❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) E1 Tashin hankali, nan fa kallo ya koma kallon kallo a palon. Wannan ya kalli wannan, wannan ma ya kalli wannan. Gwaggo tana nema ta juya musu lissafin ƙwaƙwale. "Aunty Aisha wai me kike faɗa ne? Ki yi mana bayani dallah dallah mana!" Cewar daddyn Rimsha. Aseef ne ya katse su da cewa "Ya za'ayi mu yarda da maganarki? Ya za'ayi ki ce Josephine sister daddy ce kuma yi expecting zamu yarda, kada ki kawo mana wasa da rainin hankali a nan, dukkanmu babu yaro a cikinmu!". Ya yi maganar on a serious note! With his full confidence!. Bin shi da kallo ta yi na ƴan sakanni kafin ta ce "I thinking nima bakaga nayi maka kama da yarinya or mara ilimi ba ai! Yanzu ni ban ce ku saka mini baki a maganata ba, da Dr William nake yi first, idan har kune TRIPLETS da gaske, to idan na gama da shi zan dawo kanku, idan kuma ba ku bane, kana iya yi mini shiru dan ni ba sa'ar yin ka bace! Ka bari babanka ya bani amsa!!." "Daddy amsa us, who she is?! Otherwise I will break her legs to pieces!!". Cewar Areef, ya yi maganar cikin fushi, dan fa shi ya zo har wuya gaskiya, cin mutuncin da Gwaggo take yi wa daddynsu ya ishe shi. "James i don't know her, i have never seen anyone like her until today!". TO FAH Dawo da kallon shi a kanta Areef ɗin ya yi yana faɗin "Get out, if not I will get you out after I break your legs!!". Ko sannu bata ce mishi ba ta juyo da kallonta kan Dr William tana faɗin "Zaka bani ƴaƴana ne ko kuma sai na gwada maka nan a Nigeria kake? Ai ta Allah ba taka ba, da yake Allah ba azzalumin bawansa bane, ina zaman zamana ga shi ka kawo kanka har in da nake, kuma a yanzu zaka san da A'isha kake yi!!". A tsananin fusace Areef ya ɗaga hannu zai wanke mata fuska da wani wawan mari. Cak Lion ya rike hannun nasa tare da cewa "Kada kayi wannan ganganci, ina son kowa ya sami waje ya zauna, kuma kada na sake jin muryar kowa a palon nan, ido shi ne naku!!". Dama da wuya kaga Lion ana hayani ta family a waje ya saka baki, baya yin haka sam, shiru yake yi ya zuba musu ido, idan suka yi, suka yi, zai natsu ya gane mai gaskiya a cikinsu, shiyasa a koda yaushe yake yanke hukuncin da ta dace, dan a nutse da kuma basira da ƙwaƙwalwa yake aiki. Yanzu ma zuba musu ido ya yi tun da suke hayaniyar yana tace maganganunsu har sai da yaga Areef zai mareta ne yasa baki, shi har ga Allah a jikinsa yana jin tabbas suna da alaƙa da Gwaggo, ko da ba mahaifiyarsu ba ce, to tabbas suna da alaƙa da ita, sannan bugu da kari, sai da ya kare mata kallo da kyau ya fahimci ita ce yake kallo a tare da Josephine, to a ina? Wannan ne ya kasa iya tunawa, ya kuma kasa ganewa, amma tabbas ita ce ya kallah tare da Josephine, kuma ita ce yake kallon fuskarta a tattare da Rimsha, sau da dama idan ya kalli face ɗin Rimsha, sai ya ji kirjinsa ya buga, to ba jinin kowa yake fusgarshi a fuskar Rimsha ba fa ce jinin Gwaggo. Natsuwa ya yi sam bai tada hankalinsa ba, ya nutsa cikin tunaninsa yana aiki da basira da hankali tare da kwarin gwiwa dan ya gane gaskiya. Tamkar yanda ya faɗa, zama kowannansu ya yi a saman sofa. Sai lokacin suka lura da Brr Naurat dake ta faman binsu da kallo, ita ma ta natsu ne tana tunanin waye mai gaskiya a cikinsu?. A tsananin razane Abba da Daddyn Rimsha har suna haɗa baki wajen ambatar mummy!!. Jinjina musu kai Brr Naurat ɗin ta yi alamar yes ita ɗin ce, tana murmushi tare da sanya musu yatsa ɗaya a saman baki, alamar su yi shiru kamar yanda Lion ya ce, dan ita kanta dama abin da zata ce musu kenan, tana son ta ce musu kowa ya natsu dan a san menene gaskiya!!. Cikin sanyin murya ta ce da Lion ɗin "Jikana kai ma ka samu guri ka zauna, A'isha zo nan kusa da ni ki zauna bari na tambayeki". Sam Lion bai yi mata musu ba, dan har cikin ransa yake jin kaunar tsohuwar nan. Saman sofa ya zauna yana ɗan shafa lallausan kumatunsa. Da hannu Brr Naurat ɗin ta yi wa Rimsha alama a kan ta zo ita ma ta zauna, dan ita Rimsha kawai ta sani a cikin jikokinta, shiyasa ta kirata a kan tazo kusa da ita ta zauna. Ba musu ta nufo kakan nata. A gefenta ta zauna tare da ɗan kwantowa a kafaɗarta. Rimsha sarkin son jiki. Daddyn ma komawa ya yi ya zauna, su Akila duk samun waje suka yi suma suka zauna. Gwaggonma kusa da Brr ɗin ta koma ta zauna tana cika tana batsewa. Cikin natsuwa Brr ta fara magana kamar haka. "A'isha a iya sani na dai baki yi aure ba, kuma har na bar Nigeria baki yi aure ba! Amma yanzu ki duba waƴan nan zaratan matasa da kike ikirarin ƴaƴanki ne, a yaushe kika yi aure har kika haifo su? Sannan a ina kuma kika san shi Dr William ɗin? Idan ma har da gaske kike yi ƴaƴanki ne, to ina sone ki bamu labarin ya akayi suka zama naki? Kafin mu san abin faɗa, ba zuwa zaki yi kawai ki ce mana ƴaƴanki ne sai mu yarda ba, wannan abin dai kin san da akwai ɗaure kai, to yanzu dai ki yi mana bayani". Sarai Brr ta san cewa maganganun Gwaggo gaskiya ce, babu karya a ciki, dan ta yi wa ƴaƴanta dukka farin sani, ta kuma san irin tarbiyar da ta basu, amma sai bata nuna mata cewa gaskiyar ba ce take faɗa, sai kawai ta nuna mata a kan basu yarda ba, dan dattaku irin na dattijuwa mai adalci, ai Brr ta yi a rayuwa, mutuniyar kwarai ce sosai, kowa ya zauna da ita sai ya so ta. Shiru gabaɗaya palo suka yi, kowa jiran bayanan Gwaggo kawai yake yi. Shi dai Lion ya jingina kansa da jikin head na sofar yana binsu da idanun. Tamkar ba ta son yin magana, haka ta fara da cewa "Mummy ina so ne kafin na fara baku labari a kira mini Deen da Maik sai Azharuddin, ina son kowa ya zo nan dan kowannensu da akwai tambayar da zan yi mishi a cikin maganata". Kallon daddyn Rimsha Brr ta yi tana faɗin ya kira mata su dukkansu, yanzun nan su zo ba ɓata lokacin, dan a warware komai. Okey ya amsa cikin girmamawa. A hanzarce ya ciro wayarsa ya fara neman numbersu, dan duk yana da su a email ɗinsa. Ya kuwa yi sa'a dukkansu ya samesu. Ba ɓata lokacin ya isar musu da saƙon Brr ɗin, a in da yake ƙara jaddada musu da su yi sauri. Ba ɓata lokaci. Cikin kankanin lokacin sai ga su sun iso. Da Abbi da daddyn Jelly ne suka fara zuwa kafin Azharuddin Bature ya biyo bayansu, kowannansu da iyalansa ya zo jin cewa Brr ce take nemansu. To fah yau ake yinta, yau za'ayi cakwakiya kenan, kowa yazo, duk sun haɗu saura Hjy Batoola da Aafia ta Dr Nawid, su ne basu nan. Kowa ya natsu a palon bisa umarnin Brr Naurat. Shi ma dai Lion ya zuba musu idanu dan wannan babban case ne da yake buƙatar nazari dan tantance mai gaskiya a cikinsu!. Areef ma binsu da idanu yake yi, a matsayinsa na jami'in CIA yana ƙoƙarin tantance mai gaskiya ta hanyar amfani da ƙwaƙwalwasa da kuma basirarsa. Shi kuwa Aseef ya kwantar da kansa a saman cinyar daddyn Rimsha, dan ciwo kan nasa yake yi mishi sosai, bawan Allah sam baya son hayaniya, lokaci guda azababben ciwon kan ya sauko mishi. Tga, Uncle Herry duk sai binsu da ido kawai suke yi, amma fa dukkansu idan ka kalli face nasu, zaka ga razana da firgici a tattare da su!!. To razanar me suka yi haka?!. Dr William ɗin ma kusan haka ne, sai dai shi ya fi su dakiya da taurin zuciyar iya jure komai. Jay and John, su kuwa ko a jikinsu, su ji suke yi ma an takura musu, dan sam basu yarda da abin da gwaggo take faɗe ba, kallon mahaukaciya ma suke yi mata. Gyaran murya Brr Naurat ta yi kafin ta fara magana a nutse cikin girma da dattaku tare da nuna tsantsar kauna da farinciki na kasancewarta yau gata a cikin Nigeria, kuma a cikin iyalanta. "A'isha ga su Zahradeen ɗin sun iso, sai ki gaya mana a ina kika san wannan mutumi? Ya aka yi kuma kike da ƴaƴa a wajensa?!". Su Abbi gabaɗaya sun sha ruwan mamakin ganin Brr Naurat, sai dai ta hanasu yin magana, dan kuwa wannan case ɗin ya fi muhimmanci a gabatanta a yanzu, dole dai kowa ya haɗiye mamakinsa da murnarsa suka kasa kunne suna sauraron Brr ɗin. Kallon Abbi Gwaggo ta yi tare da fara magana a nutse. "Kai Deen zaka iya gane wannan mutumin?". Ta yi maganar tare da nuna Dr William da hannu. Shiru Abbi ya ɗan yi na ƴan mintocin da basu wuce biyar ba. Can kuma ya ce "Of course a Harvard University Washington DC ko?." Jinjina mishi kai ta yi alamar e. Amsa mata ya yi da e ya tuna shi sai dai ya manta sunansa. Tashin sense! Nan fa TRIPLETS gabaɗayansu suka tsare Gwaggo da Abbi da idanun, dan suna son fahimtar wani abin. Kada ku mance da English suke magana, dan mutanen Washington daga kan William jacob har familynsa basu jin hausa ko kaɗan. "Yauwa Deen idan zaka iya tunawa ba wannan mutumin ne ka taɓa rabamu rikici da shi ba na ya mareni na rama?". Nan ma shiru Abbin ya ɗan yi kafin ya amsa mata da anyi haka!. Dakatar da su Brr Naurat ta yi a in da take cewa "A'isha ki ɗauko mana labarin abin da ya faru tun daga farko, ki gaya mana komai dallah dallah, ba wasa muke yi a nan ba, kowa jiranki yake yi!!". Shiru ta ɗan yi kafin ta ja dogon numfashi, sannan ta fara magana a nutse kamar haka. SOME YEARS AGO. HARVARD UNIVERSITY.❤️ Zaune take a saman ɗaya daga cikin wasu kyawawan chair dake wajen garden na kusa da department nasu na surgeon Drs. Ta yi shiru a in da hankalinta yake a kan wani kyakkyawan littafi dake hannunta tana dubawa, ta nutsa cikin karatun wannan littafi. Jikinta sanye yake da wandon jeans baki da T-shirt fara tas, sam babu ɗankwali a kanta, ta saki gashin kanta irin na Naurat har baya, a lokacin sam bata sha ranar Nigeria ba, fara ce tas tamkar Naurat, babu wanda zai ɗaga idanu ya kalleta ya ce ba Baturiya bace, saboda haskenta da kyan da Allah ya yi mata, ga wannan dara daran idanun nasu na gado da suka gado wajen Dr Salman. Sai safa da marwa students suke yi a wajen, amma sam tamkar babu ita a waje, bata ɗago kai bama bare ta ga wani, da alama tana ji da shariya sosai a lokacin, tana ji da kanta over. Abin ku da turawa, su basu da matsala dan sun zauna kusa da mutun in dai nasu ne ko sun yi mishi magana, sam basu da girman kai su. Wata kyakkyawar Baturiya ce ta zauna a gefenta tare da yi mata sannu da hutawa. Ganin cewa cikin mutunci Baturiyar ta ɗaga mata gaisuwa yasa ita ma ta amsa da mutunci. Hannu Baturiyar ta miƙa mata tana faɗin "My name is Cherish Daniel what of you?". A takaice mata "A'isha Salman Sultan". "Wow are you a Muslim?". Ta tambaya fuska ɗauke da mamaki. Jinjina mata kai ta yi alamar. Sosai Cherish ta ji daɗi suka kuma kulla abota. Abotansu gwanin birgewa, bambancin addininsu baya hanasu kasancewa a tare, idan lokacin ibada ya yi, Gwaggo zata tafi masallaci, da yake Cherish tana sonta, har kofar masallaci take rakata, ta kuma zauna ta jira ta. Idan kuma ranar zuwa church ne, Gwaggo zata yi mata sallama cikin mutunci. Haka suka kasance har tsawon shakara ɗaya, Cherish tana zuwa gidan Gwaggo sosai, while ita ma Gwaggo tana zuwa gidanta time to time, dan gwaggo fa akwai ji da kai ga shariya. Wata rana Abbi ya kawo mata ziyara. Ta ji daɗin zuwan kanin nata, da yake ita ce babba a kan Abbin. Ranar sun kwana basu yi barci ba, sunata hiran gida. Cherish bata san da zuwan Abbi ba, dan ranar bata zo gidan Gwaggo ba, kuma gwaggon ma bata je gidanta ba, sai washegari ne da Cherish ta zo dan su wuce school, a nan ne ta ga Abbi, nan fa ta ce ita duniya ba wanda take so biyun Abbi, lokacin fa ba wani babba bane shi ɗin, dan Gwaggo ma bata wani girma sosai ba, kuma ita ce babba a kansa, daga Abba ne sai ita sannan Abbin sai su daddyn Rimsha da daddyn Anaya. Ita dai Gwaggo sai dariya take yi wa Cherish dan ta ce tana son Abbi, shi kuma ya sha kunu ya murtuke fuska kamar wanda aka yi wa tayin mugun abu. Nan fa ya ce zai bi Gwaggo dan ya kalli makarantarsu, a lokacin shi da Abba suna Ahmadu Bello University Zaria, dan lokacin sun koma Nigeria, sun baro Russia kenan. Abba yana soyayya da Ammiensu Imran time ɗin, suna son juna sosai har ma iyaye sun sani. Gwaggon sam bata zauna a gida nan Nigeria ba, wayon Washington DC ce ita, ko a Russia bata wani zauna da su sosai ba. Kuma ita ta zaɓi Harvard University, shi kuma Dr Salman ya amince mata, Naurat ma ta bata goyon baya sosai, dan fa su a wajensu tura ƴaƴa karatu koma ina ne ba wata matsala bane suke gani. Da farko tare da Abba zasu tafi, sai daga baya Abban ya ce shi ya fasa zai zauna a Nigeria ya cigaba da karatun kawai, Nigeria ta fi yi mishi daɗi. Sam Gwaggo bata shiga harkar kowa, bata ma ɗaga idanu ta kalli mutun a cikin school ɗin, tana yawan jin ana magana a kan dangerous boss na class nasu, wanda ya kasance shi ne gaba da kowa a class ɗin, guru ne kuma jan wuya ne a fagen karatu, sam baya wasa da karatu, ga ilimi da kaifin kwakwalwa tamkar shi ya yi wa kansa. Bata taɓa sanin wanene shi ba, sai dai ta sha alwashin a wannan karon wlh sai ta zama a gaba da shi, sai ta wuce shi a karatu, kowa ya shaida shi ne na ɗaya, to sai ta buge tarihinsa ta kafa nata, duk da tana jin ana yabon kaifin kwakwarsa a makarantar over, ga shi mafaɗaci ne number ɗaya, ga bala'i zafin rai, baya shiga harkar kowa, amma idan aka sami akasi ka shiga nasa, to ka kuka da kanka, dan sai ka yi danasanin zuwanka duniya, bashi da mutunci idan aka taɓo shi. Sosai tana yawan jin labarinsa, amma bata san shi ba kuma bata nemi sani ba!, Harkar gabanta kawai take yi. Bayan sun je school Abbi ya zauna a garden yana ta aikin latsa waya, su kuma sun shiga class nasu dan suna da lecture. Bayan sun fito daga lecture ne Cherish ta ce su je su sayo kayan cima kafin su wuce wajen Abbi. Okey Gwaggo ta amsa mata da shi. A tare suka jera zuwa super mall ɗin nasu. Ita dai Gwaggo ruwan lemu kawai ta ɗauka guda biyu a cikin cup. Ita kuma Cherish duk wasu kayan zaki sai da ta kwasa abinta, su chips ma bata bari ba! Ta ɗauki abubuwa son ranta, sai dai fa komai guda bibbiyu take ɗauka, nata ɗaya, na Abbi ɗaya kamar ya ce mata zai ci. Sun gama sayayyarsu su ka juyo kowace tana rike da nata dan su wuce garden. Gwaggo na juyowa ta yi karo da mutun a in da gabaɗaya lemun dake cikin cup ɗin hannunta ya kwarare mishi a jikinsa, daga kirjinsa har zuwa shafaffen cikinsa lemun ya wanke shi. Abin haushi ɗaya shi ne, kayan jikin nasa farare ne tas, ga lemun nata ita kuma kun sani orange color ne. Bin jikinsa ya yi da kallo idanuwansa na sanye da black glass, while yana sanye da wandon jeans fari tas da T-shirt shi ma fari, ga wani dankareren sarkar gold a wuyarsa wanda ta zo mishi har kirjinsa, irin waƴan nan sarkokin ne na manyan yara masu ji da kansu. Kunnensa na sanye da ɗankunne ɗan ƙarami, daga ta saman kunnensa ya sanya wani irin ɗan kunne na zallar zinari mai bala'in kyalli. Hannunsa na dama yana ɗaure da dankareren watch mai bala'in tsada, while ɗayan hannun nasa kuma wasu sarkokin hannune na manyan yara sanye a wajen. Da kallo ɗaya zaka yi mishi kasan e lallai yana gym, dan ga jikinsa nan ya nuna alama ta hanyar murɗewa da ya yi, yana da kirar cikakkun maza masu lafiya da jini a jika, haka zalika da kallo ɗaya zaka yi mishi kasan cewa babban yaro ne ɗan gidan manyan mutane masu faɗa a ji, dan daga samansa har kasa, komai na jikinsa masu bala'in tsada ne wanda babu na kasa da 1m. Kasancewar T-shirt ɗin jikinsa mai karamin hannu ne sosai, wani zanen tattoo dake wajen damtsen hannunsa ya bayyana, zanene na tambarin kunama, kasancewarshi jawur kamar ka taɓa jini ya zuba, sai bakin zanen tattoo ɗin ta fito zar a wajen. Babu karya kyakkyawa ne over ajin farko, ga class da ilimi!. Bin jikin nasa da kallo ita ma Gwaggo ta yi kafin ta furta mishi kalmar sorry a takaice tare kuma da nuna ko in kula. Ita dai Cherish tuni ta ja gefe guda ta takure waje ɗaya, ta wani natsu tsit ta kuma sha jinin jikinta. Da alama ta yi wa guy ɗin farin sani sosai, kuma tana mutuwar tsoron shi. Raɓawa gerensa Gwaggon ta yi da nufin ta wuce, bayan wannan sannu da ta ce mishi a takaice da kuma halin ko in kula, bata sake cewa komai ba ta kama gabanta da nufin ta bar wajen, dan ita ma tana ji da kanta over. A fusace ya juyo tare da ɗauketa da wani wawan mari wanda ya sanyata har sai da ta yi tangal tangal ta kusa faɗuwa. Diff ta ji komai ya tsaya mata, ta daina gane komai saboda wannan mari, har wani abubuwa ta gani suna gilmawa ta cikin idanunta, ga wani haske da ta gani kamar wutar lantarki. Ta ɗan ɗauki ƴan sakanni a haka kafin ta fara ganin jiri yana wani ɗebanta. Zazzaƙar murnarsa ne ya dawo da ita cikin hayyacinta a in da ya furta mata "Ke dabbar ina ce?! Babu kwakwalwa a cikin kanki ne?!". Ya yi maganar cikin natsuwa. Jin hakan yasa ta dawo dai'dai. Ɗago dara daran idanunta da suka yi ja sosai saboda marin da ta sha ta yi, tare da sauke kallonta a kan fusatatcen fuskansa. Duk da ta sha jinin jikinta na ganin face ɗin nasa a ɗaure, ga uban kwarjini mai rikitarwa, ta kuma tsorata, amma hakan bai hanata ta datse idanunta ita ma ta ɗauke shi da wani gigitatcen mari ba. Cherish da ba ita Gwaggo ta mara ba, sai da ta saki plate na kayan cima dake hannunta suka zube kasa suka tarwatse a wajen, saboda tsabar mahaukacin razana da ta yi, bata taɓa tunanin za'a iya samun wanda zata iya marin dangerous boss a cikin wannan school ɗin ba, zaratan maza ma tsoronsa suke yi bare mata. Da gudu ta watsa ta bar wajen dan ta je ta sanar da Abbi abin da yake faruwa da Gwaggon. Jama'ar dake wajen ba ƙaramin razana suka yi ba, dan dayawansu sun san waye shi, bashi da mutunci, kuma iyayensa suke goya mishi baya, a kansa zasu iya buga shari'a da kowa, ɗan gidan manyan mutane ne masu karfin murya ta faɗa a ji a kasar, yayan mahaifinsa ma shi ne president mai ci a wannan lokaci, shiyasa yake yin abin da ya ga dama. Ba'a taɓa yin wanda ya nuna mishi koda yatsa a cikin school ɗin ba, yau an wayi gari wata mace ta wanke mishi kyakkyawar jajir ɗin lallausan fuskarsa da mari a gaban jama'a. Tashin hankali, ko iyayen da suka haife shi basu taɓa dukan shi ba, sai dai su yi ta lallaɓa shi tamkar jariri, ɗan gata ne over. Ita kuwa Gwaggon hankalinta a kwance dan bata ma san wanene shi ɗin ba, sai ma ƙoƙarin sake raɓawa gefensa da ta yi dan ta wuce. Cikin fushi da ɓacin rai ya sanya kafa ya kwashe kafafunta ta zube kasa wanwar. Tsadadden belt ɗin wandonsa ya ciro da nufin ya yi mata dukan mutuwa, hakan kuma ya yi dai'dai da shigowar Abbi da Cherish. Daga can baya Cherish ta tsaya. Shi kuma Abbi, da sauri ya kari so wajen tare da rike belt ɗin na Dr William ɗin yana tambayar shi me yake faruwa. Kwashe Abbin ma da wani gigitatcen mari ya yi, dan fa ya fusata a lokacin, ransa ya yi mugun ɓaci, baya ji baya gani. Sauke musu belt ɗin hannun nasa kawai ya fara yi a jiki. Da sauri sauran jama'ar da suke wajen suka yi kansu, duk da suna tsoronsa bai hana su bashi hakuri ba, saboda mace yake duka. Ainahin Dr William baya dukan mata, kowa ya san da hakan, ɗabiarsa ce, kuma shi ya koyawa su Lion dukan mace kaskanci ne, amma ita ta raina mishi wayo ne, kuma ya tsani raini a rayuwarsa, zata zuba mishi abu a jiki ba tare da ta wani damu ba zata wani ce mishi sorry cikin nuna halin ko in kula, dole abin zai ɓata mishi rai. Uwa uba ga kuma marin da ta yi mishi a bainan nasi Da kyar aka danne shi ya hakura ya rabu da ita, badan haka ba ya yi niyar yi mata ɗan banzan dukan da ko motsawa ba zata yi daga wajen ba sai an ɗagata. Cikin fushi ya yi wurgi da belt ɗin tare da wucewa ya bar wajen yana wani huci. Bayan ya tafi ne jama'a suka taimaka mata ta miƙe, jiki ba kwari suka fito daga cikin wajen. A cikin zuciyarta, ta kuduri niyar wlh bazata barshi ba, sai ta koya mishi hankali!!. Abbi ya shiga damuwa sosai, amma ita ko a jikinta, bata wani damu ba, yanayin rayuwarta a lokacin sak rayuwar Jehan, ba maraba, dan bata shiga harkar kowa ita ma, amma idan ka shiga nata, to fa wannan faɗa ba zata kare ba har sai ta ga ta yi nasara a kan abu, haka take. Sati biyu Abbi ya yi a wajenta, tun daga wannan rana kuma bata sake yin 4 eyes da Dr William ba, har sai ranar da Abbi ya koma, bayan ta raka Abbin airport ta dawo ne ta wuce shopping dan ta sayo wasu abubuwan bukata da bata da shi a gida. Shiryawa ta yi cikin wandon jeans fari tare da high neck t-shirt, shi ma fari tas, ta gyara gashin kanta tare da ɗaura wani ɗan ƙaramin handkerchief a kan nata, shi ma fari, kafarta na sanye cikin high heel fari, from up to down dukka wankar fari ta yi. Wayarta da Atm kawai ta ɗauka sai key ɗin mota ta fito. Da yake gidan nata yana hawa na goma ne ta lifter ta sauko kasa, kowa na benensu yana harkar gabansa, babu ruwan kowa da kowa. Wucewa ta yi zuwa wajen kyakkyawar motarta, shiga ta yi ta bar gidan. Bata zame ko'ina ba sai wani tampatsetsen super market. Tana parking bata ɓata lokacin ta ba wajen fitowa daga motar ta nufi cikin wajen. Sayyayya ta fara yi babu kama hannun yaro, tamkar ba kuɗi zata biya ba, da yake already Dr Salman ya zube mata kuɗi a cikin account nata ba na wasa ba. Tana sayayya tana kewaye wajen. Kamar daga sama tana yin kwana ta wajen Lotions ta yi karo da mutun. Dankareren wayar dake hannunsa ne ya faɗi kasa. Ba tare da ta ɗago ta kalli wanene bane ta duka ta ɗauko mishi wayar. Ɗagowa da zata yi da nufin ta mika mashi suka yi 4 eyes da shi. Yauma dai kamar ranar, yana sanye da bakar glass a idanunsa, haka zalika wankar fararen kaya ne a jikinsa, sai suka yi iri ɗaya da ita. Ganin shi ne yasa ta ɗaure fuska sosai tamkar hadari, rai a matuƙar ɓace ta saki wayar tasa ta sake faɗuwa kasa. Kallon up and down ta yi mashi kafin ta ja keken sayayyarta ta raɓa gefensa ta wuce abinta. Shiru ya tsaya, ya kasa dakatar da ita, ya kuma kasa duƙawa ya ɗauki wayarsa, tunani yake yi a kan abin da ya kamata ya yi wa wannan yarinyar, dan ta yi mashi abin da ko iyayen da suka haife shi basu taɓa yi mashi ba, babu wanda ya taɓa marin shi sai ita, sam bai kamata ya kyaleta ba, kamata ya yi ya mata hukuncin da sai ta gwammaci mutuwa a kan shi!!. Ya jima tsaye a wajen yana tunani kafin ya sa kai ya wuce. Isa da takama haɗe da jin cewa cikin narkakkun dukiya yake kwana ga uban girman kai ta hana shi ya tsugunna ya ɗauki wayar tasa. Ficewa ya yi daga wajen zuwa wajen motarsa. Wasu jibga jibga bodyguards guda biyu masu sanye da black suit ne tsaye a bakin motar tasa, komai da suka sanya a jikinsu black color ne. Yana zuwa ya yi musu umarni a kan su tafi, sai wani huci yake yi, zuciyarsa na saka mishi abubuwa da dama da zai yi wa gwaggo dan ya ɗauki mataki. Ita kuwa sayayyarta ta yi sosai, sannan ta wuce wajen biyan kuɗi, sam bata sake bi ta kansa ba, tama mance da cewa sun haɗu a nan. Bayan an gama yi mata lissafi ta basu Atm card dan su ciri kuɗin nasu. Bayan an gama komai ma'aikatan wajen suka kwasa mata kayan zuwa wajen motarta, da haka ta wuce izuwa gida. Da daddare Cherish ta zo suka sha hira tare da ciye ciyensu. A gidan Cherish ta kwana, sai takurawa Gwaggon take yi da maganar Abbi, ita kuwa gwaggo da ta gaji, sai ta bata number Abbin na Nigeria, dan ta daina damunta!. Washegari haka suka shirya zuwa school, a tare suka wuce a motar gwaggo, Cherish ta bar motarta a gidan na gwaggo. Kamar dai kullum bayan sun fito daga lecture, kayan cima suka je suka sayo, a in da suka dawo garden suka zauna. Suna hira suna ci har suka kammala, sannan suka miƙe dan su koma gida. Rayuwarta ita da Cherish gwanin birgewa, kullum idan sun zauna sai ta yi ta bawa Cherish ɗin labarin ƴan uwanta tare kuma da nuna mata hotunansu. Ita ma Cherish ɗin tana yawan bata labarin ƴan uwanta da hotunansu. Ainahin Cherish ƴar kasar China ce, karatu ita ma ya kawota nan, tana da kirki fiye da tunanin mai tunani, gata da son barkonci da dariya, tana da ɗan shekaru, dan ta girmi Gwaggon ma a shekarun. Washegari suka je school a lokacin zasu fara rubuta exams, sun sha karatu sosai, dan sam basu wasa, yau kowa ka gani a department nasu, zaka ganshi yana rike da handouts sosai, dan kowa dai yasan yanda karatun likita yake, ba karatu ne na wasa ba, sai masu ƙwaƙwalwa da basira sosai. Suna tafiya suna hira, haka suka nufi cikin department ɗin nasu. Kasancewar gwaggo girman Russia ce ita, duk cikin turawan ta taso, sai ya zamana dressing nata sak nasu, tamkar ba musulma ba, a lokacin kuma da gaske bata zauna a Nigeria ba, sun dawo bai fi ta two months ba ta wuto Washington DC, so babu wani al'ada da yake tattare da ita face na turawar Russia, haka zata saki gashi ba ɗankwali abinta, duk da cewa Naurat tana iyaka bakin kokarinta wajen ganin ta basu tarbiya duk da ita ma tubabbiya ce, amma tana ƙoƙarin sosai, kuma ita kanta Brr Naurat ɗin a lokacin dressing na turawar take yi, so ba zaku ga laifin gwaggo a wannan lokaci ba!. Sun zo zasu shiga class nasu, shi kuma Dr William yana fitowa, hannunsa na rike da wata shegiyar tsadaddiyar laptop da kuma takardu, sai sauri yake yi, hakan ce ma tasa bai mayar da laptop ɗin cikin jakarsa ba, da alama wani wajen mai mahimmanci zai je. Karo suka yi da gwaggo a in da gabaɗaya abubuwan dake hannunsa harta wayarsa suka zube kasa. Hakan tasa hankalin jama'a ya yo kansu. Har wa yau idanun Dr William na sanye da wata shegiyar bakar glass na manyan yara masu class. Haka kawai tun bai ɗago kai ya kalleta ba ya ji cewa duk yanda aka yi ita ce. Ita ma Gwaggo duk da ta buge da faffaɗar kirjinsa ta yi baya tana ɗan goge kanta, bata sami damar ganin face nasa ba, amma ta ji a jikinta shi ne, saboda tsadadden ƙamshin perpume nasa wanda bata taɓa jin irinsa a jikin kowa ba sai shi ɗin. Ya fita tsawo nesa ba kusa ba, duk da take doguwa, amma Dr William yana da tsawo sosai, ga kuma cikar halitta, hakan yasa kanta ya bugi tsayayyar kirjinsa har ta ji ɗan zafi. Bakin ciki ya hana Dr William ɗagowa ya kalleta, ita kuma tsoro ne ya hanata ɗagowa ta kalle shi, tana tsoron ta ɗago ta ji saukar mari a kuncinta, ba karya tana bala'in tsoronsa, amma saboda karfin hali, da dakiya na kada a rainata, sai ta daure ta ɓoye tsoron. Cherish ce ta ce mata ta duka ta kwashe mishi kayansa ta bashi kila zai yafe mata. Kafewa ta yi a kan wlh bai isa ta tsugunna ta kwashe mishi kayansa ba, ya yi kaɗan wlh, dama haushinsa take ji kamar ta shake shi ya mutu. Abinku da babban makaranta, har wasu sun ɗaukesu a video. Tunani yake yi a kan me zai yi wa yarinyar nan wanda zai kuntatawa rayuwarta?!. Can wani tuni ya faɗo mishi a kan ya sanya a ɗauko mishi ita kawai ya yi mata fyaɗe, ya yi mata kaca kaca kuma ya ɗauketa a video ya turawa duniya, daga nan ba zata sake shiga gonarsa ba. Na'am ya yi da wannan shawara da zuciyarsa ta bashi, hakan tasa ya sanya kai ya wuce ba tare da ya ɗago ya kalli face nata ba, ya bar laptop da sauran takardun a watse a wajen. Ita ma ganin ya wuce yasa ta sanya kanta ta shige cikin class ɗin. Wasu matasan students su biyu ne suka zo suka kwashe mishi takardu da laptop ɗin nasa, suka bi bayansa da shi. Tun daga lokacin har suka gama rubuta exam suka fito, sam bata ga ko wulkawar mai kama da shi ba, hakan yana nufin shi bai ma shigo class ɗin ya rubuta exam ɗin ba. Bata san cewa tabbas ya shigo kuma ya rubuta ba, dan fa baya wasa da karatu, ga wani azababben kaifin ƙwaƙwalwa da Allah ya yi mishi, ɗan baiwa ne sosai. Bayan sun kammala suka wuce wajen sayan kayan kwalam kamar yanda suka saba. Duk abin da suke yi yau basu san ana ganinsu ba, ya sanya a saka mata idanu har lokacin da zata bar school ɗin, idan ta bar school ɗin ma za'a bi bayanta zuwa gida, dan a gano mishi address ɗinta, ya sha alwashin yau sai ya yi mata fyaɗe! Kuma fyaɗen ma gagarumi na mugunta ya yi niyar yi mata, duk da bashi da tabbacin virgin ce ita, dan su Turawa dama ba lallai ne ka sami budurwa virgin ba, musamman idan tana da saurayi, ai kuma shikenan. Amma dai ya yi niyar ko ba virgin ba ce ita sai ta gane shari ruwa ne, zai ɗanɗana mata bakar azaba kuma ya yi mata video!!. Sam ita bata kawo komai a ranta ba, bayan sun koma gida, tare suka wuni da Cherish har zuwa yamma. Sannan Cherish ɗin ta ce mata zata je gida dan akwai abin da take son yi. Okey ta amsa mata a in da suka yi sallama bayan sun rungumi juna tare da sumbatar juna kamar yanda suka saba, suna Kaunar junansu sosai, kuma suna girmama juna, ƙawancensu cikin gaskiya da amana suke yin shi. Da misalin karfe tara na dare, ta gama duk abin da zata yi, kayan jikinta ya cire tare da ɗaura towel ta shiga wanda dan ta yi shirin barci. After some minutes ta fito ɗaure da towel a kirjinta, ga kirjin nasu na gado, breast na ta a cike fam, idan ta sanya kaya sai sun yi kamar zasu fasa rigar, kuma ba wai irin masu cikar munin nan ba ne, a'a irin na Naurat ce, kyawawa ne sosai masu kyan fasali, dukka ita suka gado, haka mafiya yawansu breast nasu yake. A gaban mirror ta tsaya zata shafa Lotions nata, sai sheki kyakkyawar fatar jikinta yake yi, luwai luwai da shi, gata jajir jinin Russians. Wayarta dake palo saman sofa ne ya fara kara, alamar shigowar kiran. Da sauri ta ajiye Lotion da yake hannunta ta nufi palon, sam towel ɗin bai gama rufe mata santala santalan cinyoyinta ba. Cherish ce take kiranta a waya, picking ta yi tare da karawa kunnanta tana ɗan shafa kyakkyawar bakin gashin kanta dake ɗan digar da ruwa. Daga ɗayan ɓangaren Cherish ɗin ta ce ta duba mata shin a gidanta ta manta ɗayar wayarta da hand bag nata ne?. Tana ƙoƙarin amsawa ta ji an danna kararrawar kofar, kai kallonta a kan kofar ta yi. Ba tare da tsoro ko ɗar ba ta nufi kofar. Kasancewar tana waya hankalinta ya rabu gida biyu, sai ta mance bata leƙa mahangar kofar dan ta ga wanene ba, sai kawai ta buɗe kofar tana gayawa Cherish ta cika watsar da abubuwa, ya kamata ta rinƙa kula da abubuwanta............. Wani irin mahaukacin birki ta ja da maganar nata tare da sake wayar ta faɗi a kasa saman tiles ɗin, nan take wayar ta tarwatse, dan mummunar faɗuwa ta yi. Ba komai ne ya ja mata wannan razana ba face ganin Dr William a tsaye a bakin kofar!. A tsananin razane ta fara kallon shi from head to toe. Pajama ce launin white color a jikinsa. Abin da ya fi bata mamaki shi ne dogon baƙin gashi siɗif mai laushi da tsantsi sai sheki yake yi da ya sake har bayansa, dama yana tara gashi har haka ne? Ta tambayi kanta, bata taɓa lura da gashin ba kasancewar yana ɗaureta a bayan wuyarsa. Ta yi tsananin razane na ganin blue eyes nasa, ga shi kuma dare ne, kun san da daddare kuma yanda idanun suke, har wani kara kyalli suke yi. A koda yaushe ta haɗu da shi yana sanye da black glass a fuska, bata taɓa ganin ainahin kalar kwayar idanunsa ba sai yau, abin ya tsoratata. Daurewa ta yi cikin dakiya ta ce mishi lafiya? Me yazo yi a gidanta?. Tana magana voice nata na rawa, tamkar zata saki fitsari a wando, saboda tsoro, amma ta daure ta ɓoye tsoron. Shigowa cikin palo nata ya yi tare da mayar da kofar ya rufe har da murza key. Tamkar ba shi ba, sam yaki buɗe baki ya yi magana, duk da cewa dama tun ainahi bashi da yawan magana sam, baya son hayaniya. Ganin ya rufe kofar ya murza key ne yasa ta wage baki zata yi mishi ihu. Da sauri ya toshe mata bakin nata tare da kama hannayenta dukka biyu ya mayar da su ta bayanta da hannunsa ɗaya, dan ya samu ya ɗaure hannun nata tare kuma da ya kaita kasa ta zube a kan gwiwowinta!. Ƙoƙarin kwace kanta ta fara yi da iya karfinta, sai dai ina ya fita karfi nesa ba kusa ba, da hannu ɗaya ma idan ya riketa ba zata iya kwacewa ba. Da ya ga zata bashi matsala sai ya sanya hannu a cikin aljihun wandonsa, ya ciro wata farar handkerchief, fara tas da ita. A daidai sai tin face nata ya kawo handkerchief ɗin a in da ya.............. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E2 Ƙoƙarin kwace kanta ta fara yi da iya karfinta, sai dai ina ya fita karfi nesa ba kusa ba, da hannu ɗaya ma idan ya riketa ba zata iya kwacewa ba. Da ya ga zata bashi matsala, sai ya sanya hannu a cikin aljihun wandonsa, ya ciro wata farar handkitchef, fara tas da ita. A daidai sai tin face nata ya kawo handkitchef ɗin a in da ya ɗaure mata baki da shi. Bayan ya ɗaure ne sai ya kama hannayen nata da kyau tare da fara ƙoƙarin murɗesu baya, dan ya ɗaureta gam ya yi abin da zai yi. Tun da ya shigo ko A bai furta da muryarsa ba, tamkar kurma. Da kafarsa ɗaya ya kwashe kafafunta ta zube kasa a saman gwiwowinta, har lokacin bata dai'na yunkurin kwatar kanta ba, ga shi babu halin yin ihu. Haɗe kafafun nata ya yi a in da ya takesu da kafarsa ɗaya, dan ta kwanta shiru a kasar. Amma ina, da yake hannunta ba'a ɗaure yake ba, sai ta yunkura zata miƙe. Ganin hakan tasa sai ya take mata wuya da kafa ɗaya, hakan tasa dole ta yi sanyi, ta hakura ta kwanta shiru gudun kada ta illata kanta, koma ta kashe kanta, dan yanda ya taketa ɗin nan ba zata iya kuɓuta ba, sai dai ta illata kanta kawai. Rigar jikinsa ya fara cirewa kafin ya fito da wata ƴar ƙaramar camera da yake son ɗaukarta video da shi. Kunna ta ya yi, daga in da suke ya miƙa hannu, ya ɗaura camerar a saman sofa ta yanda zata ɗauki ita gwaggo amma ban face nasa. Bayan ya cire rigar jikinsa sai ya zame kafafun nasa daga wuyar tata tare da cire wandonsa. Tsabar ta taku a wajensa, ko motsawa ta kasayi, da kyar take numfashi. Damko kafafunta ya yi bayan ya kammala cire wandon ya rage daga shi sai short. Sake gyara camerar ya yi kafin ya hau kanta da nufin ya yi abin da ya zo yi. Sai a lokacin ta fara dawowa cikin hayyacinta, ƙoƙarin ture shi ta fara yi, shi kuma yana ƙoƙarin cire towel na jikinta. Ganin ba zata iya ture shi daga kanta ɗin bane yasa ta ɗaga idanunta sama, tana hawaye ta fara magana kamar haka. "Ya Ubangiji ina tawassuli da sunanka tsarkaka, na sani babu wanda ya isa ya yi mini abin da baka kaddara mini ba, babu kuma wanda ya isa ya hana abin da ka kaddara mini, ya Allah dan darajarka da karfin mulkinka, kada ka bari wannan bawa naka ya buɗe abin da ba hakkinsa ba, idan har musulcina gaskiya ce, dominka kuma nake yi, to ya Allah ka kare mini mutuncina! Na baka amanar kai'na, Allah ka jikaina, ka ji tausayina, bani da wayo bani da dabara, kana gani babu abin da nayi wa wannan azzalumi zai zalunceni, ya Allah tun daga farkon Alkur'ani mai girma har karshe wanda ta kasance maganaka ne a ciki, ya Allah babu a in da kayi alkawarin tallafawa azzalumi, Allah ka fini sanin cewa shi azzalumi, ina mai rokonka da tsarkakekkiyar zuciya da kuma yakinin kai kaɗai zaka kareni daga zaluncinsa, ka kare ni ya Ubangijin sammai da kassai!". Sai zuba adduarta take yi a cikin zuciyarta cike da tawassulin Allah zai karɓa mata, tana ta kuka hawaye wani na bin wani, sam tama dai'na jiyo abin da Dr William ɗin yake ƙoƙarin yi mata, hankalinta har ya fara barin jikinta saboda nutsawa da ta yi wajen adduo'i da take yi. Yana ƙoƙarin shigarta sai kuma ya tsaya cak, tamkar wanda aka yi wa allura, haka ya ji a jikinsa, nan take jikinsa ya mutu, ji ya yi wani irin mugun tausayinta ya shige shi lokaci guda. Dawo da kallonsa a saman face nata ya yi, sai kuka take yi babu kakkautawa. A hankali ya sauka daga jikin nata ya koma gefe yana kallonta. Jin nauyi ya bar jikinta ne yasa ta dawo cikin hayyacinta. A hanzarce ta zaro idanunta waje sosai. Ganin ya sauka daga kanta ne yasa ta yunkura da iya karfin da ya rage mata. A ɗari ta miƙe tsaye dan ta gudu. Wannan miƙewa da ta yi tasa ya ji wani irin azababben sha'awarta ta motsa mishi kuma, abin ku da shaiɗan, nan take ya ji karfi ya zo mishi. Cikin zafin nama shi ma ya miƙe tare da tare gabanta. Har lokacin bakinta a toshe, rikota ya yi ta kafaɗa. Duka ta fara kai mishi tare da ƙoƙarin juyawa ta gudu cikin ɗaki tun da fita waje dai ya gagara. Shi kuwa hannunta ya fara ƙoƙarin kamawa dan ya ɗaure. Yana ƙoƙarin ɗaure mata hannun nata ne ta juyo da karfin gaske a in da ta faɗa saman faffaɗar kirjinsa. Wani irin azababben kifiya na wani yanayi ne ya caki kahon zuciyarsa. Wani irin diff ya ji komai ya ɗauke mishi na wucin gadin, sakamakon saukar kyawawan tula tulan breast nata da ya ji a jikinsa, ga shi kuma shima babu kaya a jikin nasa, sai short. Ita kuwa dafa kafaɗunsa ta yi tare da barin jikin nasa, a hanzarce ta nufi kofar fita, dan ta gudu ta bar gidan, tana tafiya tana ƙoƙarin kwance handkerchief da ya ɗaure mata baki da shi. Kamar daga sama taga mutun a gabanta, har lokacin bata gama kwance handkerchief ɗin ba, ba halin ta yi mishi ihu. Zuba mata idanu ya yi yana kare mata kallo from head to toe, tun da suke haɗuwa bai taɓa tsayawa ya kalli ya face nata yake ba, sai yau. Wani baƙon yanayi ya ji a tattare da shi, ji ya yi ba zai iya yin abin da ya kawo shi ɗin ba, ya ji ma ko wani ne ya zo zai yi mata hakan, to fa sai in da karfinsa ya kare, zai tsaya mata sosai!!. BA DOLE KA TSAYA MATA BA, AN GAYA MAKA ADDU'A WASA NE? ALLAH AI YA WUCE TUNANIN MAI TUNANI, DUK WANDA YA CE YA MIƘA LAMURANSA GA ALLAH, TO ALLAH KUMA ZAI KULA MISHI DA KOMAI, NAKA WASA NE DR WILLIAM, ALLAH IDAN KA YARDA ALLAH SHI YAKE YIN KOMAI, TO FA KAI DA BAKINCIKI A RAYUWARKA KUN YI HANNUN RIGA, ALLAH UBANGIJI KA IYA MANA DA IYAWARKA, MU BA ZAMU IYA BA, BAMU DA TSUMI BAMU DA DABARA!!. Ganin face nata yasa ya faɗa zazzafar soyayyarta. Kyafta idanunsa sau biyu ya yi yana mai cigaba da kallonta. Ganin hakan yasa a guje ta raɓa gefensa dan ta wuce ta fita waje. A hanzarce ha riko hannunta ta sama wajen gwiwar hannu. Fisgota da karfi ya yi, luuu ta tafi ta faɗa jikinsa. Zubawa face nata idanu ya yi na ƴan mintoci kafin ya kai hannu ya kwance mata handkerchief ɗin daga bakinta. Karo na farko da ta saurari zazzaƙar muryarsa da kyau, a in da ya ce mata ta yi mashi shiru, shi babu abin da zai yi mata. Dogon numfashi ta ja tare da sauke nauyayyar ajiyar zuciya, tsabar jin sanyi a ranta da ta yi na jin ya ce ba zai yi mata komai ba, bata ma san time da ta kwantar da kanta a saman kirjin nasa ba, sai sauke ajiyar zuciya tare da nisawa take yi. Shi kuwa, ta kara gefa shi cikin yanayi mai wuyar fita, ga shi daga ita sai towel, kasa jurewa ya yi, sai da ya sanya hannu ya rungumota da kyau a jikin nasa. Jin hakan yasa ta yi kokarin barin jikin nasa. Amma sam bai saketa ba, ya kankameta sosai tamkar mallakinsa ce ita. Da ɗan ɗaga murya ta ce mishi lafiya?. Muryarsa can kasa kasa yana sarkewa, ya ce mata babu komai. A takaice ta ce to ya saketa, ba musu ya saketa ɗin yana binta da idanu. Da sauri ta wuce izuwa cikin bedroom nata dan ta sanya kaya. Binta da kallo ya yi, yana kallon yanda mazaunanta suke juyawa idan ta taka kafarta. Sai da ta kurewa ganinsa ne ya sauke nauyayyar ajiyar zuciya tare mai da kayansa da ya cire a jikinsa, sannan ya koma saman sofarta ya zauna. A hankali ya jingina kansa da jikin head na sofar tare da lumshe idanu yana jin wani irin kaunarta daga kallon farko tana shigar shi. Ya kai 20 mins a zaune a wajen yana tunani. Kamar daga sama ya ji zazzaƙar muryarta tana faɗin "To me ka zo yi a gidana? Ya kuma baka tafi ba?". A hankali ya waro idanuwansa da suke ja sosai a kanta. Tana shirye cikin kayan barci riga da wando pink color masu kyau. Kirjinta kawai ya zubawa idanu ya rasa amsar da zai bata. Muryar tata ce ta sake katse shi da cewa, lafiya yake kuwa?. Bai san time ɗin da ya ce mata "Please can i have a green tea?". Shiru ta yi tana ɗan tunani. Tamkar zata ce mashi babu, sai kuma ta kasa faɗin hakan, dan ita mafa, tun a ranar farko da ta fara ganin shi ta faɗa mishi, ta ji tana son shi, kawai dai bata bawa hakan dama bane yasa bai yawaita a cikin zuciyarta ba, amma kam ba shakka ta faɗa!. Wucewa izuwa kitchen ta yi ba tare da ta sake ce da shi uppan ba. Green tea ɗin ta haɗa mishi, ita kuma ta haɗa nata black tea. A saman wani kyakkyawan plate ta jere two cups ɗin, cikin natsuwa ta ɗauko tare da fitowa zuwa palon. Yana zaune a in da ta barshi, bai ko motsa ba. Kawo mishi plate ɗin saitinsa ta yi dan ya ɗauki tea ɗin nasa. Ba musu ya ɗauka tare da ce mata thank you. Jinjina mishi kai ta yi ta wuce zuwa saman sofa dake ɗan nesa da shi ta zauna. Cikin natsuwa ta fara shan tea ɗin nata. Sai kallonta yake yi, ya kasa shan nasa. Sarai ta lura da hakan, amma sai ta basar ta cigaba da shan nata. After some minutes, ta gama shan nata tsab, shi kuwa rabi ya sha, dan dama ba tea ɗin yake so ba, mai tea ɗin yake son ya yi ta kallo. A nutse ta ce mishi to ya tafi gidansu mana, tana so ne ta kwanta dare ya yi. Har lokacin da akwai tsoron shi sosai a kwance a cikin idanuwanta. Zuba mata idanu ya yi na ƴan mintuna kafin ya fara magana cikin sanyin murya. "Dare ya yi sosai, kuma ni ina jin tsoron hanyar komawa, ga shi ban zo da mota ba". A shagwaɓe sosai ya yi maganar. Bata san time ɗin da dariya ya kubce mata ba, wai dare ya yi sosai yana jin tsoron hanya, lallai ya iya tsara magana, har da wani shagwaɓe murya, ko waye ya koya mashi shagwaɓa kuma? Ta tambayi kanta. Ta sani ba wani tsoron hanya, kawai iskanci ne irin nasa, da ba da kafafuwansa ya zo ba?. "A'a babu komai a hanya kawai ka tafi". Ta faɗa tana kwaikwayon muryarsa na shagwaɓar da ya yi maganar. Ɗaura cup ɗin tea ɗin ya yi a saman table da yake kusa da shi. A nutse cikin shagwaɓa ya ce "A'a, Please ki bari na yi ta kallonki, kin ji ko?". Zaro dara daran idanun nan nata ta yi, tana faɗin "Kallona kuma?!". Gyaɗa mata kai ya yi tare da gera ɗaya. Cool murmushi ta sakar mishi kafin ta ce "Meyasa to?". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Because you are so cute, very very beautiful baby!". Oho god, jin ya yabeta tuni ta kara afkawa tekun son shi, dan ya fi karfin kogin so wannan, sai dai teku. Sam bata ma san time ɗin da ta ce mishi "Same, you are very very beautiful, handsome guy, i really like your eyes color". Ɗan zaro mata su ya yi. Da sauri ta runtse idanunta dan sun bata tsoro ganin yanda suke kyalli. Muryarsa ta tsinkayo cikin kunnenta yana faɗin "I really like your eyes, your lips and your everything". Waro idanuwan nata waje ta yi tana kallon yanda ya jingina kansa da jikin head na sofar yana binta da shanyayyun idanuwansa tamkar wanda ya yi shaye shaye. Abokan faɗa sun shirya yau kam, har ma suna ƙoƙarin zama cikakkun masoya na gaskiya.......KADA KU YI COMPARING RAYUWAR NAN NIGERIA DA NASU NA CAN, DAN AKWAI MUGU MUGUN BANBANCI, RAYUWARMU DA TASU BA ƊAYA BACE SAM, SO KU DAI'NA KALLON RAYUWAR TRIPLETS DA FAMILYNSU, MA'ANA SU DR WILLIAM KENAN, KU DAI'NA KALLONSU TA SIFFAR TAMU RAYUWAR, DAN BA HAƊI, AL'ADU DABAN DABAN!!. Hannu ya miƙa mata a kan ta zo, bata musa mishi ba dan kada ku manta girman Russia ce ita ma, da ita da shi duk zani ne ta tadda muje, tafiyar duk ɗaya ce. Miƙa mishi nata hannun ta yi. Cikin nutsuwa ya jawo hannun nata alamar ta zo gare shi. Miƙewa ta yi tare da nufarsa. Tana ƙoƙarin zama a gefensa ya yi saurin zaunar da ita a saman cinyarsa. A tare suka sauke nauyayyar ajiyar zuciya. Hannunsa dukka biyu ya ɗaura a saman shafaffen cikinta tare da ɗan jawota baya ta kwanta a saman kirjinsa. Ɗan leƙo face nata ya yi yana faɗin "You are the best and you are special beb!, Kuma rigimammiya". Ɗan juyowa gare shi ta yi, suna ɗan fuskantar juna kafin ta ce "Why you say that?". Ɗan shafa shafaffen cikin nata ya fara yi a hankali yana haurawa sama kafin ya ce "Ban taɓa tunanin zan kula mace ba a rayuwata, infact ni ban san menene ma yake sanyawa a so mace ba, bani da aboki, bani da kawa, only my brother Herry, shi ne kawai na kusa da ni, i have one sister, Josephine, even her ba zan ce maki ga yanda jikinta yake ba a yanzu, because in kin ganta a area da nake ma, to dad ne ya ce ta kirani or something like that". Ɗan kwanciya ta yi a gefen kirjinsa tana faɗin "But why some peoples are calling you dangerous boss?. In the first place ka nuna mani you are the boss ɗin da gaske, and now kuma naga har da shagwaɓa ashe ka iya?". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Ni ruwa biyu ne ai, a gida wajen mum da dad ina yi musu shagwaɓa, amma idan na baro wajensu, ba zaki taɓa cewa ma ina yin magana ba, bare shagwaɓa, kin taɓa kallona a class ina magana da wani ne? Or ina surutu?". Girgiza mashi kai ta yi alamar a'a. Shafa gefen lallausan kumatunta da ɗayan hannunsa ya yi yana faɗin "Haka nake to, bana magana da mutane, kuma sunan dangerous, wait small, zaki san daga ina sunan ya samo asali kin ji?". Jinjina mashi kai ta yi tare da ɗan yunkurawa zata bar jikin nasa. Da sauri ya riketa yana kallon face nata. "Where are you going?". Da hannu ta nuna mashi saman sofarta ba tare da ta yi magana ba. "Saman jikina ɗin babu daɗin kwanciya ne?". Ya tambaya yana mai do da ita jikin nasa. Girgiza mashi kai ta yi kafin ta ce "Akwai daɗi, amma ai kaga babu kyau ko? Mum ta hanani yin hakan". "Why mum zata hanaki kuma? Is there any problem akan hakan?". Ya yi tambayar da mamaki bayyane karara a saman face nasa, dan su rungumar juna, kiss, da sauransu ba wani abin bane a wajensu, shi ne yasa yake mamaki da ta ce zata bar jikin nasa. "No any problem, kawai dai yin hakan kuskure, mum ta ce addini ya yi hani da hakan, so ni ba wani ilimin addinin nake da shi sosai ba, amma na iya karatun Alkur'ani mai girma sosai, saboda shi mum ta fi koya mini, amma dai koma me, is better na yi abin da ta ce koma yaya ne ko?". Maimaita kalmar addini ya yi kafin ya tambayeta ita a wace addin take. "I am a Muslim, what about you?". Ta bashi amsa with her full confidence. Murmushi kaɗan ya yi, wanda da ka gani kasan dole ya ƙaƙalota, dan murmushi bata da gurbin zama a face nasa, duba da yanayinsa ba mutun ne mai fara'a ba sam sam. "Am a Kristen, my name is William". A hanzarce ta miƙe daga jikinsa jin abin da ya ce, bata taɓa tunanin shi krista bane, duba da yanayin irin fuskarsa, yana da face mai kyalli sosai, idan ka ganshi, zaka yi tunanin yana sallah. "Why are you avoiding me like that dan na ce am a Kristen? Shin da kika ce mini ke musulma ce did i do something like that to you?". Girgiza mashi kai ta yi, sai kuma da ya yi magana ta fahimci ta yi kuskure na irin gudunsa da ta yi lokaci guda haka, yin hakan zai sanya ko da yana son shiga addinin musulunci ma, sai ya fasa, saboda zai ce dama haka musulmai suke? Dama basu son wani addini idan ba nasu ba?. Bai san mu musulmai kowa ma muna kaunarsa ba, kuma muna zaman lafiya da shi, addininmu mai sauki ne, addininmu mai ni'ima ne wanda ya bamu damar zama waje ɗaya da wanda ba musulmi ba, mu yi zaman mutunci, kamar da ƴan uwanmu musulmai muke tare, musulmai ne kawai za'a ci hakkinsu kuma su hakura, su yafe, su cigaba da zama da mutun, ai addinin musulunci babu biyunsa a duniya, ya yi ne kawai babu mai musawa sai dai wanda baya son gaskiya. Shiru ta ɗan yi tana ƴan kame kame, ta rasa abin yi. A lokacin sam bata da wani ilimin addini sosai, haddan Alqur'ani mai girma ne kawai gareta, shi ɗin ma ba dukka ba, kuma bata san fasarar ko sururori biyu daga ciki ba, so hakan yasa ta rasa me zata ce mishi, sai dai ƴan kame kame, ilimin boko ya fi yawaita sosai fiye da misali a kanta sama da na addini, matsalar da aka samu kuma shi ne, ita bata wani zauna da su Brr Naurat sosai ba, secondarynta ma, boarding school ta yi, so bata sami lokaci da iyayenta sosai ba, shi ne yasa. Ganin haka yasa shi ya miƙe ya koma saman sofar da take zaune. Kusa da ita ya zauna tare da ɗan riko hannayenta, cikin sanyin murya ya ce "Please kada ki gujeni, kin ji? I really love you the way you are, please love me the way i am, don't be angry because am a Kristen my angel, you hear?". Wani sanyi ta ji a ranta na jin kalamansa, ta ji daɗi sosai, hakan yasa ta ji cewa zata iya janyo shi a jiki har ya karɓi addinin musulunci. Dan haka sai ta juyo da kyau suna fuskantar juna, cikin sanyin murya ta ce "I really love you the way you are, so don't worry!". Sakin hannayen nata ya yi tare da buɗe mata hannu alamar ta zo gare shi. Ba musu ta faɗa jikinsa tana ɗan murmushi, shafa bayanta a hankali ya fara yi yana mai jin daddaɗar yanayi a tattare da shi. "What is your name?". Muryarsa ya daki dodan kunnanta. "A'isha". Ta bashi amsa, ɗan ɗago haɓarta ya yi yana faɗin "Nice nema, but can i call you my angel or my beauty?". Jinjina mashi kai ta yi alamar e. Ɗan kara matseta a jikinsa ya yi tare da sumbatar goshinta. Haka suka kasance suna ta hira dan sanin juna har wajen karfe ɗaya na dare. A nan ne ta ce mishi barci take ji, zata je ta kwanta. A kunne ya raɗa mata a kan cewa tare zasu kwanta a gado ɗaya, Okey ta ce mishi. Miƙewa ya yi da ita a jikinsa a in da ya gyara ɗaukarta da ya yi, ya zamana ya ɗaurata a saman kirjinsa, suka nufi cikin bedroom ɗin nata. Bai sauketa a ko'ina ba, sai a saman gadonta, murmushi ta sakar mashi kafin ta ce ta gode. Hayewa gadon shi ma ya yi, daga ɗan gefen da shi ta kwanta, ya so tambayarta me yasa har yanzu take gudun shi, amma sai kuma ya basar bai tambaya ba, sai ma ya juya mata baya, dan ya lura tamkar tana cikin damuwa na kwanansu gado guda. A can gidansu kuwa, su Uncle Herry sai neman shi suke yi, sun je bedroom nasa baya nan, hankalin daddynsu ya tashi, ga shi ya bar musu wayarsa ma a gidan, mum ɗinsa har da kuka ta rinƙa yi, tamkar yaro ne karami William ɗin, mutumin da ya kai 24 years a duniya, amma sun ɗaga hankalinsu har haka, da yake shi gaskiya ba mai yawan fita bane na farko, na biyu idan ma zai je party ko gidan rawa, yana gayawa mum ɗin nasa shi fa ya tafi waje kaza, kuma ba zai dawo ba sai time kaza, idan ya ce hakan, to time ɗin na yi zai dawo abinsa, hakan tasa suka ɗaga hankalinsu sosai da basu gan shi ba. Shi kuwa shiru ya kwanta ya kasa yin barci, baya son gaya mata ne or ta gane, amma ji yake yi tamkar a cikin keji yake, gidan nata ya yi mishi ƙarami over, duk ya takura, dan fa su gidansu, gida ne na madarar kuɗi, babban yayan daddynsu shi ne president mai ci a yanzu, ga uban kuɗi da suke da shi na wuce misali, gidansu aljannar duniya ce guda, bedroom nasa kawai ya kai girman gidan nata gabaɗaya har da palo da kitchen, so bai saba da ƙaramin waje haka ba, duk sai ya takura. Ita ma ta kasa barci saboda tsananin tsoronsa, sai taga kamar idan ta yi barci, zai yi mata wani abin, dan fa gani take yi kamar fyaɗe ya zo yi mata kamar yanda ya nuna mata tun farko. After some minutes, can duniya ta kara yin shiru sosai. Lallaɓawa ta yi ta miƙe zaune, a hankali ta matso kusa da shi, cikin sanɗa ta ɗan leƙo fuskansa, dan ta gani ko ya yi barci. Tana so ne ta yi barci, amma ta kasa, saboda tsoro, shi ne ta zo ta gani ko dai ya yi barci ita ma ta samu ta yi. Ganin idanuwansa a rufe yasa ta ɗan koma ta zauna zuciyarta na yi mata wasi wasi a kan bai yi barci ba, yana jiran ta yi barci ne kawai ya hake mata. Jin abin da zuciyarta yake raya mata ne yasa ta sake lallaɓawa ta leƙo face ɗin nasa. Duk abin da take yi yana jinta, sai dai bai motsa ba, dan shi ma yana son ta sami nutsuwa ta yi barci. Amma ina abin ya ci tura, sake leƙo face nasa a karo na uku ta yi, dan ta kasa sakin jiki ta kwanta, ta kasa yarda da ya yi barci. Jin haka yasa ya bari time da ta leƙo face ɗin nata a karo na ukun, sai ya jawo hannunta da ta kafa a jikin mattress ɗin ta gaban face nasa dan ta sami damar leƙa shi da kyau. Jawo hannun ya yi tare da juyowa gareta ta faɗa saman kirjinsa. Rungumeta sosai ya yi tare da juyowa da ita da kyau da kyau suna fuskantar juna. "My beauty, why zuciyarki bata yarda da ni ba?". Girgiza mashi kai ta yi tana faɗin ba komai. "Seriously babu abin da zan yi miki, idan ina son na yi miki wani abin, ki sani tsab zan iya yi ba tare da son ranki ba, amma i can't do that, so feel free and sleep kin ji?". Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke tare da ɗaura kanta a saman gefen kirjinsa, a hankali ta lumshe idanu bayan ta ɗaura hannunta a saman wuyarsa, ta ɗan saƙalo kenan. Shi ma nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, sai a yanzu ne ya ji zai iya yin barci, ji ma ya yi tamkar kwanciyar nan da ta yi a jikinsa, kamar ta karawa ɗakin nata faɗi da girma ne, so sai ya ji yanzu yana normal. Hannu ya ɗaura a saman bayanta tare da lumshe idanu shi ma. Ba jinawa barci ya yi awon gaba da su.......ASUBA TA GARI. Da yake bata yi barci da wuri ba, har wuraren uku suka sami barci, sai bata iya tashi sallar asuba, makara ya kamata, shi dama ba sallah yake yi ba!. Sai misalin karfe 7 na safe ta farka, a hankali ta waro idanunta, kai tsaye sai saman kyakkyawar face nasa. Sai zuba barcinsa yake yi hankalinsa a kwance, ɗan shafa lallausan kumatunsa ta yi tare da yunkurawa zata mike. Duk motsinta yana ji, dan sam bashi da nauyin barci, tun farkawarta ya farka shi ma. Jin zata bar jikinsa ne yasa ya waro idanunsa a hankali shi ma, kai tsaye sai saman face nata. Kasa kasa da murya irin na mai barci ya ce "Good morning my beauty". A hankali ya motsa laɓɓan nasa wajen furta maganar. Cool murmushi ta sakar mashi kafin ta amsa mishi da "Morning my Dr, how was your night?". Bai amsa mata ba, sai dai ya tsareta da idanu yana kallonta. Ganin hakan yasa ta yunkura zata miƙe, matsowa ya yi kusa da ita sosai tare da rikota. Can kasan makoshinsa ya furta "Can i have a one kiss my beauty?". Ɗan ɗaga idanunta sama tamkar mai tunani ta yi. Bai jira ta bashi amsa ba ya matso kusa da ita sosai tare da haɗe fuskokinsu, kafin ta yi wani yunkuri ma har ya fara kissing nata abinsa. Wani irin duniya suka lula dukkansu biyu, Baturen mutun akwai shegen iya soyayya, ya yi mata wayo sai bata hot kiss yake yi. Haka ya matseta a jikinsa tare da fara shafa mazaunanta da tun jiya suka tsole mashi idanu, kuma suke ɗaukar hankalinsa, cikin kwanciyar hankali yake yin komai. Karar danna kararrawar kofa ce ta dawo da shi daga duniyar da ya afka. Da kyar ya iya raba bakinsa da nata, idanuwansa sun yi jajir kamar wuta, murya kamar wanda ya yi shaye shaye, a hankali kasa kasa ya furta yana zuwa bari ya duba wanene. Okey ta amsa mashi tare da miƙewa ita ma ta nufi toilet jiki ba kwari. A nata tunanin Cherish ce ma, ta san ita kaɗai ce take zuwa mata gida without a permission. Toilet ta shige, shi kuma ya sauko ya nufi palo. Yana buɗe kofar suka yi ido huɗu da daddynsa, mummynsa, Uncle Herry da kuma ƴan'sanda guda biyar, masu sanye da kakinsu a jiki, jajir da su kamar tsada. A lokacin mummynsu tana da cikin Tyson, wato Tga kenan. Hakika babu maraba a tsakanin face ɗin Dr William da mummynsa, harta blue eyes ɗin nata ne ya ɗauko, kyakkyawar mace ce na wuce misali, shiyasa dukkansu suke kyawawa tamkar su suka yi kansu, tana da tsawo sosai, har ta ɗara daddynsu tsawo, a takaice dai wannan blue eyes da tsantsar kyau na wuce misali, tsawo zara zara da su, a wajen mummyn Dr William suka gado shi, ga black cuirly hair sosai, gashin nata kuma har kugunta ta baya. Da sauri mum ɗin nasa ta ce "My son, what brought you here? What are you doing in this dirty place? What happened to your eyes?". Harara ya wurgawa uncle Herry dake tsaye a gafe kafin ya ce "What are you doing here Herry?". Tun bai gama rufe baki ba Uncle Herry ya juya ya bar wajen, dan fa yasan ɗan uwan nasa sam bashi da sauki. Dawo da kallonsa a kan dad da mum ɗin nasu ya yi, ɗan ɗaure fuska ya yi yana faɗin "Mum why are you disturbing your self like that? Ni fa ba yaro ba ne, you have to be.........." Katse shi ta yi da cewa lallai shi yaro ne a wajenta, kuma ya zo su tafi gida. Make mata kafaɗa ya yi a kan shi dai ba zai tafi ba, daga karshe ma sai ya ce suje gidan yana zuwa. Sun yi sun yi ya gaya musu me yake yi a cikin wannan kurkukun gidan, local da shi. Amma ina, sam yaki faɗa, sai ce musu ma ya yi, idan basu tafi ba, shi zai yi kuka tun da haka ne. Basu da zaɓi, dole su tafi, dan suna mugu mugun son farincikin ɗan nasu fiye da komai a duniyarsu, su ne nan suka ɓata shi da kuɗi, suka sanya yana yin abin da ya ga dama, ya taka kowa, babu wanda ya isa ya taka mashi birki. Bayan sun tafi sai ya dawo cikin ɗakin, saman bed ɗin ya koma ya zauna yana tunanin abubuwan da suka faru a tsakaninsa da gwaggo tun daren jiya zuwa yanzu, mamakin kansa yake yi, tamkar ba shi ba, mace ta canza shi a lokaci guda. A haka ta fito ta same shi, jikinta na ɗaure da towel white color mai ɗan girma zuwa gwiwa. Binta da kallo ya yi babu ko kyaftawa. Har ta kammala shafa Lotions nata yana ta kallonta, da yake sam ita ma bata san kunya ba, sai ya zamana ko a jikinta, bata damu dan yana cikin ɗakin ba, haka ta shafa duk abin da zata shafa a gabansa kafin ta nufi dressing room na cikin ɗakin nata. Sai da ya ga shigarta dressing room ɗin ne ya sauke nauyayyar ajiyar zuciya tare da jingina kansa da jikin headboard na bed ɗin yana sauke numfashi a hankali hankali. After some minutes. A haka ta fito ta same shi. Shirye take cikin wandon jeans baki da riga mai ƙaramin hannu pink color, ta yi matuƙar kyau sosai, ta ɗaure gashin kan nan nata a tsakiya, sai tashin fitinannen kamshi take yi. Kamshin perfume ɗin nata ne ya daki hancinsa ya sanya shi ɗagowa yana bin in da ya ji kamshin da kallo. Wow ya furta da ɗan karfi tare da ɗaga mata gera ɗaya. Murmushi kaɗan ta yi hannunta na rike da dadduma da hijabi. Ta kusa da mirror ta je ta shimfuɗa daddumar tare da sanya hijabi ta tsaya ta tada sallah. Zuba mata idanu ya yi yana kallon yanda take sallar babu ko kyaftawa. Har sai da ta kammala kaf a kan idanunsa tamkar mai karanta wani abin, bayan ta kammala ne ta miƙe tare da naɗe daddumar ta nufo in da yake zaune. Cikin sanyin murya ta ɗaga mishi gaisuwa tamkar mijinta na sunna. Fuska ba yabo ba fallasa dan baya dariya, haka ya amsa mata. Duba kyakyawan ƙaramin watch dake ɗaure a hannunta ta yi tana faɗin "Dr muna da class karfe 9:30 fa, yanzu kuma 8:30, remain 1 hour, ya kamata ka je gida ka shirya, sai mun haɗu a school ko?". Nisawa ya yi tare da miƙewa tsaye, nan take ta dawo tamkar Rimsha a gaban Lion, dan ya fita tsawo sosai shi ma, kamar dai Lion da Rimsha, gara ma Dr William da gwaggo, ratar shekaru babu yawa a tsakaninsu, shi kuwa Lion ratar shekaru dake a tsakaninsa da Rimsha suna da yawa. 31 to 32 years Lion yake da shi, ita kuma Rimsha 14 to 15 years, kun ga kuwa da akwai rata sosai a tsakaninsu, so gara Dr William da gwaggo. "Bana jin zan iya tafiya na barki, dan ban gaji da ganinki ba". Ya faɗa a sanyaye, shi kansa baya sanin time da wasu kalamai suke fitowa daga ɗan bakinsa nan, bawan Allah ya faɗa tarkon mace lokaci guda, ji yake yi tamkar ba zai iya tafiya ya barta ba. Juya idanunta sama ta yi tamkar mai tunani. Shiru ya yi yana ta kallonta. "Ai zamu haɗu a school ko?". Gera ɗaya ya ɗaga mata ba tare da ya yi magana ba, idanuwansa a shanye kamar wanda ya yi shaye shaye. "Tom shikenan ka je kawai kada ka damu ka ji my Dr?". Dogon numfashi ya ja tare da buɗe mata hannayensa a kan ta zo su yi bye bye. Da sauri ta faɗa jikin nasa tana ɗan murmushi, rungumeta gam ya yi na ƴan mintuna kafin ya ɗan sassauta riƙon nata da ya yi tare da ɗago haɓarta suna fuskantar juna. Rankwafowa kanta ya yi tare da haɗe fuskokinsu. Cikin nutsuwa ya fara kiss nata tamkar matarsa ta sunna. Ko da yake su a wajensu ai lafiya lou ne yin haka, ba wata matsala ba ce. Ya Ubangiji ka hanemu da aikata duk abin da ya zamana ka haramta shi, ka tsaremu da faɗawa taka dokokinka. DA AKWAI DARUSA DA DAMA A RAYUWAR DR WILLIAM DA GWAGGO, HAKA ZALIKA A GABAƊAYA LITTAFIN TRIPLETS KEWAYE YAKE DA DARUSA DA DAMA A CIKINTA MASU AMFANI GA AL'UMMAR MUSULMAI, WANDA DUK ZAN KAWO MUKU SHI A KARSHEN LITTAFIN NAN IN SHA ALLAH, A YANZU MA NASAN KUN KOYI DARUSA DA DAMA SOSAI DA SOSAI, AMMA AKWAI ABUBUWAN DA TUNANINKU BA ZAI KAI KANSU BA HAR SAI NA WARWARE MUKU, KU DAI KAWAI KU KASANCE DA ALKALAMIN PRINCESS TEEMA DAN KU JI KOMAI DALLAH DALLAH. ALLAH KA BANI IKON KAMMALA WANNAN LITTAFIN LAFIYA, KASA NA CIGABA DA RUBUTA MAKU LABARAI MASU AMFANI DA FAƊARKAWA, ILMANTARWA, WA'AZANTARWA, HAR MA DA NISHAƊANTARWA, NA RUBUTA MAKU LITATTAFAN WAƊAN DA BABU SHIRME KO SHIRIRITA A CIKINSU, NA GODEWA ALLAH DA BAIWAR DA YA YI MANI NA RUBUTU, HAKIKA NA SAN LITATTAFAINA BABU SHIRME A CIKINSU, SAI FAƊAKARWA DA ILMANTAR, KUMA SAIDA NE KO MY READERS?. Mayar mishi da martanin kiss ɗin ta fara yi ita ma babu kama hannun yaro, nan take tasa ya fara ficewa daga cikin hayyacinsa. Ba sai na sake faɗa ba, kunsan Turawa da soyayya, akwai iya madarar soyayya zallah. Daga ita har shi kasa tsayuwa a kan kafafunsu suka yi, hakan tasa suka faɗa saman bed ɗin. Mirginawa ya yi a in da ya yi mata rumfa da kirjinsa. Hannu ta tura cikin gashin kansa tana shafawa, shi kuma hannu ya ɗaura a saman breast nata ya fara matsa mata su ta saman riga. Haka suka kasance na tsawon mintuna 20, sosai ya yi romancing nata, sai dai bai yi yunkurin kusantarta ba, dan ta ce mashi bata son hakan, amma ba shakka yana son kusantar tata, kasancewar ya kamu da sonta da tasa baya son ɓacin ranta ne yasa ya hakura ya jure, suka yi iya romance kawai. Da kyar ya iya kyaleta ba dan ya so ba, sai dan time ya tafi, mikewa ya yi daga kanta idanuwansa tamkar wuta saboda ja. Palo ya nufa yana yi mata bye bye tamkar wanda yake cikin maye. Ita ma jiki duk a mace ta mike ba tare da ta canza kaya or something like that ba, ta gyata jikinta kawai ta karisa shirinta na tafiya school. Bayan ta kammala ne ta nufi kofar fita, a nan ne ta ga wayarta a kasa kaca kaca, sai lokacin ta tuna da time da wayar ta faɗi daga hannunta. Duƙawa ta yi ta fara haɗa wayar. A saman table ta ɗaura shi, sannan ta fito hannunta na rike da key ɗin motarta, da kuma wata yar jaka karama, kanta sam babu ɗankwali kamar ba ƴar musulma ba. After some hours. Zaune take a cikin class tana duba wasu handouts dake a gabatan, Cherish bata kariso ba tukunnan. A zahirin gaskiya ba karatu take yi ba, tunanin Dr William kawai take yi, wani sabon son shi ne yake kara shigarta. Idan ka ganta zaka yi tunanin karatu take yi, ita kaɗai tasan me take yi. Ta yi nisa cikin duniyar tunanin da ta afka, kamar daga sama ta ji an rufe mata idanu ta baya. Cool murmushi ta saki kafin ta ce "My Dr me hakan?". A hankali ya zame hannun nasa daga idanun nata yana faɗin "Waye ya ce mani ni ne?". Ya yi maganar yana zagayowa ta gabanta. Sanye yake cikin wasu shegun kaya na manyan yara, crazy jeans ne mai bala'in tsada irin wanda Areef yake son yawan sakawa, sai high neck t-shirt irin wanda Lion yake son yawan sakawa, har wa yau wuyarsa na ɗaure da wanan diamond chain ɗin mai matukar kyau. Yau dai ya saki gashin kansa bai ɗaure ba, kamar kullum black glass ce a face nasa. Abin da yasa suke son saka black glass shi da Lion shi ne, basu son yawan kallo, jama'a suna yawan tsaresu da idanu, dan kalar idanunsu abin so ne da kuma abin ban sha'awa ga mutane, ko a cikin turawa da wuya ka sami mai sky blue eyes masu girma dara dara suna kyalli da kyau tamkar nasu, so jama'a suna takura musu da kallo, hakan tasa suke yawan sanya black glass dan ma kada ayi ta kallonsu. Kusa da ita ya zauna yana ɗan rungumota a jikinsa. Gabaɗaya jama'ar dake cikin class ɗin suna karatu, sai da suka saki ido da baki suna kallonsu, ko da sunan wasa, basu taɓa ganin Dr William yana magana da maza ƴan uwansa bama bare mace, idan ka ji yana magana a school ɗin, to faɗa yake yi da wani, dukan ɗan mutun yake yi, dan fa mafaɗaci ne over ga zafin rai da taurin kai, boss ɗin ne da gaske. Shi kuwa ko kallo jama'ar cikin class ɗin basu ishe shi ba, sai ma hannu da ya sanya ya zame pil ɗin da ta makale gashinta da shi yana faɗin, shi baya son ta ɗaura gashin nan, yau saboda ita yasa bai ɗaure nashi ba, dan haka ita ma ta bar nata a haka. Jan dogon hancinsa ta yi tana murmushi ba tare da ta yi magana ba. Haka suka kasance cikin so da kauna tare da nunawa juna kulawa har Cherish ta kariso ta samesu. Ta ji tsoro kuma ta sha jinin jikinta na ganin gwaggo da Dr William a tare, ita dai ta san kullum cikin faɗa suke, abokan faɗa ne, amma ya aka yi lokaci guda suka zama abokai?. Ta tambayi kanta. Ganin bata da amsa ne yasa ta kariso wajen cike da tsoro da ɗar ɗar. Ko da ta zo kallo wannan bata samu daga wajen Dr ba, tamkar bai san da ita a wajen ba, sai kallon gwaggo kawai yake yi ba tare da ya yi magana ba, dan bashi da yawan magana!. Can ya ciro sabuwar waya a kwalinta ya ajiye mata a gabanta yana faɗin ga wayarta da ya sanyata ta fasa daren jiya. Bin wayar da kallo ta yi, waya ce iya waya, ta haɗu sosai, ga tsada na wuce misali. Hannu ta kai ta ɗauka tana murmushi. Shi dai ban da wannan kallo babu wani abin da yake binta da shi. A takaice haka suka kasance har tsawon shakara ɗaya, soyayya mai zafin gaske ne a tsakaninsu, kullum cikin kara kaunar juna suke yi, a cikin shakara ɗayan nan da suka yi, daga ƴan uwan gwaggo har nasa ba wanda ya san da suna tare, babban abin dubawa a soyayyar tasu shi ne yanda suka saki jiki wa juna, wani lokaci a gidanta yake kwana, suna romancing junansu son ransu, duk da basu taɓa kwatanta saduwa ko da sunan wasa ba, amma fa suna wuce gona da iri a wajen wasannin nasu. A wannan shekara ɗayar ta je gida hutu sau ɗaya, sai dai bata wani jima ba, sati ɗaya ta yi, shi ma a daddafe ta yi shi dan tana kewar Dr, sam hankalinta baya kan mutanen gidan, bata ma lura da Dr Salman ya kara aure ba, kanta na rawa sosai a lokacin, sam bata bi ta kan amarya ba, bata sami su Abba a gidan ba, kuma bata tambayi ina suke ba, dan a tunaninta, suna makaranta, harta daddyn Rimsha lokacin baya nan, shi ma bata neme shi ba, dan ta ɗauka yana school shi ma, bata san cewa yama bar gidan bakiɗaya ba, dan lokacin su Abba sun yi mishi wannan sharrin ya bar gida, daddyn Anaya kawai ta samu a gidan, sai daddyn jelly da yake karami, kullum tana manne da waya a kunne suna hira da Dr, ko kuma tana chatting da shi a Whatsapp, ba dare ba rana aiki ɗaya. Naurat baiwar Allah, tana fama da kanta da wahalar amarya, sam bata ta kansu gwaggon, ko da gwaggon ma ta ji Dr Salman ya yi aure, ko a jikinta, ita sam bata tare da kowa sai Dr. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E3 Haka ta yi hutun sati guda a daddafe ta dawo, ko da zata dawo, sai da Naurat ta yi mata faɗa sosai tare da nasiha mai ratsa jiki, sannan ta bata makudan kuɗaɗe, shi ma Dr Salman lokacin yana cikin hayyacinsa, dan idan baku manta ba, bayan tafiyar daddyn Rimsha sun sake samun jituwa da Na'urat har aka sami cikin Alex. To shi ma ya zubawa gwaggon makudan kuɗaɗe a account nata, tare da yi mata nasiha a kan ta kula da kanta kuma ta ji tsoron Allah a duk in da take. To kawai ta amsa musu da shi, amma sam nasihar bai shiga kunnenta ba. Har ta koma bata haɗu da su Abba ba, kuma bata tambayi ina suke ba, a lokacin yes suna school basu dawo hutu ba, dan idan baku manta ba, dama hutu suka zo gida har wannan abin ya faru a tsakaninsu da daddyn Rimsha, to yanzu sun kowa makaranta. Shi ma daddyn Anaya yana ta fama da school bai bi ta kan gwaggon ba, a takaice dai kowa yana fama da kansa, hakan ce tasa har ta koma ba su haɗu ba GWAGGO Tana dawowa daga hutu suka cigaba da gashi a ɓangaren soyayarsu ita da Dr William, sam bata hana shi ya juyata yanda yake so, ya yi wasa da ita, sai dai daga cibiyarta zuwa sama kawai ta bashi dama, ta hana shi kasan sam, dan tana mutuwar tsoron Dr Salman, saboda shi ma mutun ne mai tsananin zafin rai idan aka yi mishi ba daidai ba, to dan shi take rage wasu abubuwa, take kamewa. Yanzu suna da almost shekara ɗaya da watanni a tare da Dr William, suna zuba soyayarsu, kullum tamkar ranar suka fara haɗuwa, a koda yaushe begen juna suke yi, wasa wasa har suka zama abin kwatance a cikin school ɗin nasu, kowa da su yake kwatance ta ɓangaren soyayya. Sai dai har lokacin fa Dr William dangerous boss ne, dan baya ɗaukar raini, ko kallon gwaggo mutun ya yi sai ya yi mashi hukunci, ba shi da sauki sam. Yau babu school ta gama duk abin da zata yi a gida, ta yi wanka tana shirye cikin wando short zuwa gwiwa, da ƴar ƙaramar riga zuwa kugunta mai ƙaramin hannu. Tana kwance a saman bed nata tana aikin latsa waya, chatting suke yi da Dr William, dan idan ka ganta da waya a hannu, to da shi take magana, ko daddyn Rimsha da daddyn Anaya da suke ƴan lelenta ma, yanzu ta daina nemansu a waya, a baya sai ta kirasu fin awa uku suna hira, dan duk cikin ƴan uwan nata, ta fi kaunarsu sama da komai, dama idan baku manta ba, na gaya muku twins ɗin nan, Azharuddin da Nawazuddeen mugun shiga rai gare su, duk in da suka zauna, sai an kaunace su, aji ba'a son rabuwa da su, to ita ma Gwaggo haka ne, amma yanzu tana manne da Dr William, tama manta yaushe da rabon ta da ta kira gida, ko an kirata daga gidan kuma, sai ta ce musu tana karatun exams, ko dai tana yin wani abin, bata taɓa bawa kowa lokacinta idan ba karatu da kuma Dr William ba. Sai dai abin jin daɗi a tarayyar tasu da Dr ɗaya ne, wato duk wannan soyayya da suke zubawa, sam basu wasa da karatu, suna dagewa sosai, idan Dr William ya zo first, gwaggo ce second, idan ta zo first shi ne second, ma'ana dai duk in da ɗaya ya saka kafa a karatu, to ɗayan ma yana biye da shi, kamar abin haɗin baki, amsoshinsu a Exams ma iri ɗaya ne, dan tare suke karatu, wani lokaci a gidanta yake kwana, su kwana karatu. Rashin wasa da karatunsu shi ne nasarar da suka cinma a soyayyar tasu, kuma shi ne kawai soyayyar tasu bai sa sun yi patali da shi ba. A ɓangaren Dr William ma, iyayensa har sun gaji da tambayar a kan sauyawar da ya yi, yanzu sun zuba mashi idanu ne kawai suna kallon shi, sun yi, sun yi, su bibiyi abin da yake yi, amma yaki basu dama, hakan tasa dole suka hakura suna binshi da idanu kawai. STORYN Ta tada kai da pillow a saman bed nata daga ita sai wannan short ɗin wandon nata da kuma ƴar riga, ta rungumo pillow a kirjinta tana aikin chatting da shi. Sai zubawa Dr nata shagwaɓa take yi a kan ita tana kewarsa, sai biye mata yake yi yana bata hakuri. Tamkar daga sama ta ga ya turo kofa ya shigo, dan yana da key a yanzu. Hakan na nufin duk chatting da suke yin nan ashe yana kan hanyar zuwa, kawai yaki gaya mata ne. Da gudu ta diro kasa daga saman bed ɗin ta nufe shi, buɗe mata hannu ya yi ta faɗa jikinsa tana dariya. Rungumeta sosai ya yi yana ɗan shafa bayanta. Laluɓar hannunta ya yi a in da ya sanya mata wani shegen diamond ring mai bala'in tsada, nan take hannun nata ya fara kyalli. Bai bari ta fara zuba mishi tsalle da murna ba kawai ya ɗauketa cancak sai saman bed ɗin, tamkar dama a kusa yake. Romancing na juna suka fara yi kamar yanda suka saba, sai dai a yau dai Dr William ya zo har wuya, ya kasa jurewa ya danne sha'awarsa, dan yana tsananin sha'awarta over. Hana shi ta yi a in da ta saka mashi kuka, dole ba dan ya so ba ya rabu da ita tare da barin jikinta ya koma gefe guda a saman bed ɗin ya zauna, ya haɗa kai da gwiwa yana sauke numfashi a hankali hankali. Miƙewa ta yi jiki ba kwari ta dawo kusa da shi. Hannu ta kai tare da ɗago kan nasa tana ambatar sunansa. Kasa amsa mata ya yi, saboda mawuyacin halin da yake ciki. Rungume shi ta yi a kirjinta tana bashi hakuri tare da saka mishi kuka, sam ba zata iya jurar ganin shi a cikin tashin hankali da damuwa ba, kun san zuciyar masoya! Ba abin da ba zasu iya yi wa junansu ba, in dai sun mace a wannan soyayyar tasu! To ita dai soyayyarsa ta yi mata mummunar kamu, makauniyar soyayya take yi mishi. Haka shi ma a nashi ɓangaren, makauniyar soyayya yake yi mata! Ba zai iya ganinta cikin damuwa ba, duk yanda ya kai ga son abu, in dai bata so, to ko zai mutu! Haka yake hakura, sai dai ya yi ta fama da azabar raɗaɗi a cikin zuciyarsa, amma ba shakka zai hakura. Ganin tabbas ya shiga tsakanin damuwa sosai na wuce misali ne yasa ta ce to ya zo ya biya bukatar tasa kawai, tana magana tana kuka. Da kyar ya iya ɗago kallonsa izuwa gareta, hannu ya kai ya fara goge mata hawaye, muryarsa na rawa ya fara magana. "Ni da gaske nake sonki my beauty, ba nason abin da zai ɓata maki rai, ki bari kawai na hakura kin ji ko? Yanzu dai ki gaya mani, me zan yi na sameki? Ya zan yi ki zama matata mallakina, sai nayi yanda nake so dake babu wani sha'amaki?". Cike da murna ta ce "Aure, aure ne kawai zai sanya na zama mallakinka ba wani shamaki, hakan kuma ba zai taɓa yiwu ba har sai ka zama musulmi, ba zai yiwu na aureka kana krista ba!". Cikin sauri ya ce mata "Na yarda, na yarda zan zama musulmi, ni dai kawai ki zama mallaki na!". Sosai ta rungume shi tana murna tamkar ba gobe. Ganin tana murna ne yasa shi ma ya rungumeta sosai yana manna mata kiss a lips nata. Haka suka kasance tsawon mintuna 20, sannan ya ce ta shirya bari suje gidansu sai ya gayawa mummynsa da daddynsa abin da ya yankewa kansa, a lokacin kuma TAG yana koyan tafiya. Hakika ta yi tsananin murna, zata mallaki Dr ta. Cikin hanzari ta miƙe tare da faɗawa cikin toilet. Wanka ta yi cikin hanzari, yana zaune yana jiranta, amma shi kaɗai yasan halin da yake ciki na sha'awarta. A gabansa ta shafa Lotions nata kamar ko yaushe, sannan ta wuce zuwa dressing room. Yau da yake ya ce gidan iyayensa za su je, sai ta mutunta su ta hanyar yin complete dressing mai kyau, wandon jeans ta sanya a ciki, tare da wani T-shirt da ya saya musu iri ɗaya da shi. Bayan ta gama sai ta sanya after dress baka a saman kayan, dan ta ɗan suturta jikinta, still dai kanta babu ɗankwali ta fito. Cike da tsantsar so da kauna tare da kulawa ya fara yabon irin kyan da ta yi, murmushi ta yi kafin ta taho ta faɗa jikinsa. Yana ƙoƙarin fara kissing nata, ta dakatar da shi ta hanyar sanya hannu ta rufe mishi baki. "Haba my Dr, wai kai baka gajiya da shan lips na ne?". Lumshe shanyayyun idanuwansa da suka sauya launi ya yi, cikin sanyin murya ya bata amsa da cewa "My beauty, ya za'ayi na gaji da shan lips naki? Ai ba zan taɓa gajiya ba, ni dai yanzu Please ki bani ko kaɗan ne, kin ji ko my wife?". Harara ta wurga mishi kafin ta ce "Ai ba'a ɗaura auren ba ko?". Nisawa ya yi yana mai faɗin "To ai an kusa, kin ma tuna mini, tashi muje wajensu mummy da wuri, daga nan sai mu wuce a ɗaura aure ko?". Zata yi magana ya sanya mata yatsa a saman lips nata yana faɗin ta tashi su tafi da wuri. Ba musu ta tashi suka fice daga gidan. A motar nasu ma, basu hakura ba, sai da suka ɗan yi romancing junansu kafin ta kwantar da kanta a saman kafaɗarsa, shi kuma ya kunna motar suka bar gidan. (Yanzu kun fara ganin daga in da TRIPLETS suka yi gadon nasu jarabar ko? Da uwa da uba dukka ba sauki😂 mu je dai zuwa.) Yau dai Gwaggo ta zuba kauyanci na ganin gidansu Dr, bata taɓa tunanin daga wannan aljannar duniya ya fito ba, tana tunani dai irin normal masu kuɗin, ɗan dai'dai ɗin nan, bata san mahaukatan kuɗi karesu ba. Sake baki ta yi kawai tana ta kallon gidan abinta. Sai da ya ja hannunta suka nufi ciki, lefter suka hau zuwa hawa na uku, dan ya san confirm su mummynsa suna wajen, dan sun fi yawan zama a wajen. Ita dai sai mamakin gidan take yi, dan gida ne irin high rise building ɗin nan, ga wani haɗaɗɗen lefter mai matuƙar kyau, abin ba'a cewa komai, dan ya wuce tunanin mai tunani, idan na ce zan tsaya zayyana muku gidan Jacob Roshan ba ƙaramin aiki bane, dan kuwa sai mu kare book nan kaf a kansa kawai, dan fa ya haɗa komai, babu abin more rayuwa da ɗan adam zai buƙata babu a cikin gidan. Sai yanzu gwaggo ta sake yarda cewa so gudan jini ne, yanzu idan ban da so me Dr William zai yi da ita? Irin wannan duniyar da suke ciki, ga kuɗi, kyau, isa da takama, abin ba'a magana. Tamkar yanda Dr ya faɗa na cewa iyayensa suna hawa na uku, a can ya samesu, suna zaune a palonsu tare da Uncle Herry, Josephine da TGA, sai zuba hira suke yi. Jacob Roshan yana shan green tea, ita kuma mummynsu tana faman cin wasu korayen ganyayyaki masu karawa jiki lafiya da jini, ga wani makeken Tv dake gefe guda ta gabas maso tsakiya yana magana. Tun da suka shigo palon gwaggo take bin ko'ina da kallo, ta kasa nutsuwa waje guda, gani take yi tamkar Dr William zai cutar da ita ne a irin wannan gida, ta tsorata da ganin wannan uban daular more rayuwar. Shi kuwa, riko hannunta ya yi suka nufi saman wata luntsumemiyar sofa mai matuƙar laushi da kyau, fara kal tamkar yanzu aka cirota daga kwalinta. Komai na cikin palon sai kyalli yake yi, yana ɗaukar idanu, gal gal da su, nera ta yi kuka ta kuma zauna da kyau a wajen. Ko da suka shigo palon, sam iyayen Dr basu nuna mata komai ba, sai ma karramata da suka yi, da fara'a mummynsu ta tarbeta, shi ma daddyn nasu, fuska ba yabo ba fallasa ya tarbesu, dan gwaggo dai baturiya ce ba bakar fata ba, sak Naurat take!. Josephine ta fi kowa murnar ganin gwaggo, saboda dama yayan nata yana yawan korinta a kusa da shi, a tunaninta tun da yanzu ya fara son mata, zai dai'na abin da yake yi mata. Su Uncle Herry duk sun yi tsantsar murna ba kaɗan ba. Sam Dr William bai ɓata lokacin wajen sanar da iyayensa wace ce gwaggo a wajensa ba. A nan ne tsananin farincikinsu ya kara bayyana, sun ji daɗi sosai da ɗansu ya kawo macen da zai aura, nan take mum nasu ta ce gwaggo ta dawo kusa da ita ta zauna, tamkar za su cinyeta saboda so, sai tambayarta suke yi me take so ci a kawo mata?!. Kan ka ce me an cike mata gabanta da lodin kayan cima kala kala, masu aiki sun fara zarya a cikin palon, suna kai kawo na kayan cima. Yau dai Gwaggo taga abin mamaki, abincin ma a baki suke ƙoƙarin tura mata, saboda so, kuma duk aikin mum ce, sai wani ririta take yi. Ta ɗebo abinci a cikin spoon zata kaiwa gwaggon a baki kenan, cikin hanzari Dr ya ce "Mum kada ki bata, dan ita bata cin irin abincin mu, ba komai take ci ba!". Ɗan zaro blue eyes nata mum ɗin ta yi kafin ta ce "Why?". Ko a jikinsa ya amsa mata da cewa "Be cause she is a Muslim, so ba komai take ci ba, akwai abin da ya zamana haramun a cikin addininsu su ci, haka idan muka je restaurant cin abinci ma, sai ta faɗi abin da za'a bata, bata cin irin nawa!". BABBAR MAGANA. A tsananin razane mum da dad ɗin dukka suka mike tsaye, tamkar sun ga wani abin tsoro. Nan take kuma suka canza fuska tamkar ba su ne suke dariya a yanzu ba, sun wani uban ɗaure fuska tamkar hadari, shi daddy ma har da wani zaro idanu. Cikin tsawa mum ɗin ta ce "To musulmar zaka aura ne?!". Sosai gwaggo ta yi wani mahaukacin razana!, Ta tsorata na ganin canjin da suka yi lokaci guda, tamkar ba su ba. Shi kuwa Dr, ko a jikinsa ya amsa musu da "Yeah mum, ita nake so, ita zan aura, kuma yanzu ma da muka zo, na zo ne na gaya muku zan musulta nima, be cause we're prepared to get a marriage together, so shi ne abin da ya kawo ni!". TASHIN SENSE!!! Wani uban tsawa dad ya daka musu wanda ya sanya gwaggon mikewa da sauri. Shi ma Dr William mikewa ya yi tare da yi mata alama da hannunsa a kan ta zo. Da sauri ta tafi izuwa wajensa, jikinta sai kerma yake yi. Dr kuwa ko a jikinsa ya rumgumeta yana ɗan shafa bayanta, alamar ta kwantar da hankalinta. Mum ce ta katsesu da cewa ya sake wannan yarinya ko kuma wlh yanzu ransa ya ɓaci. A zahirin gaskiya tun da yake da iyayensa basu taɓa ɗaga mashi murya a magana bama bare har a kai ga tsawa, lalaɓa shi suke yi sosai kullum. Hakan tasa ya ji wlh yana kaunar shiga musulci, dan shi duk abin da ba'a so, to fa shi yake so. (Idan baku manta ba a baya dama Dr William ɗin ya faɗa, wannan kalma ta abin da ba'a so, shi Lion yake so, a wajensa ya gaji kalma, to hakan take!.) "Mum why are you shouting like that? You already know that idan na ce zan yi abu fa, to sai na yi, so don't west your time to say something about that issue, be cause confirm sai na musulta, dan ina son A'isha, she is my life, my everything!!". BABBAR MAGANA!! YAU AKE YINTA!! "William are you out of your sense?!" Cewar mum ɗin. Dad ne ya karɓi maganar da cewa "In dai har ka ce zaka musulta, to confirm zaka bar mani gidana! Kuma sai dai ka mance da mu a matsayin iyaye, ka nemi wasu!!". A takaice ya ce "That's good daddy, i chose A'isha and Muslim religion, wai daddy ka manta abin da ba'a so shi nake so ne? To ko dan nunawa da kuka yi baku so, confirm sai na yi!!". Ya kai karshen maganar tare da juyawa tare da gwaggon a jikinsa. "William don't go anywhere, come back and say sorry to your dad!". Cewar mum, ta yi maganar tamkar zata fashe da kuka, idanuwanta duk sun cika taf da kwallah, Allah ya gani a duk cikin ƴaƴanta, ta fi son Dr William, kuma ta san halinsa sosai, tun da ya ce sai ya musulunta, to fa babu chanji sai ya yi ne, sai dai duk abin da zai faru ya faru. TIRKA SHI. A ɓangaren shi ma daddyn, kirjinsa sai dukan uku uku yake yi, dan shi ma, ya fi son Dr William sama da kowa a cikin ƴaƴansa, ba zai iya rabuwa da shi ba, ba kuma zai iya ganinsa a cikin addinin musulunci ba, dan su irin kristocin nan ne masu tsauri a kan addininsu, ba za su iya yafe ɗansu ya musulunta ba! Gara su kashe shi da su barshi ya musulta. Hakan tasa daddyn zuciya ta ɗebe shi ya yi yunkurin kashe gwaggo da wukar da mum take yanka ganyayyakin da take ci. Cikin ɓacin rai Dr William ya tare daddyn nasa, tare da kwace wukar, har ya ɗaga a zuciye zai cakawa daddyn nasu a ciki, gwaggon ta rike shi tana kuka tare da girgiza mashi kai a kan kada ya yi hakan, kada ya kashe daddynsa. Wurgi ya yi da wukar tare da rungumeta suka nufi waje. Dafe saitin zuciyarsa dad ɗin ya yi, kan su yi wani yunkuri ya zube kasa sumamme, abin ya taɓa mishi zuciya over, kuma dama dole ya taɓa shi over, ace ɗa mafi soyuwa a gareka, ka fifita shi fiye da kowa, ka shagwaɓa shi, rana tsaka wata mace ta shiga tsakaninku, har yaron ya yi yunkurin kashe ka, saboda mace, ba dan macen da yake son ɗin ta rike shi ba, da tsab zai iya kashe ka saboda zuciya ta ɗebe shi, dole wannan abin ya taɓasu over, dan zuciyar iyaye ya wuci tunanin mutun, in ma musulmi ko Kristen, duk wanda aka ce shi ya haifi mutun, to wlh ya wuce abin wasa, zai so ɗan nan ne fiye da tunanin mai tunani, koda kuwa ba zai nunawa kowa ba, ba zai taɓa yuwuwa ace iyayen da suka haifeka ba su sonka ba, sai dai idan ba zasu nuna maka son ba, amma zuciyar iyaye daban yake da kowa, suna iya sadaukar da duk abin da suka mallaka saboda ƴaƴansu, ba'a banza da Allah ya ce bayan Allah da Manzonsa sai iyaye ne kawai za'ayi wa biyayya a shiga aljanna kai tsaye ba, so iyaye sun wuci wasa koma ya ya suke!! Fatanmu dai Allah Ubangijin ya bamu ikon bin umarninsu tare da kyautata musu!!. Ko kaɗan Dr William bai juyo ba, duk da yana jin zafin rabuwarsa da iyayen nasa, amma hakan bai hana shi dagewa dan cika burkinsa ba. Ficewa ya yi daga gidan abinsa. Shi kuma dad su Uncle Herry suka yi ƙoƙari tare da taimakon ma'aikatan gidan, suka nufi hospital da shi. Ko awa ɗaya bai yi a asibiti ba rai ya yi halinsa, dama already yana da hawan jini, sara ce ta zo a kan gaɓa. Mutuwarsa ta sanya mum nasu shiga tsananin tashin hankali, wanda har sai da ya jawo mata bugawar zuciya, ita ma ba'afi awa uku da mutuwar dad ba rai ya yi halinsa, ta bi daddyn. Hakika familyn Roshan su ga tashin hankali a wannan rana, harta yayyun daddyn da suke rike da mulki, a wannan rana sun sha kuka, an yi musu hotuna da videos suna kuka da hawayensu na rashin kaninsu da matarsa tamkar wasu yara ba adadi. Sam Uncle Herry da Josephine sun ki gayawa jama'a gaskiyar abin da ya kashe Jacob da mum nasu, sun ɓoye ne saboda suna tsananin son Dr William, kuma suma sun ji suna son su musulta, sun san cewa idan har suka sanar da jama'a gaskiya, to ba shakka yayan daddy da yake kan mulki zai sanya a kashe Dr William, dan su basu yafe jininsu, ko yaya ka taɓosu sai sun rama, koda kuwa a cikinsu kake. A lokacin da za'ayi jana'izarsu su mum, za'a kaisu mutuware, wato jana'izar kiristoci, an buƙaci da Dr William ya zo ya wuce gaba a matsayinsa na babban ɗansu, amma sam baya wajen, hasalima bai san da zancen mutuwar ba, duk da cewa labarin ya baza gari, abin ku da manyan mutane, sai dai shi bai sami labari ba, dan yana babbar masallaci jumma'ar musulmai dake garin, tun da ya bar gidan suka wuce can da gwaggon, kafin ya tafi kuma sai da ya kashe wayarsa, a cewarsa kada ma su mum ɗin su kira shi, dan confirm sai ya musulunta. TASHIN SENSE. Kasancewar ba'a sami Dr William ko a waya ba, haka aka ce Uncle Herry ya wuce gaba, Josephine ta bi bayansa, dan da aka tambayesu ina Dr William, sai suka cewa jama'a ai Dr William baya nan, sun dai ki faɗar gaskiya. Haka aka kai gawarwakinsu mum ɗin mutuware, sai kuka su Josephine ɗin suke yi tamkar ransu zai fita. A ɓangaren Dr William kuwa, suna fita Masallaci ya wuce da gwaggon, a in da ya je ya gayawa liman ga abin da yake tafe da su, ya gaya mashi aure suke son yi, kuma iyayensu basu son aure, saboda iyayensa sun ce a'a, kuma sun hana shi musulta. Duba da yanayin kasar tasu, ba musu limamin ya bashi kalmar shahada tare da tambayar gwaggo shin da gaske tana son Dr William, sosai ta tabbatar musu da hakan, ba ɓata lokacin limamin ya ɗaura musu aure bayan an fito sallar azzahar, a cewarsa, ai sun fi shekaru goma sha takwas, dan haka suna da ƴanci da kansu, suna da ƴanci su yi abin da suka ga dama, shi ne yasa aka ɗaura musu aure bayan musultar Dr. Ita kuma gwaggon a lokacin idanunta sun rufe, tana ganin kamar iyayen Dr William za su zo su rabata da shi, ba zata iya rayuwa babu shi ba, shi ne kawai yasa duk abin da liman ya ce mata, sai ta ce mishi e, dan a lokacin bata da burin da ya wuce Dr William ya musulunta, a ɗaura musu aure, su mallaki juna, shi ne yasa ta yarda, bata bi ta kan iyayenta ba, dan tana ganin suma zasu tsaya ɓata mata lokaci ne har a rabata da Dr. Bayan an ɗaura musu aure, kai tsaye gidan Gwaggon suka wuce abinsu, yau sun zama sabbin mutane. Ko da suka je gidan, komai na kayan kallo a kashe, basu sami labarin abin da yake wakana a gari ba. Rungume juna suka yi suna tsananin murna da farinciki, yau sun mallaki juna na har abada. Kissing nata ya fara yi, cike da so da kauna ta fara mayar mishi da martani. Sun ɗan yi nisa cikin abin da suke yi, tamkar wanda aka muskula ta miƙe tana faɗin "My Dr bari na kira mum ɗina na gaya mata yanda aka yi komai, dan kada asamu matsala ka ji?". Idanuwansa a runtse ya jawota jikinsa yana faɗin "A'a kada ki gaya musu yanzu, kada suma su rabani da ke, ki bari sai mun sami hutu a school, sai mu je gidan a tare ko?". Jinjina mashi kai ta yi cike da gamsuwa da kuma yarda da shi ɗari bisa ɗari, dan ta faɗa makauniyar soyayya, baiwar Allah, ba laifinta bane, laifin so ne, da bashi da adalci idan ya shiga mutun. "My Dr ka bari, bari na je nayi wanka nazo ko?". A kunne ya raɗa mata yau kam a tare za su yi. Bata yi mashi musu ba, dan sun mallaki juna, kafin su mallaki juna ma, dama wani lokaci ko tana toilet yana shiga ya yi abin da zai yi, bare kuma yanzu, ai sai abin da hali ya yi. A tare suka wuce cikin toilet ɗin. After some minutes suka fito rungume da juna, tamkar wani ya ce zai kwace musu junansu. Yau dai a tare suka yi komai, kama daga shafa lotions, shiryawa cikin kananan kaya, da yake da akwai kayansa sosai a gidan, dan idan baku manta ba, wani lokaci a gidan nata yake kwana a baya, hakan tasa ya sayi wasu kaya ya zuba a dressing room nata. Komai suke yi suna yi ne suna wasan masoya cike da so da kauna. Da zata shiga kitchen ma, a tare suka shiga da shi. Duk da cewa bai iya aikin komai na kitchen ba, amma ya tayata da hira na kalaman soyayya masu daɗi, tare kuma da tana aiki yana rungumeta, ko ya shafi mazaunanta. Kayan kwalama ta haɗa musu tare da green tea mai zafi sosai. A palo suka baje abinsu, a lokacin kuma har an kaisu Jacob mutuware an dawo, duk basu da labari. Sai da suka fara shan tea ne ta ɗauko wayarta tare da kunna data dan ta yi wa Cherish massage a Whatsapp na yau sun yi aure da Dr, sun mallaki juna, ta zo ta tayata murna. Tana kunna data sakon Cherish ɗin ya shigo wayar nata na tayata alhinin rasa iyayen saurayin nata Dr William wanda yake a matsayin mijinta a yanzu kenan. Wani irin ihu ta kurma wanda bata san time ɗin da ya fito daga bakinta ba, jikinta na kakkarwa ta yasar da wayar kasa. Cikin tashin hankali ya riko kafaɗunta yana tambayarta lafiya? Ihun me take yi. Kasa magana ta yi, nan take hawaye suka cika mata idanuwa, domin tasan Cherish ba zata taɓa yi mata karya ba, tun da ta yi mata wannan massage ɗin, to gaskiya ne, iyayen Dr William sun mutu. TASHIN SENSE!!!. Ganin taki amsa mishi tambayar da yake yi mata ne, yasa ya ɗauki wayar tata dan ya duba me ta gani take wannan ihu. Dubawa da zai yi bai san time da ya saketa ya wani irin mikewa a razane ba. Ita ma mikewa ta yi tana hawaye jikinta duk sai ɓari yake yi, abin mamaki yanzu bai fi awa biyar da suka rabu da su ba, amma ace sun mutu dukkansu biyu? Wannan dole bawa ya shiga tsananin tashin hankali. A hanzarce Dr ya wuce ya ɗauko wayarsa, cikin tashin hankali, idanuwansa suna gani bibbiyu, ya fara ƙoƙarin kunna wayar. Ya kasa saboda kerma da jikinsa yake yi, wayar ta kasa tsayuwa waje guda a hannun nasa. Daga karshe ita ta karɓa ta kunna mashi. Number uncle Herry ya fara kira, bugu ɗaya ya ɗauka. Cikin tsananin tashin hankali da razana ya fara magana yana haɗe word, a in da ya tambayi uncle Herryn ɗin ina dad da mum. Ba ɓoye ɓoye ya gaya mashi sun mutu. Ya ilahi ya lillahi, bai san time ɗin da ya saki wayar tasa ta faɗi kasa ba. Kasa tsayuwa waje guda ya yi a in da ya zube gwiwowinsa a kasa a wajen, yana wani irin numfashi mai kama da gurnanin zaki. Tsugunnawa ta yi a kusa da shi tare da ɗan rungumo shi a jikinta, sai ruwan hawaye take yi. Muryarsa tamkar mara lafiyar da ya yi shekara cikin mawuyacin hali ya ce mata. "My.....my beauty.... Don't tell me that what i heard now about my dad and mum is true, say it's not a true to me". Rarrashinsa ta fara yi tare da kara mashi karfin gwiwa. Ina ai kasa hakura ya yi, zuciyarsa ba zata iya ɗauka ba, idanuwansa sun yi jajir da su. Ta yi ta yi a kan ya tashi su je gidan, amma ina ya kasa koda motsawa, dan yana bala'in kaunar iyayen nasa fiye da tunanin mai tunani, sune duniyarsa, duk abin da yake yi musun nan yana tsananin sonsu, ace lokacin guda ya rasasu? Kai abu ne wanda zuciyarsa ba zata iya ɗauka lokaci guda ba, dan ma dai yana da taurin zuciyar ce, ai da abin ya wuce hakan. Sai da ya ɗauki almost 1 hour a durkushe a wajen, sannan ne ya iya ɗan motsawa. Da kyar ya mike. Da dafa bango ya fito palo. Da sauri ta ɗauki bakullin mota ta biyo bayansa. A takaice ita ta ja motar suka nufi gidan. Har lokacin jama'a na cike taf a gidan. Bai kula kowa ba ya wuce ciki, yana tafiya tamkar zai faɗi kasa, ya rike hannun gwaggo gam dan kada jama'a su rabasu, ta je ta ɓace mashi kuma. Kai tsaye hawa na biyu suka wuce, a nan suka sami su uncle Herry da su yayyun dad ɗin nasu, sun sha kuka tamkar ba gobe, shi kuwa Dr William ya daure, idanuwansa sun yi jajir kamar wuta, amma sam bai yi kwallah ba. Sai bayan sati biyu da mutuwar iyayen nasu ne ya fara gane kansa, nan ma da taimakon gwaggo da take kwantar mashi da hankali, ba karya ya shiga tsananin damuwa da tashin hankali na wuce misali, har wata iriyar mummunar rama ya yi, tamkar ba shi ba, iyaye ba wasa ba! Kuma dukkansu a lokacin guda, a hakan ma su Uncle Herry basu gaya mashi cewa sanadiyarsa ne yasa hawan jinin dad ɗin nasu ya tashi har ya mutu ba, sun ɓoye mashi, wata kila da sun gaya mashi shi ne sula, tashin hankali ne shi ma zai kashe shi. Haka suka kasance a daddafe har tsawon wata da rasuwar iyayen nasu, sannan ne ya ce shi ba zai iya zama a wannan gidan ba, dan idan har ya zauna, kullum zai rinƙa kwana ne cikin kunci da bakinci tare da ganin tamkar iyayensu suna tare da su a gidan kamar baya, dan haka shi zai koma ɗaya daga cikin gidajen daddyn nasu ya zauna tare da gwaggon, za su ɗauki Tga su rike tun da a lokacin shekararsa biyu da ƴan watanni. Uncle Herry da Josephine suka ce suma za su bishi, ba za su iya zama ba. Tambayar gwaggo ya yi a kan zata iya zama da familynsa, cike da murna ta ce mashi e, dan haka sai suka tattara duk wani abin da za su buƙata, suka rufe gidan tare da sallamar gabaɗaya ma'aikatan, sannan suka tafi zuwa wani gidan bene mai hawa ɗaya, shi ma ɗaya ne daga cikin gidajen daddyn nasu, ba karya ya kawatu iya kawatawa gidan. A nan suka fara sabuwar rayuwa, gwaggo da Josephine sun zama very close friend, dan a lokacin shekarunsu kusan ɗaya. Cherish tana zuwa suna rayuwar farinciki. Da Josephine da Uncle Herry duk sun karɓi musulci, gwaggo ta musultar da su, daga baya ita ma Cherish ta musulta. Rayuwa mai tsabta da farinciki suke gudanarwa a gidan. Har tsawon wata ɗaya da dawowarsu gidan sam Dr William bai kusanci gwaggo ba, dan har lokacin bai warke daga raɗaɗin rashin iyayensa ba. Ita ma Gwaggo bata wani damuwa na rashin soyayya da basu yi, dan ta san halin da yake a ciki. A tare suke yin aiki da Josephine, komai tare tamkar twins, Uncle Herry kuma kullum yana tare da TGA yana koya mishi wasu abubuwa na rayuwa. Idan suka tashi tafiya school, akwai wata mai aikin TGA ɗin da take kula da shi, dukkansu suna tafiya su bar shi. Sosai Dr da gwaggon suka mayar da hankali a kan karatu, dama already kun san basu wasa da karatu.......... ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E4 *Ina yi wa ɗaukacin al'ummar musulmi ta duniya barka da sallah, Allah Ubangiji ya maimaita ma, ya karɓi ibadunmu ya sa kuma muna daga cikin ƴantattun bayi, wannan page sadaukarwa ce, barka da sallah ce ga ƴan comments section group na, ina farincikin kasancewa a tare da ku, kuma dukkanku ina ganin comments na kowa, tare da adduo'inku da yaba mani da kuke yi, tare da kwarin gwiwan da kuke kara mani, ba abin da zan ce maku face Allah ya bar zumunci, hakika kuna sakani farinciki da comments naku, hakika kuna cikin tunanina a koda yaushe ❤️* Sosai Dr da gwaggon suka mayar da hankali a kan karatu, dama already kun san basu wasa da karatu. A takaice sai da suka ɗauki almost wata biyar da aurensu kafin Dr William ya dawo dai'dai na rashin iyayen nasu da suka yi, a lokacin ma ya dawo dai'dai ne sakamakon adduo'i da kuma karatun Alkur'ani mai girma da gwaggon take yawan yi mashi. Shi ma yana koyan hadda sosai a wajen limamin da ya bashi kalmar shahada, haka su Josephine ma suna karatun addini sosai. A lokacin Josephine sunanta A'isha, dan ta ce sunan gwaggo take so a saka mata, shi kuma Uncle Herry sunansa Muhammad, TGA kuma Sudais. Suna rayuwa cikin tsantsar farinciki. Har lokacin gwaggo bata san da abin da yake faruwa a gida Nigeria ba, ita dai soyayya ya rufe mata idanu, sabgar gabanta kawai take yi. Bayan Dr William nata, bata tunanin kowa, shi ne a ranta dare da rana. A haka almost shekara guda kenan da aurensu. Yau ta kama Sunday, babu school, duk suna haɗe a gida suna hira. Cherish ma ta zo gidan nasu. Da Josephine wato A'isha da gwaggo suna kitchen suna haɗa kayan makulashe, karfi da ya ji gwaggo ta koyawa Josephine shiga kitchen, ita ma Gwaggon ba wani abin da ta iya yi face dafa tea sai ɗan snacks da ba'a rasa ba haka. Idan ta shiga kitchen hada even tea, sai ta fi 40 mins ana abu guda, amma a haka take zagewa ta shiga dan ta yi wa Dr tea da kanta, bata son ƴan aiki su yi mashi tea ɗin. After some minutes. Zaune take a saman bed nata a cikin bedroom nata tana duba wasu takardunsu, dan sun kusa fara exams, daga ita sai wando zuwa iya santala santalan cinyoyinta, da kuma ƴar riga da bata gama rufe cibiya ba, ta saki gashi har baya, tana aikin taunar chewing gum. Josephine da Uncle Herry sun ta fi yawon shakatawa, dan yau week, Cherish na palon kasa, ita da TGA, tana aikin bashi hot milk, tana bala'in kaunar TGA kamar me, sai dai shi kuma, tun yana yaro, yana da bakar zuciya na wuce misali, ga saurin fushi da taurin kai, tun yana karami idan ya ce ba zai yi abu ba, to kamar Lion yake, ba zai yi ɗin ba, sai dai a kashe shi, abin dai ba'a cewa komai. Amma da yake Cherish ta san halinsa, sai ta koyi zama da shi, tana yi mashi abin da yake so, har tasa ya saba da ita sama da yanda ya saba da su Josephine, har ɗaukarsa take yi su je gidanta su wuni, ya zama kamar ɗanta, tun Dr yana hanawa, har ya saduda, ya kyalesu kawai. Dr William, sanye yake da short irin masu kama jikin nan, kwata kwata wandon a iya rabin cikyarsa ta tsaya mashi, babu riga a jikinsa. Daga cikin ɗakin maratunsu ya fito, hannunsa na rike da wayarsa, sai aikin sauke ajiyar zuciya yake yi. Cike da so da kauna ta kalle shi tare da sakar mashi cool murmushi kafin ta ce "My Hero ya ka ji karatun?". Gera ɗaya ya ɗaga mata yana faɗin "Normal beauty, what about you?". Rufe takardun dake a gabanta ta fara yi tana bashi amsa da komai normal. "Akwai wani abin da zan kara maki ne?". Ya tambaya yana tsareta da waɗan nan shegun blue eyes ɗin nasa masu rikitar da mai kallonsu. Girgiza mashi kai ta yi kafin ta ce "Nothing gaskiya, saboda komai dai'dai nake ji, ko yanzu a fara exams kawai". "Are you sure?". Ya faɗa yana mai canza kallon da yake yi mata izuwa wani irin kallo na azababben so da kauna. Jin yanda ya yi tambayar yasa ta ɗago da dara daran idanunta izuwa kansa. Ɗan zuba mashi idanu ta yi na ƴan sakanni kafin ta ce "Are okey kuwa?". Nisawa ya yi tare da ɗan kashe mata ido ɗaya yana faɗin "Am not sure, but you have to be check me very well, so that you should now am okey or not". Ya yi maganar cikin wata iriyar murya da take nuna tsantsar so da kauna. Ƴar murmushi ta yi kafin ta ce "Okey come and sleep, let me see what to do". A hankali ya nufota, yana tafiya yana wani yarfar da hannu kamar wani ɗan baby. "My Dr, yau fa like you're feeling shagwaɓa more for me ko?". Ɗan turo mata ɗan bakin nan nasa ya yi kafin ya sake ciza ɗan red lips nasa, sannan ya ce "Ba dole ba, gabaɗaya you forget about me, kawai kina ta kula da su A'isha, ni babu mai kula da ni". Ya kai karshen maganar tare da kwanciya a saman bed ɗin ya kuma tada kai da cinyarta yana turo baki. Hararar soyayya ta wurga mashi kafin ta ce "E lallai yau rigimace ma kake ji da ita ba shagwaɓa ba, amma na san maganinka". Hannu ya kai ya ɗan shafo breast nata yana faɗin "Ga abin da zaki bani na sha sai na dai'na rigimar". A takaice ta ce "Da a baya da kake sha ni nake baka ne?". Gera ɗaya ya ɗaga tare da ɗan zaro idanu kafin daga bisani kuma ya miƙe zaune a in da ya rungumota suka kwanta tare yana faɗin to bari ya sha kayansa. Murmushi kawai take binsa da shi. Da ya fara wasa da su kuma, sai ta fara taya shi kamar yanda suke yi a baya. Nan take ta fara gigita shi da salonta. Romancing na juna suka fara yi babu kama hannun yaro, an jima ba'a haɗu ba, ya kware wajen iya wasa, duk ƙoƙarin gwaggo sai ta sakar mashi ragamar idan suka fara, bata ma wani iya jurewa su yi nisa zata sakar mashi, ta dai'na biye mashi, sai dai ta yi ta zuba mashi kukan shagwaɓa, hakan kuma kara rikita shi yake yi, yasa ya yi ta kara birkita mata ƙwaƙwalwa har ta yi kukan gaske. A takaice dai Dr bai rabu da ita ba yau sai da ya kawar da budurcinta. Ta sha bakar wahala a hannunsa, har da suma ta yi, duk ta yakushe mashi fuska, saboda ta tara faratun hannu, kun san dama turawa suna tarasu sosai, to ita ma ta tarasu zara zara, hakan tasa duk ta ji mashi ciwo a fuska da bayansa kamar ya yi faɗa da damusa. Sai dai shi kuwa sam sam bai ji tana yi ba, har sai da ya kammala abin da yake yi ne, da ya sami nutsuwa, a nan ne ya ga ɓarnar da ya yi. Ya tsorata ainun, sunanta ya rinƙa kira, amma sam bata ko motsa ba, duba da sun yi karatu mai zurfi, duk abubuwa irin haka sun karanta, hakan tasa ya sauko daga saman bed ɗin ya nufi toilet. Ruwa mai zafi ya haɗa mata kafin ya dawo cikin bedroom ɗin, ya ɗauketa zuwa toilet ɗin. Shi ya yi mata komai da kansa, sai zuba mashi kuka take yi tamkar wanda aka cewa ubanta ya mutu. Banda aikin rarrashi babu wani abin da yake yi. Duk jikinsa ta yi muguwar sanyi, dan ba karya ta wahala iya wahala, shi ma ya wahala sosai. Sai da ya samu good 3 hours yana aikin rarrashinta da lallaɓata kafin ya samu barci ya ɗauketa. Ganin ta yi barci ne yasa ya fita zuwa word room na gidan. Alluran barci ya haɗa mata tare da dawowa cikin bedroom ɗin. Alluran ya yi mata kafin nan ya ɗebo kayan aiki, da kansa ya gyara ɓarnar da ya yi tare da duk abin da ya kamata. Bayan ya kammala ya tattare komai ya mayar, sannan ya je ya yi wanka, ya shirya cikin pajama ya dawo kusa da ita ya kwanta tare da jawota jikinsa ya rungume gam yana mai jin tsantsar farinciki tare da godiya ga Allah da ya sanya shi ne ya karɓi budurcin matarsa, dama idan baku manta ba, su da wuya ka sami mace virgin a wajensu, hakan tasa ya ji tsantsar farinciki na wuce misali, ji yake yi tamkar ya mayar da ita cikin cikinsa saboda so da kauna. Haka suka kasance shi ma barci ya daukesa rungume da ita. Ba su suka farka ba sai da Josephine suka dawo can rana ya yi sanyi wuraren laasar. Josephine ɗin ce ta tashesu dan taga basu yi sallar la'asar ba ga rana na dab da faɗuwa, ita kuwa sallar la'asar ba abar wasa ba ce, Allah ya yi rantsuwa da sallar, duk halin da zaka shiga, kada ka taɓa barinta sai rana ta faɗi kayi ta. Wasu hadisai sun ce idan rana ta faɗi ma ko kayita ba'a karɓa, wasu kuma sun ce sai dai ka hakura gobe ka rama, annabi ya ce munafukai ne kawai suke bari sallar la'asar ta wucesu, dan sallah ce mai matukar muhimmanci, kada ku manta har rantsuwa da ita Allah ya yi, kunga kuwa ba abin wasa ba ce ita ɗin. Allah ka bamu ikon yinta a kan lokaci!!. Da kuka gwaggo ta tashi mashi, sabon rarrashi ya sake farawa. Sam taki kula shi, sai tambayar lafiya take kuka Josephine take yi, amma bata samu amsa ba, dan shi ma Dr yana ta faman rarrashinta ba ta kan Josephine ɗin yake yi ba. Da kyar da suɗin goshi ya samu ta yi mashi shiru. Umarni ya yi wa Josephine ɗin a kan ta fita musu a ɗaki. Ba musu ta fita, dan ta san halin yayan nata sarai, yanzu zai iya saɓa mata kamanni. Sai lallaɓa beautyn tasa yake yi, amma taki kula shi, da alama fushi take yi da shi. Da kyar ya lallaɓata ta yarda ya ɗauketa zuwa toilet dan su yi wanka. Bayan sun fito, da kansa ya saka mata kaya, sai kumbure kumburen kumatu take yi, yau babu zancen my Dr, my Dr ya yi aika aika, haushinsa ma take ji.........NI KUMA PRINCESS TEEMA MALTINA MAI SANYI NAKE SHA, YO ME YAFI RA'INA?