya fice falon, ya bar gidan baki daya Tafiya ya ke cikin konciyar hankali ya na taku cike da izza har ya karaso bakin kofar gidan su Inaya, ko me ya zo yi oho ! Ya na shirin shiga gidan Malam ya fito da cikin gidan ya yi shirin tafiya massalaci dan lokacin sallat ya yi Ya na ganin Zayd ya saki wani kyawatencen murmushi ya mika mishi hannu su ka yi musbaha sannan ya ce " a'a malam Zayd yau kai ne a gidan na mu haka , ina fatan ba dai laifi autar tawa ta yi maka ba " Girgiza mishi kai Zayd ya yi kafin ya ce " no ba maganar ta ba ya kawo ni gidan nan uncle ! " " toh , lafya kuma ? Maganar mi ta kawo ka in haka ne ? " malam ya fada ya na tsare shi da ido Sai da ya dauki lokaci kafin ya ce " uncle ina so in san dalilin ka na aura min Yarinyar nan al'halin ba ka san ko ni wanene ba ka san kowa nawa ba za ka dauki d'iyar ka ka bani ita haka kawai , Uncle na gaji wlh , na kassa gano komai , na tambaye ka , ka ki fada min ya ka ke so na yi ? " Dan murmushi malam ya yi kafin ya ce " Ni daman na sani ba za ka gano komai ba , kawai na kyale ka ne ka kai matar ka dakin ka , Zayd na fada maka in lokacin ya yi za ka sani amma tun da ka matsa bara na fada maka wani dan karamin abu saman ta , Inaya da ka ke gani ba kamar kowane mutun ba ta ke , akwai wata baiwar da Allah ya yi mata wadda ko ita ba ta san da ita ba , a kan wannan baiwar a ke bibiyar rayuwar ta , abu guda ne zai iya sa ta iya gane ta na da wata baiwa har ta iya anfani da ita shi ne ta hanyar aure , kafin mu baro kaduna wasu azaluman mutane sun so su yi anfani da ita wajen mugayan manufar su , dalilin da ya sa na aura maka ita kenan, dan kar su samu damar cin ma manufar su , ni nassan har yanzu su na bibiyar rayuwar mu su na neman inda mu ke amma ka ga cikin wani ikon Allah har yanzu ba su gano inda mu ke ba , kai baza ka san dalilin hakan amma ni na sani abu guda zan roke ka , ka kula min da yarinya ta dan rayuwar ta na da matukar mahimanci musaman a cikin rayuwar ka " Jinjina kan shi kawai Zayd ya yi ya na son ya ji wace irin baiwa ce haka wadda za ta sa ka a dinga bibiyar rayuwar mutun haka , to su da su ke bibiyar ta me su ke so da ita ? Ko kuma wannan baiwar da malam ke fada ita ce dalilin da ya sa ta ke wasu abubuwa kamar karamar yarinya ? Ya kamata ya ji micece wannan baiwar " uncle zan so na ji wace irin baiwa ce wannan wadda zai sa a dinga bibiyar ku haka ? " Zayd ya tambayi malam Murmushi malam ya yi kafin ya ce " Zayd bazan iya fada maka ba , amma zan so ka sani , Inaya ba ta tune da rayuwar mu ta baya , ko za ka bude baki ka tambaye a ina mu ka yi rayuwa kafin mu dawo kano baza ta iya fada maka ba , amma idan ka tambaye ta wani abu saman ka, ko da abun ya yi shekara 20 da wucewa za ta fada maka shi har ma wanda ba ka sani ba , amma hakan bazai yiyu ba har sai kun zama abu guda " Daga gera guda Zayd ya yi cikin zuciyar shi ya ce " kennan madubiya ce ko kuwa ? " A fili kuma ya ce ma malam " amma uncle ya za ayi ta manta rayuwar ta, amma ta san rayuwar wasu ko kuma amnesia ce ? " Girgiza mishi kai Malam ya yi kafin ya ce " Zayd abun guda na sani , duk ranar da ku ka zama abu guda , ita da kan ta za ta ba ka wannan amsar , ni da kai na na jima ina neman wannan amsar amma na rasa , Ina ji a jiki na , Inaya kamar ba ita daya ba ce a cikin gangar jikin ta , amma zuciya ta ta kassa yarda da hakan , idan ma aljanu ne gare ta ko ma minene ita kadai za ta iya ba mu wannan amsar " dan karamin tsaki Zayd ya yi ya na kauda kai gefe kafin ya juyo ya kali malam ya ce " uncle ku na son ku saka rayuwar ta cikin hatsari ne , ba ku san wanene ni ba , ba ku san da ga ina na fito ba , ba ku yi tunanin ko bibiya ta a ke ye ni ma , ba ku san irin hatsarin da ke cikin rayuwa ta ba ku na neman ku saka ta ta a cikin wannan kangin " murmushi mai dan sauti Malam ya yi kafin ya kai hannun shi saitin zuciyar Zayd ya ce " ni wannan na duba , ban duba kyawon ka , ko arzikin ka , wannan kadai na duba , saboda na San sai wanda ke da zuciyar maza zai iya ba wa autar tawa kariyar da ta dace , Zuciyar ka mai kyau ce Zayd dalilin da ya sa na yarda da kai kennan " ya kai karshen ya na janye hannun shi a hankali Zayd ya motsa lips din shi ya ce " Heart ?????? " yar karamar Dariya malam ya yi kafin ya ce " yo malam Zayd kai ka san minene hakan dan ni ban yi boko ba, yanzu dai mu tafi lokacin sallat ya yi kar mu rasa jam'i " Malam na shirin tafiya Zayd ya yi saurin cewa " uncle ina son nayi magana da Nesrine kafin mu tafi " Juyowa malam ya yi ya na kallon cike da tambaya, ko dalilin mi ya ke son magana da Nesrine ? Ya tambayi kan shi Shi kuma Zayd ya tsaya ya zuba mishi idanu ta cikin glass din shi ya kassa yi mishi magana fada mishi dalilin da ya ke son magana da ita , yau dai zai kawo karshen komai TO FA NESRINE YAU ZA KI GA FUSHIN ZAYD 🤣🤣🤣