🤔 SOYAYYA AI DA DAƊI KO? SU GWAGGO YAU DAI AN GA RIBAR SOYAYYA😂 Bayan sun yi sallah ne ya kawo mata lunch ɗaki da kansa, ƙin ci ta yi, da kyar ya lallaɓata ta sha tea kawai. Bayan ta sha komawa saman bed ta ce zata yi. Cikin hanzari ya dauketa zuwa saman bed ɗin. Haka suka kasance har tsawon kwana uku yana lallaɓata tare da jinyar kayarsa, ita kuwa sai wahalar da bawan Allah take yi. A takaice dai wannan abin da ya shiga tsakanin, ba karamar son junansu ya kara musu ba, irin soyayyarnan da ake cewa a mutu a kan juna suke yi wa junansu, abin ba'a magana. Haka suka cigaba da rayuwa tsawon shakara ɗaya da rabi. A lokacin saura shekara ɗaya da rabi su kammala school, dan ma sun ɗaura master nasu ne, ai da ba'a haka ba, da sun jima da barin school ɗin. Ga shi karatu suke yi babu wasa, ga ilimi, dukkansu akwai kaifin ƙwaƙwalwa na wuce misali, tamkar su suka bawa kansu. (Ai dole TRIPLETS su kasance suna da basira, ba'a kasa suka tsinta ba, gado suka yi daga wajen iyaye!!) Yanzu gwaggo kwata kwata ta dai'na samun labarin gida Nigeria, amma ko a jikinta, da alama ta mance da su ma bakiɗaya, abubuwa kuma sun faru da dama a gidan Dr Salman!. Haka ta yi wa Dr William zanen tattoo mai shegen kyau a bayansa, shi ma ya zana mata a nata bayan, amma ta kasa kusa da mazaunanta, ya rubuta mata sunansa a wajen, ita ma ta rubuta mashi sunata a nasa bayan. Abin gwanin birgewa na wuce misali. Babu wata matsala a tsakaninsu ko da sunan wasa. Suna rayuwar tsantsar farinciki tare da faranta ran juna. Rana tsaka ciki ya bayyana a jikin gwaggo. Nan fa bala'i ya tashi ya tsaya, nan fa Dr ya ce shi baya son ciki, baya son haihuwa, sai dai su zubar, sam shi bai shirya haihuwa yanzu ba, ita kuwa gwaggo ta ce mai rabata da cikin nan sai Allah Ubangijin da ya bata, shi kaɗai ne zai iya kwatar kayansa. Ba yanda Dr bai yi ba, ta kafe sam wlh ba zata cire cikin ba, ai ba shegu bane, da ubansu, ƴaƴan sunna ne! Dan haka dole ta haifesu kamar yanda aka haifeta ita ma!!. Shi kuma ya kafe ko da sonta ko babu sonta, ko da saninta, ko babu saninta, sai ya salwantar da cikin. Da ta fahimci hakan ne, sai ta dai'na bari suna kusantar juna, kwata kwata ta dai'na kula shi. Amma fa abin ya yi mugun ɗaure mata kai na cewa da Dr ya yi baya son haihuwa, ta san dai a baya yana yawan maganar yara, to how comes kuma sun sami cikin ya ce shi baya son yara? Ko dai dama a bayan ma yaran uncle's nasu kawai yake so ne? Abin ya sakata cikin tunani, wai baya son yara kwata kwata a rayuwarsa. Babbar magana!!. (Ashe ba a kasa Lion ya tsinci tsanar yara ba! Kunga kuwa yanzu da Lion ya ce baya son yara ai bashi da laifi ko? Dan ɗan gado ne shi ɗin, ya gada komai tsab, har ma ya ninka mahaifin nasa zafi da tsauri. Lallai akwai cakwakiya, Lion baya son yara, ga shi ya kamu da son Rimsha, ko ya za su kare?🤔 Ni dai PRINCESS TEEMA ina da Maltina mai sanyi a fridge, idan suna bala'in da na ji ba zan iya jurewa ba, sai na kora maltina ta ta kwantar mani da hankali) Wasa wasa faɗa ya yawaita a tsakaninsu har Dr ya fara ƙoƙarin illatata. Ganin zai iya illatata ita da abin da yake cikin cikin nata ne yasa ta fara ƙoƙarin barin gidan. A nan ne Josephine ta tambayeta me yake faruwa? Bata ɓoye mata komai ba, ta gaya mata, sosai Josephine ta sha kuka, dan ita tana matukar son gwaggo ta haifa musu yara, kullum tana addu'ar Allah ya bawa gwaggon ciki ta haifa musu twins, sai dai ita dama already tasan Dr William baya son yara, sam baya son hayaniya, ta san ba zai taɓa karɓar wannan ciki na gwaggon ba, dan kullum yana yawan faɗawa mum ɗinsu kafin ta mutu, yana gaya mata cewa shi da ya haifi yara, gwara ya mutu bai kula mata ba!!..... Yau ake yin ta kenan, tashin sense. Haka Josephine ta yi ta bawa gwaggon hakuri a kan kada ta je ko'ina, In Sha Allah Dr zai sauko ya so cikin, amma ina wani muguwar tsana ma ya kara yi wa cikin na wuce misali. Tsanar cikin ne ma har ya shafi ita ma gwaggon, ya tsaneta sosai. Daga karshe ma sai ya yi yunkurin kasheta ita da abin da yake cikin nata. A ranar Josephine ce ta tseratar da ita daga hannunsa, a in da ta gudu da ita izuwa ɗaya daga cikin gidajen daddynsu, wato Jacob Roshan, suka bar Dr William uncle Herry sai TGA, ita dama Cherish bata san me yake faruwa ba. A nan suka cigaba da rayuwa da gwaggon da ita Josephine ɗin, dan ta ce wlh ba zata koma wajen Dr ba ita ma, zata zauna ta kula da gwaggon, baiwar Allah tana da tausayi sosai ga kirki na wuce misali. A lokacin Cherish tana kasarsu ta je hutu. Ita kuwa gwaggo bata je hutu ba, kuma ba'a nemeta a gida ba, dan a lokacin gidan nasu ya rushe bata sani ba, tana nan ta biyewa Dr ya kaita ya barota, da ba dan Josephine ba, da bata san in da zata sanya rayuwarta ba, da kila izuwa yanzu ma ta mutu. Allah sarki rayuwa kenan. Hakika Gwaggo ta sha bakar azabar wahala na rabuwarta da Dr, tamkar ba zata yi rai ba, dan tana tsananin kaunarsa fiye da tunanin mai tunani. Shi kuwa yana can ko a jikinsa, sai ma sharholiyarsa da yake sha, da alama ya mance da ita ma, da alama fa dama ba sonta tsakani da Allah yake yi ba! Kawai ya yaudareta ne!. (Wata kila shiyasa su Lion basu jinsa sam sam a ransu🤔 to lokaci dai zai nuna mana komai, amma ni da ku duk mun san cewa alhaki kwaikwayo ne! Ga mutuwar su Jacob ma dai..hmmmm akwai abubuwa da yawan gaske, wlh wasu cakwakiyar idan aka ɓallo maku sai kun ji kanku ta buga!!) PRINCESS TEEMA..✍️❤️ Da kyar tare da addu'a da taimakon Josephine gwaggo ta dawo dai'dai, da farko da ta ji wahala na soyayyar Dr dake neman hallakata, sai ta ce wa Josephine ta yarda zata zubar da cikin kawai ta koma wajen mijinta, dan ba zata iya yin nisa da shi ba. Kasancewar Josephine tana bala'in son yaran yasa ta yi ta rarrashinta tare da yi mata dabara har ta yarda ta bar ciki. After some weeks A haka Cherish ta dawo hutu ta same su, abin kwata kwata bai yi mata daɗi ba, duk sai ta ji ta tsani Dr sosai, ta kuma tsani maza fiye da tunanin mai tunani. Zaune ta isko Gwaggon a cikin bedroom saman bed, kusa da ita ta zauna tare da fara bata hakuri. A kule gwaggon ta ce. "Cherish kin san me kike faɗa kuwa? Hakuri fa kika ce nayi? Wlh ba zan hakura ba, sai na ɗauki fansan abin da Dr ya yi mini, wlh sai na kashe shi!". Zaro kananan idanunta na ƴan China Cherish ɗin ta yi tare da dafe kirji, a ruɗe ta ce "A'isha kisa fa kika ce? Please ki dai'na batun kisa, kin san Allah ya hana hakan". "Cherish idan kika ga ban kashe William ba! To wlh ba Dr Salman ba ne ubana, William ya cuceni! Ya zalunce ni! Yanzu ki gaya mini me zan cewa ƴan uwana da iyayena? Wlh billahi ba zan zubar da wannan cikin ba, sai na haife shi! Kuma ba zan bar Washington DC ba har sai na kashe William! Wai da kike wannan magana ma Cherish kin san waye babana kuwa? Ba makawa kashe ni zai yi idan ya ji abin da ya faru da ni, dan haka kada ma ki sake kawo mini maganar na yi hakuri a nan wajen!!"................SU GWAGGO AN JI WUYA, AN TUNA DA DR SALMAN,😂 WAI SAI YANZU TAKE TUNANIN ME ZATA JE TA GAYWA DR SALMAN?🤔 SOYAYYA RUWAN ZUMA! Shiru baiwar Allah Cherish ta yi bata sake yin magana ba har Josephine ta dawo ta samesu zaune a wajen, zama ta yi suka cigaba da jira. Ita dai Cherish haka ta wuni sukuku da ita har izuwa dare, sannan ta wuce gidanta. A takaice dai haka suka cigaba da rayuwa, gwaggo tana zuwa school, sai dai bata bari su haɗu da Dr, har cikinta ya girma ya isa haihuwa, Dr bai sake nemanta ba, bai sake leƙota ba, da alama ya mance da ita, baiwar Allah, ita kuma tana ta faman dakon soyayyarsa, a kullum tana tunaninsa fiye da yanda take tunanin komai na rayuwarta. A haka har Allah ya sauketa lafiya, tashin farko ta haifo ƴan ukunta tsala tsala da su, lafiyayyun yara masu jini a jika, kyawawan gaske, jinin Roshan. Ba abin da ya fi sakata cikin tashin hankali sama da yanda ɗanta na farkon ya yi mugun kama da Dr William, harta blue eyes nasu. Biyu daga cikin yaran nata sun kasance farare ne over, ma'ana sun fi ɗayan haske, haka zalika su biyun da suka fi hasken, sun kasance kwayar idanunsu iriɗaya ne, sak irin na Dr, shi kuma ɗayan haskensa kamar na Dr ne, sannan yana kama da Josephine sak babu maraba, kai kace ɗanta ne ma, saboda tsantsar kama. Bayan ta dawo cikin hayyacinta ne ta zubawa ƴaƴan idanu, tana kallonsu, basu da maraba da familyn Dr, dukka babu wanda ya ɗaukota a cikinsu, duk su Josephine ne, jajir da su tamkar tsada, ga bala'in kyau tamkar su suka faɗi irin halittar da suke so ayi musu, abin ba'a cewa komai. A lokacin ne kuma wani bakin shaiɗani ya shiga cikin tunanin gwaggon, nan ta fara tunanin to akan me zata rike yaran Dr? Ai kawai ta kai mashi kayansa, kada ta shayar da su, dan babansu ya cutar da ita, ya ci amanarta, ya ci amanar yarda da soyayya, tun da Allah yasa sun kammala karatu last month, kawai ta bashi yaransa, ita kuma ta koma Naija, idan har ta rike yaranma ai ya cuceta da yawa............. KUSKURE KU HUKUNTA WASU DA LAIFIN DA WASU SUKA YI MAKU,❌ DR SHI YA YI MAKI LAIFI BA TRIPLETS NAKI BA! KUSKURE KI CE BA ZAKI RUKE SU BA, DAN DR YA YI MAKI BA DAI'DAI BA!! Wannan banzar tunanin ne yasa ta ɗaukesu tare da haɗa wasu kaya nata da kuma wani farar takarda da ta yi rubutu a kansa da yaren su na tatar, wato yaren Na'urat, ta haɗa da chains ɗin da Na'urat ta bata, dama chain ɗin guda shidda ne, ta bawa Josephine ɗaya, Cherish ɗaya, saura huɗu, sai ta zuba uku a cikin wani ɗan ƙaramin, bayan ta raba tambarin heart na ɗayar sarkar kenan. Sannan ta ɗebesu, sai hanata Josephine take yi tana bata hakuri, amma ina ta zuciya, shaiɗan ta buga mata ganga, kuma ta taka rawa, tukukin bakin ciki na abin da Dr ya yi mata ya dawo mata sabo, ji take yi tamkar ta kashe Dr kawai ma ta huta. Haka ta ɗaukesu zuwa gidan Dr. Da sauri Josephine ta bi bayanta, dan kada su je su yi ɓatatciya da Dr, saboda ta san halinsa. Ta kuwa yi sa'a yana gida zaune a palo, ya yi wani fresh da shi, ya yi ɓul ɓul abinsa. Babu ko sallama ta shiga palon. A saman sofa ta ɗaura yara jariran da ko kwana uku a duniya basu yi ba, nono ma sau ɗaya ta gwada basu, da ta ji zafi ta ce ba zata iya ba, ta koma basu madara, daga karshe ta kwasosu zuwa wajensa. Murje idanu Dr ya yi ya ce bai san da wannan zance ba, shi ba zai karɓi yaran ba, dan yaranta ne ba nasa ba, ta kwashesu ta fita ko kuma ya yi mata illa, ya sanyata ta yi dana sanin zuwanta duniya. Kin kwashesu ta yi, ita ma sai ta hau dokin zuciya, a in da ta shiga gaya mashi bakaken maganganu over. Abin dai sam ya zamar musu babu daɗi. Daga karshe Dr ya ɗauko sandar buka horking nasu Uncle Herry, ya ce ko ta ɗauki yaran su fita, ko ya kasheta ita da yaran. Ta dauka wasa yake yi, sai ta ce wlh ba zata ɗauke su ba, ya yi abin da zai yi!!. Babu wani tunani, babu tsoron Allah ya ɗaga sandar zai buga mata. A guje ta miƙe daga samar sofar ta nufi waje, shi kuwa yana sauke sandar sai tsakiyar kan ɗaya daga cikin jariran nan nasa. Nan take yaro ya sandare musu, ko motsawa bai yi ba, tamkar rai ya yi halinsa, amma ga jini yana malala daga kansa. Ganin hanan yasa Dr ya yi wurgi da sandar ya yi kan yaran, dan ya tsorata sosai, yasan cewa idan wani abin ya samu yaron nan, to wlh gwamnati ba zata bar shi ba, duk da uncle nasa ne yake a kan mulki, tabbas sai an hukunta shi idan ya cutar da jariri, hukunci kuma mai tsaurin gaske. Ita kuma gwaggon ta yi waje bata san me ya faru ba. Da gudu Josephine dake tsaye a bakin kofar palon tana ganin komai ta kariso cikin palon, dan ta duba jariran. A matukar haukace Dr ya kwashesu zuwa asibiti dan a duba mashi yaron ya mutu ne ko yana raye, ba shi da kwanciyar hankali da zai iya dubasu!!. Ita kuwa gwaggo, tun da ta bar palon bata sake waiwayo su ba, ta ce idan Dr ya ga dama ya kashe yaran ai nasa ne, dan haka sai ta wuce gida abinta. Tana zuwa ta hau shirin komawa Nigeria, tun da sun kammala karatu. Sai dai fa, da kyar a daddafe ta yi kwana ɗaya na rashin yaran nan. Washegari ta wuni tamkar mara lafiya. A daddafe ta kai yamma. Zuwa dare ta ji ba zata iya rayuwa babu yaranta ba, dan haka sai ta shirya ta tafi gidan Dr. Abin mamaki abin al'ajabi, ko da ta je sai Dr ya ce wlh ba zai bayar da yaran nan ba, yara dai yaransa ne! Kuma ta fita mashi a gida dama shi ba sonta yake yi ba, idan har bata fita ba, sai ya sanyata ta yi danasani mai girma. Da farko ta ki fita, sai da ta ga zai yi mata kaca kaca ne ta kama kanta tana kuka tare da danasanin sanin Dr da ta yi a rayuwarta, tamkar ranta zai fita haka ta bar gidan. A ranar Josephine ta zo har gidanta suka kwana a tare, dan ta ɗebe mata kewa. Kwana kuka Gwaggon ta yi tana danasani kai mashi ƴaƴanta da ta yi. Ita kuwa Josephine kwana rarrashinta ta yi. Abin gwanin ban tausayi, shaiɗan ya yi mummunar aika aika a tsakanin masoyan guda biyu. A takaice a cikin satin Gwaggo ta shirya ta dawo Nigeria, dan ta zo ta gayawa Dr Salman abin da yake faruwa, saboda su je su karɓo mata yaranta, ba zata iya rayuwa babu su ba, zata mutu idan ba'a karɓo mata su ba. Haka ta baro Washington ba tare da ta sake saka yaran nata a idanunta ba, bata san a wani hali suke ba, bata san ya suke a hannun Dr William ba, shin ya karɓesu a matsayin ƴaƴa ne ko yaya? Duk bata sani ba, bata sake sanin komai dan gane da su ba!!. Tana dawowa gida Nigeria ta tarar da bakin labarin da ta gwammaci mutuwa a kansa. Wato ta tarar da labarin Dr Salman ya rasu da shi da Naurat da Amarya, a yanda aka ce accident suka yi dukkansu suka mutu. Abu kaɗan ya hana ƙwaƙwalwar gwaggo bai juye ba, ga rashin iyaye, ga rashin masoyi, ga kuma uwa uba rashin jariran ƴaƴanta, ga rashin ƴan uwa. Dole ta yi hauka data ga Dr William, dan ya cutar da rayuwarta, duk shi ne silar komai a rayuwarta. Da badan son shi ba, ai da ba zata mance da kowa ba har iyayenta su rasu bata sani ba!. Tun tana kuka da hawaye, har hawayen nata suka dai'na fita. Cikin raɗaɗi da kunan rai ta nufi ɗaya daga cikin gidajen Dr Salman, in da aka ce mata nan Abba ya yi aure. Tana zuwa ta yi sa'a Abban yana gidan. Tana kuka tamkar zata mutu ta fara bashi labarin abubuwan da suka faru da ita, tun daga farko har karshe. Daga karshe ta rufe mashi da cewa, dan girman Allah ya taimaka ya karɓo mata ƴaƴanta a wajen Dr William, dan ba zata iya rayuwa babu su ba. Nan fa taga bala'i a karo na uku, dan kuwa Abba a lokacin ma bai gama dawowa cikin hanyacinsa na abin da amarya ta yi mashi ba. Dan haka sai ya yi wa gwaggo tatas, ya koreta daga gidan, wai ta zubar masu da kimar gidansu, ta je wata ƙasa ta haifi yara, shi sam bai yarda da aure ta haifesu ba, dan haka ba zai karɓo ƴaƴan shegu ba, da ace ta zo da su ma, wlh karɓarsu zai yi ya mayarwa da ubansu su, dan babu ƴaƴan shegu a kaf zuri'ar Dr Salman. Haka dai ya yi ta surfa ruwan bala'i, ta in da yake shiga, ba ta nan yake fita ba. Daga karshe ya korata waje tare da rufo gate ɗin gidansa, ya ce ta je ya yafeta a matsayin kanwa!!. A lokacin da yammane, wuraren karfe 6:30, bai yi wani tunani ba ya daketa ya koreta. Tana kuka tana rantse mashi da Allah wlh ba shegu bane ƴaƴanta, ƴaƴan sunna ne, dan Allah ya dai'na shaigantasu, amma ina haka ya sa kafa ya yi ball da ita. Ya ce bai san wannan ba. Ganin zai yi mata illah ne yasa ta baro bakin gate ɗin gidan a guje kamar mahaukaciya, tana gudu tana kuka, Ammien su Imran ta yi ƙoƙarin dakatar da Abban, amma ina, sam abin ya ci tura, yaki sauraronta, ya hau dokin zuciya, dama idan baku manta ba, a baya na gaya maku, shi mutun ne mai bala'in zuciya da zafin rai!. Bazama cikin gari gwaggo ta yi kamar mahaukaciya, da kamar zata je gidan Abbi, amma da ta tuna cewa, da Abbi da Abba halinsu iri ɗaya, sai ta gwammaci gara ta shiga duniya. Tamkar zautatciya haka ta zama. Tun tana iya gane hanyar da take tafiya a kai, har ta dai'na ganewa, ta fara ganin dishi dishi, da alama hankali ya gushe a tattare da ita. Daga karshe ma sai ta zube kasa a kasar wata bishiya ta bakin titi, kan ka ce me ta sume a wajen, saboda tukukin bakin ciki da yake cikin zuciyar baiwar Allah nan!!. Nisawa ta yi tare da goge hawayen fuskarta, sannan ta ce "Tun daga wannan suma da na yi, ban sake sanin in da kai'na yake ba, sai da na shafi shekara kwance a gadon asibiti, lokacin da na farka kuma, da fuskar kanina Nawazuddeen na fara cin karo, shi ne yake gaya mani shakarata ɗaya a sume a gadon asibiti, tsabar bakin ciki ban ko tambaye shi daga ina ya tsintoni ba, kawai na bar maganar, shi ya cigaba da kula da ni, na bashi labarin komai na daga auren da na yi, har da yayana TRIPLETS, hakuri ya yi ta bani, ya kuma biya kuɗin jirgi muka je har Washington DC, sai dai bamu sami su Dr William ba, mun yi tambayar duniyar nan, basu ko ɗaya daga cikin gidajen iyayensu da suka bari, kowa sai ya ce bai san in da suke ba. Daga karshe dai muka hakura muka dawo, zuciyata cike da kaunar yarana, ina jin tamkar zan mutu. Kullum Nawazuddeen ajiye duk wani abin da zai yi yake yi, ya dawo gida ya zauna ya yi ta bani hakuri, yana kwantar mani da hankali, a lokacin ko aure bai yi ba, shi kaɗai yake rayuwarsa shi ma. Haka muka cigaba da rayuwa a tare, na zama tamkar mahaifiyarsa, yana yi mani biyayya over, ban taɓa yin magana ya saɓa ba, ya mayar dani islami, a nan na sami ilimin addini sosai da sosai, daga nan kuma nayi danasanin abubuwa da dama na rayuwar da muka yi da Dr, da na sami ilimin addini sosai, na fahimci wani abin, na fahimci da ni da Dr mun aikata saɓon Allah sosai a cikin soyayyarmu, kila shi ne yasa Allah ya jarrabeni da wannan kaddara, dama irin wannan saɓon da muka aikata ai ba zai taɓa yiwuwa aurenmu ta yi albaraka ba". Ta kai karshen maganar tana goge hawayen fuskarta. Kowa da yake cikin palon sai da zuciyarsa ta raunata, ta kuma taɓu sosai, daddyn jelly kam kuka ya yi sosai, dan kun san shi dama, akwai shi da saurin kuka. Dayawa daga cikin jama'ar palon sun zub da hawaye. Gyaran murya Brr Naurat ta yi, cikin dattaku da girma ta ce "Dr William ka ji bayanan A'isha ko? Me zaka ce kai kuma? Bayan A'isha ta baka yaran, ka gaya mana ya ka yi da su? Ina suke? Menene kuma ya faru bayan barin A'isha gidan? Ina yaron da ka illatar da sanda? Meyasame shi? Muna jiran bayananka kai ma!!". Nan fa gabaɗaya kallo ya koma kansa. Harta ƴaƴan nasa ma shi suke kallo. Ya ɗan ɗauki ƴan mintoci kafin ya ce "Ni duk abin da ta faɗa ban sani ba, ni ban santa ba! Kuma ban taɓa ganinta ba sai yau, wata kila da wani Dr William ɗin take yi ba ni ba!"........TASHIN SENSE Brr Naurat tana ƙoƙarin sake yin magana Areef ya daka musu tsawa cikin tsananin ɓacin rai tare da tashin hankali. "Daddy kada ka mayar da mu mahaukata mana? How comes zata bada dukka wannan labari kuma ka ce karya ne? How comes ta san su kaka? How comes ta zayyano sunayen unguwar da gidajen kaka yake da sauransu?Kawai daddy ka gaya mana gaskiya!!". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa tsaye yana huci tamkar wani mayunwacin zaki. Tamkar ba Areef mai saukin kai da wasa da dariya ba. Miƙewa shi ma daddyn ya yi yana faɗin "James a said a don't know her, what do you want me to tell you again?!". Ya yi maganar cikin tsawa shi ma. Buɗe baki Areef ɗin ya yi da nufin ya yi magana. Bai kai ga yin maganar ba sai ganin Lion suka yi ya damki wuyar daddyn nasu da hannu ɗaya, ya maka shi da jikin bango tare da matse shi. Gabaɗaya ya canza lokacin guda, tamkar ba NooRin Meesha ba, idanuwansa sun yi jajir da su kamar wuta, har wasu jijiyoyi sirara ne suka fito mashi a damatsan hannunsa da kuma wuyarsa, sai wani irin numfashi yake yi mai kama da gurnanin zaki, jikinsa sai wani tsuma yake yi, ran maza ya ɓaci!. Shi kuwa Aseef miƙewa ya yi daga kwanciyar da ya yi daga saman cinyar daddyn Rimsha, ya kifa kansa da jikin hannun sofa yana hawaye, sam baya son ganin abin da yake faruwa. Sosai Lion ya shake daddy har sai da idanunsa suka juye, harshensa ya zazzago waje, yana daf da bakontan lahira. Ga shi Lion ɗin yaki ko da sassauta mashi, kuma ya ki yin magana, saboda tsananin ɓacin rai, dan daddy yana neman raina masu wayo. Can kuma cikin tsawa ya ce da daddyn nasa. "Tell us the truth, if not I'll make you regret! Me muka yi maka da zaka yi mana haka? Me bamu yi maka ba? Saboda kai muka ɓoye cewa mun musulta na tsawon shekara ɗaya yanzu, duk gudun kada mu sa ciwonka ya tashi, dan mun sanka da kishin addininka, zaka iya mutuwa idan ka ji mun zama musulmai, saboda kai muka ɓoye hakan! Duk dan mu faranta maka rai, mu kuma sauke hakkin iyaye da yake a kanmu, amma kai kuma ka gaya mana meyasa ka yi mana haka? Meyasa ka bari muka taso cikin kafurci? Ka yi mana karya! Ka ɓoye mana ainahin mahaifiyarmu, ka haɗamu da wata banza a matsayin uwa, bayan kuma sisterka ce uwa ɗaya uba ɗaya! Ka cutar da rayuwarmu! Ka cusa mana tsanar abubuwa da dama a rayuwarmu wanda bai kamata mu tsanesu ba! Ka ɓoye mana gaskiya, amma da yake, ita gaskiya komai daren daɗewa sai Allah ya bayyanata, sai ga shi Allah ya haɗani da Imran, na kaunace Imran sosai! Bana son kowa bayan TRIPLETS na, amma rana tsaka na tsinci kaina da son Imran, ta dalilinsa na dawo ainahin addinina, ta dalilinsa na tako kafata na zo Nigeria, wanda a baya ban taɓa tunanin zan zo ba, da Allah ya tashi kamaka daddy, kai ma da kafarka ka tako kazo Nigeria, ba wanda ya sanyaka dole, daga kan Imran kuma ban sake kaunar wani ɗan adam ba sai Uncle ɗin James, haka kawai shi ma rana tsaka na kaunace shi, har mamaki nake yi wani lokaci, na kasa banbance da shi da Imran wa ye na fi so a cikinsu, ashe dan Allah ya gwada mana wani aya ne yasa muke kaunarsu......". Da kyar ya kai karshen maganar saboda wani tukukin bakin ciki daya tokare mashi maƙoshi. Daga haka ya yi shiru bai sake yin magana ba, sai dai sauke dogon numfashi tamkar gurnanin zaki da yake yi, ya kuma kara shake daddyn da karfi sosai!!. Kallon Areef Abban Imran ya yi cike da tsananin tashin hankali ya ce "Areef ka dakatar da ɗan uwanka, idan ba haka ba, zai yi kisan kai, dan daddynku dab yake da ya mutu!". Ganin da gaske hakan ne yasa Areef ɗin ya nufi Lion ɗin da sauri dan kuwa da gaske ne daddyn nasu na dab da mutuwa. "Lion wlh zai iya mutuwa, dan girman Allah ka sake shi haka nan ya isa, ba kaga yanda yake numfashi ba ne?". A wani irin haukace ya damko wuyar Areef ɗin ma, da ɗayar hannunsa, ya haɗesu su dukkansu biyu yana jin wani bakin azaba a cikin zuciyarsa, tafarfasa zuciyarsa take yi tamkar an ɗaura dalma a wuta! Sam baya ji kuma baya gani, idanuwansa sun rufe, yau ne ya fito da ainahin zuciyarsa fili! Duk wajen an rasa mai iya gigin yi mishi magana, dama Areef ɗin ne kawai yake da ɗan kwarin gwiwar tinkararsa a irin wannan yanayi da yake ciki, to shi ma ga shi ya haɗa da shi ya shake. Aseef kam dama tun ɗazun daya kifa kansa da jikin hannun sofa, bai sake ɗagowa ba, duk abin da suke yi yana jinsu, amma ba zai iya ɗagowa ba, bakinciki zata iya sanyawa ya haɗiyi zuciya ya mutu idan ya ga halin da suke ciki, to gara mishi ya cigaba da runtse idanuwansa kawai zai fi mashi alkhairi, Rimsha, Jehan da Akila dukkansu guduwa suka yi, suka fita daga palon, ko wace ta san halin masoyin nata sarai, sun san me zai biyo baya idan suka tsaya, gara musu su gudu abinsu. Yau su Abba sun ga tashin hankali, an rasa mai bakin magana a cikinsu, su Imran duk sun haɗa malaman jikinsu waje guda, dan faɗar ta manya ce!!, TGA da yake jarumi ma, kirjinsa sai dukan uku uku yake yi, cikinsa na murɗawa, bare kuma saura, ai su tsoronsu a tsananin bayyane ma yake. Daddyn Rimsha ne kawai mai ɗan kwarin gwiwan da ya kalli Gwaggo ya ce mata ta yi wa Lion magana wata kila zai ɗan sassauto ya sakesu, idan ba haka ba to tabbas dukkansu zasu mutu, wlh har Areef ɗin, dan ba shakar wasa ya yi musu ba....... ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E5 Daddyn Rimsha ne kawai mai ɗan kwarin gwiwan da ya yi ta maza, ya kalli Gwaggo ya ce mata ta yi wa Lion magana, wata kila zai ɗan sassauto ya sakesu, idan ba haka ba, to tabbas dukkansu zasu mutu wlh har Areef ɗin, dan ba shakar wasa ya yi musu ba. Ganin da gaske har da Areef zai iya mutuwa ne yasa ta miƙe da sauri ta isa wajen nasu. Shi kuwa Areef ɗin sam bai yi ƙoƙarin kwatar kansa ba, dan yasan duk bala'i Lion ba zai taɓa kashe shi ba! In yaga zai mutu da gaske, dole ya sake shi, sai kawai ya zuba mashi idanu yana kallonsa, kuma dama hakan shi ne dai'dai a cewarsa, ya kamata su koyawa Lion ɗin tausayi ne, idan Areef ɗin ya zuba mashi idanu yana kallonsa, to zai ji tausayinsa ya sake shi, a haka zai koyi tausayi sosai a cewarsu. Daga ɗan bayan Lion ɗin ta tsaya, gabaɗaya idanun jama'ar palon yana a kansu, kowa so yake ya ga ya Lion zai yi idan gwaggo ta yi mashi magana....... Ni ma PRINCESS TEEMA so nake yi naga ya zai yi😂 "Saif" ta ambata a hankali, tamkar bata son yin magana, kuma kamar tana jin tsoron yi mashi maganar. Hakika ya ji sunan har cikin ransa, duk fushi da yake ciki bai hana ya ji muryar mahaifiyar tasa ta ratsa dukka ilahirin jikinsa ba, dama shi already zuciyarsa ta yardan mashi cewa ita ce mahaifiyarsu!..... Ganin bai amsa ba, kuma bai sakesu bane, yasa ta ɗan kara mastowa, gabaɗaya a tsorace take da ganin yanayin da ɗan nata ya shiga, kirjinta sai dukan uku uku yake yi, amma hakan bai hana ta daure ta dafa kafaɗarsa da hannu ɗaya ba. Cikin sanyin murya ta ce "Saif ka sakesu, kada ka yi masu illa ka ji ko?". Wani irin dogon numfashi ya ja tare da saukewa a hankali, har cikin kashi da ɓargonsa ya ji sakonta! Ya ji sautin muryarta!. Ba musu ya zame hannayensa daga wuyoyin nasu. Nan take suka zube kasa, shi daddy ya suma already dama, shi kuma Areef tari ya fara yi da karfi karfi ba kakkautawa. Uwa kenan, yau Lion ne yana cikin tsananin fushi haka har ayi mashi magana, kuma ya ji maganar ta ratsa shi? Lallai dai kam, uwa ta wuce wasa wlh!!. Da sauri daddyn Rimsha ya yi kan Areef ɗin bayan ya ɗauko mashi ruwa a cikin fridge mai sanyi. Cike da kulawa ya dafa shi tare da kafa mashi robar ruwan a baki yana yi mashi sannu. Shi kuwa Lion juyawa ya yi da nufin ya bar wajen, ya nufi bedroom nasa. Riko hannunsa ɗaya gwaggon ta yi, tana mai sake ambatar sunansa kirjinta na bugawa, dan tana tsoron kada su ce ba za su karɓeta a matsayin uwa ba, idan hakan ta kasance ba makawa zata iya mutuwa, dan tana bala'in sonsu, ko wani rana na duniya sai ta yi masu addu'a da fatan alkhairi tare da fatan Allah ya tsare mata su a duk in da suke, daidai da second guda basu taɓa barin cikin tunaninta ba, suna ranta fiye da tunanin mai tunani..... Allah sarki abin tausayi!. Juyowa ya yi gareta cikin natsuwa, zuba mata idanu ya yi na ƴan sakanni kafin kuma ya tsinci kansa da rungumeta a jikinsa. Rungume shi ita ma ta yi, tare da sauke wani nauyayyar ajiyar zuciya mai cike da tarin abubuwa kala kala a cikinsa. Nan take kuma ta fara ruwan hawaye. Wani irin sanyi shi kuma ya ji tana ratsa zuciyarsa da ya rungumeta, hakan ce ta kara tabbatar mashi da cewa lallai ita ce mahaifiyarsu, domin kuwa tun da ya taso har izuwa yau, ba'a taɓa rana guda da ya shiga cikin fushi da ɓacin rai, ace zuciyarsa ta yi sanyi lokaci guda ba, ba'a taɓa ba! Wani lokaci ma, idan ya fusata sai ya zubawa tsakiyar kansa ruwan mai tsananin sanyi, saboda ya sami sauki, dan tamkar ci da wuta zuciyarsa take yi idan ransa ya ɓaci. Amma yau rana ta farko, ya shiga ɓacin rai, daga jin voice na gwaggo kuma ya sauko cikin sauki haka, dole ba'a banza ba! Dole ita ce mahaifiyarsu ta gaskiya! Ya sami nutsuwa sosai a kanta! Yana tsananin jinta a ransa ne fiye da tunanin mai tunani! Ji yake yi tamkar ya ɗauketa a saman kafaɗarsa su yi ta kewaye duniya kawai, saboda tsantsar so da yake yi mata, ashe ba'a banza yake kaunar Rimsha ba! Ashe ba'a banza ba duk da basu son mutane, amma suka yarda da daddyn Rimsha ya zauna a wajensu, sannan kuma suka kaunace shi sosai! Ashe ba'a banza ya ji cewa dole ya tsaya tsayin daka wajen ganin ya kwatarwa da daddyn Rimsha hakkinsa na zaluntarsa da aka yi ba. Ba'a banza su Areef suke tsananin kaunar daddyn Rimsha ba, ko dan kula da mahaifiyarsu da ya yi tamkar ba gobe, ai dole ma su ji kaunarsa, uwa ta wuce wasa!!. Daddyn Rimsha ya kula da gwaggon over, shiyasa Allah dan ya saka mashi, ya jarrabi TRIPLETS ɗin da kaunarsa over!. Allah sarki rayuwa kenan, Allah mai kyauta mai kari, mai saka maka ta in da baka yi zato ba, Shiyasa ake son komai zaka yi, to ka yi shi domin Allah, dan idan ya tashi saka maka, zai yi maka babbar sakayyar da baka taɓa zato ba, a gaskiya daddyn Rimsha ɗan uwa ne na kirki da kowa zai yi fatar samun irinsa, duk bakinciki da kunci da su Abban Imran suka jefa shi a ciki, suka raba shi da mahaifinsa da Hassan nasa da suka kwanta ciki ɗaya, duk da hakan bai hana shi yana taimaka masu ba, kuma dan Allah yake yi, shiyasa da ya gamu da jarabawa na rabuwa da familynsa, sai Allah ya kare mashi familyn nasa, suka shiga hannun na gari, duk in da suka je, an rukesu hannun biyu tsakani da Allah, dan shi ma ya ruke mutane da yawa tsakani da Allah, bugu da kari, sai Allah ya bashi surukai ɗaya tamkar da million, wanda ko wani uba zai yi wa ƴaƴansa fatan samun mazajen aure irinsu, Allah ka cigaba da dafa mana, kasa komai zamu yi, mu yi shi domin ka, dan mu samu rahamarka a koda yaushe.❤️ STORY A hankali ya kwantar da kansa a saman kafaɗar gwaggon, yana sauke numfashi mai kama da gurnanin zaki. Hannu ta kai ta fara shafa lallausan gashin kansa, da yake ya rage tsawonsa ne, ya ɗan kwanto a kafaɗarta, to tana iya taɓa kansa. Jin sautin kukan gwaggon yana tashi a hankali hankali ne yasa ya ɗan ɗago kan nasa daga saman kafaɗar tata. Ganin da gaske take kuka ne yasa ya sanya hannu ya fara goge mata hawayen nata ba tare da ya yi magana ba. Tamkar jira take yi wani sabon kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro ne ya kubce mata. Zafafan hawaye ne wasu suna bin wasu a kuncinta. Hakika an cuceta ba kaɗan ba, an cutar da rayuwarta ba karya, kuma a duk wannan abin da ya faru, sam bata da laifi, duba da yanayin karantar shekarunta a lokacin, ga ƙarancin ilimin addini, sannan bata wani rayuwa da mahaifiyarta sosai ba, bata taɓa haihuwa ba sai a kan TRIPLETS ɗin, a lokacin da ta mayarwa da Dr yaran, bata gama sanin zafinsu ba, sannan zuciya ce ta ɗebeta, wanda kuma dama wannan dole ce, tama yi namijin kokarin da ta hakura ta haife cikin, duk cin amanar da ya yi mata, ta daure ta haife cikin, gaskiya ta yi namijin kokari, abin a jinjina mata nema!!. Ganin haka yasa ya ɗan raba jikinsu kaɗan tare da ɗan duƙawa ya ɗauketa cancak tamkar karamar yarinya, ya nufi bedroom nasa da ita. Gabaɗaya palon binsu da kallo suka yi, shi ma Areef binsu da kallo ya yi ya kasa motsawa, dan shi kaɗai yasan raɗaɗin da yake ji a cikin zuciyarsa. Shi dama Aseef bawan Allah sam bai ɗago kai ba ma, bare yasan me suke yi, yana kife yana kuka, Allah sarki bayin Allah!. Ita ma Brr Naurat sai bin su da idanu take yi, tana jin abin tamkar a mafarki ne!. Lion bai sauke gwaggo a ko'ina ba, sai a bakin katafaren bed nasa da yake shinfiɗe da white bed sheet mai matuƙar kyau da tsada, kamar yanda kuka sani ne, sai zuba uban daddaɗar kamshi bedroom ɗin nasa yake yi, ko'ina a gyare tsab, tsab, fes, fes!!. A gefenta ya zauna tare da ɗan juyowa suna fuskantar juna. Hannayenta ya riko cikin nasa, har lokacin zubar da hawaye take yi tamkar famfo aka bude. Cikin nutsuwa da sanyi murya ya ce "Ba zan hanaki kuka ba, ki yi sosai, dan yana rage raɗaɗi, na san duk raɗaɗin da muke ji a yanzu, ba mu kai kwatan naki ba, so just cry, cry more!". Ya kai karshen maganar tare da sakin hannayen nata ya rungumota a jikinsa yana sauke ajiyar zuciya. Kankame shi sosai ta yi tana mai cigaba da kukanta yana sauraronta, dan yasan kukan shi ne zai sa ta sami sassaucin abin da take ji a cikin zuciyarta, yau ta tuna baya, an cutar da ita over baiwar Allah. A haka gabaɗaya familyn suka shigo bedroom ɗin suka samesu, har da su Rimsha da Brr Naurat, duk sun biyo sahunsu, sun baro Dr William da yake sume, sai dai Areef ya ɗauke shi ya kwantar da shi a saman sofa, sannan suka biyo Lion ɗin. TGA da Uncle Herry suna wajen Dr William ɗin, su kuma su John wucewa suka yi nasu bedroom ɗin, wai ba za su zo ɗakin ba!. A ɗayan gefen gwaggon Areef ya zauna, ya zamana sun sakata a tsakiya. Shi kuma Aseef saman bed ɗin gabaɗaya ya haye, ya kwanta, kansa tamkar zata fashe mashi saboda ciwo, har wani jiri yake gani, yana ganin dishi dishi. Ɗago kai daga saman kirjin Lion ɗin ta yi tare da juyowa zuwa ga Areef dake gefenta. Hannu Areef ɗin ya kai ya fara goge mata hawaye yana faɗin dan Allah ta yi shiru, kukan ya isa haka nan, ba ya son ganin kukan nata, dan ba zai iya jura ba, zuciyarsa tana yi mashi zafi sosai idan yana ganin kukan. Yana magana yana goge mata hawaye, shi kuwa Lion ya dukar da kansa kasa yana tunani a kan abubuwan da gwaggon ta faɗa daga farko har karshe, yana nazari a kansu. Muryar gwaggon ne ta daki dodan kunnuwansu, a in da ta ce "Ina ɗayan ɗana? Ina cikon TRIPLETS ɗin?". Juyawa Areef ya yi izuwa ga Aseef dake kwance tamkar zai mutu, idanunsa sun yi jajir kamar jini. A sanyaye ya ce mata ga shi nan. Cikin ruɗu ta ce "Me ya same shi ya kwanta haka?". Ta yi maganar tare da kai hannu tana taɓa kansa. Turo baki ya yi tamkar yanda kuka sani ne, gidan shagwaɓa ba, ko a gadon asibiti yake sai ya yi ta, yanzu ma dai cikin shagwaɓa ya ce "Please ku dai'na taɓani, Allah idan ba haka ba in na fara kuka ba zan dai'na ba!". Shiru kawai gwaggo ta yi, dan kuwa yanda Aseef ya yi maganar sak Dr William time da suke zuba soyayya, sai ya tuna mata da baya. "My son mommarka ce fa take taɓaka, tashi ka gaya mini menene yake damunka?". Cewar gwaggon. Kara turo baki sosai ya yi yana faɗin "Ni momma to ki barni mana, bana so ne a taɓani". Girgiza kai kawai Areef ya yi, yanzu ya dai'na mamakin halin Aseef, tun da ya ji cewa daddynsu ruwa biyu ne, ɗan shagwaɓa ne ta wani fannin, ta wani fannin kuma ɗan bala'i, mafaɗaci, to kun ga kuwa shi Aseef ai shi ya yi gado, dan kuwa shi ma ruwa biyu ne, idan ka taɓo shi, ya iya faɗa, sai dai kawai ya fi Dr yawan shagwaɓa ne, dama kuma, ɗan na gada, ya fi ɗan na koya. "Tashi to ka zo na goyaka". Cewar gwaggon, ta yi maganar cikin zolaya. Ɗan ɗago kansa ya yi. A hankali ya matso kusa da ita yana faɗin "Kwanciya a saman cinyarki ma is okey my Momma". Matsa mashi waje kaɗan Areef ya yi, a nan ne ya samu dama ya kwantar da kansa a saman cinyar tata yana mai cigaba da turo ɗan bakinsa abinsa. Shiru bedroom ɗin ya yi na ɗan tsawon lokaci kafin Brr Naurat dake zaune saman sofa ta ce "To yanzu ina son sanin wani abu guda a kan wannan case ɗin". Ɗago kai dukkansu suka yi tare da kai kallonsu gareta. Lion ne ya amsa mata da cewa "No, just ki bar maganar nan a yanzu, ki bari sai gaba". Jinjina mashi kai ta yi, dan ta lura dukkansu basu a cikin nutsuwarsu. Ɗago idanu da gwaggon zata yi ne idaunta suka sauka a kan chain dake wuyar Lion ɗin, wani irin nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke wanda yasa TRIPLETS ɗin suka ɗago suna kallonta. Su daddyn Rimsha har suna rige rigen haɗa baki wajen tambayarta lafiya. Cool murmushi ta sakarwa daddyn Rimsha tana faɗin "Ina Jehan?". Da hannu daddyn ya nuna nata Jehan ɗin dake zaune kusa da Rimsha dake kusa da Brr Naurat. Alama ta yi wa Jehan ɗin da hannu a kan ta zo. Da sauri ta miƙe ta zo. Tsabar iya shege irin na Jehan ɗin a saman cinyar gwaggon kusa da Aseef ta gefe ta zauna tare da saƙalo wuyar gwaggon da hannunta ɗaya, tana wani kwaɓe fuska, tana kuma raɗa wa gwaggon magana a kunne. Binsu da idanu Areef ya yi yana tunanin irin tsiyar da ya rinƙa yi mata a kan daddynta a baya, yanzu reshe ta juye da mujiya kenan........ E NIMA PRINCESS TEEMA NA CE RESHE TA JUYE DA MUJIYA KUWA, DAN GWAGGO DA JEHAN 5 AND 6 NE, LALLAI JEHAN ZATA RAMA ABIN DA KA RINƘA YI MATA NA HANATA ZUWA WAJEN DADDYNTA😂 YANZU WASAN ZAI FARA😂 KAI ABUBUWA SUNA YI MANI DAƊI😂 AREEF KA JIRA ƊAUKAR FANSA😎🥳 DAN WLH GWAGGO DAI TANA BAYAN JEHAN💃🥳 Kome Jehan ɗin ta raɗa mata sai ga gwaggon ta fashe da dariya tana kallon Areef. Daga gani yasan gulmarsa ta kai, da wani idanunta kamar ball a cewarsa. Hannu gwaggon ta kai ta ciro sarkar dake wuyar Jehan ɗin, dama kun san nasu Jehan mai round ne, na su Lion kuma mai tambarin heart, sannan na su Jehan ɗin yana da faɗi fiye da na su Lion ɗin, kuma na su Lion zallar zinari ne, na su Jehan iya igiyar ce kawai zinari. Ciro sarkar Jehan ɗin ta yi a in da ta sanya karfi cikin dabara ta buɗe kan round na sarkar. Nan take wani tambarin ɓari na heart ya bayyana a cikin round ɗin, sai kyalli yake yi har yana ɗaukar idanu. Ciro heart ɗin ta yi sannan ta mayar da sarkar ta rufe tare da mayarwa da Jehan ɗin abinta. A hankali ta ambaci sunan Lion, ɗagowa ya yi yana kallonta. Kama sarkar wuyarsa ta yi tare da sanya ɓarin heart ɗin da ta ciro daga sarkar Jehan ɗin, ta mayar ta jona. Nan take chain ɗin ya koma tamkar ba'a taɓa raba shi biyu ba, ya zama kamar yanda yake. Sam Lion bai yi mamaki ba, dan yasan ita ce mahaifiyarsu, kuma dama yasan a wajenta kawai za'a sami rabin sarkar nan, dan har company ya je sun kasa buga mashi ɓarin da zai yi dai'dai da chain ɗin, daga karshe dai ya hakura ya bar zancen kawai, ashe yana jikin sarkar Jehan, gwaggo ta iya ajiya a in da kowa ba zai zata ba, kuma duk in da za su je yana tare da su. Cikin shagwaɓa Jehan ɗin ta ce "Gwaggo dama ashe abu kika ajiye a ciki kenan? Shi ne har da wani cemini ko za'a kasheni kada na yarda na bada sarkar nan ko? Wato yanzu dama a kan wannan abin ne har da cewa ko za'a kashe ni ko? Allah na ɓata dake". Ta kai karshen maganar tare da miƙewa dan ta bar wajen. Sake baki Areef ya yi yana kallon ikon Allah, mamaki yake yi, ashe dama ƴar rigimar nan tasa ta iya shagwaɓa kenan? Ashe da gangan take yi mashi abu kamar wata boss? Ai kuwa zai yi maganinta, ya faɗa a ransa. Bai san cewa da iya gwaggo kawai take shagwaɓar ba, bayan gwaggon ba wanda yake ganin hakwaranta ma bare shagwaɓa, sai daddynta da shi ma ba koda yaushe ba, sun fi shiri da gwaggon, mum nasu kam dama kun sani basu wani shaku ba, dan ita ta gwaggo ce. "Haba babyn gwaggo da daddynta, zo kiji wata magana". Cewar gwaggon. Kin zuwa ta yi ita a dole ta yi fushi, fuuu ta wuce zata bar wajen. Da hannu ɗaya Areef ya rikota yana faɗin "To ƴar rigima, ke kowa sai kin yi mashi ne? Sai kin nunawa kowa halinki ko?". Gwaggon ce ta ce "A'a babu ruwanka da babyna, tare ka ganmu, ka kyale mani ita, kada ka takura mata, ba wani rigimar da tayi, haka take dama". A takaice ya ce "Momma to ai ni kuma matata ce, kin ga yanzu na kwace maki ita kenan". Zaro idanu ta yi tana faɗin "Jehan ɗin tawa ce matarka? Waye ya baka ita? Wlh ba zata saku ba, a kan me? Ni ni zan bada auren Jehan, duk wanda ya bayar ba ni ba, to auren bai ɗauru ba". Jawo Jehan ɗin ya yi ya faɗa jikinsa yana faɗin "Momma uncle nane mana nima ya bani ita, ƴar rigima ba, kuma aure ya ɗauru, dan ma kin dawo da wuri ne, ai da sai dai ki zo ki ganta da ciki ko baby's". Salati gwaggon tasa, sam ƴaƴan nan nata basu da kunya ko kaɗan, shi ko kunyar iyayen Jehan ɗin su Abba da suke cike a wajen bai yi ba, kawai ya faɗi son ransa ne. Cikin fushi Jehan ɗin ta ce "Ni ka sake Ni!" Yanda ta yi maganar on a serious note, babu wasa a cikin maganarta, ya sha mamaki na jin abin da ta ce, sai dai bai kawo komai a ransa ba, kuma bai saketa ɗin ba, ita ma Gwaggo yanda Jehan ɗin ta yi maganar yasa ta fahimci da akwai matsala kenan a tsakaninta da Areef ɗin, kowa da yake palon harta daddyn Rimsha ya sha ruwan mamakin yanda Jehan ɗin ta dakawa Areef ɗin tsawa, ko a baya da take cewa bata son shi, bata taɓa yi mashi irin wannan magana a gatse har haka ba, ita kuwa ita kaɗai tasan dalilin da yasa ta yi mashi wannan magana. Gwaggon na ƙoƙarin kara yin magana Aseef ya katse su da cewa "Areef ka tuna mini ma, na ce yau zan yi wa Heartbeat surprise, har kasa na ji saukin jikina da ka tuna mani". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa zaune yana wani mustsuke idanu kamar wanda ya sha wani abin na maye. Shi dai Lion kamar babu shi a wajen, ya dukar da kai kasa kawai yana tunani. Da mamaki gwaggon ta ce da Aseef ɗin "Au kaima matar gareka?". Jinjina mata kai ya yi tare da matso da bakinsa saitin kunnenta yana mata raɗan akan ai yau ma yake son bawa matar tasa baby. Hasbunallahu. Kasa juyowa gwaggo ta yi bare ta haɗa idanu da shi, a hakan ma bata san cewa ya yi mata raɗan ne dan kada Akilar ta ji ba, ba dan Akilar tana wajen ba, ai da afili zai faɗi maganarsa, yo su ina ruwansu? Ina suka san me kunya? Ai sam basu san shi ba. Turawa ma da suke wasu abubuwa marasa ɗa'a a kan tsakiyar hanya, ai su nasu ma mai sauki ne, turawa ai iskancinsu a bayyane yake. Kawar da zancen gwaggon ta yi da cewa "To gaskiya wannan aure dai bai ɗauru ba, dan ni ban bada Jehan da Rimsha ba!". Areef zai yi magana daddyn Rimsha ya katse shi da cewa "A'a ni ai na bawa ɗana, kuma aure ya ɗauru, dan haka ba wani sharhi, Jehan matar Areef ne". Kafewa gwaggo ta yi a kan ita sam bata bayar ba, dole a zo a tsugunna a gabata a nemi aure Rimsha da Jehan, kuma sai ta tantance masu neman auren zata ba su, sai ta yi musu jarabawa masu tsanani tsauri, idan sun ci, sai a basu mata, idan ba su ci ba, shikenan ta rike ƴaƴanta, ta nema masu miji na gari. Ganin Lion yana ƙoƙarin mikewa ya bar wajen ne yasa gwaggon ta ce "Saif zauna mu yi magana ko?". Ba musu ya koma ya zauna yana faɗin "Mummy my head is penning me to much, bana son hayaniya, idan kuna yawan magana bazan iya zama a wajen ba, that's why nake son baku waje!". Hannu ta kai ta shafa kan nasa tana faɗin "Tom shikenan zamu yi maganar anjuma, je ka huta yanzu ga ji?". Ba tare da ya amsa ba ya miƙe ya fuce daga ɗakin abinsa. Shi kuwa Areef raɗa ya fara yi wa Jehan a kunne bayan ya matseta a jikinsa. Babu kunya a gaban gabaɗaya iyayenta. Ita kuwa ko kallo bai samu ta ɗago ta yi mashi ba, haushinsa ma take ji, burinta kawai ya saketa, shi kuma yaki, ya kankameta gam kamar wani ya ce zai kwace mashi ita. Nan fa hira ya ɓarke a cikin bedroom ɗin, ga Brr Naurat a wajen, ai sai ta fara basu labarin rayuwarta a Russia, su kuma suka gaya mata bayan tafiyarta Dr Salman ya rasu. Nan take ƴar tsohuwa ta fara kuka. Taruwa suka yi a kanta suna bata hakuri. Jikokin nata kuma sai dariya suke yi mata, wai ta tuna da tsohon zuwa, Imran da Irfan sai tsiya suke yi mata. Lallaɓawa Anaya ta yi ta fice daga cikin bedroom ɗin. Tamkar wata ɓarauniya haka take sanɗo. Palon kasa ta sauko, sai waige waige take yi tana neman Mark, dan ɗazun da suka shigo da daddynta, ta gan shi a palon kasan, ba halin ta yi mashi magana ne saboda daddynta. Shi kuma bai ganta ba, yana latsa waya, ba sai na sake gaya maku ba, irin halin Lion ne da Mark, abin da yake gabansu kawai suke yi, so ko mutun zai wuce ta kusa da su, sam basu ɗago kai bare su kalle shi, hakan tasa har su Anaya suka haura sama bai ɗago kai ba. Ta zo zata nufi waje ta hango shi a cikin kitchen yana aiki, wani irin tsantsar farinciki ne ya rufeta, sai sakin cool murmushi take yi. Cikin sanɗo ta lallaɓa izuwa cikin kitchen ɗin. Sarai ya ji alamar mutun, dan su suna amfani ne da sautin numfashi mutun, dan sun iya yakin sunkuru. Amma bai kawo cewa ita ba ce, ya yi tunanin Rimsha ce ko Jehan or Akila, dan sune kawai masu shigowa cikin kitchen ɗin. Hatta kariso kusa da shi bai juyo ya kalli wacece bane. Hannu ta sa ta tsaƙalo wuyarsa tare da ɗale jikinsa ta baya tana murmushi. A tsananin fusace ya juyo tare da damko wuyarta, ya dawo da ita ta gaban fuskarsa. Ta yi matukar razana na ganin yanda ya shaketa ɗin, nan take idanunta suka firfito waje, ta tsorata ainun, kirjinta sai dukan uku uku yake yi. Yana kawota saitin face nasa ya ga ashe ita ce, ga shi ta zaro mashi idanu tamkar za su faɗo kasa. Ai a dubu ya sake wuyar tata yana ɗan sunkuyar da kai kasa. Sam bai taɓa tunanin ita ɗin ba ce. Ganin tana ƙoƙarin zubawa kasa ne yasa a hanzarce ya rikota tare da jawowata jikinsa yana faɗin sorry. Ya yi maganar tare da sauke nauyayyar ajiyar zuciya, wani irin sanyi ya ji na jinta a jikinsa. "Haba my shi ne kake son kashe ni? Dan kawai nazo ganinka ko?". Ta yi maganar tamkar zata saka mashi kuka, tana yi tana turo baki. Cikin sanyin murya bawan Allah kasa kasa ya ce "Sorry my Queen, ban san ke ba ce ai, am so sorry". "Ni gaskiya ba zan hakura ba". Shiru ya ɗan yi na ƴan sakanni kafin daga bisani ya matso da face nasa daf da tata, kasa kasa kamar mai raɗa ya ce "Zaki fara ko? Wai har yanzu ba zaki dai'na wahalar da ni ba? Haba mana, kullum fa a waya sai kin yi ta yi mani kuka, kuma kin san bana son hakan, sai ki yi ta bani wahala, yanzu a zahiri ma ba zaki barni na huta ba?". (My peoples yau ga Mark ma da cewa mace sorry 🤔 duniya kenan😂 kai waye ya taɓa tunanin Mark da Lion za su furta wannan kalma ta sorry ga wani ma ba wata ba?🤔 Lallai mata mun ciri tuta, mu ɗin duniya ne, duk giman namiji da karfi izza da isarsa, muna iya juya shi son ranmu😂 dan haka dole a bimu 😂) Turo ɗan bakinta ta yi har sai da ta taɓa nasa, kasa kasa ita ma ta ce "Ai kai ne, sai ka yi ta yiwa mutun wani irin hali na basawa da bana ganewa". "Am so sorry zan dai'na duk abin da baki so kin ji ko? Amma a dai'na yi mani fushi da kuka please". Tana ƙoƙarin sake yin magana suka ji motsi a bayansu. Da sauri ya saketa, suna juyowa a tare, dan su ga wanene. Brady ne ya zo taya Mark ɗin aiki. Ajiyar zuciya Anayar ta sauke tare da wucewa da sauri, dan ta fice daga kitchen ɗin kada ma daddynta ko wani daga cikin family ya ganta. A hanzarce ya riko hannunta yana faɗin "Haba mana, ina kuma zaki je?". A takaice ta ce mashi cikin ɗaki zata koma, dan kada ma a nemeta, dama ta zo ganin shi ne kawai, tana tsananin kewarsa. Sake jawota jikinsa ya yi yana faɗin "Haba my Queen, bari na ɗan ganki tukun nan mana, kin san yanda nake kewarki kuwa? Please ki bari na ganki ko da na 1 hour ne". Sakalo wuyarsa ta fara kokarin yi, amma ina bata kai shi tsawo ba, ko ta sakalo ba zata iya tsayuwa a hakan ba, dan ko ta ɗaga kafa ba zai yi mata dai'dai ba. Ganin hakan yasa shi ya ɗan rankwafo mata da kansa kaɗan yana faɗin "Ƴar karama da ita a wajen, ba tsawo". Turo baki ta yi tare da jan gashin kansa ta wajen bayan wuyarsa. Wash ya ɗan furta kafin ya matseta a jikinsa da karfi. A can cikin bedroom ɗin Lion kuwa, sai hira ake yi, tamkar za su cinye junansu saboda tsantsar so da kauna, sai dai ko kaɗan basu taɓo hirar abin da ya faru a baya na dan gane da rayuwarsu Abba, ma'ana rayuwar gidan Dr Salman na baya, sam basu taɓo wannan hiran ba, saboda yau suna cikin tsantsar farinciki, ba su son tuna abin bakinciki. Shi dai Aseef ya makale a jikin mommansa abinsa yana ta zuba mata shagwaɓa, shi kuma Areef sai tsokanar Jehan yake yi bayan gwaggo ta gama gabatar masu da gabaɗaya uncles nasu. Shi kuma daddyn Rimsha da daddyn Anaya tamkar za su haɗiye juna, saboda kauna. Haka suka kasance har tsawo good 2 hours, kiraye kirayen sallar mangariba ne ya tashe su daga hirar ta su. Mazan suka wuce masallaci, matan kuma suka nufi bedrooms na su Rimsha. Ƴan matan kuma wato su Rimsha, suka wuce bedroom na daddynta dan su yi alwala a can. Gwaggo dai a nan ɗakin Lion ɗin ta yi alwala. Shi kuwa Lion tun da ya bar ɗakin, basu sake jin ɗuriyarsa ba. Rimsha tana shiga cikin toilet dan ta yi alwala, ta samu waje a saman chair, ta zauna ta fara tikar kuka kamar wadda aka yi wa sakon daddynta ya mutu.......... To fa kukan me kuma take yi hakan? Mu je dai zuwa. Ita ma Akila lokacin da ta shiga toilet ɗin da nufin tayi alwala bayan Rimsha ta fito, sai da ta yi kuka kamar ba gobe. Ita dai Jehan ko a jikinta, alwalarta ta yi ta fito. Umaisha ciki ya fara girma sosai, sai tura abinta take yi. Bayan sun yi sallah sun dawo ne aka haɗu gabaɗaya a palon sama. Nan fa su Abba suka ce za su wuce gida, kuma za su wuce da Brr Naurat. Suna cikin yin magana sai ga Lion ya shigo. Kusa da gwaggon ya zauna, kasa kasa ya tambayeta ya ta wuni?. Da fara'a ta amsa mashi da lafiya. Dawo da kallonsa a kan Areef ya yi kafin ya ce "Where is dad?". Yana bedroom nasa Areef ɗin ya bashi amsa. Jinjina kai ya yi ba tare da ya sake yin magana ba. Gwaggo ce ta gaya Lion ɗin uncles nasu za su koma, amma tare da ita za su tafi, kuma za su tafi da Brr Naurat. Girgiza kai ya yi yana faɗin "No momma, ke kina nan, kuma ita ma grandma a barta a nan!". Abban Imran ne ya karɓi zancen da cewa "A'a ita A'isha ta zauna a nan ɗin, dan kuna da bukatarta fiye damu, amma ita Brr zamu tafi da ita, dan mun fiku bukatarta muma, muna da bukatar mu zauna da ita, akwai abubuwa da dama da zamu tattauna da ita". Shiru ya yi bai sake cewa komai ba, gwaggon ce ta sake cewa, to shikenan hukuncin da Abba ya yanke ya yi. Miƙewa Lion ɗin ya yi tare da wucewa bedroom nasa abinsa. Cikin hanzari Areef ya bi bayansa, shi kuwa Aseef har wa yau yana kwance ya tada kai da cinyar gwaggon abinsa. Shiryawa su Abba suka yi, gabaɗayansu suka wuce izuwa gidan Abba, Jehan, Rimsha, Akila, duk sun bisu, sun bisu ba tare da su Abba sun sani ba, dan a motar Imran suka shiga, shi kansa Imran ɗin bai lura ba, dan familyn dukka sun haɗu, kuma shap ya mance da cewa su fa matan TRIPLETS ne......... Bayan anyi sallar isha, gwaggo ta idar da sallah a bedroom ɗin Lion, tana zaune a saman dadduma, su kuma sun tafi masallaci. Tana zaune a wajen har suka dawo, bakinsu ɗauke da sallama suka shigo cikin ɗakin. Su ukun dukka gwanin ban sha'awa. Fuska ɗauke da murmushi ta amsa masu sallamar tana mai binsu da kallo. Wani irin tsantsar farinciki na wuce misali take ji a tattare da ita, har wani ji take yi kamar ta mayar da su cikin cikinta, dan so da kauna. A bakin bed Areef da Lion suka zauna, shi kuwa Aseef saman bed ɗin bakiɗaya ya haye ya kwanta. Zubawa mahaifiyar tasu idanu suka yi suna ta kallonta. Sai zuba adduo'i take yi tare da askar har tsawon good 30 mins. Sannan ta shafa tare da mikewa ta dawo kusa da su. Suna ƙoƙarin matsa mata, dan ta zauna a tsakiyarsu, sai ta wuce ta zauna a saman bedside drawer. "Momma ki dawo saman bed mana?". Cewar Areef. Girgiza kai ta yi tana faɗin "Bari na zauna a nan, zan fi jin daɗin ganin fuskokinku da kyau". "To shikenan ai muma a wajen zamu fi jin daɗin ganinki our pleasure". Murmushi ta ɗan yi kafin ta ce "Son lafiya kuwa?". Ta yi maganar tana kallon Lion. Shiru ya ɗan yi na ƴan mintoci da ba su biyu ba, kafin ya amsa mata da "Nothing mum". Dawo da kallonta a kan Areef ta yi, girgiza mata kai ya yi yana nuna mata alamar shi fa Lion haka yake da rashin magana, dan haka kada ta wahalar da kanta ma wajen yin tunanin ko dai wani abin ne yake damunsa, haka Allah ya yi shi. Jinjina kai ta yi alamar gansuwa. "Son ya daddyn naku yake? Kun duba shi kuwa?". Ta sake tambayarsu Sai a lokacin ya ɗago da dara daran idanuwansa a kanta. Allah sarki soyayya, hakika Gwaggo tana tsananin son Dr har gobe, duk wannan abin da ya yi mata a baya, amma ta kasa samun natsuwa a yanzu dan yana cikin wani hali, ba zata iya sharesa yana cikin ciwo ba. Sam bata bawa Lion mamaki ba, dan dama a yanayin tarihin soyayyarsu, ya san fin hakan ma Gwaggo zata aikata, hakan ce ma tasa ya kula da lafiyar Daddyn nasu, ashe fitar da ya yi ɗazun, zuwa ya yi ya bashi kula tare da allurai, dan yasan confirm sai gwaggon ta tambayesu, ga shi kuwa ta kasa hakuri sai da ta tambaya. Jinjina mata kai ya yi yana faɗin "Yeah mum, na kula da shi". "Kai Dr ne?" Ta tambaya tana dawo da kallonta a kan Areef. "No mum, but na yi karatun a wajen daddyn". Ji ta yi tamkar ta ce musu zata je ta duba shi da kanta, zata bashi kulawa a matsayinta na Dr, sai kuma ta share, ta danne tare da kawar da zancen da cewa. "To shikenan ya kamata ku ci abinci ku kwanta ku huta ko?". Jinjina mata kai ya yi tare da faɗin "Where is Meesha?". Sai a lokacin ma ta tuna ashe babu kowa a gidan sai ita kaɗai, su Rimshan duk sun bi iyayensu, sai a lokacin kuma ta tuna ashe a labarin da Jehan ta bata, Rimsha matar Lion ɗin ne, ashe auren ta zo rabawa zancen ta sauya, sai yanzu ta tuna komai, lallau kuwa. "Son dama kai ne mijin Siha na ko?". Ta tambayi tana kallon shi. Bai amsa mata ba, kuma bai sake ɗagowa ya kalleta ba. Areef ne ya amsa mata da e. Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Ban ji motsinsu ba, kila sun bi su yaya babba ?". Nan ma shiru Lion ya yi yana kallon kasa, bai sake yin magana ba. Areef yana ƙoƙarin sake yin magana Aseef ya katse su da cewa "Kai momma har da Heartbeat ta bi su?". Jinjina mashi kai ta yi tana faɗa mashi ai dukka suka tafi. Mikewa zaune ya yi yana faɗin "Wlh i can't believe it! A kan me zata je wani waje kuma bata gaya mani ba? Ni wlh ba zai yi wu ba, gaskiya dole na je na ɗaukota!". Murmushi gwaggon ta yi tana faɗin "Yau dai sai ka hakura ka barta da iyayenta, murna take yi na ganin kakanta da sauran ƴan uwa, nima ba dan murnar ganinku ta fi yawa ba, ai da ba zan zauna a nan ba!". Kuka ya saka mata yana faɗin "Allah momma ni ba zan yarda ba, dole sai ta dawo yau, kuma sai na yi punishing nata, dama da safe ta yi mani laifi". Dariya kaɗan gwaggon ta yi dan ta ɗauka wasa yake yi, bata san halin ɗan nata ba, bata san rigimarsa ba, ai yau idan ba dawo mashi da Akila aka yi ba, to ba zaman lafiya, wannan kuka ya rinƙa yinta kenan har washegari. Waya Lion ya ɗauka ya fara kiran number Mark. Bugu ɗaya ya ɗauka. A takaice ya ce ya kawo masu abinci cikin ɗaki, sosai Mark ɗin ya yi mamaki, dan ya jima rabonsa da ya kawowa Lion ɗin abinci, sai dai ya girka kawai. After some minutes Mark ya shigo masu da abinci kala kala, a saman carpet ya jere masu. "Momma let's eat". Cewar Lion ɗin, ya yi maganar tare da miƙewa ya isa ga abincin. Make kafaɗa Aseef ya yi yana faɗin shi wlh ba zai ci ba, dole sai Akila ta dawo. Da kyar gwaggo ta rarrasheshi ya sauko, shi ko Lion ko a jikinsa, Areef ma dai bai wani kula shi ba, dan suma dukkansu kusan hakan suke ji. Shi Areef baya jin zai iya barci ba tare da ya kalli face ɗin Jehan ba, shi kuwa Lion barcin ne ma kwata kwata ba zai iya ba idan ba tare da Meesha ba, dan sun saba kwana gado guda da ita a cikin jirgin ruwa, Areef dai Allah ya taimaka dama bai taɓa kwana da ita ɗaki ɗaya ba. Shi kam Aseef na shi ai kun sani dama na daban ne, yanda suke kashe juna da love da shagwaɓa ko wani dare shi da Heartbeat nasa, yau kawai ta gudu ta barshi, ai ba zata saku ba........... E KAM BA ZATA SAKU BA, AMMA KUMA TA TAFI ƊIN😂YO ME RUWA NA NI? KO YA KUKACE MASU KARATU? ME RUWANMU? AI NAMU IDO. A tare suka fara cin abincin suna hira sama sama, Areef ya fi sakewa ya biyewa gwaggo suna zuba hira, shi kuma Aseef sai wani kumbure kumbure yake yi, shi a dole ran maza ya ɓaci, Akila ta bijire umarnin miji. Lion kuwa ba sai na faɗa ba, kun sani, magana ce baya so. A ɓangaren su Rimsha kuwa. Bayan sun isa gidan Abba ne daddynta ya ganta, faɗa sosai ya fara yi masu akan me za su baro mazajensu, su biyo su?. Kuka ta sakawa daddyn nata sosai, kuka ta gaske mai sauti da iya karfinta. Nan take kowa ya fara tambayarta lafiya kuwa? Me ya sameta take kuka?. Cikin kuka ta fara magana da iya gaskiyarta, tana yi tana kara sautin kukan nata. "Daddy wlh bana son yaya Saif, ni ba zan zauna da shi ba, ba zan sake zuwa in da yake ba, ba ruwana da shi, ba zan sake zuwa gidansa ba, dan girman Allah daddy kada kace na koma can, wlh zan mutu, ni bana son shi....." BABBAR MAGANA. Bata gama rufe baki ba Akila ta karɓi zancen da cewa "Wlh nima daddy bana son heartbeat, ni kawai na dawo gidanmu, wlh ba zan koma ba". Yau ga ikon Allah su daddy suna gani, sun ma rasa abin faɗe. Jehan ce ta katse su da cewa "Ku da dama kuke sonsu kenan, ai ni dama tun ainahi bana son shi, daddy ne kawai ya wani kakaba mani shi, kuma wlh yanzu ba ni babu shi, ya san in da dare ya yi mashi". To fa, yau ga ikon god. Ɗaure fuska sosai daddyn ya yi zai fara magana kenan Brr Naurat ta riga shi da cewa "To shikenan tun da baku son su, ku je ciki ku ku ci abinci, sai ku kwanta ku yi barci, da safe sai mu yi maganar ko". Brr Naurat akwai saurin gane abubuwa, ta gane me matsalarsu, dama ita da kanta ta yi danasanin labarin da gwaggon ta bayar a gabansu, ta san dama hakan zata iya biyowa baya, ta zan za su guji mazan nasu, dan za su yi tunanin irin abin da ya faru da gwaggon, abin da Dr William ya yi mata na cin amanar soyayyarsu, za su yi tunanin suma haka su Lion ɗin za su yi masu, tun da duk Turawan ne. TO FA BABBAR MAGANA, E DAMA DOLE ZA SU JI HAKAN AI, SABODA YANDA DR WILLIAM YA NUNAWA GWAGGON TSANTSAR SO DA KAUNA, DAGA BAYA YA CI AMANARTA, AI DOLE SU RIMSHA SU KARAYA, BARE MA ITA RIMSHA DA DAMA LION BAI TAƁA CEWA YANA SONTA BA, KUNGA KUWA AI DOLE TA GUDU DAN TA RUFAWA KANTA ASIRI, KADA TA FAƊA IRIN TARKON GWAGGO, SUN MANTA LAIFIN WANI BAYA SHAFAN WANI, SUN MANTA KOWA DA IRIN HALINSA, AMMA BA ZA KU GA LAIFINSU BA, SUNA A KAN GASKIYARSU NE❤️ Daddyn Rimsha ne ya ce "Mum zamu wuce dasu gidana na nan Kd, dama a gyare yake, nan gidan ya yi mana kaɗan, gobe da safe zamu zo". To Brr Naurat ɗin ta amsa mashi da shi, sannan ta kira shi gefe a in da ta gaya mashi kada ya yi wa su Rimsha tsawa ko faɗa a kan cewa da suka yi ba su son mazajensu, ya kyalesu zuwa gobe idan sun zo, ita zata yi magana da su. Okey ya amsa tare da yi wa su Abba sallama ya kwashesu, Rimsha, Jehan, da kuma Akilar, sai mum, suka wuce gidan nasa. Daddyn Anaya ma, ya koma gidansa da iyalansa, saura su Abbi, daddyn jelly sai Abban, Aunty ma tana nan, ita kuma Hjy Hadiza tana gida. Sune suka kwana a gidan Abba tare da Brr Naurat, kwana suka yi suna ta zuba hira. Su daddyn Rimsha kuwa, bayan sun isa gida, abinci daddy ya fita ya sawo musu, suka ci suka kammala, ko wacce ta yi wanka ta yi shirin kwanciya, da yake gidan yana da matuƙar girma, ga yelwar ɗakuna da abubuwan more rayuwa, sai kowacce ta wuce daɗinta daban, ita kuma mum ta bi daddy abinta, dan suna bala'in kewar juna. Duniya dukka sun yi barci Rimsha da Akila sun kasa yin barci, kuka yarannan suke yi tamkar za su mutu, tun hawaye na fita, har ya dai'na fita, yanda suka ga rana, haka suka ga dare, ba barci, amma duk da haka sun ki yarda ko kiran mazan nasu a waya su yi, kashe wayar tasu ma suka yi, Lion ya nemi number Rimsha a kashe, shi ma Aseef ya kira Akila a kashe, ga shi gwaggo ta hanasu zuwa su ɗauki matan nasu, ta ce yau su hakura, haka suma suka kwanta cikin kaɗaici da kewar matan nasu. Ita kuwa Jehan wlh ko a jikinta, barci ta yi har da manta a wani duniyar take, shar zuciyarta, ta bar Areef da kwana kallon hotonta bawan Allah. KAI JAMA'A YARANNAN SU RIMSHA SUNA SHA'ANINSU WLH, WAI YAU RIMSHA CE ZATA CE BATA SON LION?🤔😂 A LALLAI KUWA, AKWAI KALLO GOBE, GA SHI DAI KWANA ƊAYA KAWAI TA KASA HAKURA, SAI KUKA TAKE YI, INA GA KUMA ANYI SATI? INA GA SAI GADON ASIBITI ZA'A WUCE DA ITA😂AMMA KUMA SUNA DA GASKIYA, SU TSARE KANSU, KADA ABIN DA YA FARU DA GWAGGO YA FARU DA SU, INA GEFE NI DAI!!! JEHAN KUMA ƳAR DUNIYA, KO A JIKINTA😂 KAI LITTAFIN TRIPLETS AKWAI ƳAN AIR WLH😂 SU HEARTBEAT MA DAI AN KASA BARCI😂 KO YA ZA SU YI GOBE IDAN SUKA FITO DADDYNSU YA KALLI IDANUNSU A KUMBURE SABODA KUKA? ME ZA SU CE IDAN AKA TAMBAYESU A KAN HAKAN?😂!!!. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E6 Washegari, kasancewar mum ta san babu kayan abinci a gidan, sai bata yi ƙoƙarin tashi ta haɗa masu breakfast ba, ta bari su je gidan Abba or restaurant su karya, kwata kwata ma bata fito daga daɗin daddyn ba, suna a tare manne da juna abinsu, su kuwa su Rimsha, sun ci uban kuka tamkar ransu zai fita, idanu sun kunbura luhu luhu, har wani ja suka yi ta kasar fatar idanun, Jehan ƴar gwaggo kuwa, ko a jikinta, bayan ta tashi ta yi sallar asuba, sake mayar da barcinta ta yi, hankalinta a kwance. A ɓangaren Lion kuwa, kwana ya yi bai yi barci ba, ya kwana yana tunani tare da nazari a kan zantukan gwaggo, shi ma dai Areef bai yi barcin ba, ya nutsa cikin tunaninsa a kan maganar. Abin da ya ɗaure wa Areef kai har ya sanya shi cikin tunani shi ne, meyasa Josephine zata tsanesu? Bayan kuma ita ce ta kula da mahaifiyarsu a lokacin da take ɗauke da cikinsu? Idan da tana son kashe su, ai da tun suna cikin cikin mahaifiyar tasu zata kashe su, amma bata yi hakan ba, ta kula da su sosai, sai daga baya za'ace masu ta nemi hallakasu? Anya kuwa akwai gaskiya a wannan lamari? To meyasa Dr William ya tsaneta? Meyasa ya koreta daga gidansa, bayan kuma har TRIPLETS ɗin suka ɗan yi wayo a tare suka gansu a matsayin mata da miji da Dr William ɗin? Wannan abin akwai ɗaure kai, ya saka Areef a cikin damuwa sosai, ya sanya shi shiga cikin yanayi mara dadi, ga kewar Jehan ɗinsa, abubuwa sun haɗe mashi bawan Allah!!. Shi kuma Lion kalma ɗaya zuwa biyu ne suke mashi yawo a cikin ƙwaƙwalwasa, na farko, cewa da gwaggon ta yi TRIPLETS nata biyu daga ciki kamanninsu ɗaya, kuma dukkansu biyun blue eyes ke garesu, shi kuma ɗayan idanunsa daban, to shi dai Lion yasan su TRIPLETS da Dr William ya haifa, dukkansu idanuwansu daban daban, babu wanda idanunsu yake iri ɗaya, Areef ash eyes, Aseef brown eyes, shi kuma Lion ɗin blue eyes, kuma duk cikinsu shi kaɗai ne yake kama da Dr William kamar yanda gwaggon ta faɗa, to ya aka yi hakan ta faru?! Ina blue eyes na ɗayan?! Meyasa kuma bai yi kama da Dr William or Lion ɗin ba?! Wannan abin ya tsaya mashi a rai over, idan ya yi tunanin to ko dai ɗaya daga cikinsu Areef ba TRIPLETS nasa bane, sai kuma yaga hakan sam ba zai yi wu ba, duba da yanda suke jin bugun zuciyar juna, sannan suna da kwari da kunama, ga kuma uban shakuwa da take a tsakaninsu na wuce misali, kai bama zai taɓa yiwuwa ace ɗaya daga ciki ba cikon TRIPLETS bane! Hakan sam ba zai yiwuba! Dole dai da akwai abin da ya saɓa, kuma dole Josephine da Dr William ne za su faɗa menene ya saɓa ɗin!!. Abu na biyu da yake ta jujjuyawa a cikin ƙwaƙwalwasa kuwa, ya aka yi su Dr William suka koma Kristen? Kamkar basu taɓa musulta ba, kuma a labarin da gwaggon ta bada, har karatun Alkur'ani mai girma sun iya sosai, to ya aka yi suka canza? Canzawa mai ban mamaki haka? Ina Cherish take? Me ya rabata da su Josephine? Ina take lokacin da gwaggon zata dawo Nigeria? Waɗan nan sune tunanin da suka hana Lion runtsawa, ya rasa amsarsu, ya nutsar da brain nasa yana neman amsa cikin nutsuwa.......... NI KO NA CE AI KAI ƘWAƘWALWARKA DA BASIRARKA TA GADO CE, KA GAKI BASIRA BA KARYA, DOLE MA KA BANKAƊO GASKIYA IDAN KA SAKA KANKA, BA ABIN DA ZAMU CE MAKA FACE ALL THE BEST OUR LION!!. Hakika kuma ya shiga damuwa na rashin Rimsha a kusa da shi, shi ne ma yasa tunanin da yake na neman amsar ta kasa gudu, ya kasa samun amsa da wuri, saboda rashin Meesha a kusa da shi babbbar barazana ce ga nutsuwarsa, hankalinsa ya rabu kaso uku, kaso biyu yana kan tunanin Meesha, ɗaya kuma tunanin su Josephine, da Rimsha na kusa, wata kila a daren zai iya bankaɗo menene gaskiya, dan ya yi alkawarin bama zai tambayi daddynsa ba, saboda yana ganin kamar daddyn ba zai gaya mashi gaskiya ba, ya ce da kansa zai bankaɗo komai da komai. AFTER SOME HOURS. Da misalin karfe 9 na safe, shirye cikin wando jeans mai matukar bala'in kyau, black color, da polo t-shirt fara kal, Lion ya fito daga cikin bedroom nasa, hannunsa na ɗaure da TRIPLETS watch, still sarkan nan tana wuyarsa, ya ɗaure gashin kansa a bayan wuya, sai tashin daddaɗa kuma zazzafar kamshi yake yi, ya yi matuƙar kyau sosai, sai dai da kallo ɗaya zaka yi mashi, kasan bai sami damar yin barci daren jiya ba, dan idanunsa sun yi wani kal da su, tamkar wanda bashi da lafiya, fuskarsa ta yi wani fayau da shi. Bedroom na daddyn Rimsha in da gwaggo take ya nufa. Kasa kasa tamkar bai yi magana ba ya yi sallama, tare da shiga ciki. Areef na zaune a bakin bed nata, ita kuma gwaggon tana zaune a saman bedside drawer suna zuba hira, shi kuma Aseef yana can yana zuba barci, bai tashi ba, dan daren jiya bai yi barci sosai ba. A tare gwaggon da Areef ɗin suka amsa mashi sallamarsa, karisowa cikin ɗakin ya yi, yana taku cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, tamkar baya son taka kasa, da alama jikinsa duk a mace yake. Gefen Areef ya zo ya zauna yana tambayar gwaggo ya ta kwana?. Sai murmushi take yi ta amsa mashi da lafiya lou ta kwana, Areef ne ya fara ɗaga mashi gaisuwa, a takaice ya amsa da lafiya tare da miƙewa ya ce da gwaggon yana zuwa, zai je unguwa. "A'a zauna ina son yin magana da kai!". Okey ya amsa mata tare da gyara zama. Shi kuma Areef mikewa ya yi yana faɗin "Momma bari na je na ɗauko matata, dan ba iya jurewa zan yi ba". Ya kai karshen maganar tare da wucewa da sauri. Kafin ta yi wani magana ma ya fice abinsa. Dawo da kallonta a kan Lion ɗin ta yi tare da fara magana a nutse. "Ina Muhammad, Sudais da kuma A'isha suke?". Wato su Uncle Herry take nufi kenan. Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Just call them Herry, Josephine, and Tyson, because all of them are Kristen now, ba yanda kike tunani bane". Zaro idanuwanta waje sosai ta yi, cike da mamaki ta ce "Harda Josephine ɗin?". Jinjina mata kai kawai ya yi ba tare da ya sake yin magana ba. Shiru ta yi tana al'ajabin wannan al'amari, katse mata shirun ya yi da cewa "Momma forget about them, saboda babu mai gaskiya a cikinsu, ko kin tanbayesu, karya za su yi maki, kamar yanda suka yi mana, dukkansu bakinsu ɗaya, so forget about them, I will do something about da case, now abin da nake so da ke, kada ma ki sake yin maganar, kada kuma ki sake tambayar kowa komai a kan labarin baya, ki rufe babin kawai!". Tabbas ta sha jinin jikinta na jin abin da ɗan nata ya faɗa, ta kuma sha ruwan mamakin yanda aka yi gabaɗaya su Dr William ya zama bakinsu a haɗe, ya aka yi Josephine mace mai hankali ta biye masu? Wai menene yake faruwa ne?..... "Momma zan iya tafiya?". Ya faɗa cikin sanyin murya. "Ina zaka je?". Kai tsaye ya bata amsar gidan uncle zai je, kamar zata tambaye shi wani uncle ɗin daga ciki, sai kuma ta fasa, dan ta lura baya son yawan magana, hannu ta kai ta shafi kansa tare da fara kwararo mashi ruwan albarka da adduo'in masu ratsa jikin duk wani mumini. Wani abin sai uwa, babu wanda ya taɓa yi mashi makamancin hakan, hakan tasa ya ji wani mugun sanyi tana ratsa zuciyarsa, Allah sarki, wata kila da ace gwaggo ta rayuwa da su, da ba zai yi zafin zuciya har haka ba, da ko ma yaya ne zai rage wasu abubuwa, uwa, uwa, uwa, haka Allah ya kirata sau uku kafin ya kira uba, Allah ka karawa iyayenmu lafiya da nisan kwana, waɗan da suka rigamu gidan gaskiya kuma, Allah ya jikansu da Rahman, ya kai haske cikin kabarinsu, ya sadasu da manzon rahma. Miƙewa ya yi ya kara mastowa kusa da ita sosai, a saman cinyarta ya kwantar da kansa, a can cikin zuciyarsa kuma, yana jin tamkar ya haɗiyeta, saboda so da kauna. Ita kuwa, ta cigaba da kwararo mashi ruwan addu'a ba kama hannun yaro, tana yi tana shafa lallausan gashin kansa, ya yi shiru yana sauraronta, abin gwanin birgewa, kowa ya gansu a haka, sai ya matsa kwallar farinciki, haka ta yi wa Areef ma da ya shigo ɗazun, dan shi tun karfe 6 yana wajenta, sai hira suke yi har lokacin da Lion ɗin ya shigo. Sai da ta kai karshen addu'ar ne ya ɗago kansa tare da kai ɗan bakinsa saitin kumatunta, sumbata ya manna mata a wajen yana faɗin "I really more appreciate and happy da ya kasance kece mahaifiyarmu, i love you so much my momma". Ya kai karshen maganar tare da sake manna mata sumbata a kumatun nata. Shafa lallausan sajensa ta yi, tare da manna mashi sumbata a goshin tana faɗin "Na fika farincikin kasancewarku ƴaƴana, ina alfahari da ku, je ka wajen uncles ɗin naka ka dawo, idan ka dawo, sai ka gaya mani aikin me kuke yi? Akwai wanda ya gaje mu a karatu ne a cikinku? Ko dai babu Dr a cikinku?". Jinjina mata kai ya yi tare da miƙewa ya nufi kofar fita ba tare da ya sake cewa komai ba. Da kallo ta bishi tare da fatan alkhairi har ya fice. Yana fita Mark ya shigo mata da abinci, dan Areef ya gaya mashi ya kawo mata abinci kafin su dawo, sai su ci a tare gabaɗaya. A can gidan daddyn Rimsha kuwa. Sai misalin karfe 8:30 daddy ya fito cikin shirin kananan kaya, waje gabaɗaya ya fita, restaurant ya wuce, abinci ya sawo masu ya dawo. Kafin ya dawo mum ta jera plates da komai a saman table, tana zaune tana jiransa. Ko da ya dawo, saman table ɗin ya wuce yana faɗin su Rimsha basu tashi daga barci bane? E ta amsa mashi da shi. Jinjina kai ya yi kafin ya ce "Okey ki kyalesu duk time da suka tashi, sai su zo su ci nasu breakfast ɗin". Okey ta amsa mashi da shi. Wani irin daddaɗar kamshi perfume ne ya daki hancinsu, a tare suka ɗago kai dan ganin wanene. Jehan ce take saukowa daga saman bene, ta shirya cikin ɗaya daga cikin kayan da ta samu a cikin walldrop na bedroom nata, doguwar riga ce mai kama da baya, blue color, kaya sun yi mata matuƙar kyau, abinku da farar mace, ta haɗu da blue color, ai kunsan dole ta haska. Ta yafo gyalen kayan a kanta, light make up ne a fuskarta, sai lips gloss da ta sanya a kyawawan lausasan kananan lips nata, duk wanda ya ganta, sai ya sake waigawa ya kalleta, saboda ta fita ta yi kyau over. Kusa da su daddy ta zo ta tsaya tare da ɗaga masu gaisuwa. Cikin tsantsar so da kauna suka amsa mata gaisuwar tare da tambayarta irin wannan uban kyau haka waye ta yi wa kwalliya. A takaice ta ce "Daddy zan je naga gwaggona, ba zan iya zama ba tare da ita ba!" Ta kai karshen maganar tana yamutse fuska. Kallon mum ya yi yana murmushi kaɗan kaɗan, ya sani, ba wata gwaggon da take son zuwa ta gani, Areef take son ta je ta gani, yana ganinta da asuba da ta ɗauka mashi waya tana kallon hoton Areef ɗin, kawai bai kula ta bane, duk yana ganinsu, kuma ya yi alkawarin ba zai saka baki a maganar ba, idan suka ji uwar bari, za su mayar da kansu kamar yanda suka kawo kansu gidan, nasu wasa ne, har yanzu su yara ne, ba su san sharrin so ba, ita dai Rimsha ga idanu sun kunbura luhu luhu kamar ba lafiya ba, Akila kam ba'a magana. "Mummy ki saka baki mana, daddy ya kaini wajen gwaggona da wuri, Allah ji nake ba zan iya kara minti goma ban kalleta ba". "Gwaggo ko ko Areef surikina zaki je gani?". Mummyn ta tambaya tana ƙoƙarin zuba abincin a cikin plate. Ɗaure fuska ta yi tamkar irin basawan nan, cikin fushi ta ce "Mummy waye kuma Areef?". Galala daddyn ya saki baki yana ganin ikon Allah, Jehan akwai taurin zuciya kamar gwaggon nata, ai wanna yarinyar ba in da ta baro halin Lion, dan shi ma ya ɗauko gwaggon ta wani fannin, kamar taurin zuciyar da sauransu, tana kewar Areef kamar ta mutu a cikin zuciyarta, amma a fili ta wani dake kamar bata ma san shi ba, bayan kuma harda satan hotonsa ta yi tana ta kallo har barci ya ɗauketa. Kawar da zancen mum ta yi da cewa "To zauna mu yi breakfast tukun nan, idan kin ƙoshi, sai a kaiki wajen gwaggo naki ". "Mum nifa ba zan iya cin komai ba tare da na kalli gwaggo ba". Ta kai karshen maganar tana matsowa kusa da daddyn, shi dai sai kallonta yake yi, ƴar karama da ita wai zata yi masu wayo, kamar ba su suka haifeta ba. Mum zata sake yin magana Areef da ya shigo yanzu ya ce "Mum don't west your time, ba zata iya cin abinci ba har sai taga mijinta farincikinta, to gani na zo, nima dai na kasa cin abincin har sai na zo na ganki rigimammiya kawai". Nan take daddaɗar kamshi perfume nasa ya bule ko'ina a palon, fuskarsa ɗauke da murmushi ya kariso cikin palon. Wani irin nauyayyar ajiyar zuciya Jehan ɗin ta sauke tare da sunkuyar da kai kasa tana satar kallon shi, ya yi kyau matuka over, ji take yi tamkar ta je ta rungume kayanta, amma ina jiji da kai ba zai barta ba. Yana karisowa wajen yasa hannu ya ɗan ja kumatunta yana faɗin "Sarkin rigima, da sanyin safiyar nan ma sai kin tasa mum a gaba da rigima ko? To gani nan na zo, sai ki kyale mani mum ɗina ta huta". Harara ta wurga mashi tare da sa kai da nufin ta kowa sama abinta. Cikin sauri ya riko hannunta tare da jawowata jikinsa yana faɗin "Good morning my uncle, mum good morning". Mummy dai kunya ya hanata ta ɗago idanu ta kalle shi, kun san Jehan ce ƴar farinta, ga shi babu kunya Areef ɗin ya zo ya wani rungumeta a gabansu ko a jikinsa, dole mum ta ji kunya, shi kuwa daddy, ko a jikinsa, shi da ya kalli fin haka ma, sau nawa yana kallon Aseef yana ɗaukar Akila cancak a gabansa, sau nawa yana kallon Lion da Rimsha a garden suna sha'aninsu, Areef da Jehan ɗin ma me basu yi a gabansa? Ai shi ya ga komai, dan haka basu wani bashi kunya. "Ni ka sakeni Hai!". Ta faɗa cikin fushi, da tsawa kuma. Saketa ya yi dan shi ma baya son ya ja magana sosai a tsakaninsu, kasancewar yaga mum ta takure waje guda, duk sai ya ji wani iri. Zama ya yi a saman ɗaya daga cikin tables chars ɗin, ita kuma Jehan ɗin ta haura sama da gudu abinta. Miƙewa mum ta yi dan ta basu waje, a cewarta, ba zata iya cin abinci tare da Areef ba, dan yana surikinta, miji ga ƴar fari. Ta zo dai'dai zata hau step na stair case ta haura sama, kamar daga sama suka ji voice ɗin Lion da ya shigo yanzu yana faɗin "Ke where is my wife?".......BABBAR MAGANA, LALLAI LION DA SAURANKA, MUM ƊIN CE KE! KAI LALLAI KUWA. Baki Areef ya saki yana kallon Lion ɗin da mamaki, a cikin zuciyarsa yana faɗin "Yau Lion ne yake cewa ina matarsa? Da bakinsa yake tambayar, bama ina Rimsha ba, ina matarsa kai tsaye? Wato yanzu kenan ya yarda matarsa ce? Kenan ya yarda yana sonta? Lallai kuwa abin da mamaki, ko da yake, dama duk ɗa na halak idan ya ji irin kyautatawa da daddyn Rimshar ya yi wa mahaifinsa, to dole zai so su Rimshar suma, ko dan daddyn nasu, ai dole ma Lion ya yarda da cewa yana sonta, kuma dole soyayyarta ta karu a cikin zuciyarsa over. Sai dai sam Areef ɗin bai ji daɗin yanda har yanzu Lion baya girmana kowa ba, ya shigo musu har cikin Palo, sallama ma kasa kasa ya yi ta yanda babu wanda ya ji, ko sannu bai ce masu ba, babu gaisuwa a matsayinsu na kannen mahaifiyarsa, kawai yana wani yi masu magana tamkar shi ne ubansu, kai Lion har gobe dai akwai izzar bala'i, wato yafi karfin ya ce wa mummy mum ina kwana?! Tab lallai har yanzu da sauran aiki. Shi dai daddy, da yake yasan izzar da ta fi hakan ma Lion zai iya nuna masu, sai bai ce komai ba, idan da sabo, ai ya saba da halinsu. Mum da bata saba ba, sai abin ya ɗaure mata kai, ya yi mata wani irin banbaraƙoi, amma haka ta daure ta nuna mashi a in da ɗakin Rimshar yake. Bai sake cewa da su komai ba, ya wuce ya nufi saman tamkar shi ya gina masu gidan, akwai shi da bala'in nuna isa na wuce misali. Matsa mashi a hanya mum ɗin ta yi, ya wuce abinsa, da kallo suka bi shi, Areef yana mamakin irin tsantsar nuna wannan uban isa na ɗan uwan nasa, tamkar baza'a mutu ba.......... GASKIYA DAGA KAN LION AN RUFE ISA DA IZZA, IN DAI NUNA ISA DA IZZA NE, TO SHI KARSHE NE, SHI FA JI YAKE YI TAMKAR KOWA DOLE YA KASANCE A KARKASHINSA, KUMA DOLE AYI MASHI BIYAYYA, KO ANA SO KO BA'A SO, KAMAR SHI NE UBANSU!!. Bayansa mum ɗin ta bi, ita ma ta haura saman kenan, a in da ta wuce bedroom nata. Rimsha tana zaune a saman tsakiyar bed nata, sai kuka take yi kamar ba gobe, kayan barcin jiya ne a jikinta, wando guntu zuwa santala santalan cinyoyinta, sai ƴar riga mai siririn hannu zuwa cibiya, fararene kal kal kayan, sun yi mata kyau over, gashin kanta a sake, duk ya barbazu kamar mahaukaciya, saboda kukan da ta rinƙa yi tana burgima a saman bed ɗin, shi ne yasa gashin nata ya bazu haka, ko wanka ta kasa tashi ta je ta yi, fuska ta yi jajir kamar tumatir nunanne. A hankali ya turo kofar ya shigo, bakinsa ɗauke da sallama kasa kasa. Kamshin perfume nasa ne ya fara kai mata karo, a zabure ta ɗago kanta tare da kai kallonta izuwa bakin kofar. Ganin da gaske shi ɗin ne yasa ta miƙe da sauri tare da dirowa kasa daga saman gadon, da sauri ta nufe shi da nufin ta rungume shi, ko me ta tuna, sai kuma ta ja birki. Yana tsaye a bakin kofar yana kallonta. Zubewa kasa ta yi a saman gwiwowinta tare da sake rushewa da wani sabon kukan. Yau ga ikon Allah. Ya ɗan ɗauki ƴan mintoci kamar biyar haka, kafin nan ya tako a hankali izuwa cikin ɗakin. A kusa da ita ya tsaya, hannun rigansa ya gyara kafin ya ɗauketa cancak izuwa saman bed ɗin. Zama ya yi da ita a jikinsa, yama rasa me zai ce mata, shi dai bai san kukan me take yi ba, bai kuma san ta ya zai tambayeta ba, sai ya ɗan zuba mata idanu yana kallonta. Goga fuskarta ta fara yi a saman kirjinsa tana ɗan bubbuga kirjin nasa da hannunta ɗaya, tamkar wadda ta aikata mummunar laifi kuma tana babbar danasani. "Meesha". Ya ambaci sunanta a hankali. Kamar jira take yi ya yi magana, cikin kuka ta ce "Yaya Saif me ya kawoka gidanmu? Me kazo yi to? Ni ka tafi!". Tana kuka tana surutan. Jinjina mata kai ya yi tare da sauketa daga jikinsa, ya kuwa mike da gaske zai tafi ɗin, kofar futa ya nufa, yana taku a nutse cikin kwanciyar hankali. Da gudu ta diro kasa daga gadon, ta baya ta zo ta rungume shi tana mai cigaba da kukanta. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya juyo gareta, dama yasan ba zata iya jurewa ya fice daga ɗakin ba, ai yasan irin tsananin son da take yi mashi, da gangan ya nuna mata cewa komawar zai yi kamar yanda ta ce bata son ganin shi. Juyowa ya yi ya rungumota yana ɗan bubbuga bayanta a hankali, alamar rarrashi. Kara saka mashi kuka mai sauti sosai ta yi. Ɗaukarta ya yi suka nufi waje, dan ba zai iya jurar kukan nan nata ba. A haka ya zo ya wuce daddy da Areef a palon, ya nufi waje da ita a saman kafaɗarsa. Kai tsaye sai cikin mota, a gidan baya ya sakata, shi ma ya shiga gidan bayan, Donal ne dama ya ja motar suka zo. Har lokacin sai kuka take zuba mashi. Umarni ya yi wa Donal ɗin a kan ya fita ya basu waje. A hanzarce ya fice. Rungumota sosai ya yi a jikinsa, sai a lokacin ne ya tambayeta meyafaru take yin wannan uban kuka haka. Kankame shi ta yi, ta kasa magana, sai yii, yi, yi, take yi tamkar wata ƴar baby. "Meesha, meyasa kike son sakani a cikin damuwa ne? Kin san halin da nake ciki kuwa a yanzu?". Ya yi maganar yana ɗago haɓarta. Subhanallahi zaro idanu sosai ya yi yana kallon yanda face nata ya dawo saboda kuka, idanu a kumbure. Nan take shi ma face nasa ta sauya, ɗaure fuska sosai ya yi, cikin nuna isa da magana kai tsaye ya ce wani mai karan kwanan ne ya taɓata da har ya sakata wannan irin kuka haka? Meya sameta?. Jin yadda ya yi maganar babu wasa a tattare da shi ne yasa ta tsayar da kukan nata cak, da sauri ta waro jajayen idanun nata waje. Wani irin mahaukacin razana ta yi na ganin yanda fuskarsa take, ya ɗaureta tamau, ya haɗe geran sama da kasa, sam babu wasa ko ɗigo a tattare da shi. Nan take wani irin tsoro ya kamata, dan bata san me zata ce mashi ba, ga shi ya ɓata rai over. Narai narai ta fara yi da idanu. Tsawa ya daka mata a kan wanene ya taɓata? Me aka yi mata da har zata yi irin wannan uban kuka haka?. Kokarin barin jikinsa ta fara yi, dan ta gudu, ta koma cikin gida. Damko wuyar rigar jikinta ya yi, kasancewar rigar ɗan ƙaramin ne zuwa cibiya, sai gabaɗaya tula tulanta suka bayyana a waje. Da sauri ta koma jikin nasa ta kwanta tana mayar da numfashi, nan take ta nemi kukan nata ma ta rasa...... NI KO NACE AU, DAMA ASHE IYA SHEGE NE, DA KI GAYA MASHI ME YA SAMEKI MANA! KIGA YANDA ZAI YI BALL DAKE, DAN WLH IN DAI KIKA CE MASHI BAKI SON SHI NE SABODA DADDYNSA NA CI AMANAR GWAGGON, ZAKI YABAWA AYA ZAKINTA KUWA Wani irin shock ya ji na komawa jikinsan nan da ta yi. Kankame shi ta yi, murya a dashe ta ce "Yaya Saif ni babu wanda ya taɓani". Kai tsaye ya ce karya ne, ta gaya mashi wanda ya ɓata mata rai har ya sakata kuka haka, ko kuma ita ma ya hukunta ta, ya fara ta kanta. Shiru ta yi yana tunanin me zata yi mashi ne ya sauko? Me ya kamata ta yi mashi. Can sai ta ce "Yaya Saif ciwon ciki ne fa yasa nake kuka, tun jiya da daddare cikina yake yi mani ciwo, kuma na kasa gayawa su daddy ne, dan a lokacin suna barci, da safe kuma na kasa iya fitowa waje, kuma muryata bata fita sosai bare na yi kuka da karfi su jini". Hannu ya ɗaura a saman cikin nata. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, hankalinsa ya ɗan kwanta, da ya yi tunanin ko wani ne ya taɓata, da yanzun nan ya karɓi hukunci. Shafa shafaffen cikin nata ya fara yi yana kallon face nata, gam ta datse idanunta, dan ma kada su haɗa ido, sai sauke nauyayyar ajiyar zuciya take yi. Zazzaƙar sexy voice nasa ne ya daki dodan kunne, a in da ya ce mata "Muje gida in dubaki ko? Daga nan kuma, sai ki gaya mani meyasa baki kirani a waya kin gaya mani baki da lafiya ba, meyasa kuma kika fita ba tare da sani na ba?". Kara kankame shi ta yi tana faɗin "Kai NooRi yanzu ai na ji sauki, ni ba sai ka dubani ba, dan kada ka yi mani allura". Matso da ɗan bakinsa saitin kunnenta ya yi, kasa kasa ya ce "Alluran ne baki so?". Jinjina mashi kai ta yi tana kara lafewa a jikin nasa, har ta mance da zancen cewa bata son shi......... Yo ba dole ta mance ba, soyayya wasa ce😂 "Okey to ba zan yi maki ba, dubaki kawai zan yi". "Noorish ina gwaggona?". Ba tare da ya bata amsa ba, ya sanya hannu ya fara tattare mata gashin kanta da yake a watse. "Open your eyes". Ya faɗa a sanyaye. Turo baki ta yi tana ɗan waro idanun nata a hankali. Gyara mata kwanciya ya yi tare da ciro wayarsa, number Areef ya shiga, massage ya rubuta mashi a kan ya fito mata da hijabi. "NooRi ba zaka gaya mani ina gwaggona take ba?". Ta yi maganar tamkar zata saka mashi kuka. Matso da face nasa daf da ita ya yi, kasa kasa ya fara magana kamar mai raɗa. "Ba kin gujeta jiya ba? Dan haka kada ki tambayeni". Ɗan ɗago idanu ta yi tana kallon kyakkyawar sajensa dake a kwance luf, a hankali ta kai hannu tana shafawa. "NooRi waye ya taɓa maka sajenka?". Ɗan zaro idanu ya yi yana kallonta, ko ya akayi tasan an taba oho mata, yarinyar nan ta gama karance face nasa tsab, yanzu taɓa sajen da gwaggo ta yi ma sai da ta gane, kai Rimsha ba dai basira ba, akwai kaifin ƙwaƙwalwa. "Waye ya gaya maki an taɓa sajen nawa?". Turo baki ta yi tana faɗin "Ai nasan ba haka kake gyarawa ba, idan ka gyara ba haka yake kasancewa ba, dole bayan da ka gama gyarawa, akwai wanda ya taɓa shi, nasan yanda gyaranka yake ai". E lallai Rimsha ta daban ce, wato har ta haddace yanda yake gyara shagen nasa. Wani irin daɗi ya ji har cikin zuciyarsa, hakan na nufin yana nan a cikin ranta fiye da komai, tana sane da komai na mijin nata. Tsabar farinciki bai ma san time da ya kara matseta a jikinsa ba. "Wash Noori zaka balla ni fa". Ta yi maganar a shagwaɓe sosai. Ɗago haɓarta ya yi tare da manna mata sumbata a ɗan bakin nata, buɗe bakin nata ta yi, da ɗan karfi ta cije shi a lips nasa. Tsareta da ido ya yi ba tare da ya ce komai ba, ga face nasa kuma tamkar hadari, a ɗaure tamau. Ganin hakan yasa ta yi ƙoƙarin sake cizon nasa. Bata kai ga sakewa ba Areef ya yi masu knocking na glass ɗin motar. Da sauri ta ɗago kanta, ganin Areef ne yasa ta yi ƙoƙarin barin jikin Lion ɗin. Bai hanata ba, sai ma sauke glass ɗin motar da ya yi ya karɓi hijabin nata. Juyawa Areef ɗin ya yi ya koma cikin gida, shi kuma Lion ya miƙa mata hijabin a kan ta sanya, da sauri ta karɓa ta sanya. Umarni ya yi wa Donal a kan yazo su tafi. A hanzarce ya dawo cikin motar tare da kunnata suka bar gidan. Lokacin da suka dawo gida, da gudu Rimshar ta wuce ɗakinsu, dan tana tunanin gwaggo tana can, sai da ta shiga, taga bata nan, da sauri ta dawo izuwa ɗakin Lion, nan ma bata nan, ɗakin daddynta ta nufa kai tsaye, a nan ta sami gwaggo kwance a saman bed, ta gama cin abinci ta yi wanka. Da gudu ta haye saman bed ɗin tana dariya, shi kuwa Lion, juyawa ya yi ya fice izuwa harabar gidan gabaɗaya. Miƙewa gwaggon ta yi zaune, nan ta rungumo Rimshar suka fara hira, labari Rimshar ta fara bata na abubuwan da suka faru a baya, har da aurensu da Lion, irin rayuwar da suke yi da shi, da tafiyarsu ƙasar Russia da suka yi, sai dai ko kusa ko alama bata bata labarin Daular Mutuwa ba, da alama an shafe mata labarinsa a cikin brain nata. Sosai gwaggon ta yi mata nasiha a kan kula da miji, sannan ta kara mata da cewa, tun da har haka ne, to Lion yana sonta, dan Allah ita ma ta nuna mashi soyayya sosai, ta ga akwai ciwo sosai a cikin rayuwarsa, ta kula da shi, a yanzu tana a sahun gaba cikin mutanan da suke saka shi farinciki, dan Allah ta kasance mai saka shi farinciki sosai. Gabaɗaya sai Rimshar ta ji jikinta ya yi sanyi, ba shakka akwai ciwo sosai a cikin rayuwar TRIPLETS, ga kuɗi, ga mulki, ga mukami, ga isa da izza, ga kyau, dukka Allah ya hore masu, amma kuma tun suna cikin mahaifiyarsu suke fuskantar jarabawa, babbar bala'i ce tashi da girma cikin kafurci, hakika ba kowa da kake kallon cikin Daula na ɗumbin dukiya bane bashi da damuwa da matsaloli na rayuwa, kowa da kowa yana iya fuskantar jarabawar Ubangiji ta kowace siga a kuma lokacin da baka yi tsammani ba, so yana da kyau mu runƙa kyautatawa al'umma zato, mu kuma mayar da hankulanmu a kan abubuwan da suke gabanmu, kada mu sakawa wani mai ɗan arziki idanu, dan bamu san halin da yake ciki ba, mu kyalkyalin arzikin kawai muke gani, amma na ciki, tana ciki, Allah ka bamu dacewa, ka kuma bamu ikon cin jarabawarka a duk lokacin da ka jarrabemu. Sosai Rimsha ta ji jikinta ya yi sanyi, ta kuma yi wa gwaggon alkawarin zata yi iyaka bakin kokarinta wajen ganin ta sanya Lion farinciki. Tambayarta gwaggon ta yi a kan ina Lion ɗin yake, shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Nima ban san ina yake ba, lokacin da muka shigo dai na barshi a palon sama". Ɗaga idanu gwaggon ta yi, ta kai kallonta a saman katafaren agogon bango da yake manne a jikin bangon ɗakin, karfe 11:30 dai'dai, dawo da kallonta a kan Rimshar ta yi tana faɗin "Rimsha ashe fa mun ɗan ɗauki lokaci muna hira fa, labarin naki ne akwai tsawo, yanzu dai jeki ki duba mani Saif ɗin nan, bai ci abincin safe ba, ki kai mashi abinci ya ci dan Allah". Ta yi maganar cike da nuna kulawa ga ƴaƴan nata. To Rimshar ta amsa da shi tare da miƙewa, ta sauko kasa daga saman bed ɗin, waje kai tsaye ta nufa. Tana fita ta wuce bedroom nasu. Wanka ta tsala tare da zuba shirinta cikin wandon jeans fari tas da T-shirt pink color, ta ɗaure gashin kanta a tsakiyar kai tare da zubo jelar a bayanta, ta yi matuƙar kyau tamkar ita ta yi kanta. Perfume nata ta zuba, nan take ta fara zuba kamshi tamkar ba gobe. High heel ta sanya a kafarta, sannan ta nufo waje. A palo ta kalli ɗayar wayarta a saman sofa, cikin hanzari ta ɗauki wayar ta nufo palon kasa. Kitchen ta nufa ta ɗauko abincin Lion tare da ficewa da sauri. Garden ta nufa da abincin, dan tana tunanin zata same shi a wajen, sai dai ina baya nan, ta sha ruwan mamaki sosai. Saman table ta ɗaura kayan abincin tare da zama a saman sofa ta ciro wayarta. Numbersa ta kira, wayar ta yi ringin har ta katse bai ɗauka ba. Turo ɗan baki ta yi tare da sake kiransa, nan ma shiru bai ɗauka ba. A kule ta ɗaga wayar zata buga da kasa, ƴar kara wayar ta yi alamar shigowar sako. Cikin sauri ta fasa bugata da kasa tare da buɗe sakon. Cool murmushi ta saki ganin sunan Noorinta, tun bata ga me sakon ya kunsa ba. A hanzarce ta buɗe ta fara karantawa kamar haka. "Idan kika fasa wayar nan, babu mai saya maki wani, ke da waya har abada ƴar rigima kawai". Shi ne abin da ya rubuta mata a sakon. Ta sani sarai ba wai yana kallonta bane, kawai ya riga da ya san hali ne, ya san abin da zai biyo baya idan bai ɗauki kiran ba, ya san rigimarta sarai, shi ne yasa ya yi mata sakon tun wuri. Juya dara daran fararen Sleeping eyes nata sama ta yi, har wani walwali suka yi, ɗan girgiza kai ta yi tana magana kasa kasa ta yanda ita kaɗai zata san me take faɗa. "Allah Noorin nan nawa ya rainani da yawa". Shi ne abin da take faɗa. (E lallai Rimsha kin girma, wai NooRi ya rai'na ta?🤔 Ba shakka kin ga gadon kwanan Lion, dole ki ce haka😂) Shi kuwa, sai da ya gama ja mata rai son ransa, sannan ya yi mata massage a kan ta zo boys quarters na gidan ta same shi. Da kamar ba zata je ba, dan ta yi fushi na shanyata da ya yi tun ɗazun tana jiranshi. Sai kuma ta tuna cewa bai ci komai ba bawan Allah, yunwa yake ji ga kuma ɓacin ran da ya shiga. Tuna hakan yasa ta ɗauki abincin na nufi wajen. Shi ma bene ne mai hawa ɗaya, babu wanda ya taɓa kwana a wajen, komai na cikin wajen sabbi ne. Bakinta ɗauke da sallama ta shigo cikin palon kasan. Babu kowa sai sanyin Ac da kamshin air freshener da kuma kamshin perfume ɗin na Lion ɗin dake tashi. Haurawa sama ta yi, sai aikin turo baki take yi. Bakinta ɗauke da sallama ta shiga bedroom ɗin da ta ji kamshin perfume ɗin nasa ya fi yawa a ta wajen. Yana kwance saman bed, daga shi sai ƴar wando short zuwa kaɗan daga cinyoyinsa, ga wandon ya kama shi sosai, ya manne da fatar jikinsa, ba dan kalar wandon da yake fari ba, da ba zaka taɓa tunanin ma ya saka ba, saboda mannewa da jikinsa da ta yi. Sai dai ya ja bargon dake saman bed ɗin izuwa kugunsa. Da alama wanka ya yi, dan ga gashin kansa da akwai danshin ruwa. Daga ta sama kuma, yana sanye da ƴar riga mara nauyi, irin waɗan nan T-shirt ɗin masu laushi sosai, sannan masu kananan hannu. Tun da ta shigo ya tsareta da waɗan nan dara daran idanuwan nasa masu rikitarwa yana kallonta, tamkar zai cinyeta. Ta yi kyau ne over, ji ya yi tamkar ya tashi ya rungumota. Ita kuwa, sai aikin turo mashi ɗan bakin nan nata take yi, ita a dole tana fushi. A tsakiyar Chinese carpet dake a cikin bedroom ɗin ta ajiye abincin. Zama ta yi a gefen abincin ba tare da ta kalli in da yake ba, ta fara magana "Yaya Saif sannu da hutawa, ga abinci nan na kawo maka, ka zo ka ci dan nasan kana jin yunwa". Nisawa ya yi yana mai cigaba da kallonta, bai ce komai ba. Almost 10 mins suka ɗauka a haka, bai ce mata ko sannu ba, yana ta kallonta, ita kuma taki ɗagowa su haɗa idanuwa. Da ta ga bashi da niyar motsawa, sai ta miƙe tana kumbura kumatu ta nufi waje, ta ki yarda dai ta kalli in da yake. Ko sannu bai ce mata ba. Har ta fice daga cikin ɗakin. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da jawo wayarsa, ya yi mata massage a kan ko taku ɗaya bai yarda ta kara ba a wajen tafiyarta, ta juyo ta dawo. Tana gama karanta sakon ta zunduba ihu tamkar wanda aka kwalawa itace a tsakiyar kai, haushi kamar ta je ta shakesa, ga shi bata isa ta ki zuwa ba, dan idan har ta kara taku ɗaya ɗin ta shiga tsinuwan Mala'ikun Allah ne, har sai time ɗin da ta zo ta bashi hakuri ya kuma yafe mata, sannan Mala'ikun za su dai'na tsine mata, wannan babban musifa ce bijirewa maganar miji, ko ba daɗi ayi hakuri a bi, shi ne zaman lafiya!!!. Juyowa ta yi tana kuka da hawaye bibbiyu, da farko tafiyar yanga take yi ta kawo abincin, yanzu kuwa jan kafar take yi tana kuka dan haushi. Yana kwance in da yake, bai motsa ba. Gaban bed ɗin ta zo ta tsaya, kusa da shi, tana kuka, bata ce mashi ko kala ba. Hannu ya kai ya jawota ta faɗa jikinsa, gyara mata kwanciya ya yi izuwa saman faffaɗar kirjinsa, ɗago haɓarta ya yi ya fara lashe hawayen da ya sa suka zubo ɗin. Duka ta fara kai mashi a kirjin nasa tana faɗin "Allah Noori mun ɓata". Ta yi maganar a shagwaɓe. Kara matseta a jikin nasa ya yi tare da matse ɗan bakin nata, kasa kasa ya ce ta yi shiru ya gaya mata wani abin mai daɗi. Jin hakan yasa ta yi shiru tana shesshekar shagwaɓa tare da kumbura kumatu. "Meyasa kika cika rigima ne?". Ya faɗa a sanyaye. Turo baki ta yi bata bashi amsa ba. "Don't you know that you're my happiness? You know how sad I was before you came here? Kin san da na kalli face naki ya naji kuwa?". Da sauri ta ɗago tana faɗin "Ya ka ji to?". Lumshe idanuwansa ya yi, dan yanda ta ɗago fararen idanun nan nata, ba ƙaramin tafiya da shi suka yi ba, dan yanda ta ɗagosu, har wani walwali wal wal suka yi mashi. "NooRi to ka gaya mani ya ka ji mana?". Tana magana tana shafa lallausan bakin gashin dake kwance a hannunsa da yake rungume da ita. Bai amsa mata ba, kuma bai buɗe idanuwansa ba. Sake tambayarsa ta yi tare da saka mashi kukan shagwaɓa. Ba tare da ya buɗe idanuwansa ba, ya matso da ɗan bakinsa sai tin kunnanta, murya kasa kasa kamar mai raɗa, sai ka rantse da Allah baya motsa laɓɓansa, cikin wata iriyar murya mai tsayawa a ran masoya ya fara yi mata raɗa idanuwansa a lumshe. "Kina shigowa cikin bedroom nan, ina ganin beautiful face naki, sai na ji na mance komai, i feel like ban taɓa jin wani ɓacin rai ba, you're special!". Da sauri ta zaro idanuwanta tare da juyowa da kallonta izuwa kan face nasa sosai. Idanuwansa a lumshe, magana yake yi cike da class tare da izza, cikin kuma kwanciyar hankali da nutsuwa, a ko da yaushe babu ko ɗigon na hayaniya a cikin voice nasa, so silent zaka ji ta, bare kuma yanzu yanda yake magana kasa kasa, ya kuke tunanin muryar zata kasance? Hmmmm...... Hakika ya ji tsakanin kaunarta a ransa sosai saboda gwaggo, saboda yanda babanta ya kula da gwaggon, a haka ma bai san cewa Gwaggon ta fi son su Rimshar sama da kowa a cikin ƴan uwanta ba, wata kila idan ya san hakan, ko kasa ba zai bari Meeshar tasa ta sake takawa ba, saboda so........ Mu dai je zuwa, uwa ai ba wasa ba, bare su da suka ɗauki tsawon shakaru 31 zuwa 32 basu tare da ita, ai dole su so duk abin da uwar tasu take so fiye da tunanin mai tunani. Yau wani irin jin Rimsha yake yi a cikin ransa fiye da misali!. Sosai ta zuba mashi idanu tana mamakin kalaman da yake yi, tamkar wanda ake gayamawa. Idan a baya ne ka ce mata ya iya wannan kalamai, ba zata taɓa yarda ba, babu ma wanda zai yi gigin yarda, ko TRIPLETS nasa ba za su taɓa yarda da cewa shi yake furta kalamai haka ba. Duk da idanuwansa a rufe, a jikinsa ya ji tana kare mashi kallo, hakan yasa ya ɗaga mata gera ɗaya. Wani irin sihirtatcen kyau ya kara, ga gashin gerar nasa kullum kara cika suke yi sosai, tamkar ana saka masu taki, har ta kusa haɗe mashi, gasu a kwance luff, kyakkyawar jajir ɗin kumatunsa, wani irin laushi ne da su kamar fatar jariri, sai kyalli soft skin nasa take yi sosai da sosai, dogon hancin nan nasa, tamkar shi ya bawa kansa saboda yanda ya zauna ɗas a face nasa, sak hancin Dr William, lips nasa kuwa, ba'a magana, dan gabaɗayansu TRIPLETS Allah ya yi masu halittar lips mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali, lips nasu na saman design of heart ne, na kasan kuma yana da ɗan faɗi kaɗan, gasu jajir dasu tamkar an saka masu red janbaki, ga laushi kamar fure, ga ɗan bakin nasu ɗan karami da shi, sai dara daran idanu tamkar na Dr Salman. "Noorish, meyasa nake sanyaka farinciki idan ka kalleni?". Sai a lokacin ya waro idanunsa a kanta. A cikin idanunta ya kalli tsananin son ya ce yana sonta da take yi, tana tsananin so ta ji kalmar so daga bakinsa. Shiru ya ɗan, kafin ya ce "Ni ma ban san dalili ba, kawai dai idan na ganki, ina shiga farinciki". Wani irin yawu ta haɗiye, dan ba hakan take son ji daga gare shi ba, amma ba komai. Shi ma yasan ba hakan take son ji ba, tana so ne ta ji ya ce saboda yana sonta, da gangan ya bata wani amsa da ban, yana tsananin jin daɗi idan yana ja mata rai. "Noorish kazo ka ci abinci". Ta faɗa a takaice. "Meesha saboda ban baki amsar da kike so bane zaki nuna mani baki son cigaba da yin hira da ni?." Girgiza mashi kai ta yi tana sunkuyar da kanta ƙasa. "To meyasa zaki nuna kin gaji da hirarmu?". "Noorish ni fa nafi son ne ka ci abinci, gwaggo ta ce mani baka ci komai ba, to ka zo ka ci ga ji?". "Meesha meyasa kike koyan yin karya ne?". Zaro idanu ta yi tana kallon wuyarsa. "Yau sau biyu kina yi mani karya, ɗazun kince mani ciwon ciki ne ya saka ki yin kuka, kuma ba haka bane, na san ba haka bane, kewata ce ta saki kuka, duba da yanda action naki ya kasance lokacin da na shigo cikin bedroom ɗin naki, wanda cikinsa yake ciwo, har ya kasa yin kuka da karfi su dad su ji su kawo ɗauki, ba zai diro kasa daga saman gado da gudu har ya nufoni zai rungumeni ba, yanzu kuma kin sake yi mani karya na biyu, why?". "Noorish kenan kasan cewa ina sonka?". Ta tambaya tana hawaye, dan bata taɓa tunanin duk abin da take yi yana sane ba. Ɗago haɓarta ya yi yana goge mata hawayen, yana faɗin "Na sani mana, na san duk irin haukar sona da kika yi tun kina ƴar shekara tara har izuwa yau, kuma nima ai ina sonki ki sarkin rigima". Da sauri ta waro idanunta waje, har tana haɗe word wajen cewa "Noorish da gaske kana sona?". Jinjina mata kai ya yi yana faɗin "Yeah, i really love you so much, shikenan kin ji amsar da kike son ji?". Cusa kanta a cikin kirjinsa ta yi tana dariya, kamar ba ita ce mai zubar da hawaye a yanzun nan ba. Zuba mata idanuwa ya yi yana kallon irin tsantsar farinciki da yake a kan fuskarta. "Noorish to tun yaushe ka fara so na kai kuma?". Ta yi tambayar tana ɗan ɗago kanta. Shiru ya yi almost na tsawon 2 mins, sannan ya ce "Actually i don't know wen, amma dai abin da na sani, kin fara burgni tun time da muka tafi Russia, and ban yarda da hakan ba sai jiya, zuwa yau kuma na yanke hukunci". Lafewa ta yi a kirjin nasa tana ta sauke uban ajiyar zuciya. Zazzaƙar sexy voice nasa ne ya daki dodan kunnenta. "Ba zaki bani gift bane My Meeesha?". Da sauri ta ɗago kai tare da manna mashi sumbata a lallaudan kunatunsa. "Ya yi maka haka?". Ta tambaya tana kallon lallausar wuyarsa. Kin amsa mata ya yi, dan bata yi mashi ba, Iya sumbata kawai zata bashi? Gaskiya baya so, so yake yi yau da kanta ta yi kissing nasa. Jin ya yi shiru ne yasa ta fahimci sumbatar bai yi mashi ba kenan. "To Noorish ka rufe idanunka, sai na baka wani, tun da wannan bai yi ba". "Me idanuna suka yi maki da sai na rufe? Ina ruwanki da su?". Kuka ta saka mashi tare da komawa ta lafe a saman kirjin nasa. Shiru ya yi bai tankata ba, sai ma yatsa da ya sanya mata a cikin bakin nata. Da taga shi fa ba zai rufe idanu ba, da gaske yake yi, ya fi son ya ga komai abinsa, dan bai san kunya ba. Sai ta ɗago kai tana turo baki, sai wani kumbure kumbure take yi, ko kala bai ce mata ba, ido kawai yake binta da shi. Saƙalo wuyarsa ta fara yi, sannan ta matso da face nata dab da nasa, datse idanunta ta yi, tana ƙoƙarin fara kissing ɗin nasa ne ya dakatar da ita, tare da ce mata idan dai ba zata buɗe idanu ba, to shi baya so. Bata da zaɓi, dole da waro idanunta waje, dan furta kalmar i love daga bakin Lion ba karamin abu bane, bai taɓa faɗenta ga kowa ba bayan TRIPLETS nasa, sai mommansu a yanzu, to ba karamar kalma bace, dole a bashi tukuici mai kyau. Lips nata har kerma suke yi wajen fara kissing nasa, yana ta kallon cikin idanunta, ko motsawa bai yi ba, Allah ya gani yana matukar kaunar waɗan nan Sleeping eyes ɗin nata, suna narkar mashi da zuciya, sai ma idan ta tsorata a kan abu, ta zarosu, habawa, har rasa nutsuwarsa yake yi, sai azababen sha'awarta ta motsa mashi idan ya gansu tana a cikin tsoro. Sosai ta yi kissing nasa, sannan ta zame bakinta daga nashin, da sauri ta yunkura zata bar jikin nasa. Rikota ya yi tare da tambayarta a ina ta koyi kiss kuma?. Galala ta saki baki tana kallonsa, shi fa ya koya mata abu, amma dan neman magana yake cewa a ina ta koya. "Kai mana ka koya mani". Ta bashi amsa a takaice. "Ni na taɓa kissing naki ne?". Zaro idanu sosai ta yi, ta rasa ma me zata sake ce mashi. Tsawa ya daka mata tare da sake tambayarta a ina ta koyi kiss, dan shi bai taɓa kissing nata ba. Nan take ta tsorata, ta zaro idanu, jikinta har ya fara kerma. Rungumeta sosai ya yi tare da juyawa da ita, ya zamana ya yi mata rumfa da kirjinsa, dama burinsa kawai ya tsoratata, dan ya kalli abin da yafi kauna a tattare da ita, wato Sleeping eyes nata a cikin tsoro. Kissing nata ya fara yi babu kama hannun yaro, dan wannan tsorata da ta yi, ta saka ya shiga cikin yanayi, dole ya fanshe jefa shi da ta yi a ciki kuwa.............NIMA DOLE NA HAƊA KAYANA NA YI GABA, WANNAN LAMARI YAFI KARFINA🥳🧐 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E7 *💔SORRY FOR TODAY PAGE🧠🥺💔*. *Today I know your brain🧠 will be very confused, so I apologize for that, the story is like that, I have to write what I planned from the beginning, I can't change anything about my story, I know you won't like that, anyway I apologize💔🧠* Kissing nata ya fara yi babu kama hannun yaro, dan wannan tsorata da ta yi, ta saka ya shiga cikin yanayi, dole ya fanshe jefa shi da ta yi a ciki kuwa, kankame shi ta baya gam ita ma ta yi. A hankali ta fara mayar mashi da martanin kissing nata ɗin da yake yi. Hannu ya kai saman wuyar rigarta, a hankali ya yi ƙasa da wuyar, tare da fara shafa breast nata, sannan ya zame ɗan bakinsa daga nata da nufin ya mayar kan nipples nata. Tamkar jira take yi ya zame bakin nasa, ta ce "Noorish akwai camera a ɗakin nan ko kuma babu?". Cak ya tsaya da abin da yake yi mata, a hanzarce ya ɗago da idanunsa da suke jajir da su kamar wuta. Mikewa zaune ya yi yana sauke numfashi a hankali. Sosai ta tsorata, dan tana tunanin ko tambayar da ta yi mashi ne yasa ya rabu da ita. "Sorry Noorish". Ta faɗa tamkar zata yi kuka. "Meesha let's go". Ya faɗa tare da mikewa da sauri. A hanzarce ta ce "Noorish dan Allah ka tsaya na tambayeka". Yana ƙoƙarin shiga dressing room na ɗakin ya bata amsa da cewa yana jinta. "Na ji gwaggo ta ce yaranta masu blue eyes irin naka su biyu ne, amma kuma naga kai kaɗai ne a cikinku mai blue eyes". Cak ya tsaya, ya fasa shiga cikin room ɗin, a dubu ya juyo da kallonsa a kanta. Zaro idanu ta yi, jikinta har ya fara kerma, dan tana tunanin ta faɗi abin da ya ɓata mashi rai ne. Shi kuma mamakin ta yake, ya sani a gabaɗaya cikin palon, gabaɗaya waɗan da suke wajen time da gwaggon ta bada labarin, babu wanda ya lura da zancen da gwaggon ta ce na cewa masu blue eyes biyu, dan da sun lura, dole zasu tambaya, amma saboda kaifin ƙwaƙwalwa irin na Rimsha, ita har ta rike cewa su biyu ne masu blue eyes, lallai akwaita da basira, wato tun jiya ma abin yana cikin ranta, ta rasa waye zata gayawa ne kawai. "Kayi hakuri Noorish, ban ɗauka maganar zata saka ka ji babu daɗi ba". Girgiza mata kai ya yi yana faɗin "No baki ɓata mani rai ba, you are special My Meesha". Ya kai karshen maganar tare da karisa shiga cikin room ɗin. Shiru ta yi tana tunani, har ya fito sanye da jallabiya fara kal a jikinsa. "Let's go". Ya faɗa tare da miƙa mata hannu alamar ta zo gare shi. Da sauri ta diro kasa daga saman bed ɗin, a hanzarce ta tafi ta faɗa jikinsa tana sauke ajiyar zuciya. "Meesha pray for me more kin ji ko?". Yana magana yana shafa kanta izuwa bayanta. Gyaɗa mashi kai ta yi tana faɗin "In Sha Allah mijina, addu'a sosai zan yi maka". Hannunta ya riko tare da ɗan raba jikinsu, har lokacin idanuwansa suna nan jajir da su, yau ya so ya yi romancing nata over, amma kuma tasa ya tuna da wani abin, dole ya je ya aiwatar da abin da wuri, dan dama tun jiya abin da yake ta tunani a kansa kenan, yanzu tasa ya samu kaso talatin cikin ɗari na abin da yake nema. Da sauri ya nufi hanyar fita daga ɗakin hannunsa na ruke da nata. Mamaki take yi a kan meya faru yake sauri haka. Bai zame ko'ina ba sai ɗakin gwaggo. Zaune ya iskota ita da Aseef, sai kukan shagwaɓa yake zuba mata, ya haye mata gado tare da tada kai da cinyarta, shi dole sai an ɗauko mashi matarsa, ta ce ya yi hakuri tun da sun kira Areef a waya ya ce zai zo da ita, to ya dai'na kuka zata dawo, kwafa ya yi tare da gayawa gwaggon Allah yau ba zai kyale Heartbeat ɗin nan ba, sai ya bata wahala fiye da tunanin kowa, ita dai gwaggon, sai rarrashi kawai take yi. A gefenta ya zauna, tare da zaunar da Rimshar a gefensa. Cikin sanyin murya ya ce "Momman i want to ask you something!". Dawo da kallonta a kansa ta yi tana faɗa mashi tana jinsa. "Momma a wani gidan kaka ɗaya kika kaiwa daddy mu time ɗin? And them a wani gida kuka zauna da Josephine?". Ba tare da ɓata lokaci ko wani dogon tunani ba ta bashi amsa kai tsaye, dan bata manta komai ba, komai yana nan a cikin brain nata. Wayarsa ya ɗauko, cikin sauri ya kira Tyrone, dan dama already Tyrone ɗin ya koma shi kam. Bugu ɗaya ya ɗaga, ba tare da ɓata lokaci ba ya ce mashi ya je gidan da su Dr William ɗin suka zauna, dan gidan yana nan yanda yake, babu abin da aka taɓa a ciki tsawon shekarun nan, sai ma zuwa da ake yi ana gyara shi kowani sati, so komai yana nan normal, dan haka Tyrone ya je gidan da akwai camera a palon gidan, ya ciro mashi camerar yanzun nan, ba tare da ɓata lokaci ba, sannan ya shiga ainahin computers room da yake cikin gidan, ya duba stories, ya ɗauko mashi memory na shakaru 31 zuwa 32 baya. Okey Tyrone ya amsa da shi. Katse kiran ya yi tare da miƙewa ya nufi waje, bin shi da kallo dukkansu suka yi, harda Rimshar. Sai bayan ya fita ne Rimshar ta ce "Yaya Aseef ni ka tashi mani a saman cinyar gwaggona zan kwanta". Kin kulata ya yi, sai aikin tura baki yake yi abinsa. Gwaggon ce ta ce mata ta zo ta kwanta a gefe, ta rabu da Aseef ɗin nan, rigima yake ji dashi, yanzu ya tashi barci, ko breakfast bai yi ba, ya tsayar masu da rigimar sai an ɗauko mashi Akila. Tuna cewa Lion bai ci komai bane yasa ta miƙe tare da cewa Gwaggon a'a tana zuwa dai. Ɗakin da suka fito ta koma, abinsa ta ɗauko mashi, sannan ta dawo cikin bedroom nasa. Zauna a saman bed ta iskosa, ya sanya laptop a gaba yana ƙoƙarin kunnata. A saman carpet ta ajiye abincin, sannan ta dawo kusa da shi ta zauna. A tsananin shagwaɓe ta ce "Noorish, idan baka jin yunwa, Meeshan ka fa tana jin yunwa, ban fa ci komai ba, kuma ni da kai nake son muci abinci". Yanda ta yi maganar tasa bai san time da ya juyo gateta ba. Yana juyowa ta faɗa jikinsa tana zuba mashi shagwaɓa. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, wani irin sanyi ya ji a ransa, hannu ya kai ya shafi kanta, ƴar karama da ita, amma ta samu tarbiya sosai, ta kuma iya soyayya sosai, duk fushi da halin mara daɗi da mutun zai shiga, ta san ta yanda take kwantar mashi da hankali, yanzu ga shi dai a kage yake da ya fara binciken nan, har ya mance da cewa yana jin yunwa, amma daga zuwanta, ta zuba mashi shagwaɓa, har ya ji yunwar ta dawo sabuwa, sai ya ji hankalinsa ya kwanta sosai. "Muje to na baki abincin a baki ko?". Ya faɗa a sanyaye. Da sauri ta ɗago kanta, tana ƙoƙarin ta yi magana, sai ga Brady ya shigo ɗakin da gudu. Kai tsaye ta kanta ya bi ya haye jikin Lion ɗin, da alama bai ma lura da ita ba. Ihu ta zunduma tana ƙoƙarin ta gudu, rikota da sauri ya yi, sannan ya dakawa Bradyn tsawa a kan ya sauka mashi a jikinsa, zai haukata mashi ƙwaƙwalwar Meeshansa, yasa tana zunduma ihu haka. Haushi Bradyn ya daka masu, irin ya ji haushin nan shi ma. Hannu Lion ɗin ya ɗaga zai mare shi, ai a dubu ya diro kasa, da gudu ya nufi waje, dan ya san marin Lion fa ba wasa ba, ya taɓa marinsa sau ɗaya, a lokacin ya yi mashi ɓarna, ya kuwa wanke shi da mari, to shi ne har yanzu bai mance da marin ba, da Lion ɗin ya kara marinsa, gara ya gudu abinsa. "Kin cika tsoro Meesha, Brady is your friend, ki dai'na tsoronsa, babu abin da zai yi maki, kuma shi ba zai dai'na shigowa nan at anytime ba, yakamata ki saba". Ya kai karshen maganar tare da ruko hannunta suka mike tsaye. Wajen abincin suka nufa. Ita ta zuba masu abincin a plate. Spoon ya ɗauka tare da ɗebo abincin, yana ƙoƙarin kaiwa bakinsa, ta yi maza ta kwace tare da fara tauna. Ko sannu bai ce mata ba, ya sake ɗebo wani ya kai bakinsa. Haka suka cigaba da cin abincin cikin nishaɗi da tsantsar farinciki. A ɓangaren gidan Abba kuwa, bayan sun tashi da safe, su daddyn Anaya sun zo, haɗuwa suka yi a palon gidan Abba, sai hira suke yi, suna jiran gwaggo da TRIPLETS nata, sai daddyn Rimsha, zasu yi magana ne a kan abubuwan da suka faru a baya. Sai hira suke zubawa kamar ba gobe. Can wuraren karfe 12, daddyn Rimsha, mummy, Areef da kuma Jehan da Akila suka zo gidan. Nan fa hira ta kara armashi, abin ba kama hannun yaro. Brr Naurat ce ta dakatar da su ta hanyar gabatar masu da Alex duk da cewa baya wajen, yana gidan Lion, a kage suke da son ganinsa, amma bai zo ba, yana tare da Mark. "Zahradeen ina matanka da ƴaƴanka?". Cewar Brr Naurat, ta tambayi Abbi kenan. Cikin girmamawa ya nuna mata, Aunty, Irfan, da kuma Umaisha da take a wajen, sai ya rufe da cewa Aafia tana gidan mijinta. Murmushi Brr ta yi tare da zuba masu addu'a da ruwan albarka, sannan ta tambayi Abba ma, shi ma haka ya gabatar da nasa matar da ƴaƴan, haka shi ma ta zuba masu addu'a, sai da ta bi gabaɗaya ƴaƴan nata ta tambayesu, daddyn jelly shi ne na karshen da ta tambaya. Kallon Jelly dake zaune kusa da Ammie ta yi shiru kamar wata mara lafiya ya yi, cikin sanyin murya ya ce "Wannan ita ce kaɗai ƴata, Allah ya yi wa mahaifiyarta rasuwa, sai matar da na aura a yanzu". Ya kai karshen maganar yana juye juye dan neman Ayla, bata a wajen sam. Fuska ɗauke da mamaki ya ce "Sadiya ina Ayla take?". Da sauri Aunty ta ɗago kai tana ƴan waige waige, sam babu ita a cikin palon. Tambayar juna suka fara yi, kowa yace tun safe shi bai ganta ba. Abba ne ya ce jelly da Akila su tashi su je su dubata a ɗakunan gidan, wata kila tana can tana barci ne saboda ciki. A hanzarce suka miƙe suka haura sama. Suna tafiya Abbi ya ce "Hossain me ya sami Akila a idanunta kuma?". Girgiza kai daddyn Rimsha ya yi yana faɗin "Kuka ta yi mana". "Kukan me kuma?". Daddyn jelly ya tambaya da sauri. Zai sake yin magana su Akilar suka sauko suna gaya masu bata cikin ɗakun dukka sun duba, har a cikin toilet dukka sun duba bata ciki. Nan fa hankulan kowa ya tashi, wannan ya kalli wannan, wannan ma ya kalli wannan. Kasancewar da turanci suke magana, sai Areef ma ya saka masu baki, dan ya ji komai da suka ce, da turanci suke yin magana, saboda Brr Naurat bata wani iya hausa ba, Hausan nata a kwaɓe yake, dama bata iya shi sosai ba, sai kuma ta sake komawa ƙasar Russia tsawon shekaru, hakan tasa ɗan Hausar da ta iya ma shaf ta gudu daga bakinta, shi ne yasa suke magana da English. Mikewa suka yi gabaɗayansu, harabar gidan suka fito, duk suka rarrabu aka fara nemanta. Amma ina, shiru, babu ita babu alamarta, nan take mamanta ta fara kuka, dan ita ma tana wajen, daddyn Jelly tamkar zuciyarsa zata fashe, amma ya daure suka cigaba da nemanta. JAMA'A INA AYLA TA SHIGA⁉️ Shiru shiru fa babu ita, Areef ne ya tambayi daddyn Jelly a kan ko ta ce mashi zata je wani waje ne ya hanata, shi ne ta yi tafiyarta, nan fa ya yi masu bayani, ita Ayla bata da kowa, bata san kowa ba face su Abbi, sai su Rimsha, kuma ko harabar gidansu bata taɓa fita ba tare da shi ba, kullum tana ɗaki abinta, idan kunganta a waje, to a tare suke za su fita unguwa, ita ko waya ma yanzu bata da shi, saboda cikin nata ma ya tsani ana latsa waya a kusa da ita, dan haka in dai Ayala bata gidan nan, to wlh hannu ne ya ɗauketa, tabbas ɗaukarta aka yi!!. Tashin hankali!!! Shiru Areef ɗin ya yi kafin ya sake cewa "To waye kake tunanin zai ɗauketa? Shin kana da abokin gaba na bayyane ne?". Jinjina masu kai ya yi yana faɗin "Baban Muneer, shi ne kawai abokin gaba na wanda ya yi niyar ɗauke Jelly ya haɗata aure da Muneer a lokacin baya, to bayan shi kuma, ni bani da wani abokin faɗa". "Waye baban Muneer ɗin? Kuma a ina yake?". Areef ya sake tambaya. Kasancewar daddyn bashi da burin da ya wuce yaga matarsa ta dawo, sai ya basu labarin tsamar da take a tsakaninsu da baban Muneer ɗin, bai ɓoye masu ba, harda videon da ya yi mashi na sharri duk ya gaya masu. "Aina yake to yanzu?". Areef ne ya sake tambayarsa, nan ma basu amsa ya yi da shi dai a Kano ya barosa, so bai san a ina yake ba yanzu. Kallon Imran Areef ɗin ya yi yana faɗin "Zamu je wajen yanzu ko prof?". Jinjina mashi kai Imran ɗin ya yi. Nan take hankulan kowa ya kara tashi, ganin da gaske Ayla fa ta ɓata ne, babbar magana. Areef, Imran, da kuma Irfan ne suka nufi Kanon tare da tallafawan daddyn Jelly da ya basu number wayar babban yaronsa, wato engr Muhammad Imam, a kan idan sun je Kanon su nemesa, zai yi masu karin bayani a kan wanene Baban Muneer, zai ma kaisu har companynsa. Da farko daddyn Jelly ya ce da wuya idan baban Muneer ɗin ne ya ɗauketa, dan shi a Kano yake, sai da Areef ya gaya mashi cewa, ai zai iya turowa a ɗauko mashi ita, dan wlh mai son abinka, ya fi ka sanin hanyar kula da shi, dan ya ɗauka, shi ne sai hankalinsa ya yarda a kan hakan. Da kyar Abba ya lallaɓa matan suka koma cikin palo, su kuma mazan, wato su Abbi, sai suka fita gari nemanta, ko Allah zai sanya a ganta, daga nan su kai report station da sauransu........NIMA PRINCESS TEEMA INA TAYAKU DA ADDU'AR ALLAH YASA A GANTA ƊIN, AMMA ƁATAR AYLA BA KARAMIN ABU BANE, DAN DOLE DAI HANNU NE YA ƊAUKETA, SABODA BAIWAR ALLAH NAN KO HARABAR GIDA BATA FITA, TO WAYE YA ƊAUKETA? ALLAH SARKI, GA KARAMIN CIKI, GA UBAN LAULAYI. A ɓangaren Lion kuwa. Bayan sun kammala cin abinci, Rimsha ta kwash kayan abincin ta fitar, ta gyara wajen tsab, sai ta dawo ta haye saman bed nasa, a kusa da shi ta kwanta, tare da lumshe idanu, ba jimawa barci ya yi awon gaba da ita, saboda daren jiya bata samu damar runtsawa ba. Shi kuma Lion, yana can yana aikin latsa laptop nasa, Tyrone ya ɗauko mashi wannan memory da camera ta naɗi komai, sai dai, da kyar aka samu memoryn, dan ma dai babu nai shiga gidan nan, kuma dama ana ajiye storyn camera irin haka sosai, so suna nan a ɗakin computers ɗin, an dai ci kwakwa ne kafin a nemosu. Miƙewa Lion ɗin ya yi tare da ficewa daga bedroom ɗin. Ɗakin gwaggo ya koma, tambayarta ya je ya yi a kan zata iya tuna ranar da abin ya faru a tsakaninta da Dr William, ma'ana ranar da ta kai mashi TRIPLETS ɗin gidansa. Cikin sauri ta ce ai bazata taɓa manta wannan rana ba, biyu ga watan biyu ne. Jinjina mata ya yi da ƙoƙarinta na ruke komai na tsawon shekaru a kanta, sannan ya juya ya koma bedroom nasa. Cewa Tyrone ɗin ya yi da ya saka memoryn a laptop, ya duba mashi videon biyu ga watan biyu a shekaru 32 baya. Okey ya amsa mashi tare da fara aikin babu kama hannun yaro. Cikin ƙanƙanin lokaci ya samo video ya turowa da Lion ɗin. A hanzarce ya buɗe video, dan dama jira kawai yake yi. Shiru ya yi ya zubawa video idanu yana ganin komai kamar a gaske a gabansa ake yin komai. Tun daga shigowar gwaggon gida, tun wayewar garin ranar, har shigowar gwaggon da TRIPLETS ɗin, yanda ta faɗa, ga yanda ta kwantar da su a saman sofa, komai da komai yana gani kamar a zahiri. Dai'dai lokacin da Dr William ya bugawa jariri ɗaya santa, sai da Lion ɗin ya datse idanunsa, saboda har cikin ransa ya ji saukar wannan sandar, babu irin azabar kalolin kisa da Lion bai gani ba, amma ba zai iya jure gani ko ɗan ƙaramin bulala ne ya taɓa TRIPLETS nasa ba, shiyasa lokacin da ya ga Dr ya kwalawa ɗaya ɗaga cikinsu sandar, sai da zuciyarsa ta amsa, ji ya yi tamkar shi aka bugawa. A hankali ya waro idanunsa ya cigaba da kallon video, yana ganin gwaggo ta fice waje da gudu, shi kuma Dr William ya yi kan yaran da gudu bayan ya jefar da sandar, ita ma Josephine da gudu ta kariso cikin palon. Ɗaukar jaririn Dr ya yi, da gudun gaske ya nufi waje da shi, sai zubar da jini kansa yake yi, kai tsaye asibiti ya nufa shi da Uncle Herry, ita kuma Josephine, kan sauran jarirai biyun ta nufa, da sauri ta ɗauko ɗaya ta ruke a hannunta tana shafa ɗayan da yake kwance a saman sofar da hannunta, dan ta tabbatar da lafiyarsu. Sai ruwan hawaye take yi. Kamar daga sama wani mutun ya faɗo cikin palon, wani dogo da shi, yana sanye da bakaken kaya, long cut ce baka a jikinsa, daga ta cikin kuma T-shirt ce mai karamar hannu, ita ma baka, ya sanya wata hula mai gashi a kansa, fuskansa na a sanye da black mask, hannayensa dukka biyu suna sanye a cikin hands gloves bakake kirin suma, kafarsa na'a sanye cikin Booth baka kirin, baka iya ganin komai na daga jikin mutumin nan fa ce idanunsa da suke ashe color masu tsananin haske kamar glass, tamkar ba na mutun ba. Hannunsa na ruke da jariri sabon haihuwa cikin towel baka kirin, ga jaririn fari kal da shi, kasancewar yana jikin bakar towel ga shi fari kal, sai ya haska sosai. Kai tsaye Josephine mutumin ya nufa, yana zuwa ya miƙa mata jaririn da yake a hannunsa, karɓa ta yi, ita kuma sai ta miƙa mashi ainahin cikon TRIPLETS da yake a hannunta, tana yi tana shafa kan baby ɗaya da yake kwance. Juyawa mutumin ya yi da ainahin cikon TRIPLETS ɗin a hannunsa, ta kofar da ya shigo, ta nan ya fita, ita kuma Josephine, sai ta cirewa jaririn da mutumin ya kawo waɗan nan bakaken kayan da suke jikinsa, sai ta ɗauko wani towel fari daga cikin ɗaki ta rufe shi da shi, sannan ta kwashi bakaken kayan ta nufi waje da su. Jim kaɗan ta dawo, kusa da jariran ta dawo ta zauna tana kare masu kallo, babu wanda zai iya banbanta su, babu wanda zai iya cewa su ba TRIPLETS bane, wancan ɗin ya saje da ɗayan. Wani irin datse idanuwansa gam Lion ya yi da karfin gaske, tamkar zai fashe idanun nasu, karo na farko a rayuwarsa da ya fara danasanin gani abu, da ya sani, da bai kalli video nan ba, dan wlh ba zai taɓa yarda ace ɗaya daga cikinsu ba cikon TRIPLETS nasa bane, da bai kalla ba, da ya rufe maganar sun tafi a haka har su mutu, ba zai iya taɓa rabuwa da ko ɗaya daga cikin TRIPLETS nasa na yanzu ba, yau an zo gaɓar da ya kasa, ba zai iya ba. Toma a cikinsu wanenen jaririn da mutumin nan ya kawo? Kuma ina shi wanda aka ɗauka? Me aka yi da shi? Meyake faruwa ne? Josephine ta sadaukar da shi kenan? Ko yaya ne? Wanne ma wannan mutumin? Meyasa dukka hakan ta faru?. Wannan shi ne tashin hankali. Cikin tsananin zafin rai Lion ɗin ya ɗauki laptop ɗin ya makata da jikin bangon ɗakin, ji kake yi war, ta tarwatse, dafe kansa dake yi mashi barazanar tarwatsewa ya yi, cikin fitar hayyaci ya miƙe tsaye, wani irin azababben jiri yake gani, duniya juya mashi take yi, gara ace mashi mutuwa ɗaya daga cikinsu ya yi da wannan bakin abin da ya gani, wlh sai dai ya rufe maganar nan, amma ba zai taɓa iya rabuwa da Areef ko Aseef, su ne bugawar zuciyarsa, shi kam ya yarda sune TRIPLETS na sa, a bar mashi su kawai........ Ba shakka da akwai ciwo na wuce misali a cikin rayuwar TRIPLETS tamkar yanda Malika ta gayawa Rimsha a baya, to a hankali dai ga shi abubuwa sai bayyana suke yi, mu je zuwa dai, ku kasance da PRINCESS TEEMA, dan ni kaɗai ce zan iya warware maku wannan babbar al'amari, kun dai ga abin da Dr William ya karyata na cewa bai san gwaggo ba, to ga gaskiya ta fito, ga komai kamar yanda gwaggon ta faɗa!! Lallai akwai wani abu wai shi ruɗanin kwakwalwa a cikin TRIPLETS!!. Waje ya nufa, sam baya ganin gabansa, dan wani irin jiri da uban duhu da yake gani, ji yake tamkar zai haɗiye zuciya ya mutu kawai ya huta. Ɗakin gwaggo ya nufa, da hannu biyu dukka ya dafe kan nasa da ƙarfin gaske, yana tafiya yana huci tamkar ransa zai fita, iska mai tsananin zafi ce take fitowa daga bakinsa, ya ilahi ya lillahi!!. Da sauri gwaggo ta mike tana tambayarsa lafiya. Ina ai bai kai ga karisowa in da take ba, ya zube kasa wanwar, baya numfashi!. A dubu gwaggon ta kariso wajen da yake kwance, shi ma Aseef da yake kwance yana aikin zuba shagwaɓa, a ɗari ya sauko daga saman bed ɗin, bai ma san time ɗin da ya iso wajen ɗan uwan nasa ba. Sunansa suka fara kira babu kama hannun yaro, ina ko motsawa bai yi ba, tamkar rai ne ya yi halinsa. Fridge Aseef ya nufa da sauri. Ruwa mai bala'in sanyi ya ɗauko, tsabar shiga tashin hankali har kerma jikinsa yake yi, da kyar ya iya ɓalle bakin robar ruwan. Tashin hankali ya hana shi ma ya iya tarbo ruwan a hannunsa, da bakin rofar ya fara zazzagawa ɗan uwan nasa, ita kuma gwaggo, sai ambatar sunansa SAIF!! SAIF!! SAIF! take yi. Tas Aseef ɗin ya zazzaga mashi ruwan, amma ina ko motsawa bai yi ba. Ganin duk wannan uban ruwa mai bala'in sanyi da ya zuba mashi bai farka bane yasa ya zunduma uban ihu tare da fara jijjiga shi da karfi yana kiran sunansa da ya tashi, kada ya mutu ya barsu, ba zai iya rayuwa babu shi ba, dan Allah ya tashi. Wannan ihun da ya zunduma ne yasa Uncle T ya shigo ɗakin a guje. Ganin abin da yake faruwa ne yasa ya kariso ciki da sauri. Sai kuka Aseef yake yi tamkar ransa zai fita, bawan Allah!. Babu ɓata lokacin TGA ya naɗe hannun rigar jikinsa tare da sanya karfi ya saɓi Lion ɗin a kafaɗarsa, kai tsaye sai waje ya nufa. Da sauri suka rufa mashi baya. Bai tsaya tambayarsu me ya faru ba, kawai ya sanya shi a cikin mota tare da bawa Mark umarnin a kan ya ja su zuwa asibiti. Kafin su gwaggon ma su iso harabar gidan, har Mark ya tashi motar. Gabaɗaya sojojin da suke gidan, kowa ya nufi sauran motocin dake cikin gidan dan su rufa masu baya. Donal Aseef ya kira cikin kuka, ya ce mashi ya ɗauko mota su bi su TGA, sai ringin wayar Aseef ɗin take yi, amma ina hankalinsa baya a tattare da shi, kuma Areef ne yake kiransa, dan ya kira wayar Lion yafi sau a kirga, amma bai ɗauka ba, shi ne ya kira Aseef ɗin dan ya ji ko lafiya, saboda a jikinsa yana jin tamkar basu lafiya, kamar akwai wani abin. Amma ina Aseef ɗin ma yaki ɗaukar kiran, shi burinsa kawai Lion ya tashi....... MASU KARATU, WANNAN SHI NE ASALIN CAKWAKIYA, LITTAFIN TRIPLETS YANZU ZAI ƊAUKI ZAFI JAU KAMAR WUTA, KADA KU MANTA BOOK 4 MUKE, KUMA SHI NE LAST IN SHA ALLAH, TO MUNA FATAN AYI KOMAI A NAN A GAMA, HAR KULLUM PRINCESS TEEMA TAKU CE TA AMANA.💋 Gwaggo babu ko mayafi a kanta, daga ɗankwalin doguwar rigar jikinta, shikenan, haka ta bi su a motar Donal ɗin. Bayansu TGA suka bi, Uncle Herry kuwa, yana can yana kula da Dr William, bai ma san abin da yake faruwa ba, John da Jay kuwa basu ma a gidan gabaɗaya, sun tafi yawonsu!. Rimsha sarkin rigima, tana can tana barci ga Noorish nata tamkar rai ya yi halinsa! WANNAN KENAN, ABIN DA YAKE FARUWA A GIDAN LION, BARI MU LEƘA GIDAN ABBO, WATO WAJENSU DR NAWID, WATA KILA KAFIN MU DAWO, ABUBUWA SUN ƊAN YI SANYI, GIDAN ABBA BA SAUKI, AYLA TA ƁATA, GIDAN LION KUMA YA MA KAMA DA WUTA BAL, BAL NE MA GABAƊAYA, SABODA BALA'IN TASHIN HANKALI DA SUKE A CIKI, TO BARI MU JI GIDAN ABBO KUMA KO DA ƊAN SAUKI SAUKI. GIDAN ABBO. Gabaɗaya familyn Abbo, wato Ummi, Dr Nawid da Aafia, suna a cikin tsananin tashin hankali, suna tsaka mai wuya, yau tsawon kwana uku kenan Dr Nawid yana kwance rai a hannun Allah, ko motsawa baya yi, ga idanuwansa a buɗe garau, amma baya iya ko motsawa, likitoci daban daban Ummi ta kira, amma kowa ya zo, sai ya ce babu wani abin da yake da munsa, su basu ga ciwon komai ba, ga shi Abbo dai baya nan, shiru babu shi babu labarinsa, haka Ummi ta daure ta fara shirye shiryen fitar da Nawid ɗin kasar waje. Abin da ya faru shi ne, suna tsaye a kitchen suna aiki shi da Aafia, ranar bai je office ba, sai ya bita kitchen yana tanaya aiki kamar dai yanda suka saba, sai zuba soyayyarsu suke yi kamar ba gobe, bawan Allah lafiyarsa lou wlh, babu ko ciwon kai a tattare da shi. Haka kawai ya yanke jiki ya faɗi kasa, sai wani bakin ruwa ya fara fito mashi daga bakinsa, abin ya yi mugu mugun girgiza su Ummi, Aafia ba'a magana, ta yi mummunar rama yarinyar nan, dan kun sani, tun farkon littafin nan, tana bala'in son Dr Nawid, Ummi kuwa, shi kaɗai ne ke gareta, bayan shi bata da wani yaro, dole ta shiga tashin hankali na wuce misali, bayin Allah, wannan shi ne abin da ya faru. Sai shirin fitar da shi kasar waje suke yi. Yau ta kasance ranar Friday, bayan an sauko daga sallar jumma'a, Aafia tana zaune a gefensa a saman bed nasu, ta yi mashi alwala dan ya yi sallah ko da da idanu ne, dama haka take yi mashi kullum, tana yi mashi alwala idan lokacin yin sallah ya yi, ita kuma Ummi bata nan, tana gidan Abbin Irfan, dan suma sun san abin da yake faruwa, Abbin ne ma yake shirya masu fita kasar waje dan neman lafiyar Nawid ɗin, so ta je su yi magana da Abbin. Shiru Aafia ta zauna tana ta kallon mijin nata, shi kuma sai kallon sama yake yi, dan ko juya idanun nasa ma baya iya yi. Hawaye masu matuƙar zafi ne suke gangaro mata daga cikin idanunta, duk ta bushe ta yi wani irin baki tamkar mai cutar kanjamau, sai idanu kawai zaka gani dara dara a face nata, duk wanda ya ganta sai ya matsa mata kwallah. Yau tsawon kwana uku Dr baya motsawa, ta yi nisa cikin tunanin da take yi, kamar daga sama ta ji voice nasa yana faɗin "Aafia ba zan tashi ba, mutuwa zan yi, ki yafe mani idan na taɓa yi maki wani laifi, sannan ki roka mani gafara a wajen Ummi, ta yafe mani, ina tsananin sonku, amma ba zan rayu da ku ba, sannan ki sani wannan cuta da ta kamani........" Bai kai karshen maganar ba ya sake yin shiru ɗiff tamkar an ɗauke wutar nepa. Tun da ya fara magana, a tsakanin razane Aafia ɗin ta ɗago tana kallonsa, still idanuwansa suna kallon sama, sun kafe, bai iya motsasu, kuma bakinsa ma bata motsawa, kawai dai ga muryarsa nan tana fitowa ana magana da ita, amma sam sam babu wata gaɓa da ta motsa daga jikinsa!. Toh fa!! Ta tsorata sosai na ganin hakan, sunansa ta fara kira, Yah Nawid, Yah Nawid, amma ina shiru bai amsa mata ba, tana ƙoƙarin ta sake yi mashi magana, sai ta ga idanuwansa sun sauya color izuwa purple eyes. Zaro idanu sosai waje ta yi, tamkar idanun nata za su fito su faɗi kasa, tana ƙoƙarin gudu ta sauka kasa, sai ta sake ganin idanun nasa sun sake sauyawa izuwa bakin kirin, babu ɗigon fari ko kaɗan a cikin idanun nasa, wani irin hayaki ne mai matukar warin gaske ya fara fitowa daga bakinsa, bakin ruwa mai kaurin gaske ya fara zuba mashi daga hancinsa, haka zalika kunnuwansa ma hayakin ne ya fara fitowa. Wani irin uban ihu ta zunduma tare da sauka kasa da uban gudun gaske, a dubu ta nufi waje. Tamkar zararriya haka ta bazama izuwa harabar gidan, dai'dai lokacin kuma motar Ummi ya danno kai, ta dawo daga gidan Abbi, ta je ma bata samu ganawa da shi ba, saboda suna cikin tsananin tashin hankali na ɓatar Ayla, so suma yau ba'a zaune suke ba. Ganin yanda Aafiar ta fito a gigice tana zunduma ihu ne yasa Ummi ta dakatar da motarta ba tare da ta karisa parking space na gidan ba. A hanzarce ta fito daga cikin motar, Aafia kuwa bata ma bi ta kanta ba, ta nufi waje da gudu, tamkar ƙwaƙwalwarta ya taɓu ne, da alama ta zauce. A hanzarce Ummin ta ce mai gadi ya rufe gate ɗin, kada ya bari ta fita, sannan ta yi maza ta rikota tana ambatar sunanta, amma ina banda wannan ihu da take zunduma, babu wani abin da take yi. Da kyar Ummin ta jata izuwa cikin palo, ɗaki ta sakata ta rufe kofa, sannan ta ɗauko wayarta, cikin tsananin tashin hankali ta kira Abbi dan ta sanar da shi abin da ta zo ta tarar a gidan again. Ta yi sa'a ya ɗaga kiran, bayan ta gaya mashi, sai ya ce mata to Akil yana zuwa yanzu, daga haka suka yi sallama, sannan ta kira ƴan uwanta a Katsina ta gaya masu halin da yau kuma suke a ciki. A palonta ta zauna, ta kasa shiga ta sake duba Aafiar, shi dama Dr Nawid bata san me yake faruwa da shi ba, bata san me Aafiar ta gani ta haukace haka ba, baiwar Allah, tana zaune ta buga uban takumi tana jin yanda Aafiar take yi mata watsi da kayan ɗaki har Akil ya kariso. Tana ganinsa ta miƙe a hanzarce tana kara yi mashi bayanin abin da yake faruwa. Ina Aafiar ya tambaya, da sauri ta nuna mashi ɗakin da take, ba ɓata lokaci ya nufi cikin ɗakin. Yana buɗe kofar Aafiar tana gefo mashi kwalbar perfume a goshinsa, nan take ya fashe wajen, jini ya fara tsastsafa. Salati Ummin ta fara yi, komai na cikin ɗakin Aafiar ta yi watsi da shi, har kayan jikinta ta cire, ya rage daga ita sa underwears, suma sai ƙoƙarin ciresu take yi. Sam Akil bai damu da ji mashi ciwo da ta yi ba, karisawa cikin ɗakin ya yi tare da yin bismilah ya damkota da karfi, kokawa ta fara yi da shi da iya karfinta, shi ma saka karfi ya yi sosai ya murɗe hannayenta izuwa baya, sannan ya kaita kasa, dan ta kwanta, hakan zai taimaka mashi wajen danneta ya yi mata addu'a. Ummi kam ban da kuka babu abin da take yi. "Ummi jeki waje". Cewar Akil ɗin, dan ya lura idan bata bar wajen ba, ba zata dai'na kukan ba. Jiknta har kerma yake yi ta koma palo ta zauna. Shi kuma ya fara tofawa Aafia ɗin adduo'i har barci ya ɗauketa a wajen. Dogon numfashi ya ja tare da saukewa a hankali na ganin ta yi barci, runtse idanuwansa ya yi yana tunanin meyake shirin faruwa da FAMILYNSU ne? Ayla ta ɓata, gwaggo ta kira waya cikin tsananin tashin hankali ta sanar masu Lion yana asibiti tamkar babu rai a tattare da shi, yanzu kuma ga Aafia ta haukace, anya kuwa ba wani gagarumin bala'in bane yake shirin afkuwa? Anya lafiya kuwa? Meyasa kuma dukka abubuwan a lokacin guda rana ɗaya?! Sannan a hankali abubuwan suna ta shafar kowa da yake a cikin familyn? Wai shin menene gaskiya? Waye zai warware mana wannan rikicin?........ Alkalami PRINCESS TEEMA ce kawai zai warware maku menene ainahin abin da yake shirin faruwa dama wanda yake faruwa a yanzu, ku dai ku kasance tare da ni!!. Ganin ta yi barci ne yasa ya saketa tare da fitowa palo wajen Ummi, har lokacin sai kuka take yi, hakuri ya bata tare da tambayarta ina Dr Nawid yake bari ya duba jikinsa, sannan zai wuce gida da Aafiar dan a ragewa Ummin wahala. To kawai ta ce mashi, sannan ta wuce gaba zuwa ɗakin Dr Nawid ɗin, bayanta ya bi cike da tausaya mata. Baki ɗauke da sallama suka shiga, yana kwance tamkar yanda yake kullum, idanuwansa sun koma yanda suke, kamar basu taɓa canza launi ba, wannan hayaki da Aafia ta gani ta zauce, duk sun dai'na fita, komai ya ɓace, ya koma kamar yanda yake. A gefen gadon Ummi ta zauna, shi kuma Akil ya matso kusa da shi da nufin ya tofa mashi adduo'i. Kallo ɗaya ya yi mashi ya san cewa rai ya yi halinsa, babu rai a tattare da shi. Zaro idanu ya yi, sannan ya kalli Ummi dake ta faman ruwan hawaye, nan take zuciyarsa ta karaya, ya ji ba zai iya gaya mata cewa Dr Nawid ya rasu ba, dan shi ne kaɗai gareta, idan ta ji zuciyarta zata iya bugawa wlh, Innallilahi wa Innallilahi ilaihir raji'un, hasbunallahu wani'imal wakil. Daurewa ya yi ya tofawa gawar addu'a, sannan ya ce mata yana zuwa, to kawai ta bishi da shi. Fitowa waje ya yi ya kira Abbi a waya, ya sanar mashi wlh Dr Nawid Allah ya yi mashi rasuwa, Allah ya karɓi abinsa. Ba karamin girgiza Abbin ya yi da jin wannan bakin labarinba, dukkansu Ummin kawai suke tausaya, baiwar Allah, da ma ace tana da wasu yara ne, to da da sauki, amma shi kaɗai, ga shi Allah ya karɓi abinsa, innallilahi wa innallilahi ilaihir raji'un, yanzu ta yaya za su iya gaya mata wannan bakin labarin? Matar da kullum take zarya a kan rashin lafiyar nan tasa, ko abinci bata iya ci, ta rame fiye da tunanin mai tunani, duk ta fita a cikin hayyacinta, ta firgice kamar ba ita ba, ashe maganar da Dr ya yi wa Aafiar nan shi ne maganarsa ta karshe a duniya, ya ilahi ya lillahi. Cewa Akil ɗin Abbin ya yi a kan suna zuwa yanzu, amma kada ya bari Ummin ta gane komai. Okey ya amsa tare da katse kiran ya dawo cikin palon. After some minutes sai ga su Abbin sun iso, har da Abban Imran da daddyn jelly, shi dai Abbo shiru babu shi babu labarinsa, kuma babu wanda ya iya tunawa da shi. Wayo suka yi wa Ummin, suka ce mata za su tafi da Dr wani asibiti ne mai kyau kafin komai na su ya kammala su wuce kasar India, dan haka ta bi Akil ya kaita gidan Abba ita da Aafia, dan kada a barta ita kaɗai a gidan. Ita dai ta amsa masu da to ne kawai, amma har cikin ranta tana jin ba lafiya ba, gabanta sai faɗuwa yake yi, sai dai bata musa masu ba, ta bi Akil bayan an saka Aafia a motar, haka ya wuce da su izuwa gidan Abba, su Imran kuma, sun ɗauki hanyar Kano dama already. Suna tafiya su Abba suka kira jama'a, aka yi wa Dr wankar gawa irinta addinin musulunci, sannan aka shirya shi a cikin likkafani, dan su kai shi makwancinsa kuma gidansa na gaskiya......... To masu karatu zan dakata a nan wajen, sai Allah ya kai mu gobe. *Yau na san kwakwalwarku zata shiga ruɗu sosai, to ina mai bada hakuri a kan hakan, labarin ne yake a haka, dole kuma zan rubuta abin da na tsara tun farko, ba zan iya canza komai na labarina ba, na san ba zaku so hakan ba, amma ina bada hakuri dai!!* ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E8 Suna tafiya su Abba suka kira jama'a, aka yi wa Dr wankar gawa irinta addinin musulunci, sannan aka shirya shi a cikin likkafani, dan su kai shi makwancinsa kuma gidansa na gaskiya. A takaice su Abbi suka kai shi kabarinsa, ma'ana su suka yi jana'izarsa, sai dai duk cikinsu an rasa wanda zai iya gayawa Umminsa ga abin da yake faruwa, sai faman nuku nuku suke yi, dan suna tsananin tausayawa baiwar Allah'n nan. A ɓangaren su Imran kuwa, sun isa Kano lafiya, kuma sun haɗu da baban Muneer a companynsa, a cikin office nasa, ya yi masu iso. Ba tare da ɓata lokaci ba Areef ya fara jefa mashi tambayoyi, sai dai Areef ɗin da kallo ɗaya zaka yi mashi, kasan yana cikin tsananin tashin hankali, duk da bai san abin da yake faruwa da Lion ba, amma a jikinsa yana jin lallai ba shakka ɗaya daga cikinsu bashi da lafiya, dan bugawar zuciyarsa sauri take yi tamkar yanda na Lion ɗin take bugawa da sauri, duk ya firgice tamkar ba shi ba, har Imran ya iya ganewa, ya tambaye shi ko bashi da lafiya ne? Ko kuma tafiyar da suka yi a mota mai tsayin ne ya jijjiga shi?. A'a ya amsa masu da shi, sannan ya ɗaura masu da cewa, shi ai idan ya je kasar da bai sani ba, yana yin tafiya mai tsawo a cikin mota, dan ya zagaye wasu daga cikin states na garin, dama dai Aseef ne ko Lion, sune za'a ce ba lallai su iya jure tafiya mai tsawo a mota ba, dan basu saba ba, ko'ina za su je, to wlh suna zaune a cikin gida, basu fita yawace garinma bare sauran states dake makwabtaka da garin, amma shi ai yana yawo sosai abinsa, su kwantar da hankulansu, kawai dai yana jin jikinsa ba daɗi ne. Bawan Allah bai san cewa Lion yana kwance a gadon asibiti ba, kuma kamar yanda yake kwance bashi da lafiya, haka shi ma Areef ɗin yake tafiya da ciwo a jikinsa, da alama zuciyoyinsu a haɗe take over. Kafe masu baban Muneer ya yi a kan shi bai ma san waye daddyn Jelly ba, kallon Imran Areef ɗin ya yi, sai ya yi mashi magana da larabci a kan, su kyale shi da mutumin bari ya gyara mashi zama!. Da baban Muneer ɗin yaga za su matsa mashi, sai ya ɗauko wayarsa ya yi ƙoƙarin ɗaura videon daddyn Jelly da ya ɗauke shi a media kowa ya gani, ya yi ƙoƙarin cin zarafin familyn Dr Salman kenan. Ganin yana latsa wayar jikinsa har wani kerma yake yi, ga shi kuma sai musa masu yake yi a kan shi bai san wanenen ma daddyn Jelly ba, sai yasa Areef a cikin tunani. Duk cikin office ɗin, cikin Imran da Irfan babu wanda ya lura da abin da baban Muneer ɗin yake yi, shi kuma Areef ya lura da lallai ba abin arziki yake yi da wannan wayar tasa ba, dan kuwa ga jikinsa sai kerma yake yi, hannunsa sai ɓari take yi, dama haka mara gaskiya yake, duk in da za'aje a zo, baya ɓuya. Shammatarsa Areef ɗin ya yi ya fusge wayar da karfi, har wani miƙewa baban Muneer ɗin ya yi tare da nufin ya kwaci wayar, wani irin wawan mari Areef ɗin ya ɗauke shi da shi, nan take hakwaransa biyu suke fita daga bakinsa. Tsawa ya daka mashi a kan ya koma ya zauna, idan ba haka ba, yanzun nan ya yabawa aya zaƙinta, an gaya mashi su sha'anin wasan sa ne?. Ƙoƙarin gudu ya yi ya fita daga cikin office ɗin, Areef yana daga zaune yasa kafa ya kwashe kafafunsa, sai ga baban Muneer ya zube a kasa wanwar yana baza babbar riga, ya yi shiga ta mutunci tamkar mutumin kirki, ashe dai babbar rigar ce kawai. "Prof ɗaure mani shi mu tafi da shi, dan jikina duk a mace, i can't do anything yanzu, ina son in je gida first, dan haka mu wuce da shi gidan kawai". Cewar Areef, yana maganar yana duba wayar baban Muneer ɗin. Ganin abin da yake cikin wayar na shirin yin posting na video a media da ya yi ne ya kara ɓatawa Areef ɗin rai, sannan ya kara mashi shakku da zargin baban Muneer ɗin a cikin zuciyarsa, idan ba rashin gaskiya ba, menene na yin yunkurin posting na video daga tambayarka ina Ayla? Da farko ma cewa ya yi shi bai san daddyn Jelly ba, to a ina ya samo wannan video kuma? Ga shi dai daddyn Jelly ne a cikin videon. Ƙoƙarin kurma ihu baban Muneer ɗin ya yi, dan ma'aikatansa su kawo mashi agaji, sai dai ina, bakinsa ma ya yi muguwar kumbura, saboda hakwaransa guda biyu da suka fita, ga jini da yake malala kamar me, kun san hakori ba wasa ba, fitarta akwai azaba ga zubar da jini, bare ma shi da hakwaran suka fita ba shiri, dama gasu ba kyan gani, duk sun yi baki, saboda busar sigari, nan take bakin ta sunduma suntum, tamkar ruɓaɓɓen alala. "Areef ni fa ba zai iya ɗaura mutumin nan ba, wannan aikin sai ku". Cewar Imran. Harara Areef ɗin ya wurga mashi, da dara daran ldanun nan nasa, kafin ya ce "Prof ba zaka canza ba har gobe, ka yi auren ma baka gyaru ba?". Shi ma hararar ya wurga mashi yana faɗin "Kai kam da ka yi auren ka gyaru ne? Ko dama akwai wanda ya ce maka aure yana gyara mutun ne? Kai ma ai gaka a yanda kake da shegen mugunta kamar Saif, yanzu kawai ka kama ka cirewa mutun hakwara da mari, dan tsabar zafin zuciya". "Ka dai'na cewa kamar Saif, just call me Saif ɗin kawai kai tsaye, kuma ni ai ban san me auren bane shiyasa ban gyaru ba, amma kai fa? I think ma your wife has pregnant ma ko?". Cewar Areef ɗin. "A'a Jelly bata da ciki, muna dai fatan samu, kai ba zaka dai'na saka mani ido ba ko? Wai waye ma ya gaya maka ni ma na san menene aure?". Allah sarki shi dai Irfan, sai binsu da idanu kawai yake yi, yana ɗan murmushi, dan bashi da ta cewa, bai ma san me auren ba bawan Allah. "Ka san aure mana, kai ne ma kasa na fara sha'awar yin auren". "Ni kuma?". Ya faɗa yana zaro idanunsa irin na Jellyn nasa. "Yeah kai mana, ko na tuna maka wen aka yi hakan ne?". Ganin abin kamar wasa Imran ɗin yake yi, sai ya ce "Yeah tunan mani". "Time da ka yi dis virgin na matar taka a gida, a time ɗin ka fara saka mani sha'awar yin aure, and then yan da kuke da matar taka, rigimammiya mara jin magana, tana baka wahala, abin yana yi mani daɗi, ina jin daɗin in ga tana wahalar da kai". Ya kai karshen maganar yana switch off na wayar baban Muneer ɗin. "Wato Areef har gobe ba zaka canza ba ko Areef? Sai mutun ya kalli kamar baka san meyake faruwa ba, amma ka san komai, wato yanzu duk zaman da na yi da Jelly a gidan kasan komai ko?, Amma ban taɓa tunanin haka ba, sai mutun ya ganka kamar wani malamin islami, har ma jin daɗi kake yi idan Jelly tana wahalar da ni ko?". Mikewa ya yi yana ɗan bincika cikin office ɗin ko zai samu igiyar da zai ɗaure baban Muneer ɗin, yana tafiya yana faɗin "Ni ai har abada ba zan canza ba, an gaya maka C.I.A wasa ce? Ai ni da ido ma idan naga mutun nasan ina ya dosa, just kawai kai ne ba zaka gane nasani ba, saboda already basaja a cikin jinina take, zan iya yi maka basaja kamar mace, kuma mu zauna da kai a haka". "Da wannan murɗaɗɗen jikin naka ne zaka iya zama macen". Cewar Irfan, ya yi maganar da mamaki a kan face nasa, ya ga ne damatsan hannun Areef ɗin ma kawai abin kallo ne, sannan ga shi da tsawo da cikar halittar namiji, sannan ya ce mashi zai iya basaja a matsayin mace? Ai dole ya tambaya da mamaki a saman face nasa, dan ba gym na wasa shi ma Areef ɗin yake yi ba, jikinsa ta murɗe sosai. "No Irfan, idan nace basaja a matsayin mace, ba ina nufin zan ɗauki kayan mata or something like that in yi amfani da su ba, you are not a C.I.A, that's why ba zaka gane ba, i mean zan iya zama da kai cikin raunin zuciya like mace, you will feel like bani da wayo, ina da raunin zuciya, and ina da ragonta, like yanda mace dai take, shi ne nufina". Jinjina kai Irfan ɗin ya yi, sai yanzu ya gane nufin Areef ɗin. "Kai Prof waye ma ya ce ka ɗauka mani matata jiya ka tafi da ita? Na baka izini ne?". Ya yi maganar yana bubbuɗe drawers dake a cikin office ɗin na wajen ajiyar takardu. "Waye ya ce maka ni na ɗauke ta?". Harara ya sake wurga masu kafin ya ce "Ban samu peace of mind a daren jiya ba har sai da na bincika a motar waye ta biku, na san Lion ma ya bincika, kuma sai ka yi mashi bayanin dalilin da yasa ka kwashe mana bebs namu, ka hanamu jin daɗi". Dariya sosai Imran ɗin ya yi, sannan ya ce "Ka ce jiya na ɓata maka harka? To ni nama san ta biyo ni ne". "Ka dai ɓatawa Aseef harka, kuma wlh ba zai kyaleka ba, dan tun safe yake rigimar a bashi matarsa, kuma tun jiya da safe ya gaya mani ba zai kyaleta ba, idan suka dawo daga unguwa, sai ya yi dis virgin ɗinta, shi ne ka rusa mashi shirinsa ba? Zaku haɗu ne wlh, kasan halinsa, ni matata yarinya ce ai, sai ta girma, zan dai yi ta tsokanarta". Wani irin dariyar iyashege Imran ɗin ya yi yana faɗin "Au dama haka aka yi? Kace Allah ya kuɓutar mani da sisterta, baiwar Allah, da yanzu tana can tana fama da azaba, da Aseef ya wahalar mani da ita". "Au kai ba sister tamu ka azabtar ba kenan?". Cewar Areef Shi dai Irfan tamkar babu shi a cikin office ɗin, shiru abinsa, sai binsu da idanu yake yi, sai da ya ji sun shigo da hirar Akila da Aseef ne ya ji zuciyarsa ta yi bakinkirin, sai ya ji dama bai biyosu ba, su kuma da alama Imran ya mance da cewa Irfan ɗin shi zai auri Akilar a baya, shi dama Areef bai san waye zata aura aka fasa auren ba!. "A'a ni ban yi wa sisterku komai ba, ita ta ce mani tana son baby, ni kuma na bata, amma ina da tabbacin Akila bata cewa Aseef tana son baby ba, kawai zai azabtar da yarinya dan mugunta ba? To Allah ya kama shi, ta gudu ta koma gida". Cewar Imran. Hawa sama table Areef ɗin ya yi yana ƙoƙarin kwance camerar dake a cikin office ɗin, ya ce "Jalilar ce ta ce maka tana son baby? Yarinyar da ita da kanta ma baby ce, wannan a ina zata iya renon yaro? Ita kanta yaushe ta gama kuka ana rarrashinta? Ai da ita da Rimsha ni ban san waye gwamma ba, kai dai prof ka ji tsoron Allah, ka dai'na azabtar da ƴar mutane, kada ka je ka bata ciki, wlh wahala kawai zaku sha". "Ai jelila ba zata ɗauki ciki yanzu ba In Sha Allah, dan idan ta ɗauki ciki a yanzu, to na shiga uku, ta bakin naka ne, yanzu haka idan ta fara yi mani kuka, to sai na yi zaman rarrashi, ina ga kuma mun sami baby? Ai na shiga uku kawai, barmu dai mu cigaba da soyayya, zuwa gaba, idan ta kara girma, ta rage shagwaɓa, sai mu nemi baby, amma dai Areef kai mugun ɗan sa ido ne, waye wai ya gaya maka halin Jelly?". Shiru ya yi bai bashi amsa ba, dan tun da yake, bai taɓa tsayawa ya yi hira mai tsawon haka da wani ba idan ba TRIPLETS nasa ba, ba shi da yawan magana, amma da TRIPLETS nasa yana magana, yau ɗin ma abin da yasa ya zage yake yin maganar, saboda yana so ne ya manta abin da take a zuciyarsa na tunanin gida, abin ya tsaya mashi a rai, so yana so ne ya ɗan rage damuwar, shi ne yasa ya biyewa Imran ɗin, ban da haka, ba zaka taɓa jin ya yi magana ta tsawon minti biyu mai kyau ba, zaka gan shi kamar bai san komai ba, amma wlh babu wani abin da bai sani ba, duk zaman da su Imran da Jelly suka yi a gidan, ya san komai, duk abin da suke yi, yana sane da komai, kawai dai baya shiga harkar kowa, kuma baya da yawan magana, shi ne yasa sam yake kamar bai san komai ba. "Prof ka ji tsoron Allah, dama ni nasan abin da ya sa kayi aure kenan, amma kana musawa friend naka a kan ba auren kashe sha'awa ka yi ba". Cewar Areef. A wannan gaɓar Irfan ne ya karɓi zancen da cewa "Kowa ya sani mana, auren rage zafi ya yi, amma yana musa mana, yanzu idan ba haka ba, me na hana Jelly ɗaukar ciki? Ai idan ta samu ciki ma dole zata rage shagwaɓa, kuma daga haka zata girma". Ganin suna neman kure shi ne yasa ya ce "Ni ban hana Jelly ɗaukar ciki ba, ai ciki na Allah ne, idan Allah ya ƙaddara lokacin zuwansa, to kome zamu yi, sai ta ɗauke shi". "Yanzu mu kenan zaka gwadawa Allah ba? To ai komai sai da sanadi, mun san Allah yake bada ciki, amma ta sanadin sex ko?" Cewar Areef....... Dama wannan magana ta rashin kunya ai sai Areef ɗin, shi da bai san kunya ba.🧐 "Ni ba zan biye maku ba, dan ni nasan gaskiyar tsananina da Jellyna, ni da yanzu gado ma daban daban muke kwana da ita". Wani irin kallon Areef ɗin ya wurga mashi, irin kallon nan na bashakka haka ne, basu ma kwana ɗaki ɗaya ba iya gado daban daban ba, dakin ma daban daban suke, ɗan rainin wayo kawai. Irfan ne ya ce "A'a karshe ma dai kana palo tana cikin ɗaki, shi ne karshe ba gado ɗaya kuke kwana ba". Areef kuwa cewa ya yi "Ni prof sam ban san daga ina ka samu wannan jarabar tsiya ba, Allah dai ya bawa sister hakurin juriya". Irfan ne ya ce "Kila dai ina ga mata huɗu zai aura, dan wannan mace ɗaya ta yi mashi kaɗan". Allah sarki yau walaƙanci suke jin yiwa Imran, sun saka shi a gaba, bawan Allah. Shi kuma Imran ɗin cewa ya yi "Yanzu kai Areef har kana da bakin cewa wani yana da jaraba? To aishekenan, Allah ya kwaci Jehan, dan da kake cewa sai ta girman nan ma, duk na san zance ne kawai, bari ka samu dama, hmmm na dai yi shiru". "Irfan mata huɗu fa ka ce? A nan ku kuna auran mata huɗu kenan?". Cewar Areef ɗin. Jinjina mashi kai Irfan ɗin ya yi tare da tabbatar mashi. Girgiza kai ya yi yana faɗin "No, we are marring only one girl, mu ko biyu ma bamu yi, Just 1 is okey, amma why zaku auri mata biyu ma? Ɗaya bata isa ba? Me zaku yi da har guda biyu? I can't share my heart to two girls, i can't share my love to two girls, is better for me to share the love and the heart with my childrens and 1 girl, so that we should get more happiness". Ya kai karshen maganar yana saukowa daga saman table ɗin, ya kammala kwance camerar. Shi kuma baban Muneer baki sai kara kumbura yake yi, ya yi suntum, raɗaɗi da azaba sun hana shi ko motsawa. Imran ne ya ce "Ni kai'na ba zan iya auran mata biyu ba, but most a time zaka samu masu auren mata biyu ɗin, jaraba ce ta yi masu yawa, and then suna ganin like matan ba za su iya kula da komai nasu ba, wasu kuma rashin samun soyayya daga wajen matan ne yake kaisu ga ƙara aure, wasu kuma rashin samun farinciki ne yake saka su yin wani auren". Maimaita kalmar soyayya da farinciki Areef ɗin ya yi kafin ya ce "I think namiji shi ne yake bawa mace farinciki, i think shi ne ya kamata ya koya mata sanya shi farincikin, idan har kana sanya matarka farinciki, kana yi mata soyayya, to dole ita ma zata sanyaka farinciki, ga example a kan ni da my baby, before bata sona, amma yanzu ina mai tabbatar maka, wannan tafiya da nayi tana cikin damuwa, kuma ni na koya mata so na ɗin, ni na koya mata menene so, menene kuma farinciki, so duk abin da ka ɗaura mace a kai tun farko, a haka zata ɗaure, komai jarabar namiji, mace tana iya ɗaukarsa tsab, saboda halittarsu ce a hakan, duk yanda ka rukesu, to a haka zasu ɗaure maka har abada, idan baka bata farinciki ba, ta yaya zata baka ita ma? Idan baka kula da ita ba, ta yaya zata kula da kai? Ni ban ga wani dalili na kara aure a nan ba, is better na yi sharing love ɗina da yarana, na kuma sanyasu farinciki, seriously i love Jehan more than your expectations, then i can't share her love with other girls, she is special in my heart, bazan iya haɗata da kowa ba, dan ba zan yi adalci ba, daga kanta an gama". Ya kai karshen maganar yana ciro wayarsa dake ruri yana neman agaji. My uncle, shi ne sunan da ya bayyana a saman screen ɗin wayar. Cool murmushi ya saki kafin ya ce "My diramati, ba zata iya rabuwa da ni ba, and then kuma ba zata barni na zauna kusa da ita ba, amma for sure zan yi maganinki". Ya kai karshen maganar tare da ɗaukar kiran. Kamar yanda ya yi tsammani cewa ita ce ba daddynta ba, haka kuwa ita ɗin ce. Sallama ta yi mashi cikin nutsuwa, amsa mata ya yi yana mamakin ya aka yi ta nutsu muryarta akwai girmamawa a ciki haka? Bai san cewa mum ce ta yi mata faɗa sosai ba, lokacin da ta yi mashi tsawa a palo a gidansu da safe, bayan ya saketa ta koma sama, da mum ta haura saman, zuwa ta yi ta sameta, ta yi mata faɗa sosai tare da tunatar da ita cewa, Allah yana tsinewa mace mai ɗaga murya sama da na mijinta, sannan kuma yakamata ta sani miji ba abin wasa bane, dan ta samu yana sonta, yana biyemata a duk shirmen da zata yi mashi, to wlh gara ta yi amfani da damarta, idan ba haka ba, lokaci ya kure mata ta dawo tana danasani, Areef yana da hakuri sosai, ta sani mai hakuri fa bai iya fushi ba, fushinsa bashi da kyan gani, to wlh kada ta kuskura ta kure shi, zai yi mata ba daɗi, to shi ne nasihar ta shiga kunnan ta, dama kuma da ni da ku dukka mun san tana tsananin son shi, kawai iyashege ne irin nata, yanzu ma ba wai dan nasihar mum ɗin ce tasa ta kira shi ba, a'a tsananin kewarsa ne ya takura mata har ta ɗauki wayar daddynta ba tare da saninsa ba, ta ɓuya ta kira mijin nata............. Ni ko na ce ana so ana kaiwa kasuwa, ni idan ta yi mashi walakanci na janye shi daga gareta ato, dan samun irin Areef a zamanin nan da kamar wuya, abin sai an tona, ko ya kuka ce masu karatu? In yi wuff da abina, yo meyafi ra'ina? Miji na gari a zamanin nan wasa ne?. Gaisuwa ta ɗaga mashi cikin girmamawa. Mamaki ce tasa har ya ɗago yana kallon su Imran, tare kuma da ɗan raba wayar da kunnansa, dan ya tabbatar ita ɗin ce, shi dai yasan wannan voice nata ne, dan ko muryar kowa zai ɓace mashi, to muryar TRIPLETS nasa, daddynsa, Rimsha da kuma ita Jehan ɗin, sai gwaggo a yanzu, muryoyinsu ba zai taɓa bace mashi ba. Ya yi shiru ya kasa amsawa, sanyayyar muryarta ta sake dakan dodan kunnensa. "Yaushe zaku dawo?" Shi ne tambayar da ta sake yi mashi. "Kina son na dawo ne?". Jinjina mashi kai ta yi tamkar tana a gabansa, sannan ta ce "E ina so". "Why kike son na dawo?". Shiru ta ɗan yi kafin daga bisani ta amsa da "I want to see you close..." Sai kuma ta kasa karisawa. Dogon numfashi ya ja tare da saukewa a hankali kafin ya yi kasa da murya sosai ya ce "Meyasa kika kasa karisa maganar? Kina kewata ne?". "E a'a ni dai kawai ka dawo"............ Ji wata amsa, wai e a'a kai Jehan duniya ce. Murmushi kaɗan ya yi yana faɗin "Sai after one week zan dawo". Shiru ta yi, sai kuma ta katse kiran. Shiru shima ya ɗan yi yana ɗan murmushi, almost 2 mins, sannan ya sake kiranta. Kira na farko bata ɗaga ba, sai a na biyun ne ta ɗaga. "Ya naji kin katse kiran kuma?" Ya tambaya yana kokarin ciro wata igiya da ya gani a wajen kusa da Ac. Muryarta kamar na mai kuka, da alama kuka ta yi, ta fara magana kasa kasa. "Na ji kace sai after one week zaka dawo ne, shi ne na barka sai bayan one week ɗin". "To me kuma ya sanya ki kuka?". A takaice ta ce "Ni ba kukan da na yi!". "Am so sorry my baby, wasa nake yi maki, naja kin zubar da hawaye a banza, idan na dawo dole zan biya hawayen nan, ai nima ba zan iya yin kwana ɗaya ba tare da na ganki ba, anjuma kaɗan zan dawo, me kika ajiye mani?". Sam bata san time ɗin da murmushi ya subce mata ba, ga hawaye a face nata falala. "Duk abin da kake so". Ta bashi amsa tana goge hawayen nata. "Are you serious?". Jinjina kai ta yi tana faɗin yeah. "Okey tom shikenan, idan na dawo zan gaya maki abin da nake so ɗin, amma yanzu Please give me a kiss". Ya kai karshen maganar cikin wata iriyar murya mai kama da na shagwaɓa. Kafewa ta yi a kan ita bata iya kiss ba, jinjina kai ya yi yana faɗin "Ba zan yi maki dole ba, ki kula mani da kanki kin ji ko? Ko palo ma ni bana son ki fito, ba dan daddy da mummy ba, ai da ba zan barki ma a gidan ba, amma dai ki kula sosai kin ji my pleasure?". Kamar daga sama ya ji ta sumbaci wayar, sannan ta katse kiran ba tare da ta amsa mashi ba. Murmushi ya saki yana mayar da wayar a cikin aljihunsa, sannan ya nufi baban Muneer da yake kwance shame shame a cikin jini. Ɗaure shi ya fara yi, shi kuma Imran, mikewa ya yi tare da ciro wayarsa ya nufi waje yana faɗin "Nima dai bari na ji voice ɗin tawa pleasure ɗin, da dai bani da ita ne sai ka yi mani gori". Ko sannu bai ce mashi ba, ya ɗaure baban Muneer, sannan ya mikar da shi tsaye yana faɗawa Irfan su tafi ko?. Ko da suka fito, ma'aikatan dake companyn, sun yi ƙoƙarin hanasu tafiya da shi, amma sai Areef ya nuna masu tsab zai yi ball da su idan basu tashi mashi a kan hanyarsa ba. A hanzarce wasu daga ciki suka kira office ɗin ƴan'sanda, sai dai kafin ma ƴan'sandan su zo, sunbar company ma abinsu. Haka suka kamo hanyar Kaduna. A ɓangaren Lion kuwa, sai da ya ɗauki good 3 hours a asibiti ba tare da ya motsa ba, sai zarya likitoci suke yi a kansa, Aseef kuwa, da shegen saurin kuka kamar daddyn Jelly, sai zuba kukansa yake yi, har idanuwansa sun kumbura suntum, yaki yarda ya matsa kusa da Lion ɗin, yana zaune a saman bed ɗin, gwaggo na zaune a gefensu, ga sojojinsa suna tsaye cirko cirko a kofar shiga ɗakin, Mark ne kawai ya shigo cikin ɗakin, sai Tga dake ta faman magana da likitoci. Duk wanda ya doso ɗakin da Lion ɗin yake kwance, sai ya juya a dubu ya koma, dan waɗan nan zaratan sojojin da suke tsaye a bakin kofar, ganin su ba ƙaramin razana al'umma yake yi ba, ga su jajir da su, tamkar ka taɓa jini ya zuba, dukkansu babu wanda yake sanye da uniform a jikinsa, duk fararen kaya ne a jikkunansu, fuska kam ba'a magana, kamar na shanu! A ɗaure tamau!. Har sai da Lion ya kara good 1 awa, sannan ne likitocin suka yi nasarar saita bugawar zuciyarsa, suka kuma yi sa'a ya farfaɗo. Yana buɗe idanuwansa, da Aseef ya fara cin karo, ido huɗu suka yi da Aseef ɗin. Da sauri ya mayar da idanunsa ya lumshe, yana tariyo abubuwa da dama a cikin ƙwaƙwalwarsa. Tabbas jaririn da mutumin nan ya kawo, mai brown eyes ne, jaririn da Josephine ta miƙa mashi kuma mai blue eyes ne, shi ma ɗayan jaririn da yake kwance, blue eyes ke gare shi, wanda Dr William ya fita da shi kuma ash eyes ke gare shi, abu biyu ne suka sanya Lion zuciyarsa ta kusa bugawa a cikin wannan video da ya gani, kuma kunsan abin da zai sanya shi suma duk da irin taurin zuciyar nan tasa ba ƙaramin abu bane!!. Abu na farko, jaririn da ya ga mutun ya kawo, tabbas mai brown eyes ne, idan hasashensa gaskiya ce, to Aseef ne kenan, dan wanda yake kwance a saman sofa dai, mai blue eyes ne, hakan na nufin shi ne kenan, babban abin da ya fi ɗaga mashi hankali shi ne, ya fi kaunar Aseef ɗin sama da kansa, ya fi son Aseef fiye da Areef, ya fi son Aseef fiye da kowa, sun fi shakuwa, shakuwar da take a tsakaninsu baki ba zai iya faɗarta ba! Gara ace mashi mutuwa ya yi, da ace mashi Aseef ba jininsa bane! Ba zai iya jurar hakan ba, ko na rana ɗaya ba zai iya rabuwa da shi ba! Yana kaunar shagwaɓatinsa! Yana son ɗan rigimammensa! Yana son pleasurensa! Shi ne bugun zuciyarsu! Ko daddynsu ya fi kaunarsa sama da kowa! Ya ilahi ya lillahi, ina zai saka ransa ya ji sanyi! Josephine ta cuce shi! Ta gama da rayuwarsu, sai da suka saba! Suka taso a tare! Komai tare, shakuwa tasa har suke jin juna a jikinsu, yanzu ya Areef zai ji? Anya zai iya yarda kuwa? Babbar tambayar da Lion ɗin yake yi wa kansa shi ne, to meyasa suka yi hakan? Meyasa aka canza masu ɗayasu? Me suka yi da wancan ɗayan da suka ɗauka? Ina suka kai shi? Yana raye ne ko ya mutu? Shin Aseef mutun ne ko aljani? Cikakken mutun ne kuwa? Ko shi ne yasa yake wasu abubuwa da bana cikakkan mutane ba? Dole dai akwai dalilinsu na yin waɗan nan abubuwa dukkan, haka kawai baza'a canzasu ba! Haka kawai baza'a kawo wani yaro daban a cikinsu ba!! Ni kuma PRINCESS TEEMA abin da yake cikin ra'ina, yake kuma damuna shi ne ya Akila zata yi? Ya zata ji a ranta? Shin zata zauna da wanda ba mutun bane? Ko dai yaya? Anya zata iya rayuwa babu shi kuwa? Tana son heartbeat nata fiye da kanta, wai Meyasa Aseef ya cika mugu mugun shiga ran mutane dayawa har haka ne? Meyasa kowa ya fi son shi? Wannan ma ayar tambaya ce!!. Abu na biyu da ya sanya Lion ɗin zuciyarsa ta kusa bugawa shi ne, wannan mutumin da ya kawo wannan jariri ba kowa bane face uncle Herry, ba shakka uncle Herry ne, dan da kallo ɗaya Lion ɗin ya yi mashi, ya kalle shi da idanun basira, nan ya fahimci uncle Herry ne, duk da ya ɓoye komai na jikinsa, yana cikin shigar bakaken kaya, hakan bai hana kaifin ƙwaƙwalwa Lion ta gane cewa shi ɗin bane, saboda idanun uncle Herry, John, Jay, GTA, daddynsa, Aseef, Areef, ba za su taɓa canzawa ko su ɓoye mashi ya kasa gane su ba, ba zai taɓa kasa ganesu a ko wani irin yanayi ba, zaka gan shi wani lokaci kamar baya kallo abubuwa, amma yana sane da komai, tabbas uncle Herry ne ya kawo jaririn. Tambayar da Lion ɗin yake yi wa kansa, to ina uncle Herry ya baro daddynsu? Ina ya baro Dr? Bayan kuma a tare suka fita daga gidan a lokacin, ko dai ya yi wa Dr ma wani abin ne? Wai shin menene gaskiya? Me yake faruwa ne?!!!. Waɗan nan sune abubuwan da suka hargitsa zuciyar Lion, ace kannen babansa dukka maciya amana, kuma su rasa amanar waye za su, sai na yayan nasu, kai duniya ina zaki damu, ɗan uwa ya ci amanar ɗan uwan sa, sun cutar da rayuwarsu, to wai me suka yi da jaririn da suka ɗauka? Kuma a ina suka samo jaririn da suka kawo ɗin? Ga dukkan alamu dai suma aiki suke yi a karkashin wata kungiya, ko kuma wani, dan ga dukkan alamu umarni suke karɓa, duba da yanda suka tsara abin, a lokacin shekarasun ya yi kankantar da za su iya tsara hakan, sun yi kananan wajen shirya wannan abin, dole akwai wanda ya fisu shekaru da yake shirya masu komai, wannan dalilin yasa Lion ɗin bai ji cewa yana bukatar ya zauna da su, dan su gaya mashi gaskiya ba, dan ya san irin wannan case ɗin, ko kashe su zai yi, wlh ba za su taɓa faɗar gaskiya ba, so is better for him ya nemo gaskiya da kansa, babbar magana, ta ina zaka fara kenan? Waye zaka fara tunkara?!! Murya a dashe saboda kuka Aseef ɗin ya ce "My Lion, please ka tashi ka ji?". Kara datse idanuwansa sosai Lion ɗin ya yi, har cikin ransa yake jin muryar Aseef ɗin, yanzu idan gaskiya ta gama bayyana, shi Aseef me makomansa? Kenan idan ba mutun bane tafiya zai yi ya barsu? Ko yaya ne? Ya ilahi ya lillahi. Gwaggo ce ta matso tana faɗin "Saif ka tashi dan Allah". Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da waro idanuwansa a hankali, kai tsaye sai saman face nata kallonsa ya sauka. Shiru ya ɗan yi kafin ya kai hannu ya ɓalle karin ruwan da aka sanya mashi, ya cire, sannan ya yunkura ya mike zaune. "Saif meyasa ka cire ruwan kuma?". Cewar gwaggo. Girgiza mata kai ya yi alamar baya da bukatar ruwan. Matsowa ta yi tare da dafa kafaɗarsa tana shafa kansa da hannu ɗaya. Ɗago idanu ya yi yana kallon TGA dake tsaye a gefe guda, tun da yake da Uncle T ɗin nasa, bai taɓa tsura mashi idanu yana kare mashi kallo irin na yau ba, zuciyarsa na gaya mashi cewa har da uncle T ɗin yanzu a tafiyar su Josephine ɗin, amma yaki yarda da hakan, saboda wasu dalilan guda biyu, na farko TGA yana sonsu so na tsakani da Allah, dan an taɓa yin yunkurin harbin Lion ɗin ma da bingida, GTA ya tare, ya shiga tsakaninsu bullet ɗin ta same shi, na biyu kuma, TGA yana ɗan ƙaramin yaro lokacin da abubuwan suka fara faruwa, sai dai abin da ya sanyawa Lion ɗin shakku a kan Tga ɗin shi ne, meyake kai shi wajen Josephine a yanzu? A gaban idanunsu zai nuna baya son Josephine, amma a bayan idanunsu zai saci kafa ya je wajenta, ga uncle Herry ma, a gaban idanunsu yana nunawa baya sonta, amma a bayansu kuma 5 and 6 suke da ita. Wannan abin akwai matukar ɗaure kai over. Ganin ya mike zaune ne yasa uncle T ɗin ya kariso wajen nasa da sauri, shi ma Mark karisowa wajen ya yi yana yi mashi sannu. Zuro kyawawan fararen kafafunsa kasan gadon ya yi ba tare da ya ce masu komai ba. A hanzarce Mark ya bashi takalmar dake kafansa, dan ya sanya, saboda ya san halin Ogan nasa da bala'in kyankyani. "Momma let's go". Shi ne kawai abin da ya iya furtawa, sannan ya mike tsaye. Daga Mark har TGA kallon gwaggo da ya kira da momman suka yi, mamaki Mark yake yi, tambayar kansa yake yi wacece gwaggo kuma? Shi dai ya shiga duhu. Wani irin jiri yake gani da ya mike, har wani layi yake yi. Ganin hakan yasa da sauri Mark da Tga suka yi ƙoƙarin tallafa mashi. Hannu ya ɗaga masu alamar baya bukata, sannan ya juyo da kallonsa a kan Aseef dake ta binshi da kallo. Alama da hannu ya yi mashi a kan ya zo ya tallafa mashi su fita, Allah sarki sam baya son Aseef ɗin ya fahimci komai, ya zai ji a rayuwarsa? Ya zai yi da ransa idan ya san gaskiya?. Mikewa ya yi, duk jikinsa a mace, ya nufo Lion ɗin. Ɗan rungumo shi Lion ɗin ya yi yana shafa kansa gwanin ban tausayi, haka suka nufi waje. Da sauri gwaggon ta mike ta rufa masu baya, su Tga suka rufa mata baya. Shi dai Mark kansa ta shiga duhu....... NI KO NA CE MARK BA KAI KAƊAI BA, KOWA MA KANSA TA SHIGA DUHU, WAI KAI DAN MA BAKA SAN ABIN DA MUKA SANI BA, AI DA DUHUN DA ZAKA SHIGA MA BA ZAI FAƊU BA!!. Suna fita sojojinsa suka rufa masu baya izuwa wajen motocinsu. Lion haka kawai yake jin babu daɗi zuciyarsa, tunanin Rimsha dake ta faman sheka barci a gida ne ya faɗo mashi a cikin ƙwaƙwalwarsa, nan take ya ji kirjinsa ta buga, tasbihi ya fara yi a cikin zuciyar nasa, dan ya samu salama, abubuwan sun yi mashi yawa, tunani yake yi bai kamata ya yi nisa da duk waɗan da suke da kusanci da shi ba, dan a wannan point da suke a yanzu, kamata ya yi ya haɗe familyn gwaggon gabaɗaya waje guda, domin kuwa, a yanzu koma suwaye suke bibiyar rayuwarsu, sun san ya san komai, ba shakka za'a cutar da su, kuma tabbas familyn gwaggon za'a cutar, dan familyn daddynsu kam suna da hannu dumu dumu a kan komai, so yana da kyau ya haɗa gabaɗaya ƴaƴa da jikokin Dr Salman waje guda, sannan a saka masu matakan tsaro, idan ba haka ba, za'ayi masu ɗauki ɗai'ɗai!!. Babbar magana. Wayar Aseef ne ta fara kara dai'dai lokacin da suka shiga cikin motar. A hanzarce ya cirota daga aljihunsa, ya sha ruwan mamakin ganin uban miss call na Areef, dan lokacin da Areef ɗin ya yi ta kiransa, sam bai ji ba, baya a cikin hayyacinsa. My uncle, shi ne sunan da ya bayyana a saman screen ɗin wayar. A hanzarce ya ɗauki kiran, a lokacin kuma har motocin nasu sun fara tafiya, sun fito daga asibitin, yana zaune kusa da Lion, shi da gwaggo sun saka Lion ɗin a tsakiya a gidan baya na motar. A hand-free ya sanya wayar, daga ɗayan ɓangaren daddyn Rimsha ya ce "Aseef kuna tare da Akila ne? Ta zo asibitin ne?". Jin tambayar daddyn Rimshar yasa Lion ya juyo da kallonsa a kan wayar. "A'a uncle, ni tun da kuka tafi da ita jiya, ban sake ganinta ba, na kira numberta da safe ma a kashe". "E ba shakka wayarta a kashe, muma mun kira bata shiga, amma ina zuwa". A hanzarce Aseef ɗin ya ce "Uncle lafiya dai ko? Meyasameta? Bata gidan ne? Ina ta ce dama zata je?". Ya yi maganar a rikice. "A'a babu abin da ya sameta Aseef, ka kwantar da hankali, ina zuwa zan sake kiranka". Bai jira masar da zai bashi ba, kawai ya katse kiran. TOH FAH INA AKILA KUMA TA SHIGA⁉️ Karɓar wayar Lion ɗin ya yi, cikin sauri ya fara kiran number Rimsha, dan dama ya kawo wa ransa za'ayi wa matan familynsu gwaggo ɗauki ɗai'ɗai, kuma idan basu yi saurin ɗaukar mataki ba, duk za'a kashe matan ne, dan da alama babu wasa a lamarin masu aikata hakan, bare ma da suka san yanzu asirinsu na gab da tonuwa, ai sai dai wanda Allah ya ƙaddara kwanansa na gaba, amma za'a zubar da jini kam ba kaɗan ba!, Kuma dole hankalinsa zai tashi, saboda a halin yanzu Rimsha ta fi kusa da shi sama da kowa, kuma ga shi shi ne yake shirin bankaɗo gaskiya, shi ne babban makiyin mutanan, ko dan a sanya shi ya rusina, za'a iya yi mata wani mummunar abin, so dole ta kasance a tare da shi a ko da yaushe, rayuwarta yana cikin hadari sosai, da alama ya yi shigar sauri wa mutane, bai shirya ba ya shiga yakin, hakan kuma zai wahalar da shi da na kusa da shi ba kaɗan ba!!. Sai kiran wayar yake yi, amma ina bata ɗauka ba, number Areef ya kira, su kuma a lokacin sun kamo hanyar Kaduna, babu network sam, number bata shiga, tsaki ya ja tare da dakawa Mark tsawa a kan ya taka motar nan da sauri su kai gida da wuri, dan ya duba ya tabbatar Rimsha tana gida or not. Babbar magana. Mikawa gwaggon wayar Aseef ɗin ya yi, cikin sanyin murya ya ce "Momma ki gayawa dukka uncles namu yanzu ba sai anjuma ba mu haɗu a gida, dukkansu da ƴaƴansu gabaɗaya". "Saif meyake faruwa ne? Ɗazun Abban Imran ya kirani ya ce Ayla matar uncle naku Maik ta ɓata, daga baya ya sake gaya mani mijin Aafia ya rasu, ita kuma Aafiar bama su san a wani point zasu ajiye ta ba, yanzu kuma na ji Nawazuddeen yana tambayar Aseef ina Akila, me dukka wannan ne?". Nisawa ya yi kafin ya ce "Momma babu komai, just tell them what i said kawai, and ki yi sauri ki bani wayar ina son in gayawa Areef a duk in da yake, ya yi sauri ya zo gida ina son yin magana da shi......." Bai kai ga rufe baki ba Mark ya ja wata mahaukaciyar burki, waddata sanya su suka tafi luuuu suka buga kansu da jikin sofar motar, shi ma Mark ɗin sai da ya buga kansa da jikin steering motar. Kusan a tare suka ɗago kawunansu tare da kai kallonsu a gaban motar, dan suga menene ya sanya Mark ɗin taka irin wannan burki haka................... ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E9 Kusan a tare suka ɗago kawunansu tare da kai kallonsu a gaban motar, dan suga menene ya sanya Mark ɗin taka irin wannan uban burki haka. Ko da suka ɗago kansu, babu komai a wajen, kan hanyar wayam, da mamaki Aseef yake kallon Mark ɗin, bawan Allah shi kuma wata halitta ya gani tsaye a tsakiyar hanyar, shiyasa ya yi kokarin kauce mata, ashe gizo kawai aka yi mashi, da alama an shirya masu hakan ne domin su yi accident, sai kuma Allah ya karesu da kariyarsa. Aseef ɗin zai yi magana, Lion ya dakatar da shi, sannan ya ce da Mark ɗin su tafi kawai. Kunna motar ya yi suka cigaba da tafiya, ita kuma gwaggon ta kira su Abba kamar yanda Lion ya ce mata, daga haka babu wanda ya sake yin magana a cikin motar. Har sun kusa isa gida, kome Lion ya tuna, sai ya karɓi wayar Aseef ɗin ya turawa Areef massage a kan ya tsananta addu'a sosai a duk in da yake, kada ya bari askar ta kubce daga bakinsa, dan fa akwai gagarumin matsala ba kaɗan ba. Motarsu na yin parking a cikin gida, motar su daddyn Rimsha ma ya shigo cikin gidan, gabaɗaya familyn sun haɗu waje guda, ita ma Akilar sun ganta, ashe makwabtansu ta shiga, ta je su gaisa ne, dan kunga tun da ta yi aure, ai bata je ba, shi ne yanzu da dama ya samu, sai ta leƙasu. Ita kuma Ayla shiru, babu ita babu labarinta. Mark yana kashe motar Lion ya fita daga cikin motar, bai bi ta kan kowa ba ya wuce cikin gida da sauri. Kai tsaye bedroom nasa ya nufa, ya sha ruwan mamakin ganin Rimsha tana zuba barci har iyanzu, kai kallonsa a kan agogon bangon dake manne a cikin ɗakin ya yi. Almost 4 to 5 hours tana zuba barci, anya barcin nan na lafiya ne kuwa? Ya tambayi kansa. Karisawa cikin ɗakin ya yi, cikin nutsuwa ya haye saman bed ɗin, hannu ɗaya ya sanya ya tallabo kanta, sannan ya sanya ɗayar hannunsa ya shafa kyakkyawar face nata. Cool murmushi ta saki har sai da dimples nata suka yi wani irin lotsawa mai matuƙar ɗaukar hankali. Cikin magagin barci ta fara faɗin "Kai Noorish ka bari mana". Kamar tasan shi yake taɓata. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya kai ɗan bakinsa ya sumbaci lallausan lips nata, sannan ya kankameta gam a kirjinsa, yana mai jin wani irin tsananin kaunarta tana ratsa shi. Ya ɗan ɗauki lokaci a hakan kafin ya mayar da ita a hankali ya kwantar, sannan ya diro kasa ya nufi toilet, ita kuma, cigaba da barcinta ta yi cikin kwanciyar hankali. Hakika tabbas an so ɗaukar Rimshar kamar yanda Lion ɗin ya yi tunani, Malika ta ɓoyeta, ko da aka zo ɗaukarta ba'a ganta ba, Malika ta lulluɓeta da nasu siddabarun na aljanu, a gaskiya Malika tana kaunar Rimsha sosai, sannan kuma tana kula da ita sosai, sau da dama tana tare mata abubuwa da dama wanda idan ba ta gaya maku ba, ba zaku taɓa zaton ita ce ta tare ba, so ake ta karfi da ya ji a ladabtar da Lion, so suke su rufe mashi baki a kan case ɗin, so dole suna son yin amfani da rauninsa, dan su sanya ya rusina, sai dai kuma kash, dukka raunin nasa baza su taɓu ba, barema Rimsha da take tare da Malika, ba zata taɓa taɓuwa ba, sai dai idan shammatar Malikar aka yi, tun da dukka abune na tsafi da aljanun, so babu abin da ba zai iya faruwa ba. Wanka Lion ɗin ya yi, sannan ya fito ya shirya cikin kanana kaya, wando three cuter fara kal, da T-shirt sky blue bara nauyi, bai ɗaure gashin kansa ba, ya saketa. Wayarsa ya zo ya ɗauka a saman bed, number Areef ya sake gwada kira, still dai bata shiga, zama ya yi a bakin bed ɗin, number Mark ya kira a kan ya zo ya gyara mashi bedroom nasa, ya kwashe laptop da ya fasar nan. Yana katse kiran ya ji saukar hannayenta a saman kugunsa ta wajen flat tummynsa, ta rungume shi ta baya, a hankali ta kwanto da kanta a saman bayansa, da murya irin na mai barci ta fara magana. "Noorish shi ne baka tashe ni daga barci ba ko?". Nisawa ya yi, har cikin ransa ya ji sassauci na abin da yake ji, ya ji sanyi sosai, hannun nata ya riko ba tare da ya yi magana ba. "Noorish na yi mafarkin wani waje, in gaya maka ina ne?". Tana magana kamar wadda barci bai isheta ba. Juyowa ya yi a hankali, sannan ya jawowata ta dawo saman kirjinsa, zubawa face nata idanu sosai ya yi. Idanunta a rufe ruf take zuba surutu, sai guntun murmushi dake a saman face nata, ga dimples nata duk sun lotsa sosai, sai ta kara kyau matuƙa. "Meesha tun da na bar gidan nan baki tashi daga barci ba?". Ya faɗa cike da tantamar irin barcin da ta rinƙa zubawa kamar ba gobe, abin da bai sani ba shi ne, Malika ce ta sakata yin wannan barci, dan da ta farka, to babu abin da zai hana Josephine bata ɗauketa ba! Saboda yanzu farautar rayuwarta suke yi tamkar ruwa mai sanyi a sahara mai tsananin zafin rana, a gefe guda, ga Queen of Daular Mutuwa tana nemanta ruwa a jallo, daga ɗayan gefen kuma, su Josephine suna nemanta ko ta halin kaka ne su ɗauketa, dan hawai su karyar da zuciyar Lion ɗin, hakan tasa Malikar ta sakata wannan uban barci kamar ba goben, har sai da ya dawo, sannan ta tafi ta basu waje, shi ne ma Rimshar ta iya farkawa. "Noorish ban tashi ba, nifa yanzu na tashi, dama ka fita ne? Shi ne baka tashe ni na raka ba? Na ɓata da kai to". Ta kai karshen maganar tana haɗe mashi fuska, irin ta yi fushin nan. "Open your eyes first, sai ki kalli cikin idanuna ki ce mun ɓata". Make mashi kafaɗa ta yi. Hannu ya kai ya shafi lallausar wuyarta dake kara ɗaukar hankalinsa a koda yaushe. "Open your eyes". Ya faɗa yana gangaro da hannun nasa izuwa kirjinta. A hankali ta waro idanun bata tare kumbura kumatu. Zubawa juna idanu suka yi, yau ɗaya ta iya dakewa ta kalli cikin kwayar idanunsa, anya ita ce ta iya wannan juriya na kallon cikin idanunsa kuwa? Anya babu sa hannun Malika a ciki kuwa? Shi ma ya ɗan yi mamakin yanda ta zuba mashi idanu tana kallon shi, babu ko kyaftawa. "Noorish meyasameka?". Ta yi maganar tana kai hannunta a saman kumatunsa. Riko hannun nata ya yi tare da manna shi da jikin kumatunsa ba tare da ya saki ba, ya haɗe hannayen nasu waje guda a wajen, shiru bai yi mata magana ba, ita kuma sai kallon mamaki take yi mashi, taga ya yi wani irin rama ne, ita dai tasan kafin ta yi barci, ba haka ta barshi ba, ga idanunsa sun kara girma, alamar ya rame kenan. Baki ɗauke da sallama Aseef ya shigo cikin ɗakin. Juyawa ta yi tana kallonsa, sai kuma ta yunkura zata bar jikin Lion ɗin, sai dai bai sake ta ba, yana rike da ita, yana ta kallon face nata, shi kaɗai yasan me yake ji a duk lokacin da yake kallonta. Sam Aseef bai bi ta kansu ba, saman bed ya haye abinsa, ya kwanta tare da ciro wayarsa ya fara aikin latsawa, sai dai fa ya sha ruwan mamakin na ganinsu a manne da juna, kawai baya son ya yi magana ne, dan kada ya katse masu jin daɗinsu. Mark ne ya sake shigowa cikin ɗakin, kallo ɗaya ya yi masu ya kawar da kansa gefe, sannan ya wuce dan ya yi aikin da ya kawosa. "Meesha zaki raka ni ƙasar China?". Ya faɗa a sanyaye, tamkar bai san da Mark da kuma Aseef a cikin ɗakin ba. Jinjina mashi kai ta yi tana faɗin "E zan raka ka". Shiru ya yi yana tunanin a ina zai sami Cherish? Dan ba shakka duk yadda aka yi, tana da sa hannu a duk abubuwan da suke faru, saboda very close friend ɗin gwaggo ce, ya za'ayi daga haihuwar gwaggon shikenan ace Cherish ta ɓace? Ko dai dama ita ma ba mutun ba ce? Wannan abin da akwai ruɗani, dole ya nemo jigon haɗa wannan rikicin dukka. Sallamar Areef ce ta dawo da shi daga duniyar tunanin da ya afka, tun da Areef ɗin ya shigo, ya tsare shi da idanu har ya kariso cikin ɗakin, a saman bedside drawer ya zauna yana faɗin "Kai Aseef momma tana nemanka kana nan ko?". Turo baki ya yi yana faɗin "Ni ba zan je ba, kuma fushi nake yi da su, saboda sun ce wai ba zan yi punishing na Heartbeat ba, a kan me zata fita bata tambaye ni ba? Ni gaskiya ba zan kyaleta ba!". Sake Rimshar Lion ɗin ya yi yana mai dawo da kallonsa a kan Areef dake kare mashi kallo shi ma. "Me kake zuwa yi a wajen Josephine time da kake zuwa wajenta?". Shi ne tambayar da Lion ɗin ya wurga mashi. Miƙewa daga jikinsa Rimshar ta yi, sannan ta nufi kofar fita. Hannunta Areef ɗin ya riko yana tsokanarta "Sister yau kin mance da ni ko? Wato ma fita zaki yi kamar baki ganni ba ko?". Katse shi Lion ɗin ya yi da cewa "Saketa ta wuce, sannan ka juyo ka bani amsa ta". Kasa sakin nata Areef ɗin ya yi, dan shi ya ji ne ma kamar bai san wacece Josephine ɗin ba, baya son a kawo mashi maganarta, dan haka sai ya ce "Wai kai Lion ka bari mu gaisa da ita mana". Sosai Aseef ya yi mamakin abin da Areef ɗin ya yi, shi dai a iya saninsa ya san cewa Areef ɗin yana yawan tsawatar mashi a kan kada ya kuskura ya rinƙa rungumar Rimsha, or ya kamata hannunta a gaban Lion, idan ba haka ba, to za su yi babu daɗi da Lion ɗin, dan wannan uban kishin nasa, to ya aka yi yau shi kuma Areef ɗin da kansa ya rike mata hannu, kuma har Lion ɗin ya ce ya saketa, amma yaki, anya kuwa babu wata alamar tambaya a nan?. Shi kuwa Lion ɗin sam bai ɗauki zafi ba, saboda ya lura, yanzu koma ta halin ƙaƙa, so ake a kai shi ƙasa, so ake a rinƙa fusata shi, yana ɗaukar zafi, har ta kai ta kawo zuciyar ta kasa ɗauka, ta buga ya mutu kowa ya huta, tun da ya fahimci haka kuwa, to ba shakka zai yi taka tsantsan wajen ganin ya danni zuciyarsa ba zai ɗauki zafi ba!! Wannan shi ne yaki sunkuru, Lion dai yana faɗa da aljani, shi baya ganinsu, amma su kuma suna ganin duk wani motsinsa. Hannun Rimshar ya riko tare da jawota ta dawo jikinsa, cikin sanyin murya ya ce da Areef ɗin "Now amsa me". Ita dai Rimsha yau tana ganin abin mamaki, ta lura yau gabaɗaya TRIPLETS ɗin a tsai tsaye suke magana da junansu, kamar ba lafiya ba, magana suke yi kai tsaye kawai. "Saif ni ba wani abin da nake zuwa yi gidanta face gaisuwa, shi kawai nake zuwa yi". Aseef ne ya amsa da cewa "Ba wani gaisuwa, akwai dai abin da yake kaika, Allah gara ma ka rabu da matar nan, duk da cewa ta taimakawa Momma a baya". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa zaune yana wani yamutse fuska. "Anywhere zamu koma Washington gobe idan Allah ya kai mu, kuma gabaɗayanmu zamu tafi, saboda mun gama abin da ya kawo mu Naija, so idan mun bar Naija, mun barta kenan har abada!". Cewar Lion. Da sauri Rimsha ta ɗago kai tana kallonsa, da mamaki fal a face nata ta ce "Noorish to ita kuma gwaggo fa?". Shiru ya yi bai amsa mata ba. Areef ne ya amsa mata da cewa "Da Momma da ke da my baby, Heartbeat, dukka zamu tafi da ku mana, ai ku kun sallami Naija kenan". Zaro dara daran idanuwan nan nata ta yi, a tsorace ta ce "To daddyna da mummyna fa?". Aseef ne ya amsa mata da "A nan zaki barsu mana". Sam bata san time ɗin da ta furta, "Na shiga uku na! Wlh ni ba zan je ko'ina ba, sai dai ku tafi ku barni". Bata san time ɗin da ta furta hakan ba, sai da ta ga irin kallon da Lion ya wurga mata ne, nan ne ta fara tunanin wai shin me ta faɗa nema?. Gwaggo ne ta katsesu ta hanyar shigowa cikin ɗakin bakinta ɗauke da sallama. Ita ma tun da ta shigo Lion ya tsareta da idanu yana kare mata kallo, wani irin tausayinta ma yake ji a yanzu, an cuceta ba kaɗan ba. Da sauri Rimsha ta bar jikinsa, ta nufi gwaggon tana dariya. Rungume juna suka yi, a tare suka kariso cikin ɗakin. A gefen gado kusa da Lion ta zauna, ita kuma Rimsha ta zauna a gefenta tare da kwanto da kanta a saman kafaɗunta. "Saif kuzo muje palo, akwai maganganu da zamu tattauna da su Abban Imran and Brr". Cewar gwaggon kenan. Jinjina mata kai ya yi yana faɗin "Ki shirya gobe zamu koma ƙasarmu". Har tana haɗe word wajen cewa "Wace ƙasa kuma?!". Shiru ya yi bai bata amsa ba. Areef ne ya amsa mata da kasar da ake nufi, wato Usa. "A'a ni zan zauna a cikin ƴan uwana, ku dai ku koma, duk time ɗin da kuka sami lokaci, sai ku kawo mani ziyara". Miƙewa Lion ɗin ya yi ba tare da ya sake yin magana ba, ya nufi waje abinsa, dan ya san babu abin da zai hana su tafi da ita, ta gama zantukanta dukka, Nigeria kam sai ta barta..........Babbar magana. Miƙewa suka yi dukkansu suka rufa mashi baya. A palo suka isko su Abba gabaɗaya, sai hira suke yi, amma ga dukkan alamu, suna cikin matsananciyar damuwa. Saman sofa Lion ya zauna yana kallon baban Muneer dake a tsakiyar palon, Areef ya ɗaure shi da igiya kamar ba lafiya ba, ga bakinsa a kumbure suntum. Da kallo ɗaya ya yi wa baban Muneer ɗin ya fahimci koma me wannan dai ba mai laifi bane, amma sai bai tambayi meyayi suka ɗaure shi haka ba, ya zuba idanu kawai yana kallonsu, dan shi ciwo ma kansa take masa. Tun ɗazun Akila sai jin sautin Muryar Ablah kanwar Haroon take yi ana kiranta, tun ana kiranta daga nesa har ta ji an matso kusa, sai ta ji kamar a harabar gidan ma ake kiranta. Mikewa ta yi tare da gaya masu tana zuwa, tana fita daga palon shikenan ɓat ta ɓace tamkar wata aljanna, an ɗauketa. To fah. Su kuma jama'ar cikin palon, Brr Naurat ce ta yi gyaran murya tare da fara yin magana cikin dattaku da nutsuwa. Nasiha ce mai ratsa jiki ta yi wa Ummin Dr Nawid, sannan ta ce mata ko sun ɓuyo mata yanzu, gaba dole zata sani, to gara su gaya mata kawai, ta yi hakuri Allah ya yi wa Dr Nawid rasuwa. Yadda suka yi tunanin Ummin zata ɗauki abin, sai ya zamana ba haka ta ɗauka ba, sai ma wani irin murmushi wadda da ka ganta, kasan dole aka ƙaƙalota, shi ta saki kafin ta ce "Dama ni bani na bawa kai Nawid ba, Allah ne ya bani shi, kuma duk yanda nake son shi, na san Allah ya fini son shi, ni ba zan taɓa butulcewa Ubangijina wajen yin kuka ko makamancin hakan dan ya karɓi rayuwar Nawid ba, na yi imani ya fi kowa sanin zuciyata, kuma a hakan ya ɗauki ran Nawid, ina farinciki da hakan, kuma ina kara godiya ga Allah, duk wanda bashi da yaro, ina rokan mashi Allah da ya bashi masu albarka, ni kuma ina rokan Allah daya kara mani hakuri, ina farinciki cewa ɗana ya rasu a ranar jumma'a, yanzu kawai ku kai ni naga gawarsa, zan yi mashi addu'a". Baiwar Allah, kowa yasan maganar nan ma da take yi, da kyar take fita, karfin imani ne kawai, da kuma yarda da ƙaddara, ta yarda da Allah shi ne mai yi, tana tawassuli da sunayensa tsarkaka, Allahu Akbar, a gaskiya samun uwa irinta a wannan zamani, zai yi matuƙar wahala, Imran da yake iya matsayin aboki a wajen Dr Nawid ma, sai da ya shiga tsakanin tashin hankali na wuce misali, bare kuma uwar da ta haifesa, kuma shi ne kawai ɗanta, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allah ya kara mata hakuri, a gaskiya ta nuna jarumta da karfin imani. Sosai suka tausaya mata, kowa sai addu'a yake yi mata, ita kuma Aafia, sai da suka samu aka yi mata alluran barci, sannan ne suka sami zaman lafiya, in ba haka ba, sai buge buge take yi masu. Brr Naurat ɗin ce ta sake shigo da maganar case ɗin daddyn Jelly bayan ta sanar da Ummi ai an rigada an kai Dr Nawid makwancinsa, sai dai su je makabartan Ummin ta ziyarce shi a can kawai. Tambayar baban Muneer Brr Naurat ta yi, a kan shi ya ɗauki Ayla ko ba shi ba? Idan shi ne, ya dubi girman Allah ya dawo da ita, dan tana da karamin ciki wlh. Girgiza masu kai ya rinƙa yi a kan shi wlh ba shi bane, amma bakinsa bata iya yin magana, dan ya kumbura sosai. Rimsha ce ta katse su da cewa "Nashiga uku, Ayla ta sake ɓata?! Allah dai yasa ba Daular Mutuwa suka mayar da ita ba, shikenan wlh kasheta za su yi, dama Duna ya gaya mana in dai muka kuskura muka bari muka dawo wannan gida, to wlh babu mai iya fitar da mu, wayyo mummyna!!". Ta kai karshen maganar tare da mikewa da sauri ta faɗa jikin daddynta tana sakin wani irin kuka mai tsuna zuciyar mai sauraro. Tabbas an shafewa Rimsha tunanin Daular Mutuwa a cikin ƙwaƙwalwarta, yanzu ba ita ce ta yi maganar ba, Malika ce ta yi maganar, dan ita ta san Ayla tana can, bata da wata hanya da zata bi ta gaya masu Ayla tana can, dole sai ta hanyar shiga jikin Rimshar, saboda ita ce kaɗai ta taɓa zuwa Daular Mutuwar bayan Aylar, kuma tana son su san cewa head of the familynsu gabaɗaya wato Dr Salman yana can, shi ne yasa ta bi masu ta wannan hanyar ta shiga jikin Rimshar kawai. Kowa na cikin palon mamakin jin sunan Daular Mutuwa yake yi, nan take Imran da Areef suka tuna da labarin da ta taɓa basu a baya, tabbas sun tuna da zancen, dan haka sai suka fara bawa jama'ar palon labarin irin ukubar da su Rimshar suka sha a wajen, shi ma daddyn Jellyn, sai a lokacin ya tuna da cewa tabbas Ayla ta taɓa gaya mashi zancen Daular Mutuwar nan, sosai abin ya dawo masu cikin kwakwalensu. Ganin hakan yasa Malikar ta fita daga jikin Rimshar, tun da sun tuna komai, sai ta kyalesu ta koma gefe kawai tana kallonsu. Jin sunan Daular Mutuwa yasa Hjy Umaiya ta yi wani irin firgita sosai, a tsananin razane ta fara tambayar ina Akila, Akil, da kuma Imran?. Da mamaki suke tambayarta lafiya, bata iya bawa kowa amsa ba, ita dai kawai tambaya take yi ina yaranta. Imran ɗin ne ya ce "Ammie gamu nan ai, lafiya meyake faruwa?". Banda girgiza kai babu wani abin da take yi. "Kai ina Akila? Ya ban ganta a nan ba?". Cewar Akil. Nan fa suka fara waige waige. Shi dai Lion binsu da idanu kawai yake yi, ya rasa meyasa gwaggo ta ce sai dai yazo anyi magana da shi, suna ta surutu suna kara mashi ciwon kai a banza. Wasa wasa suka fara neman Akila, shiru babu ita babu labarinta, nan fa Hjy Umaiya ta birkice masu, ta yi masu karamar hauka, faɗi take yi wlh Queen ta dawo mata da ƴarta, idan ba haka ba, to a wannan karon za su yi kare jini biri jini!!. Zuba mata idanu kawai suka yi suna kallon ikon Allah. Brr Naurat ce ta tambayi Abban Imran wai matar nan tasa lafiyarta kuwa?. Shiru shi ma ya yi ya kasa yin magana, dan kuwa bai san me zai ce ba. Gwaggo ce ta miƙe ta riko Ammien tana tambayarta lafiya? Wacece kuma Queen?. Cikin kuka ta basu amsa da mahaifiyarta ce, kuma ita ce shugabar wannan Daular Mutuwar da Rimsha ta ambata a yanzu. Daga Imran har Areef sai da suka zaro idanu tamkar idanun nasu zai faɗi kasa, irin wannan bala'i na cikin Daular Mutuwar dukka Ammie ta ce uwarta ce shugabansu? Lallai kuwa, akwai cakwakiya. Ita kuwa Rimsha miƙewa zaune ta yi tana karewa Ammien kallo, sai a yanzu komai yake dawo mata sabo, sai a yanzu take kallon tsananin kama na Ammien da kuma Duna, hakan na nufi duna ɗa ne ga Queen? Ko kuma ɗan uwanta ne? Dan sun yi kama sosai......WATA SABUWAR CAKWAKIYA KENAN, ME KUMA YA HAƊA AMMIEN DA DAULAR MUTUWA?. "Abba menene ya haɗa Ammienmu da Daular Mutuwa?". Cewar Imran, da yake shi yasan labarin Daular a wajen Rimsha. Zubawa Abban idanu kowa ya yi yana jiran amsa daga gare shi. "Imran nima ban san me zan ce maku ba, amma ita Ammien taku ce kawai zata iya yi maku bayani". Juyo da kallonsu a kanta suka yi, yau suna ganin tashin hankali, labarin yau kuma ya juya ta kansu Imran.......... TRIPLETS GIDAN SURPRISE, YAU KUMA LABARIN MU YA JUYA TA KAN SU IMRAN, SHIN AKWAI WANDA YA TAƁA TUNANIN QUEEN MAHAIFIYAR AMMIENSU IMRAN CE? TO YAU MA DAI SABUWAR BABIN CAZA KWAKWALWA MUKA BUƊE😂 KU DAI KU KASANCE DA PRINCESS TEEMA KAWAI, NI CE KAƊAI ZAN WARWARE MAKU WANNAN CAKWAKIYA!. Cikin kuka da tashin hankali ta fara magana kamar haka. "Hakika kamar yanda na gaya maku cewa Queen mahaifiya ta ce, to ba shakka hakan ce, mun kasance kabilar igbo mazauna garin Enugu, kuma mun kasance kiristoci ne, karatu ya kai ni Kaduna state, a nan na haɗu da Abbanku, dama already tun kafin na tafi karatu, na san da gidan Daular Mutuwa, kakana ne ya kirkireta, kowa ya san kabilarmu da tsafi kamar baza'a mutu ba, to muma muna ɗaya daga ciki, Mahaifiyarmu, wato Queen, ita kaɗai kakana ya haifa, Shiyasa da ya mutu, sai ta gaji karagar mulkinsa a Daular Mutuwa, ni da kai'na ina zuwa har cikin Daular, kuma a lokacin babu wani abu na tsafi wanda ban iya ba, duk wata tsubbace tsubbace na iya nima, da ni da kanwata, sai kuma wani ɗan uwan mamana, mune na kusa da ita a Daular, a takaice dai na san komai, Allah da ikonsa, da Allah ya so ni da rahama, sai ya jarrabeni da son karatu, ita kuma kanwata, tana tare da Queen a cikin Daular, a gabana za'a yi tsafi da mace, a gabana ake komai na abubuwan subbace subbace da siddabaru, ko a jikina, dan lokacin zuciyar kafurci ne ke gareni, manyan mutane ne suke zuwa cikin Daular dan a biya masu bukatunsu, da akwai manyan manyan gidan matsafa da suka dogara da Daular, akwai abubuwa da dama wanda ni a yanzu na mance da shi ma gabaɗaya, kuɗi kuwa, habawa ai idan munaso ma mukam, zamu iya yin gadon kuɗi ku kwanta, muna da arziki na wuce misali, mu da mumuke bawa wasu ma, manyan mutane daga kasashen dake makwabtaka damu, suna zuwa neman arziki da abin duniya a wajenmu, wasu su kawo ƴaƴan ƴan uwansu mu yi masu kuɗi da su, wasu kuma ƴaƴan cikinsu, abubuwa dai da dama, mun shahara a duniyar tsafi. To a takaice dai sai Allah ya ƙaddara na tafi Kaduna state karatu, a can na haɗu da Abban Imran, wasa wasa muka fara soyayya, ina son shi sosai kasancewarsa Bature, kun san turawa da mugu mugun shiga rai ga farinjini, ga kyau na wuce misali. Daga karshe dai na musulta, saboda da shi, da ya kasance Allah yana sona da rahma, sai Allah ya saka mani kaunar addinin sosai, na yi karatun Alkur'ani mai girma sosai da sosai, ina jin alokacin da akwai abin da ya ɗaukewa Queen hankali, shi ne yasa bata lura da abin da nake yi ba, idan ba haka ba, wlh duk wani motsinmu tana gani a cikin madubin tsafinta, amma ga mamakina har na musulta, na kuma yi karatun addini, kuma bata gane ba. To a takaice dai, lokaci da muka yi hutu, sai Abban ya ce zai bini muje gidanmu ya gaida iyayena, daga nan ayi maganar aurenmu, da yake ni wlh na mance da ya gidanmu ma suke, sai na yarda mashi kawai, na ce muje, ba tare da sanin iyayensa ba, muka kama hanyar Enugu, a ranar naga bala'in da ban taɓa gani ba, dan da muka je gida, Queen ta ce wlh dani da Abban duk kashemu zata yi, to dama na gaya maku already nima a lokacin na iya tsafe tsafen nasu dukka, hakan tasa na yi fito na fito da mahaifiyata, dan na kare Abba kada su kashe shi, duk da na musulta, hakan bai hana ni na haɗa kayan tsafina dan muyi faɗa da ita ba, domin a lokacin a cewata, tsafin ne kawai zai kwacemu daga hannunta, mun sha azaba ta yanda sai da muka koma yin karatun Alkur'ani mai girma, sannan muka iya kuɓuta daga hannunta, a nan ne na kara yarda cewa tsafin ma dukka shirmen banza ne, tun da ga shi ya kasa kuɓutar da mu daga hannunta, karatun Alkur'ani mai girma ne ya kuɓutar da mu, tun daga lokacin sai na kara nesanta kaina da tsaface tsafacen, ita kuma Queen ta sha alwashin da ni da duk waɗan da suka tallafa mani, sai taga bayanmu, ni kuwa na ce mata idan ta fasa bata cika Queen of Daular Mutuwa ba, abin ya yi tsananin kona mata rai, dama kun san yanda kabilar igbo suke da tsananin zafi idan aka ce yau ga nasu ya musulunta, to haka nima dangina suka ɗauki wannan zafin, akwai wani ɗan uwanmu da dama shi zan aura, to da ya ji abin da ya faru, sai ya ce shi ma ba zai kyale Abba da gabaɗaya familynsa ba. In takaice maku dai haka muka baro garin Enugu babu daɗi, da kyar ma muka iya kaiwa airport muka dawo Kaduna, babban abin da ya kara sakawa naji ina son addini musulunci sosai, shi ne yanda iyayen Abba suka karɓeni, basu ji kyamata ba, dan na kasance Kristen kuma ƴa ga magicians, sam ba su guje ni ba, mahaifinsa Dr Salman yana da kirki sosai, ita kuma matarsa Amarya tana da bakar zuciya, sai dai ni ba zata iya cutar da ni ba, saboda already a dafe nake, jinin Queen ce ni, ta dalilina ma asirin da ta yi wa Dr Salman ɗin ya karye, dan wannan a jininmu yake, mune gidan asiri, mune asiri da kanta, duk girman asiri in dai ina wajen, to ba zai yi tasiri ba, ni ban san me Queen ta yi mana a jininmu tun muna yara ba, to haka gabaɗaya su Imran suka taso, ba'a iya cutar da su, saboda jina ne su, in takaice maku ita kanta amaryar sai da ta zo ta kaunace ni fiye da ƴarta Batula, ta soni tamkar ta yi mani numfashi, a gidansu Abba na cigaba da rayuwata har muka yi aure, ƴan uwansa dukka suna kaunata sosai, barema Dr Salman bawan Allah, yana sona sosai, a lokacin ya ce mani yana son matarsa Naurat, amma bai isa ya je kasar Russia ya ce zai ɗauketa ba, idan ya je, ƴan uwanta za su kashe shi, dole ya hakura da ita, sosai a lokacin suka nemi ɗan uwansu Nawazuddeen wanda ni banma san shi ba, na dai ji labarin ya bar gida, amma basu gan shi ba, bayan aurenmu da Abban Imran, daga nan abubuwa suka fara faruwa, haɗarin da Dr Salman ya yi shi da amarya, ina da tabbacin da sa hannun Queen, a lokacin na cewa Abban Imran zan sake komawa ruwa, wato zan haɗa kayan tsafina, dan na yi maganin Queen, saboda idan ba fito na fito muka yi ba, in dai ban rushe Daular Mutuwa ba, to ba zata barni ba, dan ba zata iya yafe ni ba, sosai Abba ya yi mani nasiha, ya kuma yi mani faɗa a kan ko bayan ransa bai yarda na sake komawa tsafi ba, kamar yanda na barta, to ya zamana na barta kenan har abada, sosai naji nasiharsa, dan haka sai na hakura, muka cigaba da rayuwa muna karatunmu cikin farinciki, amma mutuwar Dr Salman ya girgizani, ina tuna bawan Allah nan, mutun mai farar zuciya, sai dai fa har gobe ina jin kamar bai mutu ba, ina ji kamar wata sharrin Queen ta haɗa mana, amma dai Allah masani. (Masu karatu i hope yanzu kun fahimci dalilin kasancewar Dr Salman a Daular mutuwa?) Tun daga wannan lokacin muka cigaba da yin rayuwarmu cikin farinciki, na rike kannan Abba kamar kannena, na mance da tawa kanwar da mahaifiyata, na sami sabuwar ahali, a haka muka kasance har Abbi wato Deen shi ma ya yi aure, ya auro wata ƴar Katsina da suka haɗu ita ma a school, ita ce mahaifiyarsu Irfan, mafadaciya ce sosai, da ta nemi ta kawo mani wargi, na taka mata burki, akwai wata rana da na yi mata dukan mutuwa har sai da aka kai ta asibiti, daga lokacin aka rabamana gida da ita, Abbin ya ɗauketa zuwa ɗaya daga cikin gidajen Dr Salman, in takaice maku labari ni ban sake waiwayar iyayena ba har rana mai kanata yau, na rufe babinsu, kuma nasan wlh Queen ba zata rabu da ni ba, ba shakka ita ce nan ta ɗauki Akila, kuma ita ce ta ɗauki matar Maik, sai dai fa sun canzawa Daular Mutuwa tasu waje, bata a in da na santa da, tun kafin na bar gida dama na ji suna shirye shiryen kara mata wasu matakan tsaro, sannan kuma su canza mata mazauni, a yanzu ita Rimsha ita kaɗai ce zata iya gaya maku in da Daular Mutuwar take, saboda ita ce ta shiga cikin ta kwanannan, amma kuma a gaskiya duk wanda ya shiga Daular Mutuwa ya fito da rai, to dole a jinjina mashi!! Dan duk yanda kuke tunanin Queen ta wuce hakan wlh, sam bata san menene imani or tausayi ba!!. Masu karatu yanzu kun fahimci dalilin da ya sanya waɗan nan dodannin suke zane su Abba? Kun fahimci menene ainahin tushen matsalar? Bari na kara maku wata haske, a duk shekara dama already kun san da cewa dodannin suna zuwa gidan Abba, abin da yasa suke zuwa kuma, saboda tun bayan haihuwar Akila, lokacin sauka daga kan karagar mulkn Queen ya yi, kuma dole sai Ammien su Imran ɗin ce zata karɓi mulkin, dan ita ce babbar ƴarta, ita kuma kunga ta musulta, tama ki yarda ta sake haɗa hanya da su, wannan karya doka da ta yi ne yasa mukarraban Queen ɗin suke zuwa su zaneta, Queen ɗin ma tana zuwa gidan, amma ana ɗaukar lokaci sosai kafin ta zo, har ga Allah tana kaunar Ammien su Imran, shi ne ma yasa bata kashe ɗin ba, ta ke bata wahala dai kawai, kuma tun da Queen ɗin take zuwa kawowa Ammien ziyara, bata taɓa haɗuwa da su Akila ba, saboda rikonsu da addini, sai dai mukarraban tane suka taɓa haɗuwa da Imran, shi ma an samu akasi ya shigo ba tsarki a jikinsa ne, ya gama shan lemon tsaminsa bai yi wankar tsarki ba ne ya shigo cikin palon, kun tuna lokacin da suka taɓa zane shi ko? To lokacin ne suka san Imran ɗin, ai kunga shi Akil yana shigowa suka gudu, saboda yana da tsraki, kuma a lokacin ƙira'ar karatun Alqur'ani mai girma yake sauraro. Abin da ya faru a yanzu a wannan shekara Queen ɗin ta zo kawowa Ammien ziyara da kanta ne, a nan ne kuma taga Ayla, dama kunsan already tana neman Ayla, Rimsha, da kuma Kausar, shi ne yasa ta ɗauki Aylar, da ace Rimsha tana wajen, da ba makawa har da ita za su ɗauka, ita kuma Akila abin da ya sanya Queen ɗin ta iya ganinta har ta ɗauketa duk da tana karatun Alqur'ani mai girma, anyi katari ne da Queen ɗin ta kawo ziyarar dai'dai lokacin da Akilar take period, wato bata da tsarki, shi ne yasa ta samu damar ɗaukarta, ita Kausar dama already sun ɗauketa da jimawa, dan ba wani riko da addini ke gareta ba, yanzu Rimsha, Imran, Akil, su Queen take hari, ita Rimsha kun sani saboda karya mata record na gidanta da ta yi ne yasa suke son kamata, su Imran kuma, saboda ƴaƴan Ammie ne, idan baku manta ba dama Queen ɗin ta ce ba zata taɓa barin Ammie da duk wanda ya goya mata baya or yake kaunarta su zauna lafiya ba, shi ne yanzu dataga su Imran, sai take son ɗaukesu gabaɗaya, kuma dukkansu tsafi take da niyar yi da su............. (Jama'a za'ayi tsafi da Shaikh Akil fa😂mahaddacin Alqur'ani mai girma, mu gayawa Queen ba zata iya bane? Ko kuma mu bari duniya ta gaya mata? Dan in har ta ɗauki waɗan nan malamai guda biyun, wato Akil da Imran, to tana tsaka mai wuya, dan fa Alqur'ani mai girma ba wasa ba!!) Allah sarki Ammie duk zaneta da dodannin nan suke yi, ba zata iya tuna wannan ba, saboda goge mata shi ake yi a cikin ƙwaƙwalwata, baiwar Allah, ita ma ta sha kuncin rayuwa ba karya, kuma hakika Allah yana sonta da rahma, har ta fito daga kabilar igbo, kuma matsafiya, sannan ta musulta, ta kuma rike addinin da kyau, kai gaskiya ta zama zakarar gwajin dafi! Ba abin da zamu ce mata face Allah ya daɗa kareta daga sharrin Queen! Amma dai Ammie ta yi kokari na wuce misali!". Salati su gwaggo suka sanya, abin gabaɗaya ya sanya sun rasama ina za su kama, sun rasa abin faɗe. Ita kuwa Ammien, kuka take yi sosai tana faɗin wlh a dawo mata da Akilarta, ta san ba makawa kasheta Queen zata yi, dan ba imani ne da ita ba, in kuma ta kashe Akila, to wlh ba zata rabu da su ba! Shi ma Aseef kuka ya saka masu a kan wlh shi dai a nuna mashi ina ne wannan Daular Mutuwa ya je ya ɗauko matarsa, dan wlh shi ba zai yarda ba, in suka taɓa ko da mayafinta ne, duk sai ya kashe su........... E LALLAI ASEEF BAI SAN SUWAYE NE A CIKIN DAULAR MUTUWA BA, JAMA'A MU GAYA MASHI NE, KO DAI MU BARSHI YA JE ƊAUKO AKILA?😂 HAR DA WANI CEWA ZAI KASHESU HMMM QUEEN TA WUCE TUNANIN NAI TUNANI. ita kuwa Rimsha, ganin Ammien Imran tana zaune kusa da Abba dake kusa da daddyn tane, yasa ta bar jikin daddyn nata da gudu, a dubu ta je ta ƙanƙame gwaggo tana ihu a kan tashiga ukunta, su taimaketa, tun da an ɗauki Ayla, yanzu ita kenan za'a ɗauka next, wlh bata son koma Daular Mutuwa, kashe mutane ake yi a can! Umaisha ma dai guduwa ta yi daga kusa da Ammien, saboda sun tsorata da jin labarin Daular Mutuwa. Yau Ammie ta zama dodo a wajensu, har surukanta suna gudunta. Rimsha baiwar Allah, tamkar zautatciya ta zama masu a cikin palon, sai surutai take zubawa marasa kan gado. Riketa sosai gwaggo ta yi tana ambatar sunanta, ina ai tun da ta ji Queen na kawo wa Ammie ziyara, shikenan kuma ta birkice, zunduma ihu take yi tsakaninta da Allah, ita kaɗai tasan bala'in Daular Mutuwa, su dan basu sani bane, bata fatan ta sake komawa can baiwar Allah......GA ABIN DARIYA, GA ABIN TAUSAYI. Karin wani haske, zaman Rimsha a gidansu Imran, Malika ce ta taimaka mata har tasa Queen bata ganta ba, Malika ce tasa Ammien ta ce bata son Rimshar, ta yi hakan ne kuma dan bata son Rimshar ta zauna da Ammien inuwa ɗaya har Queen ta kawo ziyara ta ganta su ɗauketa, to kun ji yanda aka yi da kuma dalilin da yasa Ammien ta ce bata son Rimshar, Malika ce sila, na san kowa yana son sanin ainahin wacece Malika, to muje dai zuwa, lokacin sani ya kusa.......... LALLAI AKWAI CAKWAKIYA, AYLA TANA TSAKA MAI WUYA, NA FARKO SUN KARYA RECORD NA QUEEN, NA BIYU KUMA TA ZO TA SHIGA CIKIN FAMILYN DR SALMAN A MATSAYIN SURUKA, FAMILYN DA QUEEN TA FI TSANA FIYE DA KOWA A DUNIYA, ITA MA RIMSHA TANA TSAKA MAI WUYA, DA CAN BAYA QUEEN BATA SAN CEWA RIMSHA ƊAYA DAGA CIKIN FAMILYN DR SALMAN BANE, KAWAI TANA NEMANTA NE DAN RECORD NATA DA SUKA KARYA, YANZU KUMA, TA GANE TANA ƊAYA DAGA CIKIN FAMILYN DR SALMAN, KUNGA KUWA BA ZATA KYALETA BA, LALLAI AKWAI CAKWAKIYA, AKILA KAM BA'A MAGANA, GATA ƳAR AMMIE, GATA JIKAR DR SALMAN, TAB AKWAI CAKWAKIYA, ITA KUMA RIMSHA, GA SU JOSEPHINE A GEFE SUNA HARINTA, WASAN YANZU ZAI ƊAUKI ZAFI JAU, HAR YANZU AKWAI SAURAN RINA A GABA BA KAƊAN BA, DAN HAR YANZU BASU SAN CEWA DR SALMAN YANA RAYE BA, GA KAUSAR ƳAR YARABAWA MA QUEEN TA DAUKETA, TA YI TSAFI DA SUNE KO SUNA RAYE? ALLAH MASANI, SAI KUMA ALKALAMIN PRINCESS TEEMA, WAI SHIN YANZU A INA MA DAULAR MUTUWA TAKE? RIMSHA ZATA SAN HANYA NE? KADA KU MANTA DAJI SUKA BIYO, SU KANSU BASU SAN WANI HANYA BANE, TSAWON KWANAKI SUKA SHAFE SUNA TAFIYA, ZATA IYA SANIN TA INA SUKA FITO NE MA? WAYE ZAI JE ƊAUKO AYLA DA AKILA? NA BARKU HAKA NAN, KADA NA KARA CAZA MUKU KAI, MA'ASSALAMA!!. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 20/4/2024 E10 Ihu sosai take zunduma, sai ƙoƙarin dannanta gwaggo take yi, amma ina, taki tsayawa. Da dai Lion ya lura ita fa Rimsha sam bata a cikin hayyacinta, ta ruɗe masu ne sosai, ga shi sai tumurmusa masu jikin mommansu take yi, kamar wadda ake hurawa wani abin a kunne, haka take tsalle tana ihu, sai ya kai hannu ya rikota da hannu ɗaya, a lokacin kuma su Abba duk sun yunkura zasu karɓeta daga hannun gwaggon, saboda gwaggon ba zata iya riketa ba. Ganin Lion ya riketa ne yasa kowa ya fita harkarsu, dan duk wanda ya kwana ya tashi a wannan gidan, to yasan waye Lion, so basu ma son wani abin ya haɗasu, basu yarda hanya ta haɗasu. Jawota jikinsa ya yi, ya haɗa hannayenta dukka biyu da take ta faman yarfarwa tana ihun nan, haɗesu ya yi ya rike da hannunsa ɗaya yana tofa mata addu'a, saboda ya samu ta nutsun mashi. Shiru palon ya yi na ƴan mintoci, ban da kukan Rimshar da yake tashi kasa kasa, babu wani motsi da zaka ji a palon, tamkar babu mutane, kowa ya zubawa Brr Naurat idanu, ita kaɗa suke jira ta yanke hukunci, daga nan sai a san abin yi. Shi kuwa Lion, sai da ya tabbatar ta dawo dai'dai, sannan ya dakata da tufa mata addu'a yana kallon face nata, idanunta a rufe ruf, da alama ma barci ya ɗan yi awon gaba da ita. A hankali ya ɗago da kallonsa izuwa kan Brr Naurat dake ta kallon shi ita ma. Kowa binsu da idanu yake yi sosai, sun ƙagu su ji menene abin da zata ce. Ita kuma shiru ta yi tana nazarin maganganun Ammien, ta ɗan ɗauki lokaci kafin ta fara magana cikin nutsuwa. "Tun farko kune ma muka yi kuskure, ko in ce shi Abba shi ne ya yi kuskure, tun da ka san ga daga in da ka ɗauko mace, ai da sai ka san irin babban matakin da ya kamata ka ɗauki, wani faɗan ai baka isa ka yi shi kai kaɗai ba, tun kafin ka shiga gidanka da kuka zauna, sai ka sanya ayi maka saukar Alqur'ani mai girma, ayi walima ayi maku adduo'i, ta yanda zaku ɓacewa ita Queen ɗin gabaɗaya, karfin addu'a zai taimaka maku Allah ya tsareku, sauran ƴan uwanka ma, sai ka gaya masu su ga halin da ake ciki, sai suma su shirya su tsananta addu'a, tun da a gaban idanunka Queen ɗin ta sha alwashin ba zata rabu da kai da familynka ba, sai baka yi hakan ba, ka ɗauka abin wasa ne, yanzu koma me ya faru da ƴan uwanka, to laifinka ne, dan su basu san ma daga ina take ba, suna rayuwarsu ne yanda suka saba, kuma shi karatun Alqur'ani sai wanda yake da kokari sosai ne yake iya yinsa kullum, saboda shaiɗan ba zai barsu ba, amma kaga idan sun san da wannan matsala, dole za su yi taka tsantsan sosai, dole zasu yi ƙoƙarin yin addu'a sosai, za su kula da askar, dan su kare kansu daga irin wannan musifu haka". Ta kai karshen maganar tana mai kara jinjina wannan al'amari, dan ita wlh sam bata taɓa tunanin ire iren waɗan nan matsafa akwaisu a gaske a zahiriya ba, kun san Turawa dama, su sam basu damu da irin waɗan nan shirme ba, to yau dai ga shi ta samu gagarumar matsafiya a cikin surukanta!. (Anya da Brr Naurat tana nan a lokacin zata yarda Abba ya auri Ammien kuwa?🤔 Shiyasa Allah ya kawar da ita a lokacin, ta koma kasar Russia, domin rabon su Imran da yake a tsakanin Abba da Ammien, kun san shi fa rabo har kisa yanayi, to Allah ya ƙaddara akwai auren ne, shi ne ya matsar da Brr Naurat, dan yasan ba zata taɓa yarda da auren ba!!) A hankali sautin zazzaƙar muryar Rimsha ya fara tashi, kasa kasa take magana ta lafe a jikin Noorish nata. "Noorish Allah ni bana son komawa Daular Mutuwa, please kada ka bari Queen ta ɗauke ni, Allah Duna ya ce mani cinyeni zata yi idan na sake komawa". Tana magana wasu siraran hawaye suna zubo mata a kuncinta. Shafa face nata ya yi tare da goge mata hawayen, a hankali ya motsa laɓɓansa, ba sai na sake faɗa ba, dama kun sani already shi idan yana magana, kasa kasa yake yinta, idan ba kana kusa da shi sosai ba, to ba zaka taɓa jin meyake faɗa ba, a yanzu ma haka ne, duk cikin palon ban da Areef dake zaune kusa da shi sosai, to babu wanda ya ji abin da ya ce mata, kasa kasa ya yi maganar. "Babu wanda ya isa ya mayar mani dake can, just calm down kin ji ko?" "Noorish Allah tsoro nake ji". Ta yi maganar tare da kankame shi sosai. Tabbas yaga tsananin tsoro kwance a cikin idanunta, hakan ya kara tabbatar mashi da cewa ba ƙaramar ɓarna suke aikatawa a cikin wannan Daular Mutuwar ba!,. "Meesha bai kamata ki ji tsoron wani abin ba idan kina a tare da ni, ba zan bari ayi maki komai ba". Ya yi maganar yana mai cigaba da goge mata hawayen da suke ta gangaro mata. "Is okey, a tsayar da kukan nan haka nan". Ya kai karshen maganar yana ɗago da idanuwansa izuwa kan Brr Naurat dake kallonsu. "Brr just close this case like that, ni ban ga abin dawo da abin da ya wuce ba, a have alot of things da nake son zuwa na yi, so momma I will going to leave". Cewar Lion ɗin. "No Saif, wannan ba shi ne maganar da na kiraka ka zo mu yi ba, tsaya ka ji maganar mana". Cewar gwaggon. Shiru ya yi bai sake magana ba. Rimsha ce ta sake ce mashi "Noorish am feeling hungry too much". "Okey you can go and eat". Ya bata amsa. Su Imran dai mamakin Lion ya hanasu yin magana, wai yau shi ne ya zauna yake hira da mace haka, macen ma ƴar yarinya kamar Rimsha, komai ta ce mashi zai bata amsa, mutumin da a baya sai ka yi magana goma sannan yake bada amsa ɗaya, ba ya taɓa baka amsa a kan kowace magana, wani lokaci ma amsar ma ba zaka samu ba, amma ita Rimsha kowani maganarta sai ya amsa, Allah mai iko!!. Zaro idanu ta yi tana faɗin "No ina tsoro sosai gaskiya, ba zan iya zuwa kitchen ba". Shiru ya ɗan yi kafin daga bisani kuma ya sake cewa "Jeki cikin ɗaki, a cikin trolleyna da muka je Abuja dake ɗin nan, ki duba zaki ga wani littafin adduo'i, ki ɗauko ki kawo mani bari na koya maki wata addu'a dan ki rage tsoro". Kasancewar a palon sama suke, sai ta ji tsoron ya ragun mata, dan daga palon suna iya hango cikin bedroom ɗin nasa, so tana jin motsin mutane, dan haka sai ta miƙe ta nufi cikin bedroom ɗin. Su kuma suka cigaba da tattaunawa, ana mai da yanda aka yi wasu abubuwa a baya. Da shigarta ɗakin bai fi da minti uku ba, ta zunduma wani irin uban ihu mai tsananin rikita ƙwaƙwalwa. Mazan dake a cikin palon suna yunkurin mikewa su nufi cikin bedroom ɗin, sai gata ta fito a guje. Tsayawa suka yi suna kallon ikon Allah, kowa ya yi tunanin wani abin ne ya kamata, ko Queen ce ta ɓullo a gabanta, amma sai suka ga akasin haka, gata ta fito lafiya lou hannunta na rike da wasu hotuna tana zunduma ihun kuma again. Bata zame ko'ina ba sai wajen daddynta, jikinsa ta faɗa tare da miƙa mashi hoton, tana kuka tana faɗin "Daddy wlh tallahi wannan ma ɗan uwan su Queen ɗin Daular Mutuwa ne, na gan shi a cikin Daular Mutuwar, sunansa baba, muna zama muyi hira da shi ni da su Ayla, Allah ban manta shi ba, wayyo nashiga uku, yanzu kenan har ɗakin yaya Saif akwai ƴan Daular Mutuwa a ciki, daddy Dan Allah mu koma gidanmu na Abuja kawai, ni dai wlh bana son Daular Mutuwar nan". Tun da ta fara surutan nan suka zuba mata idanu, baiwar Allah duk ta firgice yau. Shi kuwa daddy karɓar hoton ya yi dan ya kalli wanene. Ai kuwa yana gani ya yi wani irin zabura, a hanzarce ya sauketa daga jikinsa tare da miƙewa tsaye yana faɗin "Daddy kuma a Daular Mutuwa?!!". Da sauri shi ma Abba ya karɓi hoton yana kallo, zaro idanu shi ma ya yi ganin cewa hoton Dr Salman ne, to su a saninsu mutuwa Dr Salman ya yi, ya haka kuma, anya Rimsha shi ta gani kuwa? Wannan shi ne tambayoyin da suke yi wa kansu. Masu karatu idan baku manta ba, time da Lion ya je Abuja, akwai wasu hotuna na familyn daddyn Rimsha daya kwasa daga ɗakin mum, kun tunasu? To a cikin waɗan nan hotunan ne da akwai hoton Dr Salman, shi ne yanzu da ta je ɗaukar littafin addu'ar, sai taga hoton, ita kuma kunga yanzu tunanin Daular Mutuwa kaf ya dawo mata a cikin ƙwaƙwalwata, ta san Dr Salman a can, tana tsaka da kallon hotunan ne, sai taga hotonsa a ciki, kunga kuwa dole ta birkice ai, tun da ita dai a Daular Mutuwa ta san shi, yanzu kawai taga hotonsa a cikin trolleyn Noorish nata, ai dole ta yi hauka, dole ta yi tunanin ko dai ƴan Daular Mutuwa sun fara biyota har nan ne kuma, to shi ne abin da ya faru. Mamaki ya hana kowa magana, sun jima shiru kamar waɗan da ruwa ya cinyesu, sai al'ajabin wannan al'amari suke yi. Can Brr Naurat ta ce "Meesha kin tabbatar shi kika gani a can?". Da sauri Lion ya ɗago idanu yana kallon Brr, saboda ya ji sunan da ta kira Rimsha da shi, shi dai yasan sunansa ne, shi kaɗai yasa mata wannan suna. (Brr Naurat ya da haka kuma? Ina ruwanki da sunan masoya?🧐) Tamkar Brr tasan kallon me yake yi mata, sai ta ce "Ka yi mani kishi, na yi shiru bai yi magana ba, har da sake mata suna, to ba zai yiwu ba, nima dole ka sake mani suna, kuma nima da wannan suna zan kirata, dan ni ce uwar gida ai, duk ido zan saka maku". Kawar da kallonsa ya yi ba tare da ya yi magana ba, wannan tsohuwa akwai sa ido, ya faɗa a cikin zuciyarsa, a cikin jirgin ruwa fa ta ji yana faɗin Meesha, shi ne har ta rike sunan, Brr kenan!. Cikin kuka Rimshar ta ce "Brr wlh shi ne, shi ne baba na Daular Mutuwa, Allah ban manta shi ba, kullum yana zaune a ɗakinsa, ya tsufa, muna zuwa mu yi hira da shi". Ammie ce ta karɓi zancen da cewa "Ba shakka tun da Rimsha ta faɗi haka, to wlh haka ne, ni dama na ce wannan accident ɗin shirya shi Queen ta yi, ai kunga ko gawar Dr dama ba'a kawo mana ba, sai dai aka ce babbar motar da ta bi ta kansu ta yi raga raga da su over, sai dai kasusuwansu, to wlh ba shakka Dr Salman yana raye, kuma yana cikin Daular Mutuwar kamar yanda Rimshar ta faɗa!". Jin ance wannan baban kakanta ne yasa ta sake zunduma ihu tana faɗin "Wlh ba kakanmu bane, shifa yaron Queen ne, dan Allah ku dai'na cewa kakanmu ne, a Daular Mutuwa fa yake, wai daddy ka san Daular Mutuwa nan kuwa? Wlh ina gaya maka shi ma baban namar mutane yake ci, dan Allah ku dai'na cewa kakanmu ne, ni kam zan mutu yau". Ganin suna neman su juyawa Meeshansa kwakwalwa, suna neman su sanyata ta birkice gabaɗaya, sai ya miƙe tsaye tare da nufar in da take, hannu yasa ya saɓeta a kafaɗarsa, sai kuka take yi, ya wuce da ita izuwa bedroom nasa. Jama'ar palon ma babu wanda ya lura da su, sai jajanta wannan al'amari kawai suke yi a tsakaninsu. Yana shiga ya shinfiɗeta a saman bed nasa, sannan shi ma ya haye. Rikota ya yi tare da fara yi mata raɗa a kunne, kan kace me, sai gata ta koma sakin murmushi, ga guntun hawaye a gefe, ga murmushi kuma a gefe, jim kaɗan ka fara dariya har da kyakyatawa, tamkar ba ita ce yanzu take zunduma ihu a palo ba, kome Noorish ɗin nata yake ta gaya mata a kunnen?. Juyowa ta yi da kyau ta shige jikinsa tana faɗin "Amma Noorish ba'a jirgin ruwa zamu tafi ba ko?". Shiru ya yi yana kallon kyakkyawar face nata, duk hawaye ya bubbushe. "Bakison tafiya a jirgin ruwa ne?". Jinjina mashi kai ta yi tana faɗin "Ina tsoron mu nutse kasa ne". Shiru ya ɗan yi na ƴan mintoci kafin ya ce "Ba kina son shiga cikin ruwa ba? Idan mun nutse ai sai ki yi wanka ko?". Turo baki ta yi tana faɗin "A'a ba irin wannan ruwa ba". Shiru ya yi yana ta kallonta. "I like your lips". Ya faɗa a sanyaye. Ɗago idanunta da suke jajir saboda kuka ta yi, kai tsaye cikin idanunsa ta kai kallonta, ya tsareta da ido sosai. "Noorish nima lips naka suna yi mani kyau over". Gyara kwanciyarsa ya yi, a in da ya rage tsawonsa, ya zama face nasu tana dai'dai da juna. Zubawa juna idanu kawai suka yi, suna zuba kallon tsantsar so da kaunar juna. Romeo and Juliet kenan!. Sun ɗan ɗauki lokaci a haka kafin ita ta kawar da kallonta tare da shigewa cikin jikinsa tana dariya. Hannunsa ɗaya ya ɗaura a saman bayanta yana shafawa tare da ɗan ciza laɓɓansa na kasa kaɗan. A can palo kuwa, cigaba da maganar neman mafita ta yanda za'a ɗauko Dr Salman suka rinƙa yi. Sai can Areef ya ce masu dan Allah su bar mutane su huta haka nan, ai sun san cewa ko babu kowa nasu a cikin Daular Mutuwar nan, in dai Lion ya ji abin da ake aikatawa a ciki, to zai san yanda za'ayi a ruguje gidan, ballantana da akwai nasu har rayuka uku a ciki, bugu da kari kuma da akwai matar Aseef a cikinsu, ai dole ko ba zasu yi rai ba, dole su fito da su, dan haka shi dan Allah su dai'na damunsa da zancen wannan gida ta Mutuwa, idan suna magana, jikinsa har tsuma yake yi, ji yake yi ba zai iya hakuri ba, ji yake yi a yau zai tafi ya ɗaukowa Aseef matarsa, ya kuma kashe Queen ya ɗauko Dr Salman. Gwaggo ce ta danne shi, dan ba shakka suna kara ɓata mashi rai idan suna maganar, ji yake yi tamkar ya tashi ya tafi a lokacin. Miƙewa ya yi yana faɗin "Baby yunwa nake ji, na dawo baki bani abinci ba". Ya yi maganar yana kallon Jehan. Harara ta wurga mashi, zata yi magana idanunta suka sauka a kan mummynta, fasa yin maganar kawai ta yi. Wucewa ya yi yana faɗin "Dan Allah kowa ya je ya ɗan huta, kunga lokacin yin sallar mangariba ta kusa, ku huta kafin lokacin ya cika, maganar nan ta isa haka, tun da mun gano matsalarmu, to In Sha Allah zamu yi maganinta cikin gaggawa". Ya kai karshen maganar tare da sauka izuwa bedroom nasa. Gwaggo ce ta haɗa kan gabaɗaya matan, ta ce masu su je bedroom nata su huta, ina nufin su Ammie, Mummyn Rimsha, Aunty, da kuma mummy Anaya kenan, sune suka bi gwaggo, su kuma su Jelly, Anaya, Zaira, Umaisha, Jehan, suka wuce bedroom nasu Rimsha, Imran shi ya raka su Abba boys quarters na gidan, sannan ya wuce izuwa harabar gidan, dan ya sha iska abinsa, Aafia kuwa tana ɗakin gwaggon, dan dama tun shigowarsu aka kaita can, sai zuba barci take yi baiwar Allah, har wa yau, uncle Herry yana tare da Dr William a ɗakinsa, Dr William ɗin ya farfaɗo, amma ƴaƴan nasa sam sun ki zuwa wajensa, bare ma Lion, sam baya son haɗa hanya da su, ɗan gara Areef ma, time to time yana zuwa ya duba shi, wani likita Lion ya sanya aka kawo yana kula da shi, amma shi ko leƙawa yaki ya yi, daddyn kuma ba shi da burin da ya wuce ya ga yaran nasa, yana tsananin kaunar TRIPLETS nasa fiye da tunanin mai tunani, Aseef kam kowa ya sani, ɗan baruwana ne, yana can wajen gwaggo, dan haka shi yama mance da Dr William abinsa, yanzu ma da kyar suka lallaɓa shi ya wuce bedroom nasa, ban da haka ya ce shi wlh sai ya je Daular Mutuwa ya ɗauko matarsa. Wanke Jehan ta je tayi, bayan ta fito ta duba time, karfe 6:10pm, mangariba ya kusa, ga shi Areef ya ce mata yana jin yunwa. Sauri sauri ta shirya cikin kananan kaya, sannan ta ɗaura after dress a samansu, sai binta da kallo su Jelly suke yi, ita kuwa, basu isheta kallo ba, ba wanda ya sami kallon arziki a cikinsu daga wajenta, tamkar ba ƴan uwanta bane, kun santa dama da iya tsare gida da jiji da kai, to ko sannu bata ce da su Umaisha ɗin ba, haka ta gama abin da zata yi, ta zuba perfume kamar ba gobe, sannan ta fito izuwa cikin kitchen, kafanta na sanye cikin flat shoe mai matuƙar kyau na Rimsha, dan ita bata da kaya a gidan har yanzu, kuma bata ce a saya mata ba, dana Rimsha kawai take amfani, duk da sun yi mata kaɗan, haka take sanyawa. Abinci mai rai da lafiya ta shirya mashi a saman tray, sai dai dukka zaɓinta ta ɗebo, dan ita bata ma san irin abincin da yake so ba, shi ne yasa ta ɗauka mashi zaɓinta. Ɗauka ta yi ta nufi waje, kai tsaye bedroom nasa ta nufa. Baki ɗauke da sallama ta shiga ɗakin, wayam babu kowa a ciki, bata yi mamaki ba, dan tasan halinsa da son ƴan uwansa, wata kila ya tafi wajensu ne. A saman carpet ta ɗaura mashi abincin, sannan ta koma saman bed nasa ta bakin ta zauna, sai kallon ɗakin take yi, ko'ina tsab kamar sabo, sai tashin daddaɗar kamshi mai kwantar da hankali yake yi, ga sanyi Ac mai ratsa zuciya. Ta ɗan yi nisa cikin tunanin irin kyawawan halayensa da kuma tsanar madarar kyau da Allah ya yi mashi, kamar daga sama ta gan shi a gaban mirror yana tsaye, ya bata baya, kugunsa na ɗaure da white towel mai matuƙar kyau, daga wanka ya fito, jikinsa duk danshin ruwa, ga gashin kansa yana ɗan zubar da ruwa. Kallo ɗaya ta yi mashi ta yi saurin kawar da kanta gefe guda, har cikin ranta ta tsorata da ganin kyakkyawar kuma kakkarfar surar jikinsa, suna da halitta mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali over. Ganin kamar baya kallonta ne yasa ta mike a hankali dan ta bar ɗakin, saboda ta lura shi fa tsab zai iya yin komai a gabanta, dan ba kunya ne da su ba. Tana tafiya tana tunanin irin yanayin jikinsa da ta gani, duk da kallo ɗaya ta yi mashi, amma ya tsaya mata a rai, jikin nasa kamar madara, soft skin nasa luwai luwai da shi. A dai'dai tsakiyar ɗakin, bata yi aune ba sai ji ta yi ya rungumeta ta baya tare da zuro hannayensa a saman shafaffen cikinta, a hankali ya kwanto da kansa a saman shoulder ɗinta. Dogon numfashi ta ja tare da saukewa a hankali, ya sanya mata sanyin gashin kansa a wuya. "Hyyy baby, ina zaki je kuma?". Ya yi mata maganar a cikin kunne. "Zan fita ne na baka waje ka shirya". "Ni nace maki ina son ki bani waje ne?". Ya kai karshen maganar tare da sumbatar lallausan wuyarta. Shiru ta yi bata bashi amsa ba. "Ina abin da kika ajiye mani? A waya kin ce kina kewata, na dawo kuma shi ne ba zaki zo ki ganni ba, sai da na roka ko? Na rokanma kin zo kuma zaki tafi tun ban ganki ba, kin san adadin kewarki da nake yi kuwa? Kin san me nake ji kuwa?". Hannayenta ta ɗaura a saman nasa dake saman flat tummynta, kasa kasa ta ce "To ka bari sai ka gama shiryawa zan dawo, sai muga juna". "Why ba zaki zo ki tayani shiryawa ɗin ba? Yakamata ace kin saka mani kaya da kanki, please mana my baby". Kasa jurewa ta yi, dan wlh tana tsananin kewarsa sosai, ga shi yanda yake yi mata magana a cikin kunne kasa kasa, duk sai ya kara tsumata, hakan yasa ta kasa jurewa, a wannan karon ta kasa dannewa sai da ta juyo ta faɗa saman faffaɗar kirjinsa da kyau. Ajiyar zuciya ya sauke tare da rungumeta da kyau da kyau, tamkar wani ya ce zai kwace mashi ita. Da yake ita tana da tsawo sosai, Kamar gwaggo take, tafi Rimsha tsawo, sai tsayinta ya kai ta kwantar da kanta a saman ɓul ɓul ɗin breast nasa. Hannu ya kai saman bayanta yana ɗan shafawa izuwa mazaunanta masu burge shi, kowa yasan matan turawa basu da halittar mazaunai sosai, shiyasa dirarren halittar su Rimsha yake ɗaukar hankulan TRIPLETS over, suna son mazaunan nasu sosai, barema Rimsha, Jehan, Akila, Umaisha, sun fi kowa diri a cikinsu, tamkar su suka yi wa kansu....... "Baby". Ya ambata a hankali, kasa kasa ta amsa mashi da na'am. "Zaki tayani saka kayan?". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce e zata taya shi........... JEHAN DUNIYA, BAFA ABIN DA YARINYAR NAN BATA IYA BA, KAWAI TSIYA CE IRIN NATA, SAI TA NUNA KAMAR MA BATA SAN KOMAI BA, SABODA SHEGEN JAN AJI DA TSARE GIDA. Ɗaukarta ya yi cak, sai cikin dressing room ya sauketa, dressing room ɗin nasa sak irin na Lion. "Ki zaɓa mani kaya to". Ya faɗa tare da harɗe hannayensa a saman kirjinsa. "To ka rufe idanunka". Ta faɗa tare da wucewa izuwa wajen kayan nasa. Ba musu ya rufe idanuwan nasa, yau wani irin daɗi yake ji, saboda ta bashi kulawa, babu tsawa, babu tsiwa, babu haɗe fuska, bai san cewa ita ma sonsa yana neman yi mata illa bane yasa ta nema wa kanta mafita, yasa ta saduda ta fawwalawa Allah ta dawo ta fara kula da shi...... NI KO NA CE WAYE YA GAYA MAKI SOYAYYA WASA CE? DA KI CIGABA DA JAN AJI MANA, DA KIN MUTU A KAN SON SHI😂 KEBAKI GA AYA A KAN GWAGGO BANE? HAR YANZU SON DR WILLIAM NATA TAKE YI BAIWAR ALLAH, SO AI BA'A YI MASHI GARAJE! YANZU ZAI YI MAKA ILLAH, BA'A WASA DA ZUCIYA!. Wandon jeans baka da T-shirt sky blue masu matukar kyau ta ɗauko mashi, kusa da shi ta dawo, yana tsaye ya datse idanunsa yana jiranta. Kasa kasa ta ce "To ai ka fini tsawo, kuma ni ban san ta yaya zan sanya maka kayan bama". Idanunwansa a rufe ruf ya bata amsa da cewa "To yanzu dai kin yarda na buɗe idanuna? Sai na nuna maki yanda zaki saka mani". E ta amsa mashi da shi. Buɗe idanun nasa ya yi tare da matso da chair dake kusa da wajen watchs nasa, ya zauna a saman chair ɗin yana kare mata kallo. Ita kuma babu abin da take kallo a jikinsa saman da ɓul ɓul ɗin breast nasa, mamaki suka bata yanda suke ɓul ɓul kamar na mace. Jehan akwai dakiyar zuciya, ba irin Rimsha ba, da Rimsha ce ba zata iya tsayuwa tana ganinsa babu riga a jikinsa haka ba, tun da Rimsha take da Lion bata taɓa ganin surar jikinsa babu riga ba, ba zata iya ba, ita kuwa Jehan kun sani ba sai na sake faɗa ba, fin haka ma ta gani, ita da har video ta yi wa babban mutun tsirara a gidan Hjyr daɗi, ko kun manta ne? To na tuna maku,.....(Ita Jehan harta gogan nasu ma ta san ya yake abinta😂😂) Ganin tana ta satar kallon kirjin nasa da mamaki a face nata ne yasa ya kai hannu ya jawota jikinsa. Zaunar da ita a saman cinyarsa ya yi, cikin sanyin murya ya ce "Sun yi maki kyau ne kike ta kallonsu?". Hannu ta kai tana shafa kyakkyawar bakin gashin dake kwance a kirjin nasa. "A'a sun ban mamaki ne". Ta bashi amsa. Shi kuma jin saukar lallausan hannunta a kirjinsa ne yasa ya furta ash tare da datse idanunsa yana mai kara kankameta. (Da alama zancen Imran gaskiya ne, da ya ce wa Areef ɗin dan bai samu dama a wajen Jehan ɗin bace yasa yake cewa zai barta sai ta girma😂) Jin abin da ya furta ne yasa ta yi saurin zame hannunta daga wajen tare da yin ƙoƙarin barin jikin nasa, kankameta ya yi tare da riko hannun nata ya ɗaura a saman breast ɗin nasa, kasa kasa ya ce "Ina zaki je?". Ɗago idanu ta yi tana zubawa face nasa kallo, idanunsa sun sauya launi izuwa jajir, shi ma ya zuba mata idanu yana kallonta. Kasa kawar da kallonta ta yi, shi ma ya kasa kawar da nasa kallon. Almost 5 mins suna a haka, kirar sallar mangariba ce ta dawo dasu daga duniyar kallon soyayyar da suka faɗa. Da sauri ta sauke idanunta kasa tare da yunkurawa zata miƙe, sam bai hanata miƙewa ba, dan baya wasa da lokacin Sallah, tun da ankira sallah, to komai dole ya tsaya sai ya yi sallah. A hanzarce ya miƙe tare da karɓar kayan da ta fito mashi da su ɗin, cikin sauri ya sanyasu, ita kuma ta nufi waje. Ko da ya gama shiryawa ya fito, bata a cikin ɗakin, waje shi ma ya nufa dan zuwa masallaci, a palo ya ci karo da Lion ma ya fito. Babban abin burgewa da TRIPLETS shi ne. ba su wasa da lokacin sallah, kome suke yi, in dai an kira sallah, to bari suke yi su je su yi sallah, shi ne yasa a koda yaushe Allah yake karesu daga duk wata musifa da zata tinkaresu, dan Ubangiji ya ce duk wanda ya tsayar da sallolin farillah guda biyar ɗin nan a rana, yana yinsu a kan lokaci, yana kula da su, yana yinsu yadda yazo a rubuce, to ba zai taɓa taɓewa ba, ba dan haka ba, wlh da TRIPLETS izuwa yanzu ba zasu kai labari ba, da angama da rayuwarsu, amma saboda riko da addini, gasu nan a tsaye gam, ko jijjiga basu yi ba bare rashin lafiya, kai addinin musulunci duniya ne jama'a, TRIPLETS suna mugun burgeni wajen riko da addininsu, yanzu dai da wani ne yanda Areef yake da Jehan, yanda bata taɓa bashi fuska ba sai yau, da wlh ko ya ji an kira sallah ba zai rabu da ita ya tafi masallaci ba, ko yaya sai ya tsaya ya ɗan cigaba da wasa da ita tun da yau dama ta samu, amma shi ina, sallah tana gaba da komai a wajensa, ya fifitata sama da komai, bayin Allah, Allah Ubangiji ka bamu ikon riko da addininmu hannu goma goma ma idan akwai, ka bamu ikon tsayar da sallah a kan lokaci, dan yin sallah a kan lokaci, tana tare manya manyan musifu dake dinfaro bawa. Gabaɗaya mazan fitowa suka yi suka tafi masallaci, su kuma matan suka yi sallah a gida, bayan sun dawo daga masallaci ne kowa ya wuce bedroom nasa, da yake boys quarters ɗin ɗakuna uku ne a kasa, ɗakuna biyu a sama, sai daddyn Rimsha da daddyn Anaya suka ɗauki ɗaki ɗai'ɗai a sama, kasan kuma Abban Imran ya ɗauki ɗaki ɗaya, Abbi ma ya ɗauki ɗaki ɗaya, daddyn Jelly duk da yake gauro, sai ya zauna a ɗaki ɗayar, haka matayensu suka kawo masu abinci a cikin ɗakunnansu, ma'ana su mummyn Rimsha kenan, zaman gidan Lion ya kamasu dole, dan dole sai an shawo kan wannan matsala, komai ya dai'daita kafin su koma gidajensu, shi kam Akil ya ce wlh gidansa zai koma, ba Queen ba ko ubanta da ya mutu ne ya zo ya ɗauke shi yana jiransu, dan haka sai ya ɗauki Umaisha suka nufi gidansa da yake cikin unguwar, bai san cewa ba iya Queen kawai ake gudun mashi ba, akwai su Josephine a gefe guda, Imran ma ya ɗauki jelly suka bi Akil ɗin, ya rage saura Irfan kawai, shi dama yayan Anaya Feroz baya kasar, yana Uk abinsa. Bayan sun yi sallar isha, su daddyn Rimsha kowa ya wuce ɗaki da matarsa, su kuma su Rimsha, suna ɗakin gwaggo suna tayata hira bayan sun kammala cin abinci kenan, yau a tare da gwaggon da Brr Naurat suka ci abincin, sun baro mazajensu a ɗakunnansu. Misalin karfe 9 dai'dai, sanye cikin kayan barci ash color masu matukar kyau da tsada Areef ya fito daga cikin bedroom nasa ya nufi na gwaggo, dan ya je ya yi mata sai da safe ita da Brr Naurat, sai tashin kamshi yake yi. Dai'dai zai shiga ɗakin, ita kuma Jehan tana fitowa, zata koma bedroom nasu ne, ta ce ta gaji da surutun Brr Naurat, gara ta je ta kwanta, kun san dama ita ma bata son yawan surutu. Kayan barci ne riga da wando a jikinta, sai ta ɗaura hijabi a saman kanyan. Karo suka ɗan yi, baya kaɗan ya koma, dan a tunaninsa ma Anaya ce, dan idan baku manta ba, Anaya tana kama da Jehan ɗin sosai, ganin ita ce ba Anaya ba yasa ya ce "To a bani hanya na wuce". Gyara tsayuwarta da kyau a bakin kofar ta yi, ta tare mashi hanya tana faɗin "Ba zaka shiga maki ɗakin gwaggo na ba, barci take yi yanzu, ka tafi sai da safe". Ɗan shafa kansa ya yi yana tuna lokacin da ya yi mata irin haka a kan tazo zata shiga bedroom na daddynta, wato yanzu ita ma ta rama kenan, Jehan duniya. Amma da yake ya fita iya duniyanci, sai ya masto da face nasa dab da ita, kasa kasa ya ce "Da gaske? To idan momma ta yi barci, ai ke baki yi barci ba ko? Dama ni ai ke nazo ɗauka ba wajen momma nazo ba, muje bedroom ki bani abinci a baki, ni kuma na baki abin daɗi sarauniyar rigima ta duniya". Matsa mashi a hanya ta yi tana faɗin "A'a gwaggo bata yi barci ba, ka shiga". Kugunta ya damko tare da jawota jikinsa. "Baby waɗan nan balls ɗin naki suna saka ni shiga wata duniya, kuma suna sani ɗaukar chaji". Da yake bata gane nufinsa ba, a tunaninta da magana yake yi a kan idanunta, bata san a kan breast nata yake magana ba, sai ta ce mashi "To ba sai ka ciresu su dai'na kallonka suna saka maka chajin ɗin ka huta ba". Ai kuwa tana rufe baki ya kai hannu ya capko ɗaya yana faɗin "Bari dai na sa su sauke mani chaji, ai ban isa in ciresu ba, dan sune first thing da suke ɗaukar hankalina a jikinki". Jin yanda ya capko su bata san lokacin data kware baki zata kurma mashi ihu ba, dan bata yi tsammanin a kansu yake magana ba, ya wani capko mata su da karfi, har cikin ranta ta ji zafi. Ganin zata yi mashi ihu ne yasa ya rufe mata baki tare da ɗaukarta cak bayan ya saki breast ɗin nata, kai tsaye bedroom nasa ya wuce da ita. Suna barin wajen ita kuma Anaya ta fito dan ta je wajen Mark ɗin ta, tana kewarsa over, itama kayan barcin ne a jikinta, sai dai ita ma ta ɗaura hijabi mai ɗan girma a samansu. Rimsha kuwa da tana ganin kamar bata girma ba, sai bata wani sanya hijabi a saman kayan barcin nata ba, haka ta kwanta a saman cinyar gwaggo tana zuba hira da Brr Naurat abinta, ta mance da Noorish nata, bata sani bama ya ci abinci ne ko bai ci ba, ita dai kawai ta samu hira mai daɗi. Can gwaggo ta ce mata "Rimsha Saif ya ci abinci kuwa?". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Nima ban sani ba". Brr Naurat ce ta karɓi zancen da cewa "To tashi kije ki duba". To ta amsa da shi tare da mikewa ta nufi waje, bedroom ɗin ya rage daga Brr Naurat, sai Zaira kanwar Anaya, da kuma Aafia dake kwance, sai gwaggo. A dai'dai tsakiyar palo ta ci karo da Lion ɗin zai nufi bedroom nasa, sanye yake da kayan barci a jikinsa, da alama daga gadin ya fito, hannunsa na ruke da wayarsa. Wuceta ya yi ba tare da ya yi magana ba, tamkar bai ma kalleta ba, da sauri ta bi bayansa tare da rungume shi ta baya. A tsananin fusace ya fisgota ta dawo ta gabansa, hannu yasa ya shake mata wuya sosai yana bin kayan jikinta da kallo. Sai a lokacin ta gane me yasa ya yi mata hakan, tsananin tashi ne da shi kamar me, ya ji tsananin zafi na fitowa da ta yi da wannan kayan barcin nata ba tare da hijabi ba, kana iya hango shatin tula tulanta gabaɗaya, dan kayan basu da wani kaurin kirki, ga shi ita bata sanya breziya, tana ɗaukar kanta ƴar karamar yarinya sosai har a yanzu, bata kawo cewa ransa zai ɓaci sosai idan ta fito a hakan ba. Yana rike da wuyar nata ya jata har izuwa cikin ɗakin, a saman sofa ya hankaɗeta ta faɗi, cikin fushi ya ɗaga hannu zai ɗauketa da mari, tuna cewa idan fa ya mareta wlh tsab zata iya sumewa ko mutuwa, yasa ya fasa, ya sa kai ya wuce izuwa saman bed nasa ba tare da ya sake kallon in da take ba. Har ga Allah ransa ya yi mugun ɓaci, yana da tsananin kishi na wuce misali, ga shi yau gidan nasu a cike da mutanen, su Irfan, Imran duk suna nan, abin ya kona mashi rai over, abin da kuma yasa bai biye mata ya daketa ba na biyu, baya son a ƴan kwanakin nan ya rinƙa ɗaukar zafi, idan yana zaukar zafi, yana zuciya, za'a samu matsala, shiyasa kawai ya wuce saman bed nasa ya kyaleta a saman sofar, ba dan haka ba, yau da ya zaneta sosai. Ta sha jinin jikinta sosai, kuma ta ji babu daɗi. Jiki ba kwari ta miƙe ta nufi saman bed ɗin, hayewa ta yi tare da kwantar da kanta a saman bayansa, kirjinta dai dukan uku uku yake yi, amma haka ta daure, ta zuro hannayenta ta saman kirjinsa, cikin sanyin murya tare da shagwaɓa ta fara magana......... ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 21/4/2024 E11 cikin sanyin murya tare da shagwaɓa ta fara magana. "Kayi hakuri Noorish, ba zan sake ba". Shiru ya yi bai kulata ba, tamkar babu shi a cikin ɗakin. Ganin bashi da niyar kula tane yasa ta dawo da gabansa, ta kwanta tare da shigewa jikinsa, hannu ta kai tana shafa sajensa, kwaikwayon abin da yake yi mata na wasa da lips nata ta fara yi mashi ita ma, yatsanta ɗaya ta ɗaura a saman lips ɗin nasa, tamkar zata sanya mashi kuka ta ce "Please mana My Noorish, na tuba, ba zan sake ba, kasan fa Allah bana son ɓacin ranka, kuma......." Kasa karisa maganar ta yi saboda wani irin kallo da ya wurga mata. Da sauri ta zame hannunta daga saman lips ɗin nasa, a hanzarce ta shige cikin kirjinsa ta lafe tana mai sauke numfashi, a hankali hankali wasu siraran hawaye suka fara bin kuncinta, bata san time ɗin da kukan mai gabaɗaya ya kubce mata ba. Har cikin zuciyarsa yake jiyo sautin kukan nan nata, wani irin ba daɗi ya ji a ransa, kukan mace yana da tsananin tasiri a zukatan maza, komai zafin da namiji zai ɗauka, in dai mace ta iya kuka mai tsuma zuciya (kukan munafurci ba😂😂) to wlh nan take take iya sanya zuciyar namiji ya yi sanyi. Shi ma dai wannan kukan nata ta yi tasiri a zuciyarsa, dan kukan haɗe yake da shagwaɓa ga shi ta iya kuka mai ratsa zuciya, ga salo. Hannu ya ɗaura a saman kanta, cikin sanyin murya, kasa kasa ya ce "Why Meesha? Why zaki fita da irin wannan kayan? Kuma babu hijab" "Kayi hakuri, ba zan sake ba". Ta faɗa cikin kuka, da murya a shagwaɓe. Ɗago haɓarta ya yi tare da tsura mata idanu, yana tsananin kaunarta sosai, ta rigada ta shige can cikin zuciyarsa bawan Allah, ta zama rauninsa, ba zai iya ganin hawayenta ba. "My Meesha sarkin rigima, in dai rigima ce, to daga kanki an rufe kofa, yanzu me na kuka ni da ba dukanki na yi ba?". Turo ɗan bakin nan ta yi tana hura kumatu. Sumbatar lips ɗin nata ya yi, ɗago kai ta yi tare da sumbatar lallausan kumatunsa. Masto da face nasa dab da tata ya yi, cikin salo ya haɗe bakinsu waje guda. Kissing nata ya fara yi babu kama hannun yaro. A tare suka sauke nauyayyar ajiyar zuciya, sun yi kewar juna, tun a jirgin ruwa rabonsu da jin ɗumin juna har haka, tun da suka dawo matsaloli suke ta faru, sam basu samu lokaci a tare ba sai yau. Hannu ya kai saman wuyar rigarta, a hankali ya cire botiran rigar gabaɗaya ba tare da ya zame bakinsa daga nata ba. Wani irin nisawa ya yi lokacin da ya sauke hannunsa a saman lallausan tula tulanta. Ita kuma mike mashi ta kara yi tare da kara nutsewa a cikin jikinsa tana sauke numfashi a hankali hankali. Duk wata gajiya tasa sai da ya sauke mata yau, romancing nata sosai ya yi, har sai da ta rinka yi mashi kuka sosai, dan yana yi mata abin da yake fin karfin shekarunta ne, yana juyata son ransa, gata ƴar karama dai'dai wasa. Sai da ya sami ɗan salama, ya ɗan ji nutsuwa ta ɗan sauka mashi, sannan ya rabu da ita, tare da komawa ya kwanta, ya jawota jikinsa yana mai lashe hawayen kukan da take yi. "Meesha sarkin ragwanta". Ya faɗa kasa kasa. Dukan wasa ta kai mashi a kirji bam tana faɗin "Duk ba kai bane kake sakani kukan, sai ka rinƙa yi mani abubuwa da zafi zafi". Hannun nata ya riko, da yake su kwata kwata a rayuwarsu basu san menene kunya ba, kai tsaye sai a saman Heronsa ya sauke hannun nata, ta miƙe sosai, tana tsaye gam, kasa kasa ya ce mata. "Tun ban baki wannan ba kike kuka haka?". Ihu ta zunduma mashi, lokacin guda kuma ta ɗauke diff kamar an ɗauke wutar nepa, ta ji abin da ya fi karfinta, duk da cewa akwai kaya a jikinsa, abin bana wasa bane, ya wuci lissafin ƙwaƙwalwarta, ita dai tasan yes idan an yi aure ana having sex, Akila ta gaya mata, amma bata taɓa sanin ya heron Noorish ɗin nata yake ba ma, shi kansa Noorish ɗin ma tsoronsa take ji bare kuma bananansa? Tab sai Akila ta dawo ta kara mata lecture sosai, sai dai kuma abin mamaki shi ne, da gwaggo da mummynta duk kallon kamar mai yaron ciki ma suke yi mata, basu taɓa kawowa a ransu cewa har yanzu babu abin da ya shiga tsakaninta da shi ba, a tunaninsu ta san komai izuwa yanzu, har fatan su samu nutsuwa mum take, dan tana son ta gyara yar tata, ta ji babu daɗi da suka yi aure bata nan, a cewarta basu sami gyara ba, to shi ne take fatan su samu nutsuwa, waɗan nan matsaloli duk su kau, zata ajiye ƴaƴan nata ta yi masu nasiha, sannan ta tsumasu sosai. (Ni kuwa nace tab to su Rimsha kam har yanzu virgin ne, kada ayi masu wani jike jike da tsome tsome 😂 in yi masu karin bayani ne ko dai na kara gaba readers?😂) Jin cewa ta suma ne yasa ya saki hannun nata tare da cigaba da shafa bayanta har barci mai tsananin daɗi ya yi awon gaba da shi. A ɓangaren Jehan da Areef kuwa, tun da ya ɗauketa, bai zame da ita ko'ina ba sai cikin bedroom nasa, a saman bed ya kwantar da ita, sannan ya kashe wutar ɗakin tare da rufe kofar. Kusa da ita ya dawo ya kwanta. Ganin ya kwanta ne yasa ta yunkura dan ta gudu, kamar yana kallonta ya kuwa capkota, ga ɗakin da duhu sosai, saboda kashe wutar da ya yi, kuma bai kunna blue light ba, saboda shi tun ainahinsa baya son haske sosai. "Ina zaki gudu ki je?". Ya raɗa mata a kunne. "Ɗakinmu mana". Ta bashi amsa tana ta ƙoƙarin raba jikinsu da juna. "To yau dai a ɗakin babynki zaki kwana, ƴar rigima, sai ki barni na yi ta barci ni kaɗai ko?" Zata yi magana wayarsa ya fara kara, hannu ya kai ya laluɓota a saman bedside drawer, ganin number Usa ba ƙaramar mamaki ya sha ba, shi dai yasan bayan his excellence, ba shi da number kowa daga Usa a yanzu, ga shi kuma ba ainahin wayarsa bace a hannunsa, da ainahin wayarsa ce, zata nuna mashi suna kai harma daga in da aka kira shi, ma'ana area da aka kira shi. Kamar dai ba zai ɗauki kiran ba, ko me ya tuna, sai kuma ya ɗauka. Yana ɗauka ya sanya a hand-free yana mai cigaba da shafa mazaunanta. Muryar macece ta cikin wayar ta fara da cewa "Baby good evening?". Da sauri ya waro idanu yana kallon wayar, ita ma Jehan ɗin ɗago kai ta yi tana kallon shi, sai surutu wacce ta kira wayar kuma take zuba mashi. Da alama parrot ce. Ganin yanda Jehan ɗin ta ɗago a hanzarce tana kallon shi ne yasa bai ma san time ɗin da ya katse kiran ba, shi dai bai san wacece bace har ga Allah. Ƙoƙarin barin jikinsa Jehan ɗin ta yi. A hanzarce ya rikota yana tambayarta ina zata je, kin yi mashi magana ta yi, da karfi ta sanya karfinta zata kwaci kanta tare kuma da fara ruwan zafafan hawaye, labarin gwaggo ne kawai ya dawo mata a cikin ƙwaƙwalwata, kenan yanzu da gaske suma TRIPLETS amanarsu za su ci? Ta tambayi kanta da kanta, gudun irin haka yasa sam bata son soyayya, kuma bata kula kowa, amma Areef ya zo ya shiga rayuwarta, yanzu ga shi har wata ne take kiransa da baby a gabanta, hakan yasa ta kara karfin gudun kukan nata har yana fitar da sauti kaɗan kaɗan. Yadda kuka ga Lion a kan kishi, haka ita ma Jehan take da bala'in kishi over, haka gwaggo ma take da wannan kishi, kun san ita Jehan abin da yasa wani lokaci ɗabi'unta suke kusan kamanceceni da Lion, saboda wasu halaye na gwaggo da ta ɗauko, shi kuma Lion gadan halayen gwaggon ma mai gabaɗaya ya yi, a cikin jikinsa yake, shiyasa nasa ya fi over. Wani irin bakin ciki ne ya turnuke mata zuciya, haushin Areef ɗin ma gabaɗaya take ji, cikin tsawa ta ce "Ni ka sakeni!". Yadda ta daga mashi tsawan abin ya kona mashi rai, sai ya sanya hannu ya damko wuyarta da kyau, cikin fushi shi ma ya daka mata tsawa tare da fara magana cike da ɓacin rai "Ni sa'an wasan ki ne? Har ni zaki dakawa tsawa haka? Kuma ina yi maki magana kina ce mani ke tafiya zaki yi, to na saki wuyar take, ki tafi in gani! Ko motsi ma ki sake yi in gani". Ya kai karshen maganar tare da zame hannunsa daga wuyar tata. Kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro ta saki tare da komawa ta kwanta shiru, zuciyarta zafi yake yi mata, tamkar an ɗaura shi a saman garwashin wuta, ji take yi tamkar ta haɗiyi zuciya kawai ta mutu kowa ya huta. Kasancewar shi Areef na daban ne, yana da zuciya mai kyau, kuma yasan ya kamata, ya iya rarrashin mace, yasan cewa a yanzu shi ne ya yi mata laifi, ya san cewa tana son shi ne yasa take kishinsa, idan bata son shi, ba zata yi kishi har haka ba, a yanzu dai shi ne ya yi mata laifi, tun farko ma meyasa zai ɗauki kiran waya suna a tare da ita? Ai dare lokacinta ne, dan haka ya shiga hakkinta, shi ya ja koma me ya faru, bawan Allah yana da dogon tunani, ya san yakamata, yana da nutsuwa da hankali, sai ka rantse da Allah daddyn Rimsha ne ya haifeshi, saboda halinsu iri ɗaya, shi ya yi sa'a, halin familyn gwaggon ya ɗauko, amma da yake jini ba wasa ba, akwai wasu ɗabi'u nasa da suke kama da family William kamar yanda shi ma Lion da ya ɗauko family William gabaɗaya da akwai wasu ɗabi'u nasa irin na familyn gwaggon, irinsu kyauta, sadaka, jinkan nakasa da sauransu, ba sai na sake faɗa maku ba, kun ji da kunnanku Aseef ya ce su daddynsu basu kyauta, su idan ba pastor ba, to babu wanda yake cin kuɗinsu, amma su TRIPLETS suna da kyauta sosai. A hankali ya matso kusa da ita, ta bashi baya tana ta murzan kukan kishin mijin nata, wata ta kira shi da baby a gabanta, bata ma san wacece bace, amma take irin wannan kishi, shi kansa bai san wacece bace, kila his excellence ne ya bata numbersa, dan tsohon nan ya iya haɗa aure. Tallabota ya yi da hannayensa dukka biyu, sannan ya ɗagota da kyau izuwa saman faffaɗar kirjinsa, rungumeta sosai ya yi, kafin ya kai hannu ya kunna lamp dake saman bedside drawer, nan take haske ya gauraye wajen gadon nasu. Cikin nutsuwa ya fara magana "Am so sorry my baby, na san nayi laifi, amma ki yi hakuri". Tamkar ba da ita yake yi ba, ta share shi, ta cigaba da zuba kukanta. Ɗan bakinsa ya kai saman face nata, hawayen ya fara lashewa, yana yi yana ɗan bubbuga bayanta alamar rarrashi. A dai'dai lallausan lips nata ya tsayar da tongue nasa, cikin kwanciyar hankali ya fara lashe lips ɗin nata. Turo baki ta yi tare da ɗan ture shi kaɗan, cikin kuncin zuciya ta ce "Ni banaso, ka rabu da ni, ka je can ka yi wayarka, babynka tana jiranka". Bata gama rufe baki ba aka sake kiran wayar. Guntun tsaki ya ja tare da kai hannu ya ɗauko wayar, picking call ɗin ya yi, tare da sanya wayar a hand-free, cikin faɗa ya tambayi yarinyar wacece ita?. Tamkar yanda ya yi hasashe ne, his excellence ne nan ya bata number, jikarsa ce, yana son ta auri ɗaya daga cikin TRIPLETS. Warning ya daka mata da babbar muryar a kan idan ta kuskura ta sake kiran numbersa, to sai na lahira ya fita jin daɗi, yanzu haka kawai ta sanya ran matarsa farincikinsa ya ɓaci, wlh a kan hakan ma ba zai kyaleta ba, sai ta yi zaman prison ko na shekara ɗaya ne, dan ɓatawa Jehan rai ba abin wasa bane. Cikin ɓacin rai sosai ya yi magana, yana gama kora mata jawabi ba tare da ya jira amsarta ba, ya katse kiran tare kuma da kashe wayar gabaɗaya. Ransa ya ɓaci sosai, yana tunanin irin ruwan bala'in da zai surfawa his excellence da safe, a kan me zai rinƙa bawa ƴan'mata numbersu? Su sunce mashi ya nema masu matan aure ne? Meyasa baya bada number Lion ko Aseef, sai dai numbersa shi kaɗai? Wato shi his excellence ya renawa wayo ko? To wlh zai yi maganinsa ne! Sai surfa bala'i yake yi a cikin zuciyarsa. Ganin ransa ya ɓaci sosai ne, kuma ta ji duk abin da ya faru a tsakaninsa da yarinyar, dan a hand-free ya sanya wayar, hakan yasa ta koma ta kwanta a jikinsa, cikin sanyin murya ta ce "Kayi hakuri". Sai a lokacin ya dawo da kallonsa a kanta, nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, tare da kara rungumeta da kyau da kyau. Ita ma rungume shi ta yi tana ɗan shafa bayansa. "My baby ki dai'na saurin yin fushi haka mana, kin san fa ni ke kaɗai nake so". Jinjina mashi kai ta yi tare da dawo da hannunta da gaba wajen kirjinsa, botiran kayan barcin jikinsa ta fara ɓallewa tana faɗin "Ni ba zan dai'na yin fushi ba in dai zaka rinƙa magana da mata". Haɓarta ya ɗago yana faɗin "Idan da ni mai kula mata ne, da a yanzu matana sun fi dubu, ke kaɗai ce kika yi mani a rayuwata, bayan ke banga wata ba, rigimammiya sarkin kishi kawai". Ya kai karshen maganar yana sumbatar lips nata. "Kai ma ai rigimammen ne". Ta yi maganar tana buɗe kirjinsa, ta gama cire botiran rigar. Shafa lallausan gashin dake kwance a kirjin nasa ta fara yi tana kara lafewa a jikinsa. Wani irin daɗi mara misaltawa ya ji, hannu ya kai ya kara gudun Ac, tare da ja masu bargo, sannan ya kashe lamp ɗin, dan na gaya maku shi baya son haske ko kaɗan, ba kaman Lion da yake iya barci da lamp a kunne ba, shi baya iyawa. Cikin dabara ya laluɓi laɓɓanta, da wani irin salo na daban ya fara kissing nata, shi already babu abin da bai sani ba dan gane da soyayya, saboda shi kunga ya yi rayuwa a wajaje da dama, ya zauna da mutane daban daban, ya iya salon soyayya kala kala. Bata hana shi ba, sai ma biye mashi da ta yi, ta cigaba da shaga gashin dake kwance a kirjin nasa, tana wasa da tongue ɗinta a cikin bakinsa. Sosai ta kara sakawa ya shiga wata duniya, cikin tsananin sha'awarta ya fara ɓalle mata nata botiran rigar bayan ya mayar da hijabin jikinta wuyarta. Zame bakinsa daga nata ya yi dan ya sami damar sauke nauyayyar ajiyar zuciya, rabata da hijabi da kuma rigar jikin nata ya yi, sannan ya kara jawowata jikinsa sosai. Wani irin dogon numfashi ya ja lokacin da hannunsa suka sauka a saman lausasan tula tulanta, a hankali ya fara wasa da su, kara shigewa jikinsa sosai ta yi tana karɓar irin wannan zazzafar sakon da yake aika mata ɗin. Ɗan bakinsa ya kai a saman nipples nata, tongue nasa ya fitar a in da ya fara wasa da nipples ɗin nata, kewaye ɗan kansu ya fara yi da tongue ɗin nasa, yana matsa ɗayan breast ɗin kuma da ɗayan hannunsa. Wani irin yanayi ta fara ji wanda ya fara wuce lissafin ƙwaƙwalwarta, ta kasa gane wani irin abu take ji a jikin nan nata ne, ji take tamkar kankara ake manna mata, tun daga tsakiyar kanta har izuwa tafin kafarta take jin wannan abin. Juyi ta fara ji mashi tana zillo tana son kwace kanta, dan bata taɓa jin makamancin wannan yanayi ba. Kara kankameta ya yi, ya cigaba da abin da yake yi, da ya ga tana neman katse mashi jin daɗinsa, sai ya haye kanta tare da yi mata runfa da faffaɗar kirjinsa. Cikin dabara ya shammaceta, ba tare da ta ankara ba ya rabata da wandon kayan barcin jikinta. Ba ƙaramin daɗi ya ji ba ganin cewa babu pant a ciki, saman mararta ya ɗaura hannunsa, wani irin ɗauke wuta ta yi na ƴan mintoci. Lokacin da ta dawo dai'dai, can a gabanta ta tsinkayo shi yana wasa da wajen. Kuka ta fara yi mashi, cikin fitar hayyaci take faɗin "Yah Areef ka bari dan Allah, jikina yanayi mani wani iri, please ka ji mijina, wayyo gwaggona". Haka take ta zuba mashi kuka da surutai. Yana jinta sarai, amma bai dai'na wasa da ita ba, saboda ta haɗa duk wani abin da yake da bukata a tattare da mace, ba shi da niyar yin sex da ita a yanzu, amma fa zata sha wasa, dan sai ya koya mata son wasar tasa sosai, har yazamana idan bai yi mata bama, ba zata iya barci ba... BABBAR MAGANA. Kuka ta cigaba da yi mashi, shi kuma juyata ya cigaba da yi son ransa, daga karshe ma tongue nasa ya zura a gaban nata, wasa ya fara yi da wajen sosai da sosai. Wani irin ihu ta zunduma mashi cikin fitar hayyaci, ta rasa ina zata sanya ranta, sai ƙoƙarin janye jikinta take yi, amma ina ko kusa ko alama ba zata iya ba, dan ba rikon wasa ya yi mata ba. Sosai yake juya tongue nasa a wajen, ba shiri ya fara zuba mata sambatu shi ma, da alama shi ma yanzu ya fita a cikin hayyacinsa, jikinsa har wani tsuma yake yi, gabaɗaya tsikar jikinsa ta tashi zara zara, bukatar kawai ya ji shi ya shigeta, ya shiga cikin jikinta sosai, sai dai ba zai yi gigin yin hakan ba, saboda lokacin da suka je yin sallar Issha, Lion ya ce mashi gobe za su tafi Enugu state, so ba zai iya yin dis virgin nata a yau ba, dan idan ya yi hakan bai kyauta mata ba, na farko bashi da tabbacin zai dawo a raye! Na biyu kuma ba zai so ace ya yi dis virgin nata kuma bata sami kulawa daga gsresa ba, ya tafi ya bari wasu su kula da ita, su yi jinyarta, sam ba zai so haka ba, waɗan nan dalilan ne suka sanya ya daure ya cije bai shigeta ɗin ba, amma iya kurewa ta kure hakurinsa gaskiya, ya zurfafa da yawa a wasan nasa, kuma daɗi ne ta rinjaye shi, daɗi ne tasa har ya zurma da yawa haka ba tare da ya ankara ba, shi Lion da yake yasan kansa, yasan idan ya zurma fa to ba zai iya rike kansa ba, sai ya zama ko kusa ko alama baya tunkarar gaban Rimsha idan suna wasa, a iya tula tulanta kawai yake tsayawa, suma bai cika taɓa su ba, ko kiss baya son yi mata sosai, sai dai sumbata, dan yasan idan ya fara kissing nata, zai kai hannu ya taɓa tula tulanta, daga nan kuma labari zai canza, to shiyasa yake takaka tsantsa sosai, bawai dan baya sonta ko baya son wasa da ita ba, a'a izuwa yanzu kowa yasan Lion yana tsananin kaunar Rimsha, kuma yana da karfin sha'awa sosai, a kullum yana tsananin sha'awarta over, kawai tsaro ne yasa yake kawar da kai, kuma dama ai sai kana son mutun zaka yi sha'awarsa!, Shi kuwa Areef, tashin farko ya zafafa a wasan nasa, kunga kuwa dole a sami matsala. Idanuwansa tamkar wuta saboda ja, ita kuwa DPO, sai kuka take yi mashi. Wani irin juyata ya yi tare da kara zura tongue ɗin nasa da kyau a HQ ɗin nata, sanna ya kai hannu yana matsa mata tula tulanta da karfi karfi, kan kace me tuni ta sume mashi, shi kuma da yake lokacin yana dab da samun nutsuwa ne yasa ya tsananta wasan sosai har ta sume bai sani ba. Sai da ya samu nustuwa ne ya lura da ta sume, mamaki yake yi wai a iya wasa da suka yi ne har da sume mashi, da wani ɗan bakinta na tsiwar nan a wajen, ga fuska jaga jaga da hawaye, ashe duk iya tsiwar tata ko wasanin sa kawai ba zata iya ɗauka ba? Ya faɗa a cikin zuciyarsa tare da matsowa yana lashe hawayen nata. Kissed na lips nata ya yi kafin ya miƙe ya saɓeta a kafaɗarsa suka nufi toilet. Wanka ya fara yi mata, tun da ya tsundumata a cikin ruwan ta farfaɗo, kuka ta cigaba da yi mashi, bai kulata ba har sai da ya kammala, ya naɗota a towel. Saman bed ya mayar da ita ya kwantar, sannan shima ya je ya yi wanka. Yana fitowa ya wuce dressing room. After some minutes ya fito sanye cikin wasu kayan barcin white color, hannunsa na ruke da wasu kayan kuma, kayan barcinsa ya ɗauko mata. Kusa da ita ya zo ya zauna, cikin sigar rarrashi ya ce "My baby menene abin kuka kuma daga wasa? Ban fa yi dis virgin naki ba bare ki yi mani kuka, shi ne dai nasan da akwai zafi, amma wasa ai babu zafi sai dai daɗi ko?". Ya kai karshen maganar yana kunna lamp dake bedside drawers ɗin. Harara ta wurga mashi kafin ta ce "Allah ba zan kyaleka ba, zan rama ne". Hannu ya kai yana zame towel ɗin dake jikinta yana faɗin "Tom shikenan zamu gwada watarana, sai ki rama mu gani". Kankame towel ɗin da karfi ta yi tana faɗin "Ni kada ka cire mani kaya". Matsowa dab da ita ya yi, kasa kasa ya ce "Kaya kuma na nawa? Ai babu abin da ban gani ba, yanzu kinga idan nazo yin dis virgin naki ma nasan hanya, tongue ɗina ya nuna mani hanyar, dan haka kawai ki sake mani abubuwana na moresu, na kuma baki baby's masu kama dake, kyawawan gaske masu manyan idanu kamar ball". Zaro idanu ta yi tana mamakin rashin kunya irin na TRIPLETS, duk rashin kunyarta ashe bai kai kaso 1 cikin ɗari nasu ba, su kwata kwata basu ma san me ake kira da saya magana ko a ɓoyeta a faɗeta ta wasa siga ba, ba kai tsaye ba saboda kunya, su basu san wannan ba, kawai maganarsu suke yi kai tsaye, yanzu fa ba ƙaramin aikin Areef bane da ya tuɓe mata kayan jikinsa rankatakaf abinsa, babu ruwansu su kam, Allah mai iko. Ganin ta afka duniyar tunani ne yasa ya zame towel ɗin tare da kara matsowa kusa da ita, sosai ya zubawa kyakkyawar surar jikinta idanu, a hankali ya kai hannu ya shafi jajir kuma lausasan tula tulanta, hakan ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta afka, cikin sauri ta ce "Wai ba zaka rabu dani ba? Kuma.....". Bai bari ta karisa maganar ba ya zura tongue nasa a cikin bakinta, yana zurawa ya rungumota sosai suka kwanta a tare, ya janyo masu bargo, sannan ya zuro hannunsa daga ta cikin bargon ya kashe lamps ɗin. A kunne ya raɗa mata cewa yau ba kaya zata kwana, ya fi so ya ji komai suna tsokalinsa. Shiru ta yi bata kula shi ba, tana jinsa yana mammatse mata breast nata har barci ya yi awon gaba da ita. Tana yin barci ya lallaɓa ya kwantar da ita, miƙewa ya yi tare da duba time, 1:30am dare ta tsala sosai. Kasan gadon ya diro, da sauri ya nufi waje. Kai tsaye garden na gidan ya nufa. Bakinsa ɗauke da sallama ya shiga, Lion yana zaune a wajen yana aikin latsar waya, kusa da shi ya zo ya zauna, ba ɓata lokaci suka fara tattaunawa a kan tafiyar da za su yi gobe, dan Lion yasa a bincika mashi ta ina Daular Mutuwa take a yanzu, kuma ya sanya ayi masu addu'a sosai, dan yanda ya kalli Rimsha ta rikice hakan nan, yasan ba'a banza ba, taga bala'i ne. A ɓangaren Anaya kuwa, time da ta fito daga cikin bedroom na gwaggo, kai tsaye wajen Mark ta nufa, baya a kitchen time ɗin, dan haka sai ta fito waje harabar gidan. Tafiya ta fara yi tana ƴan waige waige dan nemansa. Ta wajen pool na gidan ta nufa. Can ta hango shi shi da Alex a wajen pool suna zaune a saman ɗaya daga cikin kyawawan kujerun dake a wajen. Da sauri ta karisa wajen, da yake bata san cewa Alex uncle nata ne kanin daddynta ba, sai tana zuwa ta faɗa jikin Mark ɗin tana murmushi. Shi ma Alex ɗin bai san cewa ƴar yayansa bace, ya ɗauka ma matar Mark ɗin ce ko dai wata makusanciyarsa, tun da basu gama sanin juna da Mark ɗin ba, bai san abubuwansa da kuma jama'arsa ba, dan haka sai ya bisu da idanu kawai. Cikin shagwaɓa ta ce "My na yi kewarka sosai fa". Shafa face nata ya yi tare da ɗan sumbatar kumatunta. Sai kallonta Alex ɗin yake yi, tabbas ta yi mashi kama da Brr Naurat, dan idan baku manta ba, daddyn Rimsha da daddyn Anayar duk da Brr Naurat suke kama, Anaya da Jehan kuma suka yi kama da mahaifan nasu, kunga dole a sami kamanin Brr Naurat a fuskar Anaya da Jehan ɗin, tamkar zai tambayi Mark ɗin wacece wannan kuma? Sai kuma ya fasa, da ya gaji da shagwaɓar Anayar ma, sai ya miƙe ya sabu waje abinsa. Haka suka murji soyayyarsu son ransu, sai zuba mashi shagwaɓa take yi, shi kuma yana biye mata, tana tsaka da yi mashi magana, bata ankara ba sai jin saukar lips nasa a saman tata ta yi, ga shi tana kwance a jikinsa, kun san su a wajensu hakan ce soyayya. Bata hana shi ba da farko, daga baya da ta tuna da maganganun da Rimsha ta yi mata a school, sai ta yi maza ta mike daga jikin nasa tare da komawa gefe da sauri. Da mamaki yake kallonta, kafin ya yi magana da gudu ta bar wajen, kirjinta sai dukan uku uku yake yi, fatan ta ɗaya, shi ne kada ta samu ciki kamar yanda Rimsha ta ce mata idan wani ya taɓata zata samu ciki.. BABBAR MAGANA. Tana shiga cikin gida, kai tsaye ɗakinsu Rimshar ta nufa, a lokacin kowa ya yi barci, saman bed ta haye tare da kudundunewa a cikin bargo, nan take ta fara hawaye tare da danasani. Shi kuwa Mark, wayarsa ya ɗauka ya fara kiran numberta, amma ina taki ɗagawa, daga karshe dai ya hakura ya kyaleta, dan bashi da zaɓi. A haka barci ya yi awon gaba da ita. A ɓangaren shi kuma Aseef, da kyar da makyarkyata ya samu barci ta yi awon gaba da shi, Allah sarki, yana tsananin kewar Heartbeat nasa, har wani zazzaɓi mai tsananin zafi ne ya rufe shi, a haka dai barci ɓarawo ya ɗauke shi. Ummin Nawid ƴan uwanta na Katsina sun zo sun ɗauketa, dan sun sami labarin rasuwar Dr Nawid, abin gwanin ban tausayi. After one day. Haɗe suke gabaɗaya a palo, a yau ne su Lion suka shirya tafiya Daular Mutuwa, suna hira a palon na ban kwana da ƴan uwan nasu. Gwaggo ce ta ce da Lion "Amma Saif ba da Rimsha zaku tafi ba? Naga ita kaɗai ta san hanya ai". Kai kallonsa a kanta ya yi, tana kwance a saman cinyar daddynta. Shi ba don hanyar ma yasa yake son tafiya da ita ba, saboda su Josephine yasa yake son tafiya da ita, baya son barinta a nan, dan kada su Josephine ɗin su yi mata wani abin, hankalinsa zai fi kwanciya idan ya tafi tare da ita. "Yeah momma da ita zan tafi......" Bai gama rufe baki ba ta zunduma ihu tare da miƙewa tsaye tana faɗin "Wlh ni ba zan je Daular Mutuwa ba, in dai a kan Daular Mutuwa ne to wlh sai dai mu ɓata da yaya Saif ɗin, kowa ya kama gabansa, ni sai dai idan gawata za'a mayar can, amma da kafata, wlh ba zan je ba, na shiga uku na lalace, wayyo daddyna kasheni kawai gwaggo take so aje ayi, kila ta gaji da ganina ne a duniya, daddy ka gaya mata kai kana sona tun da ita ta dai'na sona, mummy dama nasan ke kinfi kowa sona, ki gaya masu kada su taɓa maki ƴarki". Ta kai karshen maganar tata tare da watsawa a guje ta nufi cikin bedroom nasu, sai kuka take yi tamkar ranta zai fita. Shiru palon ya yi, babu wanda bai tausaya mata ba, harta shi kansa Lion ɗin ya yi mugun tausaya mata, ba'a banza take waɗan nan surutan ba akan Daular Mutuwar, baiwar Allah. Miƙewa Areef ya yi ya bi bayanta izuwa cikin ɗakin nata, su kuma suka cigaba da tattauna yanda za'ayi. Yana shiga ya sameta kwance a saman bed, ta yi shiru ga hawaye a jaga jaga a saman face nata, sai tunanin yanda ta baro Daular Mutuwar take yi. Saman bedside drawer ya zo ya zauna, cikin zolaya ya fara magana "Rimsha ƴar Queen of Daular Mutuwa fa ta ga Yaya Saif naki, kuma ta ce idan ba shi ba wlh mutuwa zata yi, ita shi take so, Queen ɗin kuma ta ce ta kwantar da hankalinta babu shakka sai ta mallaki Lion ko ana ha maza ha mata". A dubu ɗari ta mike zaune, tare da zaro idanunta waje tamkar zasu faɗi kasa, kome ta tuna, sai ta zunduma ihu da iya karfinta tana faɗin "Ni wlh babu wanda yaya Saif zai sake aura, ni kaɗai na ishe shi, Allah koma Queen ɗin ce bata isa ta taɓa mani shi ba, ai ba tsoronta nake ji ba, a kan shi zan iya yin komai, shegiyar mata mai bakar aniya, wlh azumi da tsayuwar dare zan yi mata, dan taga yaya Saif na kyakkyawan gaske ko? Bakar azzaluma, to wlh yaya Saif yafi karfinta, kuma shi baya son aljana, Allah idan ta sake ta kalle shi da ido ma kawai, sai na kwakwale mata idanu!!". (Ko a ina zata gan Queen ɗin har ta ga idanun da zata kwakwale mata ɗin?🤔 Anya Rimsha ƙwaƙwalwarta bai taɓu ba kuwa?) Tana magana tana ihu. Areef me zai yi? Ai yau dariya har da rike ciki, Allah mai iko, kamar ba yanzu ta gama cewa ita ta dai'na son yaya Saif ɗin ba, in dai a kan Daular Mutuwa ne, to wlh babu ruwanta da shi, amma daga jin batun zai auri ƴar Queen, har ta mance bala'in dake cikin Daular ta fara kishi kuma, kai jama'a Rimsha tana yin son ranta. Ganin irin dariyar da yake yi mata ne yasa ta kara tsananta kukan nata. Tana ƙoƙarin sauka daga saman bed ɗin idanunta suka sauka a saman face ɗin Lion, yana tsaye a bakin kofar shigowa bedroom ɗin. Wani irin yawun wahala ta haɗiye, nan take ta yi shiru, dan yanda ta ga face nasa babu almun wasa a tattare da shi, nan take ta haɗe malaman jikinta waje guda ta nutsu tsit. Wani irin muguwar harara ya wurgawa Areef dake kallonshi yana dariya. A takaice ya ce mata "Zoki wuce mu tafi". Ba musu sumui sumui ta sauko kasa daga saman gadon ta nufe shi. Gaba ya yi ta rufa mashi baya, kai tsaye bedroom nasa ya wuce, cikin jin kunya ta keta jama'ar dake a cikin palon ta bi bayansa zuwa bedroom ɗin nasa............ ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 22/4/2024 E12 Gaba ya yi ta rufa mashi baya, kai tsaye bedroom nasa ya wuce, cikin jin kunya ta keta jama'ar dake a cikin palon ta bi bayansa zuwa bedroom ɗin nasa. A zaune a bakin bed ta isko shi, kusa da shi ta zauna tare da kwanto da kanta a saman laps nasa. Nisawa ya yi tare da kai hannunsa yana goge mata guntun hawayen dake a saman face nata. "Meyasa kike son yin kuka sosai ne?". Ya yi maganar yana mai da kallonsa a saman zanen sunansa dake saman tudun tula tulanta da suka ɗan bayyana saboda yanayin kwanciyar da ta yi. Hannu ya kai wajen yana ɗan shafa zanen, kasa kasa ya ce "I really like it". Ɗan turo baki ta yi tana mai kamo hannunsa ɗayar dake a saman kumatunta. "Noorish ni dan Allah kada ka bari a mayar da ni Daular Mutuwa ka ji ko?". Dawo da kallonsa a saman face nata ya yi, zuba mata idanu ya yi na tsawon mintocin da a kallah zasu kai biyar, kafin ya ja godon numfashi sosai ya fara magana a nutse. "I will going to miss you my Meesha, ba zan tafi da ke ba, kuma babu wanda ya isa ya kai min ke can, stay with your dad and mum safe, ki kula mani da kanki sosai, don't come out without hijab, even wajen momma zaki je, you now i hate that, so be careful kin ji ko? I really love you from the button of my heart". Ya kai karshen maganar yana shafa lallausan wuyarta. Nan take ta ji jikinta ya yi mugun sanyi, mikewa ta yi zaune tare da faɗawa jikinsa da kyau. Rumgumeta sosai ya yi, ji yake yi tamkar idan ya tafi ya barta, wani abin zai iya faruwa da ita, yana jin tamkar za'a rabasu. "My Noorish i really love, ban taɓa son wani abu a rayuwata kamar yanda na so ka ba, tun ban san wacece ni ba nake dakon sonka, hotonka kawai idan na gani yana ɗaukata tsawon lokaci ina cikin tsananin farinciki, a duk lokacin da na tunaka, ina jin tamkar ba'a duniya nake ba saboda daɗi, ban taɓa kawowa a ra'ina zan ganka ido da ido ba, ban taɓa kawowa a ra'ina zan zauna a kusa da kai ba, amma duk da haka, a kullum sonka karawu take yi a cikin zuciyata, bani da abin da zan ce ga Allah sai dai Alhamdulillah, Alhamdulillah daya mallaka mani kai a matsayin miji, ya kuma sa kana sona nima, ko yau na mutu wlh nayi farinciki, burina kuma ya cika, ka kula mani da kanka sosai ka ji?". Ta kai karshen maganar tana ruwan hawaye sosai. Kara matseta sosai a jikinsa ya yi, da wata iriyar murya wanda bai san yana da ita ba, cikin tsananin so da kuma kaunarta ya fara magana "Hakane my Meesha, duk abin da kika faɗa gaskiya ce, kin soni tun baki san ke kanki wacece ba, na shaida hakan ni da kaina, amma fa ki sani a yanzu na fi sonki sama da yanda kike sona, ban taɓa tunanin zan ɗaga idanu na kalli wata ƴa mace ba a rayuwata sai a kanki, ranar da na fara ganin zanen sunana a kirjinki, abin ya tsaya mani a ra'ina sosai, sai dai a lokacin zuciyata a rufe ruf take, kece da kanki kika nemo key ɗinta, kika buɗeta, kika shiga cikinta, sannan kika mayar kika rufe, you are so special my Meesha". Ɗago kanta daga saman kirjin nasa ta yi, face nasa ta zubawa idanu sosai tana kallon shi, hawaye wasu suna bin wasu a saman kuncinta. Shi ma ita yake kallo, sun tsare juna da idanu babu ko kyaftawa. Almost 5 mins suna a haka, sannan ne ta matso da face nata dab da tasa, lallausan lips nasa ta sumbata, tare da kai hannu ta sakalo wuyarsa. Ganin yana bata wahala ne dan ya fita tsawo sosai, yasa ya rankwafo mata kaɗan, hakan ya bata damar samu ta fara kissing nasa cikin nutsuwa. Kara kankameta sosai ya yi, yau wani irin kiss take yi mashi tamkar babu gobe, cikin salo ya shiga mayar mata da martani shima, tamkar zasu cinye juna. Sun jima suna kissing na junansu kafin nan ya zame bakinsa daga nata, kasa kasa ya ce "Zan tafi, time ya cika, ki kula sosai my happiness". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa da ita a jikinsa. Kai tsaye palo ya nufa, har lokacin su daddy suna zaune suna ta mayar da zantuka. A tsakiyar palon ya sauketa, kunya tamkar zata shige cikin kasa, shi kuwa ko a jikinsa, sai ma kallon gwaggo da ya yi yana faɗin "Momma pray for us, zamu tafi". Ya kai karshen maganar tasa tare da nufar hanyar sauka kasa. Gabaɗaya family suka rufa mashi baya, gwaggo idanunta sun cika taf da kwallah, ƴaƴanta har guda biyu zasu tafi Daular Mutuwa, waje mafi haɗari da bata taɓa jin biyunsa ba, ji take tamkar ta dakatar da su, sai dai kuma mahaifinta yana a can, tana kaunarsa shi ma, dole su je su ɗauko mata shi, hakan yasa ta danne ta jure, Aseef sai kuka yake yi a kan shi gaskiya zai bisu, ba zai yarda su tafi su barshi ba, koma yaya ne sai dai su tafi tare. Da kyar Lion ya shawo kansa ya hakura, suka ce mashi ya zauna ya kula da gwaggo da ƴan gida. Shi kuwa Areef yana can yana haɗa kaya, sam bai sanar da Jehan da shi za su tafi ba. Bayan ya kammala haɗawa ne ya fito waje harabar gidan, a nan ya sami kowa da kowa, kai tsaye cikin mota ya fara nufa, sai da ya ajiye jakar tasa, sannan ya fito, kusa da gwaggo ya zo, cikin nustuwa ya ce mata "Momma be strong please, just pray for us, everything will going to be normal In Sha Allah". Har lokacin idanunta cike tab da kwallah, addu'a ta fara zuba masu babu kama hannun yaro, sai amin amin kowa yake amsawa da shi. Bayan ta kai karshen addu'ar ne, ba zato ba tsammani Jehan ta saki baki tana kallon jama'a, sai ji ta yi ya jawota ta faɗa jikinsa, rumgumeta sosai ya yi yana faɗin "Zan tafi my baby, ki kula mani da kanki sosai kin ji ko?". Tamkar zata yi kuka ta ce "Dama har da kai za'a tafi Daular Mutuwar ne? Shi ne baka gaya mani ba?". Kara matseta sosai ya yi a jikinsa yana faɗin "Am so so sorry, mantawa nayi". Dukan wasa ta fara kai mashi a kirjinsa tana faɗin "Ni bana son kaje, dan bana son wani abin ya sameka, ni dai ka fasa zuwa"."Da gaske baki son wani abin ya sameni?". Da sauri ta gyaɗa mashi kai "E bana son wani abin mana ya sameka, ni bana son na rabu da kai". "To shikenan, pray for us, In Sha Allah babu abin da zai same mu". Ya kai karshen maganar yana mai kara matseta sosai a jikinsa. Da alama sun mance da cewa a gaban family suke. Haka suka cigaba da zubawa juna kalaman kauna har sai da ya ishe su, while shi kuma Lion yana magana da gwaggo da kuma daddyn Rimsha. Bayan sun gama zuba kalaman love ɗin ne ya saketa tare da nufar wajen motar tasu, sam yaki yarda ya juyo su haɗa idanu da ita, dan baya son ganin kukanta, ita kuwa hawaye wani na bin wani. After some minutes Lion ya kammala maganarsa da su gwaggo, sannan ya juya ya nufi wajen motar, har Donal ya buɗe mashi kofar motar zai shiga, da gudu Rimsha ta tafi ta faɗa bayansa, tana sakin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro. Cikin kukan nata tana faɗin "Noorish ni zan bika, bazan iya bari ka tafi kai kaɗai ba, gara muje tare kawai, gara komai zai faru ya faru a kan idona, ina tare da kai, ko mutuwa zan yi, nafi son na mutu a hannunka, please Noorish". A hankali ya juyo ya rungumeta, har cikin ransa shi ma baya son rabuwa da ita, rabuwarsu babban ciwoce a gare shi, yasan zai sha wahala sosai, amma ba shi da zaɓi, dole ne ya barta a gida, dan bai san me zai je ya tarar a wajen ba. Hakika har cikin zuciyarsa yake jin wannan kuka da take rerawa, amma sam ya kasa yi mata magana, ganin haka yasa daddynta ya kariso wajen, hannu yasa ya karɓeta daga jikin Lion ɗin. Ihu take zunduma masu bana wasa ba, faɗi take yi "Daddy ka ce ya tafi da ni, bana son ya barni, bana son rabuwa da shi". Wucewa ya yi ya shiga cikin mota zuciyarsa na yi mashi zafin rabuwa da ita, shi kuma daddy wucewa da ita ya yi izuwa wajensu gwaggo. Yana zuwa gwaggo ta karɓeta suka hau rarrashi, amma ina, taki yin shiru, ihu take yi tana faɗin ita wlh zata bi mijinta........... RIMSHA MANYA MAI MIJI, TATTABARA UWAR SOYAYYA❤️😂 Da gudu Jehan ta juya ta bar wajen, ta koma cikin gida, dan ba zata iya ganin tafiyarsu ba, shi ma Aseef da sauri ya bar wajen, dan ba zai iya jurewa ba, dama da kyar Lion ya lallaɓa shi ya yi masu shiru. Mark ne ya nufi motar su Lion ɗin, dan ya ja su su tafi airport. Dai'dai zai buɗe kofar motar, Anaya ce ta zunduma ihu tana faɗin "Nashiga ukuna! Dama my da kai za'a tafi? Wlh ba zan iya jure rashinka ba! Ka dawo wlh ba zaka je ba, Rimsha fa ta ce mutuwa ake yi a can". Yau ga ikon Allah, iyaye dai suna ganin tsantsar rashin kunya ta yayan zamani, amma da yake duk jirgi ɗaya ya kwasosu, wato duk jinin turawan ne, sai ya zama ko a jikinsu, basu damu da abin da ƴaƴan nasu suke yi ba. Da gudu Anayar ta tafi wajen Mark ɗin, ta kuwa yi sa'a dai'dai lokacin ya juyo domin ya kalleta. Tana zuwa ta faɗa saman kirjinsa tana kuka, ita wlh ba zata bari ya tafi ba, ai ta ji Rimsha ta ce mutuwa ake yi a wajen. Shi dai Azharuddin Bature, wato daddynta, baki ya saki yana ganin ikon Allah, a iya saninsa bai taɓa sanin ƴarsa tana soyayya ba, kwatsam sai ya ganta da wani? Lallai kuwa ya yi sakaci ba kaɗan ba. Ita dai Brr Naurat ko a jikinta, daɗi ma ta ji na cewa duk jikokin nata sai auren family suke yi, zumunci na kara ninkuwa. Babu kunya Mark ya rungumeta sosai, kasa kasa ya fara rarrashinta. Ina ai kin sauraronsa ta yi, sai kuka take zuba mashi. Daddyn Rimsha bawan Allah, yana ganin abubuwa, shi ne dai ya sake zuwa ya kama Anayar, daddynta kam ya kasa motswa daga in da yake, duk ya yi la'asar, mamaki kamar zai kashe shi, wai ace kamar su Anaya sun san so? Shi yana matsayin daddynta sam bai san da zancen ba?! Abin ya bashi mamaki, sai kallon mummynta yake yi, ita ma shi take kallo, dan bata san komai ba............. Ni kuwa nace ta ina zaku sani? Ku ba ƴan boko ba, mummynta tana wajen aiki, kai kuma daddynta baka gari, ai kunma yi sa'a da Allah ya haɗata da Rimsha, da yanzu wani labari ake yi, da Mr Emmanuel ya jima da buɗe maku aiki, idan da rabo sai dai ku kanta da ciki ba tare da kun san ya aka yi ba, Allah ya baku amanar ƴaƴa, amma kun sake su kun tafi neman duniya, kun barwa masu aiki ragamar kula da su, tamkar ba ku aka bawa amana ba, tamkar ƴan aiki aka bawa amanarsu, ga duniyar yanzu yanda amana ta yi ƙaranci, baku san su masu aikin ya halinsu yake ba, yanda lesbian ya yawaita a duniyar nan, ku dai kawai kun sakar masu komai ba tare da dogon tunani da kuma yin aiki da faɗar Manzon Allah manzon tsira ba, wayewanku dai bai amfaneku ba! Wlh idan baku tuba ba, sai Allah ya kamaku, dan duk wani ɗa a duniyar nan, sai Allah ya tambayi iyayensa ta yanda suka kula da shi, hakki ne da kuma amana ya basu, dan haka sai ku kara zage dantse, Allah ka bamu dacewa. Daddyn yana karɓar Anayar, Mark ya yi saurin shigewa cikin motar, shi ma zuciyarsa tana yi mashi zafi da kuna, Alex ya so ya rakasu, Lion ne ya hana shi, haka motocinsu ya tashi ya bar gidan, suka nufi airport, sai dai kafin su bar gidan, sai da Lion ya ja kunnan gataman a kan kada ya bari wani ya shiga gidan ko kuma wani ya fita ba tare da ya basu izini ba. A gabaɗaya sojoji goma sha biyu da suke gidan, sojoji uku Lion ya barsu a kan su cigaba da kula da family, ya tafi da guda tara. Da yake motocin suna sharara uban gudu sosai, cikin ƙanƙanin lokaci suka isa airport ɗin, an gama shirya masu komai, dama tun jiya Lion ya shirya wasu abubuwa da zai buƙata, dan haka suna zuwa kawai suka ɗauki hanya, ba ɓata lokacin jirginsu ya ɗaga zuwa Enugu state........... TO FATAN MU DAI ALLAH YA TSARE HANYA, YA KUMA KAREKU DAGA SHARRIN QUEEN!!. A gida kuma, komawa cikin gida gabaɗaya family suka yi. A palon sama suka zauna, rarrashin Rimsha da Anaya suka hau yi, da kyar suka samu suka yi masu shiru, ita Rimsha ta tada kai da laps ɗin gwaggo, barcin wahala da kewar mijinta ya ɗauketa, ita kuma Anaya ta tada kai da laps ɗin Brr Naurat, sai tunanin Mark nata take yi, tana bin jama'ar palon da kallo, ita dama Jehan already tana barin wajen bedroom nasu ta koma, saman bed ta haye, haka ita ma ta murji kuka tamkar babu gobe, daga haka barci ya yi awon gaba da ita cike da tunanin mijinta kuma abokin diramarta, yau ina zata sanya ranta? Ya tafi ya barta, yau babu tsokana, yau babu rigima, Allah sarki, dukkansu gwanin ban tausayi. Bayan ƴan kuka sun yi shiru ne Brr Naurat ta sami damar nuna masu Abba Alex, cike da murna suka rungumi ɗan uwansu, duk da cewa daddyn Rimsha da daddyn Anaya suna kama sosai da Brr Naurat, amma Alex ya fisu kama da Turawa sosai, shi ba zaka taɓa cewa Dr Salman bane ma mahaifinsa, saboda shi da su Trump wato kakan Mark ya yi kama, da su yake muguwar kama, duk cikin ƴaƴan Brr babu mai wani irin launin idanu irin na ƴan uwanta, sai shi Alex ɗin, shi kaɗai ne mai blue eyes irin nasu Trump, sai kuma a cikin jikokinta, kanwar Anaya Zaira, idanunta ash color ne, sune kawai masu wani launin idanu ta ɓangaren Brr. Daddyn Anaya ne ya katse masu hiran da cewa "Daughter a ina kika san wannan mutumi da kika rike yanzu kina kuka?". Tana daga kwance, babu kunya ko ɗigo a idanunta, cikin tsantsar shagwaɓa ta fara magana. "Daddy Mark ne fa, kuma shi nake so, kuma shi ma yana sona, kullum ma yana yawan ce mani na gaya maka yana son kawo maka ziyara". Cikin nuna ko in kula, bai ɗauki zafi ko kaɗan ba, dan wayayyun mutane na wuce misali, sun kwankwaɗi boko, dan haka sai ya ce "To kin san shi ne? Su waye iyayensa? Kuma a ina yake?". Turo baki ta yi tana faɗin "Daddy dukka wannan shi zaka tambaya mana, ni ban san kowa nasa ba bayan mijin Rimsha da yake ogansa, shikenan". Salatin mummynta ta sanya tana faɗin "Yanzu daughter baki san iyayensa ba, baki san halinsa ba, kawai ke ƴar soyayya sai kika fara son shi ko? Wai ni yaushe ma kika girma ne? Yau ga ikon Allah, ko secondary school fa yanzu kika fara, amma kike zancen son wani?". Kuka ta saka masu tana faɗin "Daddy baka ga mummy ba, yanzu zaki fara ko mummy? To ai shi yana da kirki, kuma ai kinga idan bashi da kirki ba zai zauna a gidan nan ba, ni mummy dan Allah ki bari mana, ke komai mutun ya yi sai kin yi complain, sai ki rinƙa cewa mutun yarinya, kullum ba'a kara girma a wajenki, kullum sai naci marking sosai a school, amma sai kice bana ƙoƙari, daddy ne kawai yake cewa ina ƙoƙari, shiyasa fa yanzu zan dai'na nuna maki papers ɗina, daddy da Yah Feroz kawai zan rinƙa nunawa". Ta kai karshen maganar tare da mikewa daga kwanciyar da ta yi, tana turo baki ta sa kai zata wuce izuwa ɗakinsu Rimsha. Daddyn nata ne ya dakatar da ita ta hanyar cewa "Zo nan abinki my daughter, rabu da mummy, ni nasan yana da kirki sosai, yanzu dai zo ki gaya mani a ina yake aiki dan na binciko wanene shi?". Ba musu ta nufi daddyn nata, a jikinsa ta kwanta tana tura baki tana faɗin "Daddy kai'na yana yi mani ciwo, ni ba zan iya jure Mark ya je wannan waje ba". Dafa kan nata ya yi tare da fara ce mata sorry, Zaira ƴar auta tana zaune shiru kusa da daddyn Jelly, baiwar Allah sam bata da rigima, tamkar ba ƴar auta bace ita, Anayar da take babba ta fita yawan rigima da shagwaɓa. Brr Naurat ce ta katse masu zancen da cewa "Mark dai jika ne ga babban yayanmu, haka jika yake a wajena kamar yanda kuke jikokina, so bana tunanin mutumin banza ne, tunda har yana tare da su Saif, to a gaskiya shi ɗin ba mutumin banza bane, a gabaɗaya su Saif babu na banza a cikinsu, kuma sai hali yazo ɗaya ake abota, dan haka ina kyautata mashi zato, kuma ina farinciki da Allah yasa jinin babban yayana zai auri nawa jinin, duk da sun gujeni, sun koreni a cikinsu, to ga shi Allah zai sake haɗa ni zumunci da su ta kan jikokinmu kuma, mu zamu aurawa Mark Anaya in har tana son shi yana sonta, shikenan sai ya karɓi musulci ayi masu aure". Kusan a tare dayawa daga cikin jama'ar palon suka sauke nauyayyar ajiyar zuciya, daddyn Anayar ya ji daɗi sosai, ita kuwa Anaya cool murmushi ta saki tana faɗin "Good ƴar tsohuwa that's why i like you, ashe gwara da baki mutu bama, ga shi kin yi amfani". Ita dai mummyn Rimsha baiwar Allah, duk kunya ya rufeta, kunyar Brr Naurat ma take ji sosai, ga su Abban Imran dukka surakananta ne, hakan yasa duk ta takure waje guda,. A duk cikin palo ita da aunty matar Abbi ne kawai suka san menene kunya, sune kawai masu kunya, ita ma Ammien su Imran ba kunya ke gareta ba, kowa yasan kabilar igbo dai ba kunya ce da su ba. Duk Anaya ta san mummyn Rimsha ta ji wani irin kunya, ta kuma ga laifin mummyn Anayar sosai, dan kome Anaya zata yi a yanzu, to laifin mummynta ne, saboda Anaya yarinya ce, kuruciya na a kanta sosai, tun farko ya kamata mummyn nata ta koya mata kunya, kamun kai, kamala, da dai sauransu, amma ji yanda Anaya take magana abu sam babu tsari, iyayenta ne a cike a cikin palon nan, amma ita babu ruwanta, tamkar da sa'aninta ko kannanta or kawayenta take hira, abin sam bai yi wa mummyn Rimsha daɗi ba, bayan ita da Aunty kowa a cikin palon babu wanda ya ga aibin abin da Anayar ta yi, shi ma daddyn Rimshar bai ga aibin hakan ba, dan a cewarsa, ai yarinta ce kawai tasa Anayar yin hakan, idan ta girma zata dai'na........Babban magana girma kuma na nawa?. Haka suka cigaba da zuba hirarsu har zuwa rana ta ɗago, Anayar ma tuni ta yi barci a kwance a saman laps na daddynta, sai sauke nauyayyar ajiyar zuciya suke yi a cikin barci, sun sha kuka sun ƙoshi, ita ma Jehan barci ne ya ɗauketa, ta ci kuka kamar ba gobe. After 2 days. A cikin wannan kwana biyu da suka wuce, abubuwa da dama sun faru, bari mu fara da ɓangaren su Lion, sun isa Enugu state lafiya, kamar yanda Ammie ta basu address ɗin gidansu, haka suka yi amfani da shi, sai dai ko da suka je, gidan babu kowa, gate ɗin gidan ma a rufe yake ruf, da alama an ɗauki lokaci babu mutane a cikin gidan. Zubawa gidan idanu sosai Lion ya yi, kai daga ganin gidan kasan ba iya kuɗin nema ne kawai ya gina shi ba, wannan uban kuɗi da aka narka wajen gina gidan, ai dole sai da kuɗin TSAFI, dama already Ammien ta gaya masu Queen bata zama a gidan, bata nan a cikin gidan, kuma gidan babu kowa, dan haka ko sun je, wahala za su sha, shi kuma Lion abin da kuka sani ne, a duk lokacin da ake magana, to yana nutsuwa ne ya saurari maganar da kyau, dan tattare zancen mai maganar a cikin ƙwaƙwalwarsa yake yi, saboda samun mafita, yana aiki ne da kaifin basirarsa sosai da sosai, a lokacin da Ammien take bada labarin Daular Mutuwa, a lokacin ya nutsu sosai yana jinta, a maganarta ta ce a baya tana shiga har cikin Daular Mutuwar, which means da akwai hanyar da zai sadaka da Daular Mutuwa daga ta cikin gidan kenan, kuma dama ai da kamar wuya ace babu wata hanya daga cikin gidan Queen da zai sadaka da Daular, tun da ita ce shugaban Daular, to dole akwai hanyoyi ma ba hanya ɗaya ba ta cikin gidanta, hakan tasa ya ce da Ammien ta bashi address na gidan Queen ɗin, kun ji masu hikima da basira, ita kuma Ammien sam bata kawo cewa da haka zai yi amfani ba, dan ita bata taɓa shiga Daular Mutuwa daga ta cikin gidansu ba, ta waje take shiga, Queen ta ɓoye masu hanyar cikin gidan, hanyar sirrice wanda babu wanda ta yarda ya sani, sai ita kaɗanta. Duk sojojin sun tsaya suna jiran su ji me Lion ɗin zai ce, basu ankara ba sai ganinsa suka yi ya yi bismilah ya kama gate ɗin gidan ya haye, dan ba mutane a cikin gidan. Wani abin da basu sani ba shi ne, tun da suka baro garin Kaduna a kan idanun Queen suke tafiya, har suka iso Enugu, duk motsinsu tana ganinsu, ta barsu ne kawai su iso, dan a cewarta a cikin satin nan, suna da liyafa a gidan nata, dodan tsafinsu na bukatar jini sosai, akwai wasu sabbin ma'aikata da suka karu, dama idan baku manta ba, duk waɗan da suka jima a Daular Mutuwa, in dai Queen ta kasa kashe su, to tana mayar da su mutanenta ne, sai ta juyar da su izuwa irinsu barbushi, to akwai wasu mutane guda biyu ciki har da Mustapha da wani, a satin nan za'ayi liyafar mayar da su mukarraban Queen, wato su zama magicians suma. BABBAR MAGANA, shi ne yasa Queen ɗin ta bar su Lion ɗin su iso kawai ta bawa dodan tsafinsu su, asha jininsu a ji daɗin yin liyafa da kyau, har shiga cikin gidanta da suka yi a yanzu, duk tana kallonsu, dariya ma suke bata. Su kuwa bayan sun dira a cikin gidan, kai tsaye kofar da zata sadasu da babbar palon gidan Lion ya nema, babu tsoro ko ɗarɗar a tattare da shi, kai tsaye ya shige cikin gidan, kamar gidansa ne, yana shiga har da kunna wutar palon, dan ya gani ko suna aiki, sai dai a ganin sojojinsa ne suke ganin ya kunna wutar ne dan yaga ko suna aiki, shi kuma akwai dalilin da ya sanya ya kunna wutar, kunsan baya abu haka kawai, sai da dalili. Yana kunna wutar ya nufi wata ɗaki da take fuskantar kugu maso gabas, tsohowar ɗaki ce sosai, dan da alama a kaf cikin gidan, ɗakin ce kawai ba'a buɗe kofarta, saboda kofar ta kama sosai. Har lokacin idanun Queen na'a kansu, ta kuma cire duk wasu matakan tsaro na koforin dake gidanta wanda zai sadasu da cikin Daular Mutuwar, ma'ana ta buɗe masu hanya kenan, jira kawai take yi su shigo. Su kuma bayin Allah, sam basu sani ba, babu wanda ya kawo wa ransa cewa Queen ɗin tana kallonsa, ɗan gara Lion ɗin ma, shi dama yasan matsafan nan babu abin da ba za su iya yi ba. Yana isa wajen kofar, babu tsoro bai yi wata wata ba ya kai hannu ya murɗa handle ɗin kofar, nan take kofar ta buɗu, ganin ta buɗe ne yasa ya gane cewa lallai akwai wata a kasa, dan wannan kofa ta jima a rufe, bai kamata ace daga ya ɗan taɓata ta buɗe ba, dole da akwai wata a kasa, ga shi kuma gidan babu mutane ma, tun daga nan ya fara zargin wani abin a ransa, sai dai bai nunawa sojojinsa da alamar matsala ba, saboda kada ya sare masu gwiwa, ita kuma Queen bata taɓa tunanin cire makullan kofofin da ta yi zai iya sanya Lion ya fara zargi ba, bata kawo haka a ranta ba ,dan bata san kaifin basirarsa da kwakwalwarsa ba, sai dai hakika ta jinjinawa jarumtarsa, musamman yanda ya shigo mata gida kai tsaye, ya kuma nufi wannan kofa babu ko tsoro a ransa, yana acting tamkar shi ya gina mata gidan.......... (ni kuwa na ce in dai lion ne fin haka ma zai yi, shi gida nawa ma ya shiga ya nuna masu izza tamkar shi ya gina masu gidan? ya kuma aikata abin da zai aikata ya fito lafiya lou, ya shiga gidan Abba tamkar gidansa, ya je ya ɗauki Akila, ya kuma ɗaura mata aure da Aseef, sannan ya taka kafarsa har kasar Russia, ya je ya ɗauko Brr Naurat, su ma ya shiga gidansu tamkar shi ya gina masu, har ma da ɗaure gabadaya ƴan gidan ya yi, haka kuma ya fito kasar Russia lafiya lou, saboda tsantsar karfin hali da nuna isa, haka ya shiga gidansu Rimsha kamar gidansa, ya ɗaukota ya fito, ai shi Lion dama dai'dai yake da kowa, ko ya kuka ce READERS? Yanzu kuma ga shi a gidan Queen of Daular Mutuwa, kamar gidansa ya shige😂 Queen taga iko da nuna isa😂) Cikin ɗakin suka shiga, gabaɗaya cikin ɗakin babu komai, wayam yake, sai lallausan carpet na alfarma dake sumfuɗe a cikinta. Zuba masu shegun idanunta Queen ɗin ta yi ta cikin ruwan tsafinta dake kwance a tsakiyar faɗarta kamar pool, sai kallonsu take yi, tana son ganin gudun ruwansu. Areef dai yana goye da uban jaka a bayansa, sai Allah yasan me ya lodo a cikinta!. Sai bin ɗakin da kallo sojojin suke yi. Wani irin sihirtatcen kamshi ne ya fara tashi a cikin ɗakin, shi dai Lion har cikin ransa bai yarda da wannan kamshi ba, dan haka sai ya ce da sojojinsa su sanya face mask a face nasu dan kada su shaki kamshin. Bai kai ga rufe baki ba, nan take sojojin nasa suka fara zubewa kasa kamar gawarwaki, dama wannan kamshi wani tuggune da Queen ɗin ta haɗa masu, ta ha kance kawai zata ɗaukesu izuwa cikin Daular Mutuwar. Lion kafin ya yi wani yunkuri shima sai ya ji gabaɗaya jijiyoyin jikinsa sun tsaya, nan take ya ji tamkar an sare mashi ƙafafuwansa, dole shi ma ya zube kasa, dan already dukkansu sun shaki wannan kamshin turaren. Areef yana ƙoƙarin yin kan Lion ɗin, shima sai ji ya yi tamkar an raba kafafunsa da jikinsa ne, nan take ya zube kasa, duk suka zama kamar gawarwaki, ga dai idanuwansu a buɗe, amma sam jikinsu babu karfi, babu mai iya motsa ko da ɗan yatsansa. Haka suka cigaba da shaƙar wannan daddaɗar hamshin duk wasu gaɓɓai na jikinsu suna mutuwa, har idanunsu ma ya rufe ruf, kamar babu rai a tattare da su. An ɗauki tsawon lokaci suna a haka, har sai da yamma ta yi, rana ta faɗi, sannan ne Queen ɗin ta fara ɗaukar mataki a kansu. Wasu zaratan mazaje jarumai masu ji da lafiya da karfi Queen ɗin ta aiko, zu ashirin cif, haka ta aikosu aka kwashi su Lion ɗin gabaɗaya, ɗakin dai babu wata kofa bayan wanda su Lion suka bi suka shigo, daga ta sama waɗan nan zaratan maza suka ɓullo, haka kuma da suka ɗauki su Lion ɗin, suka bi da su ta saman suka fita, ɓacewa suke yi ɓat........ KAI QUEEN SHEGIYA CE, TA WUCI TUNANIN MAI TUNANI TUNKARARTA SAI AN SHIRYA. Kai tsaye sai cikin Daular Mutuwar aka wuce da su Lion, basu san ta hanyar da aka bi da su ba, dan Daular Mutuwa fa a yanzu bata da hanyar shiga sam sam. BABBAR MAGANA TASHIN HANKALI DA BA'A SAKA MASHI DATE, SU LION ZA SU FITO KUWA?. A takaice dai a wani killatatcen waje Queen tasa suka kulle su Lion ɗin, waje ne mai cike da abubuwan ban tsoro da juya kwakwale, ashe ita Rimsha a cikin kaso ɗari ko kaso ɗaya na bala'in da kuma ɓangarorin dake a cikin Daular Mutuwar bata gani ba, akwai abubuwa da dama sosai. Gabaɗaya su Lion ɗin an kasasu ɗakuna daban daban, ba'a haɗasu waje guda ba, da alama Queen ta fi tsanar Lion a cikin tawagar, shi wani waje na daban mai cike da tsaro na bala'i ta kai shi, babu wani abin da idanu zai iya gani a wajen, saboda tsananin duhu dake a cikin ɗakin, ta sanya sarka ta ɗaure shi, ko motsi baya iya yi. Su kuma sauran sojojin ɗakunan da aka kai'su da akwai haske, suna iya ganin komai, kuma bata ɗaure su ba, kawai an zubasu a saman tiles ne aka barsu. Tsawon kwana biyu suna a sume, Queen kuwa tana ta harkar gabanta, bata bi ta kansu ba tukun nan. A can gida kuwa, sai adduo'i ake ta yi masu babu kama hannun yaro, kowa hankalinsa a tsananin tashe sosai, Rimsha kam har da zazzaɓi take fama da shi, ko sallar dare bata iya tashi ta yi, saboda rashin lafiya, abin kamar ba lafiya ba, sam ta kasa yi wa Noorish ɗin nata addu'a, ta zama tamkar kurma, ciwon nata ma akwai ayar tambaya a kansa, dan fa ko kallonta mutun ya yi sai ta daka mashi tsawa, ta zama tamkar ba ita ba........ Wannan shi ne abin da ya faru a cikin kwanaki biyun da suka wuce, dan haka mu koma kan story. Yau shi ne kwana na uku na kasancewar su Lion a Daular Mutuwa, sai a yau kuma Queen ta waiwayesu, a in da ta fara yi masu ɗauki ɗai'ɗai tana bawa dodan tsafinta, wayewar garin yau, ta kashe sojoji biyu daga cikinsu, kafin ta kashe su kuma, sai da ta dawo masu da hankulansu jikinsu cif, a kan idanunsu tasa aka ɗauresu, suna ji suna gani ta sanya aka fasa cikinsu, ta ɗebi abin da zata ɗeba, jininsu kuma kamar yanda kuka sani ne, an kaiwa dodan tsafi, sauran sassan jikinsu kuma tasa aka wuce da shi izuwa wajen da suke kulla harkokinsu da sauran gidajen matsafa dake a duniya, dan ta sayar masu da abubuwan da suke buƙata daga ciki....... Innallilahi wa Inna ilahirrajiun, ya ilahi ya lillahi, wannan musifa dame ta yi kama?. Mutun na uku a yanzu shi ne a kan layi da za'a kashe, ba kowa bane kuma face Areef na Jehan, shi Lion ma sai Allah ne kaɗai yasan halin da yake a ciki, shin yana raye ne ko ya mutu?. Ɗakin da Areef ɗin yake kwance yana sume suka nufa, babu Queen ɗin a cikinsu, waɗan nan zaratan kyawawan matasan igbo ɗin ne, sune masu aiwatar da komai, ita Queen idan an gama fasa cikin mutun, da tsafinta take ɗaukar abin da take so dan gane da sassan jikin wanda aka kashe, a takaice dai, ita bata fitowa, komai tana daga cikin faɗarta take aiwatarwa. Kamar yanda suka kwantar da Areef ɗin tun ranar da suka kawo su, haka suka zo suka same shi, bawan Allah, ko motsawa bai yi ba. Turo wannan gadon da suke yanka mutun a kai ɗin suka yi izuwa tsakiyar ɗakin. Zaratan maza biyu ne suka ɗauko Areef ɗin, suka kwantar da shi flat a saman bed ɗin, sannan suka zura hannayensa a cikin lock na bed ɗin, suka rufe, ta yanda ko an dawo mashi da hankalinsa, ba zai iya yin yunkurin komai ba, haka kafafunsa ma suka zurata a cikin lock suka datse gam. Sannan ɗaya daga cikinsu ya fito da wata sharɓeɓiyar wuka, sai kyalli take yi, har wani ɗaukar idanu take yi, ga kaifin bala'i, dama su shidda ne zaratan mazan, da mai rike da wukar sun haɗu bakwai dai'dai kenan. Tsayuwa suka yi shiru a kan Areef ɗin suna jiran Queen ta dawo mashi da tunaninsa, dan bakar zalinci da mugunta, sai mutun yana cikin hayyacinsa ma suke yin duk abin da za su yi, yana ji yana gani babu yadda ya iya da su, a da can baya, sai sun gusarwa da mutun hankali suke yanka shi, yanzu kuma tun bayan fitar su Rimsha suka kawo sabbin tsare tsare da wasu abubuwa na tsubbace tsubbacensu. Cikin ƴan sakannin da basu fi 30 ba, sai ga Areef ɗin ya buɗe ash eyes nasa, tamkar wanda aka tasa daga barci, idanuwansa sun kumbura sosai, saboda kwana biyu yana sume. Dishi dishi ya fara gani, saman ɗakin yake ta kallo, su kuwa waɗan nan maza, suna tsaye a kansa, suna jiran ya gama dawowa dai'dai su yanka shi, dukkansu kyawawan gaske ne, farare tas da su, sai dai shi mai ruke da wukar nan, haskensa na daban ne, ba hasken Nigeria ba ne, haka zalika kyansa na daban ne, ya sanya wata bakar handkerchief ya ɗaure daga hancinsa izuwa bakinsa, dan kada jini ta yi mashi fallatse, kuma yafi gabaɗaya matasan wajen tsawo, ya fisu cikar halitta ta kasance cikakken namiji. A hankali kallon Areef ɗin ta washe. Ya sha ruwan mamakin ganinsa a cikin wannan ɗakin, a hankali ya fara juya kallonsa, ya fara bin ɗakin da kallo. Cak ya tsayar da idanuwansa a kan waɗan nan matasan, da mamaki yake ganinsu, ya san dai sojojin Lion ba haka suke ba, fararen Turawa ne, waɗan nan kuma hasken Nigeria ke garesu, bakake ne ma a idanun Areef ɗin. To suwaye su kuma? Ya tambayi kansa da kansa. Yunkurawa ya yi zai mike, sai ya ji ko motsi ba zai iya yi ba, kokarin juyar da kansa ya yi dan ya kalli abin da ya hana shi tashi, ina shi ma kan nasa ba zata iya motsawa daga in da suka kwantar da shi ba, abin ba ƙaramin ɗaure mashi kai ya yi ba, ya yi yunkurin yin magana, nan ma abin ya ci tura, tamkar an ɗaure mashi harshensa ne, ya gagara ambatar sunan Allah, ga shi yana son ya tambayi mutanen su waye su, amma ba hali, Queen ta rufe mashi baki. Sake juya idanuwansa ya yi, dan idanun ne kawai suke motsawa a gabaɗaya jikinsa, sake fara bin waɗan nan zaratan mazan da kallo ya yi. Cak ya tsayar da kallonsa a kan wanda yake ruke da wukar, sosai ya zaro idanuwansa waje yana kallon matashin, shi ma matashin shi yake kallo. A dai'dai wannan lokaci Queen ta turo masu da sakon ta bada umarni a datse kan Areef ɗin. Hannu wanda yake rufe da wukar ya kai saman face nasa, a hankali ya janye wannan handkerchief ɗin daga face nasa, ya buɗe fuskar tasa kenan, sannan ya ɗaga wukar sama dan ya aiwatar da umarnin Queen. Tsabar shiga tashin hankali da ruɗu Areef bai san lokaci da waje baki da iya karfinsa ba, nan take harshensa ta sake, da iya karfinsa na karshe ya furta sunan Aseef, ya yi maganar yana kallon matashin dake ruke da wukar yana ƙoƙarin cire mashi kai. Ba shakka Aseef ne, ko mutuwa ya yi ya dawo, ba zai taɓa mance Aseef ba, idan zai kasa gane kowa a duniya, to banda TRIPLETS nasa, meya kawo Aseef Daular Mutuwa? Yanzu kenan Aseef kashe mutane yake yi? Me haɗinsa da su Queen? Menene gaskiya? Shin ma wanenen Aseef ɗin?!!! Idan baku manta ba Josephine sun canza ɗaya daga cikin TRIPLETS, kuma Lion yana zargin Aseef ne, hakan na nufin Aseef ɗin ne da gaske? Kenan shi ba mutun bane? Kada fa ku manta a gida suka baro shi yana kukan rabuwa da su! Kenan dama Aseef zai iya kashe TRIPLETS nasa? Ko dai yaya ne, wai wanenen shi!!!!!!!!!!!!!!, Ko dai ba shi bane? Amma dai Areef ba zai taɓa iya kasa gane Aseef ba gaskiya, tun da ya ambaci sunansa, to ba makawa shi ɗin ne!!!! Tirkashi, yau ake yinta, wata sabuwar cakwakiya mai ƙulle kai🧠. Na barku lafiya, har kullum taku ce PRINCESS TEEMA ta amana mai salon ban mamaki da ruɗa kwakwalwa!. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 23/4/2024 E13 "Aseef what are you doing here?". Ya yi maganar cikin tsananin fitar hayyaci, da ruɗu, dan ko a mafarki bai taɓa tunanin zai ga Aseef a Daular Mutuwa ba, kuma a nan ɗin ma yana ƙoƙarin kashe shi, wlh zai iya rantsuwa har ga Allah wannan Aseef ne ba gizo ba. Shiru Aseef ɗin ya yi bai amsa mashi ba, sai ma sanya hannu da ya yi ya mayar da handkerchief ɗin face nasa, sannan ya ɗaga wukar da gaske zai datse mashi wuyar, cikin kwanciyar hankali da kwarin gwiwa yake aikwatar da komai nasa, ga kuma tsantsar nutsuwa a tattare da shi, ba zaka taɓa cewa Heartbeat na TRIPLETS da ya kasance rago mai shagwaɓar tsiya bane, a nan ya zama mai taurin zuciya, mara imani da tausayi. "Aseef before you kill me, talk to me fist pls, duk da nasan cewa kai ne, amma ka kara share mani tantama kafin ka yi abin da zaka yi". In a cool voice ya ce "Yeah Areef, it's me, what's next that you want me to tell you before the time of your death". Cikin kwarin gwiwa, jarumta, da nuna isa ya yi maganar, sam babu shagwaɓa ko ɗigo a muryarsa. Tashin hankali, ai shi Areef ganin Aseef ɗin da kuma tabbatarwa da shi ɗin ne yafi kashe shi ɗin da za'ayi ɗaga mashi hankali, yanzu dai da gaske Aseef ɗin me babu tantama, kuma da kansa zai kashesu? Innallilahi wa inna ilahirrajiun, ya ilali ya lillahi. Godiya ga Allah Areef ɗin ya fara yi da Allah yasa shi ne ya kalli Aseef ɗin ba Lion ba, da Lion ne zuciyarsa zata buga, yanda yake tsananin kaunar Aseef ɗin fiye da kansa, sai dai bai san cewa Lion ɗin ma yana a kan hanya ba. "Babu wani abin kuma da nake son sake sani face na ce maka kada ka cutar da Lion, kome zaka yi mana ni ka yi mani ni kaɗai, please ka bar Lion ya huta, ya wahala a kanmu ɗan tahalikin nan, tun muna yara, a kanmu ya koyi faɗa, a kanmu ya koyi zafin zuciya, ka fi kowa sanin cewa saboda kai Lion ya koyi faɗa, a primary school shi yake tare mana faɗa, komai muka kwaso shi yake tare mana, ya tsaya mana a kan maraicinmu na rashin uwa, ya bamu farinciki fiye da kansa, ya kula da mu fiye da rayuwarsa, burinsa kawai ace muna yin yanda muke so, please Aseef ka kashe iya ni kaɗai, ka bar Lion, ka barshi ya huta, kada ka ci amanarsa". Ya kai karshen maganar idanunsa sun yi jajir tamkar jini. Cool murmushi Aseef ɗin ya saki, daga bisani kuma ya ɗaure fuska tamau, cikin muryar shagwaɓa tamkar yanda yake magana a gida ya fara magana yana turo baki "I can't kill you my Areef, i can't do anything to you my TRIPLETS, ku ne ni, kune bugawar zuciyata, kune farincikina, haka zalika ba zan iya bari ko kuda ya taɓaku ba, kamar yanda Lion ya tsaya mana tun muna yara har izuwa yanzu, bai yarda ko kuda ya taɓamu a rashin son ranmu ba, to nima a yanzu Allah ya ara mani lokaci da dama na taimake ku, na ceceku my TRIPLETS!" Ya kai karshen maganar tare da juya wukar hannun nasa ya datse kan ɗaya daga cikin matasan dake tsaye a gefe da gefensa, nan take matashin ya zube kasa bai shura ba, sai jini dake malala a kasa kamar an buɗe bakin fanfo. Kafin sauran su yi wani yunkuri, ya sake datse kan ɗaya. Cikin zafin nama sauran suka yi kansa, ita kuwa Queen dake kallonsu, a zabure ta mike tsaye, dan bata taɓa tunanin cewa ba mutuminta dake yanka mutane bane, tambayar kanta take yi ina wancan mutumin nata mai yanka mutanen kenan? Tashin hankali, wato gaba ma da gabanta, wai aljani ya taka wuta, Queen ta iya bibiyar su Lion tun da suka baro Kaduna, har suka shiga Enugu, har izuwa Daular Mutuwa, amma bata iya gane ya aka yi mutuminta mai datse kan mutane ya sauya ba, bata iya gane shi ɗin ina yake ba, bata iya bibiyar Aseef ba, shin ta yaya aka yi Aseef ma har ya shigo cikin Daular Mutuwar ba tare da ta sani ba? Ya aka yi har ya kashe ainahin mutuminta mai kashe mutane ba tare da saninta ba? Ya akayi har ya shiga cikin tawagar mutanenta ba tare da saninta ba? Wanenen shi ɗin to? Wai wanenene Aseef?!!!!!!. Idan kuwa da gaske Aseef ya zo taimaka masu ne, to kenan hakan yana nufin da wata manufa na daban Josephine ta sanya shi a cikinsu? Ke nan ba ta canza ɗayan TRIPLET'S ɗin bane dan ta cutar da su? Ko dai yaya abin yake ne? Amma to tun farko ma menene makasudin canza TRIPLETS ɗin? Manene yasa suka kawo Aseef suka ɗauki na ainahi? Ina na ainahin yake? Shi Aseef ɗin su waye iyayensa? Dole dai akwai wani dalili mai mugu mugun karfi na yin hakan, akwai babbar cakwakiya da kulla kulla a wannan lamarin, wanene mai gaskiya a cikinsu Josephine? Alkalamin PRINCESS TEEMA ce kawai zai warware maku gaskiya, dan haka ku kasance da ni taku PRINCESS TEEMA mai abin ban mamaki. Babbar magana, a tsananin razane Queen ta mike daga saman kujerar mulkin nata, sai dai kafin ta yi yunkurin yi wa mutanenta dake faɗa da Aseef ɗin wani tsafi, tuni Aseef ɗin ya kashe su dukka, babu imani babu tausayi ko ɗigo a tattare da shi, haka ya yi masu kisan kiyashi, tamkar ba Heartbeat namu ba. Babban abin da ya girgizata ya kuma jijjiga tunaninta, bai wuce yanda ta ga Aseef ɗin ya buɗe Areef daga lock da suka sanya shi ba, ita dai tasan cewa bayan ita babu wanda ya isa ya buɗe waɗan nan locks ɗin, to ya aka yi Aseef ya buɗe shi? Kuma dai da tsafi ake buɗewa, hakan na nufin shima yana da tsafi kenan?. Ta saki baki tana mamaki, bata ankara ba sai gani ta yi dukkansu biyun sun miƙe tsaye, Areef sai tambaya yake yi ina Aseef ya samu karfi haka? Shi kuma Aseef ɗin sai tambayarsa yake yi ina Lion nasu yake? Wannan shi ne cakwakiya....... JAMA'A NI KAI'NA INA SON SANIN WANENE ASEEF FA? DAN A GASKIYA WANNAN ABIN AKWAI ƊAURE KAI. Ganin Areef ɗin zai ɓata masu lokaci wajen tambayarsa wanene shi, sai ya riko hannunsa tare da jansa suka fita, har sun fita ɗakin, sai kuma Aseef ɗin ya dawo ya ɗauki jakar da Areef ya zo da ita. Ita kuwa Queen sai kallonsu take yi ta cikin ruwan tsafin, bata ɗaga hankalinta dan sun fito daga ɗakin ba, dan a cewarta, ai tana da zararan mukarrabanta da za su yi gunduwa gunduwa da su, su cinye namarsu ɗanya, dan haka sam bata wani damu ba, bata san cewa abin ba haka yake ba, ko a tsafin ma ai akwai iyayenka wajen yin shi, gaba ne da gabanta, ita har yanzu a iya Africa take tsafinta, su kuma tsafinsu bugawa suke yi da manyan kasashen duniya masu faɗa aji, su ba kananan kwari irinta bane, iyayenta ne a iskanci da bala'i. E KAM BABU SHAKKA IYAYENTA NE, GA ALAMA TA FARKO, ASEEF YA IYA SHIGOWA HAR YA KASHE MUTUMINTA MAI YANKA MUTANE, YA KUMA SHIGA CIKIN JAMA'ARTA DUK BATA IYA GANEWA BA, BABBAN ABIN TAMBAYAR MA SHI NE, TA YAYA YA SHIGO CIKIN DAULAR?. Suna fitowa harabar wajen, wasu jiga jigan maza masu kama da su barbushi ne suka kewayesu, zaratan maza ne majiya karfin gaske, yanayin nunfashinsu ma kawai abin tsoro ne, dan suna numfashi yana fitar da hayaki tamkar waɗan da aka ɗaurasu a saman garwashin wuta mai tsananin zafi, wasu jibga jibga da su, ga gashin kansu kamar jijiyar bishiya, a tsai tsai kamar kawon shaiɗan, idanunsu kawai abin tsoro ne, tamkar ba idanun bil adama ba, wasu jajir dawu tamkar sun zuwa jini ne a ciki, hannunsu kawai abin kallo ne, wasu dama dama da su, kirjin nan nasu a tsaye tamkar bishiyar kuka, sam yanayin halittarsu ya fita daban da ta mutane, kai daga gani kasan da tsafi suke amfani, da tsafi suka mayar da halittarsu hakan, jikkunansu babu riga, sai dai ta kasa ne kawai suka rufe, sun kasance su goma ne cif. Hakika Areef ya tsorata da ganin waɗan nan halittu, ya girgiza na ganin munin halittarsu, sai dai bai sare ba, bai ji sanyin gwiwa ba, dan hukumar C.I.A idan ba gani suka yi an kashe su ba, to wlh basu taɓa tsarewa a kan abu, komai gani suke yi za su iya, haka Areef yake ganin kamar zai iya faɗa da su, yana ganin mutane tamkar gunguma gungumar kumaka da aka sassaka da dafaffiyar karfe, amma hakan bai sa ya ji ba zai iya yakarsu ba. A tare waɗan nan gunguma gungumar mutane suka nufesu, suna taku kasa na amsawa da dib, dib, dib. Su kuwa suna tsaye suna kare masu kallo. Sai da suka isa wajen ne Aseef ya ciro da wata sharɓeɓiyar wuka daga kugunsa, shi kuma Areef ya yi bismillah dan su fara yaki, sai kuma me? Yana ambatar wannan bismillahi gabaɗaya dakarun Queen ɗin suka ja baya da su, tamkar waɗan da aka janye da tsafi. Ita dai Queen tana cikin faɗarta har wa yau, sai kallon abin al'ajabi da mamaki take yi, wani irin zaro shegun idanun tan nan ta yi na ganin yanda mukarraban nata suka ja baya daga tunkarar su Areef ɗin, irin wannan jan baya kamar an janyesu haka? Abin ya ɗaure mata kai. Amma bata sare ba, sai ta sake yin amfani da tsafinta ta sake turasu suka tunkari su Areef ɗin. A karo na biyuma bismillahi Areef ya yi, dan su TRIPLETS komai za su aikata, to fa da bismillah suke farawa, sunan Allah shi ne a farko kafin su yi komai, kun tuna lokacin da Lion zai shiga gidan Queen? Sai da ya yi bismillah, ko zama za su yi a saman sofa, sai sun yi bismillah, ta yanda koda akwai wani abin da aka kullah masu, to wannan sunan Allah da suka kira, zai zama sanadiyar warwarewar komai, idan suka yi bismillah za su zauna a waje, to duk wasu shaiɗanun dake zaune a wajen za su watse, kowa zai kama kansa, hakan zai sa da wuya su zauna a waje kuma kuga sun yi faɗa ko makamancinsa, saboda da sunan Allah suka fara zama, babu wani shaiɗani a wajen da zai iya zugasu su yi faɗa, shiyasa kuke ganin kullum cikin Kaunar juna suke, babu faɗa babu kyaran juna. A karo na biyu da ya yi bismillah ma, a dubu ɗari jakarun suka sake ja da baya, abin ya yi matuƙar girgiza Queen ba kaɗan ba, dan haka sai ta miƙe tsaye, cikin nuna isa da izza ta sanya hannu a saman ruwan tsafin nata, tare kuma da fara surutansu irin na matsafa, nan take ruwan nata ya fara juyawa kamar fanka. Shi ma Aseef ya yi mamakin ganin yadda mukarraban Queen ɗin suka kasa iso su, sai dai bai nuna ba, kuma already shi ma kun san musulmi ne, akwai dai wata a kasa, amma ban da haka, duk wata addu'ar da Areef zai yi, shima zai iya yinta, so dama kunsan already shi bai yi nisa a karatun addini bane, bai san ma'anonin wasu adduo'i ba, ya dai iya karantawa ne kawai, ita kanta bismillahi bai san me ma'anar yinta ba, ya dai san sunan Allah ne. Wannan surutai da Queen take yi ba komai bane face karawa jama'ar tata karfi, da kuma dakiya. Haka kuwa aka yi, bayan ta gama surutanta, sai ta sake turasu ga su Areef ɗin, bayin Allan, su kuma suna tsaye gam, babu alamar tsoro ko sarewa a tattare da su, sai ma kwarin gwiwar da suka sake ji mai karfi yana kara ratsasu. Da wani irin mahaukacin zafi mukarraban Queen ɗin suka nufosu a karo na uku, dafe kai Areef ya yi yana faɗin "La ilahaillah anta subahanaka inni kuntunminazzalumin, wai ku idan za ku zo mu kashe juna kawai kuzo mana, amma saboda walaƙanci sai ku tinkaro mu, sai mun shirya kuma ku sake ja da baya, wannan abin fa ya fara kona mani rai, wani irin abu ne wannan? Ku yi maza ku karisu in ma kashe juna ne sai ayi komai a wuce wajen, ban son jan rai, zuciyata ta fara hasala".......faka faka kenan. Bai kai karshen surutan nashi ba ya ji an taɓa shi, da sauri ya ɗago kansa, Aseef ne ya taɓa shi, yana ɗagowa ya ce mashi "To ai sai ka dai'na surutun haka ko? Mutanen da sun ɓace kamar haske, kai katsaya sai wani zuba magana kake yi kai kaɗai". Zaro idanu ya yi yana faɗin "Ban gane sun ɓace ba? Ina kuma suka je? Ba kashe mu suka zo yi ba wai? Yaushe suka ɓace?". Duk waɗan nan tambayoyi ya jerosu ne da mamaki a saman face nasa. Shiru Aseef ɗin ya yi na ƴan sakanni kafin ya ce "Oho time da ka fara surutanka mana, ni muje hai". Shiru Areef ɗin ma ya yi yana tunanin to a kan me za su ɓace kuma?. Bai san cewa wannan kalma ta lailahaillah anta subahanaka inni kuntuminazzalumin da ya faɗa bane yasa gabaɗaya suka yi wani irin ɓacewa ɓat, ita kanta Queen ɗin sai da kalmar ta sanyata ta yi wani irin baya baya ta faɗa a sama kujerarta na mulkin, karo na farko a rayuwarta da har wani jiri jiri take gani, kanta har wani sara mata yake yi........... My peoples, wannan shi ne banbancin duk wata shirka da kuma sunan Allah, idan mutun zai yi shirka, ko wani saɓon Allah, to ba makawa sai ya ɗauki lokaci yana haɗa abubuwa, sai ya sha wahala kafin ma ya iya aiwatarwa, kuma ko da ya yi bata taɓa ɗorewa, misali, mushiriki, sai ya haɗa abubuwa da dama ya sha bakar wahala kafin ya iya yin tsafin nan nasa, ya azabtar da kansa ta hanyar shan jini da sauransu, kuma koda sun yi tsafin, baya taɓa tabbata, haka za su yi ta shan wahala, amma ba zai tabbata a jikin wanda suka yi wa ɗin ba, domin annabi ya ce tabbas tsafi bata tabbata a jikin bawa, dole akwai time da zai warware, lokaci gare shi, ɓarawo, sai ya sha wahala wajen yin sata, yana yi zuciyarsa tana bugawa da karfi karfi, saboda yana tsananin tsoron kada a kama shi, idan rana ta ɓacin mashi, to fa har kashe shi ana iya yi, idan kuma ya tsira, to abin da ya sata ɗin ba zata taɓa yin albarka ba, kamar iska haka zata wuce, kunga a nan ya sha bakar wahala sosai a banza, mazinaci, yana yin zina zuciyarsa na dukan uku uku, tsoron kada a kama shi, ko kuma wani abin ya faru yake yi, sannan idan har ya yi zina sau ɗaya, to kofa ce ta wahala da talauci a rayuwarsa take buɗe mashi, mashayin giya, idan ya sha giya, ya shiga cikin maye, ya fita a hayyacinsa, zai iya zuwa ya hau babban titi mota ta take banza ma ba tare da ya sani ba, babban musiface mutun ya gusar da hankalinsa daga jikinsa, masu yin luwaɗi, su maɗigo da sauransu, duk suna kasancewa cikin mufisa da wahala, masu yin lesbian a hankali hankali za su fara wari, ana tafiya ana tafiya har gabansu ta lalace, saboda sun kauce hanyar yadda Allah ya ce ayi, masu bada bayansu ayi zina da su ta wajen, su lalacewarsu ma tafi munin gani, dan har tsutsa suna yi, Allah ai ba abin wasa bane, Allah yana son bayinsa fiye da yanda suke son kansu, dan haka ba zai taɓa hana bayinsa wani abin na jin daɗin rayuwa ba, duk abin da kuka ji Allah ya haramta, to ba makawa wannan abin cutarwa ce ga bayinsa, masu yin bleaching wlh har wani irin wari suke yi, suyi ta zuba turare a jiki, amma kamshin perfume ɗin daban, warin jikin nasu daban, komai za su yi wa jikinsu, wlh ba za su dai'na wannan wari ba, saboda me? Saboda sun kauce hanyar Allah, Ubangiji ya fi kowa sanin abin da zai dace da bawansa, bai yi ki a bakar fata haka kawai ba, haka zalika bai halicci fararen fata haka kawai ba, yasan da cewa shi ne yafi dacewa da kowa daga cikinmu, amma ku ƴan iya, ƴan bani na iya, fit kin daka tsalle kina baka kice sai kin dawo fara, Allah yasan da farar fatar, amma ya baki baka, sai ki gode mashi ba wai ki ra'ina yanda ya yi maki har kina ƙoƙarin canzawa ba, a takaice dai duk masu aikata aikin saɓon Allah, to wlh a wahale suke, su kuma waɗan da suka ce Allah ya isar masu akan komai, wlh ko barci suke yi Allah yana isa masu ɗin, nafi jin daɗi a koda yaushe na yi maku misali a aikace ba wai da baki ba, dan ta hakan ce kawai za su fi ganewa, yanzu misali, ita dai Queen kunsan ba karamar wahala ta sha wajen gina waɗan nan dakarun nata ba, ko da ido ku kunsan dakare ɗaya ya isa ya kashe TRIPLET'S gabaɗayansu, ya isa ya cinyesu gabaɗaya, amma su TRIPLETS ɗin kuma sun ce Allah ya isa masu a kan komai, kuma ga shi ya isa masu ɗin, ƴar ƙaramar kalma ce a baki wajen faɗa, amma babbace a aikace, wato bismillahi munfara da sunan Allah kenan, ga shi su basu sha wahala ba, da iya bismillahi suka ruguje dakarun, ku sani bawai kankantar kalmarce abin dubawa ba, girman abin da ta kuntsa ce abin dubawa, bismillahi, mun fara da sunan Allah, tun da kuwa suka fara da sunan Allah, to ba makawa Allah zai tsaya masu, dan shi suka sako a gaba, shi ne kuma zai shige masu gaban a komai, abin da nake son nuna maku a nan shi ne, duk wani mai aikata saɓon Allah, to wlh a wahale yake har karshe raywuarsa idan bai tuba ba, idan ka ruke Allah, ka gama komai, ba zaka taɓa shan wahala ba, babu wanda zai iya kareka a kan komai a duniyar nan sama da Allah, to ni dai PRINCESS TEEMA na ce Allah ya isa mani akan komai da na saka a gaba a duniyar nan, kuma shi ne a kan gaba a komai nawa, shi na ruke babu wani ja in ja, saura ku kuma my READERS?. STORY. Wucewa gaba Aseef ɗin ya yi yana faɗin "Kai Areef ka cika tambaya". Ya yi maganar a tsananin shagwaɓe, yadda dai yake yi masu magana a gida. Harararsa Areef ɗin ya yi yana faɗin "Kai ni kazo ka gaya mani ta yaya aka yi kazo nan wajen, ba zan yi mamaki da wannan karfin da ka samu ba, dan nasan kai jininmu ne, dole dama kana da karfi, shagwaɓa ce kawai ta cinye karfin, amma ya aka yi kazo nan? Shi nake son sani". Miƙa mashi jakarsa Aseef ɗin ya yi, ba tare da ya dakata daga tafiyar da yake yi ba ya ce "Kai kanka fa baka san ta yaya ka zo nan ba, amma kake tambayar wani ta yaya ya zo? To ta sama na faɗo, ni ka ruke jakarka na gaji ba zan iya ba, ya fi karfina". Ya kai karshen maganar tamkar zai saka kuka. Duka Areef ɗin ya kai mashi a dantsen hannunsa. "Ba wani nan sai ka gaya mani ta ya aka yi kazo nan". Kukan shagwaɓa ya sanyawa Areef ɗin yana faɗin "Kai fa mugu ne, to nima na san tayaya na zo ne? Kawai na ganni ne a kusa da kai, daga haka kuma sai ban sake ganina ba". Jinjina kai Areef ɗin ya yi yana faɗin "Sarkin rainin wayo na duniya ba, yanzu Aseef ni zaka kalla ka yi wa wannan tatsuniyar na cewa kawai ka ganka ne, sai kuma daga baya baka sake ganinka ba, to yanzu kuma da waye nake magana kenan?". Turo baki ya yi kamar zai sa kuka ya ce "Da Heartbeat na TRIPLETS kake magana mana, ni ka karɓi jakarka ya yi mani nauyi, ba zan iya rukewa ba". "Amma kuma ai ka iya kashe mutane rai shidda ko? Jaka ce ba zaka iya rukewa ba?". Kuka ya saka yana ƙoƙarin fara bubbuga kafa a kasa, da sauri Areef ɗin ya karɓi jakar yana faɗin "Rigimamme kawai, ni bani kayana". Ya karɓi jakarsa tare da wucewa gaba abinsa. Haka suka cigaba da tafiya, Areef yana gaba, shi kuma Aseef yana baya, sai wuce ɗakuna suke yi suna neman sojojinsu da kuma Lion. "Aseef wai ina Lion ne?". Areef ne ya tambaya. Shiru Aseef ɗin bai amsa mashi ba, ko da ya juyo dan ya ga meyasa ɗan uwan nasa bai amsa mashi ba, sai ya kalli wajen wayam, babu Aseef babu dalilinsa. Da mamaki ya juyo da kyau yana kallon hanyar, babu wata kofa dai da za'ace Aseef ya bi ya tafi, hanya ce doguwa, sai ɗakunan mutane da suke a rufe ruf. Shiru ya yi yana al'ajabin ina Heartbeat nasun kuma ya yi?. Ina da tantanma a kan Aseef sosai wlh!!. Ya jima a tsaye a wajen ya kasa motsawa, tamkar wanda ruwa ta cinye. Almost 20 mins yana tsaye yana ta tunanin abin yi, kwatsam sai ji ya yi daga ta bayansa an taɓa shi. A razane ya juyo. Cool murmushi Aseef ɗin ya sakar mashi yana faɗin "Muje". "Aseef ta ina kabi ka bar nan wajen?". Ya yi maganar on a serious note. Turo baki Aseef ɗin ya yi tare da wucewa gaba ba tare da ya bashi amsa ba. Kamar ba lafiya ba Areef ɗin ya ji ya mance da tambayar da ya yi wa Aseef ɗin a yanzu, kuma ya mance da tambayar da zai sake yi mashi, haka ya sake bin bayansa suka cigaba da tafiya a wannan shegiyar doguwar hanyar, suna tafiya Areef yana ambaton sunan Allah a cikin zuciyarsa, dan shi dama baya rabuwa da yin tasbihi, wannan tasbihi da yake yi kuma shi ne ya yi mugu mugun taimaka masu wajen kubcewa daga kan idanun Queen, kwata kwata ta dai'na ganinsu a yanzu, gabaɗaya sun fita daga idanun tsafinta, dan haka sai ta tashi ta fara gagarumin sabuwar shiri, dan ta lura abin da take gani ƙaramin abu, to yana neman ya zama babban abu, gara ta miƙe tsaye. A takaice dai sun yi tafiya mai nisa kafin su samu su fita daga cikin wannan waje, suna fita kuma wata duniya suka sake gani, dan faɗawa wani ɓangare na gidan suka yi, gani suke yi tamkar a wata sabuwar duniya suke, Daular Mutuwa gidan akwai girman gaske, babu abin da basu da shi a ciki, Daular ce ta gasken gaske kuwa. "Areef yana da kyau mu raba hanya a yanzu, zan je neman fadar wancan tsinanniya, dan ita ce kawai zata nunamana gidan uwar da ta kai Lion, kai kuma ka nemo su kaka, Heartbeat da sauransu". Cewar Aseef. Ya kai karshen maganar tare da matsowa sosai kusa da Areef ɗin, a kunne ya raɗa mashi "Ka nemomini Heartbeat tawa da wuri, dan ko a yau muka koma gida sai na yi dis virgin nata, bafa zan kyaleta ba". Ya kai karshen maganar tare da juyawa ya nufi ɓangaren hagunsa. Areef ɗin yana son ya yi mashi magana, amma ya kasa, yana son yi mashi tambayoyi sosai, amma sai ya ji ya kasa, harshensa ta yi nauyi, hakan na nufin kenan shi Aseef bada tsafi yake amfani ba? Ko dai yaya ne? Wannan abin akwai ruɗu da ɗaure kai. Areef bawan Allah ya jima tsaye a wajen kafin daga bisani ya nufi nasa hanyar, dan su aiwatar da abin da ya kawosu da sauri su fita a cikin gidan, sai dai kuma zuciyarsa cike take fal da tunanin irin jarumtar Aseef ɗin, tashi ɗaya ya zama jarumi na gasken gaske, kuma ga dai shagwaɓar bai barta ba, idan ta motso mashi yana yi, ga kuma karfin bala'i da yake da shi tamkar wani shararren sadaukin mayaki. Haka dai suka rabu kowa ya yi hanyarsa, suka bazama neman ƴan uwansu, ita kuma Queen tana can tana shirya masu gagarumin shiri ta yadda za ta kashesu gabadaya lokaci guda, tana ta ƙoƙarin taga ta haɗesu waje guda ta konesu ta huta...... Mu leka gida kuma muga me yake faruwa. KADUNA. Wasa wasa Rimsha rashin lafiya sai karuwa yake yi, da mummynta da gwaggo dai kamar yanda kuka sani ne, sun ɗauka laulayin ciki ne, saboda kusan duk abin da take yi a yanzu, ya yi kama da mai ƙaramin ciki, a koda yaushe tana zaune shiru tamkar gunki, bata son hayaniya, kuma ga masifar tsiya idan ka yi mata abu, duk zafi da tsiwa irin na Jehan, to fa yanzu ta shafawa Rimsha lafiya, dan yanzu Rimshar ta fita iya bala'i, jiya ma saura kaɗan su buga dambe, dan Jehan ɗin ta kalleta da ido kawai. Gwaggo da daddy kuma sun hana ayi wa Rimshar abin da bata so, dan gwaggo ta gayawa daddyn wai ciki ne da Rimshar, so dole a kula da ita a lallaɓata. (Kai jama'a ana al'amura a littafinTRIPLETS, wai Rimsha ce mai ciki?🤔 Ita da ko...... Ba ayi ba🤔) Daddy kam murna a wajensa ba'a magana, sai wani ririta suke yi, Jehan kuwa kamar zata fashe saboda haushi, sai Rimsha ta yi mata laifi, amma haka tana ji tana gani su gwaggo za su hanata ɗaukar mataki, abin yana bakanta mata zuciya ba kaɗan ba. A ɓangaren ita kuma Aafia, ta farfaɗo, ko da ta farfaɗo sai ta farfaɗo masu a kurma mara magana, sam sam bata cewa komai, da idanu kawai take bin mutane baiwar Allah, kome aka ce mata, da idanu kawai take kallon mutu, ba um bare umm. Daddyn su Lion ma ya sami lafiya sosai, sai dai har yanzu yana a kan bakarsa na cewa shi wlh bai san gwaggo ba, yana fitowa har palo ya zauna da su Uncle Herry, amma baya ko ɗaga idanu ya kalli gwaggon, ita ma bata bi ta kansa, dan Lion ya gaya mata kada ta kula kowa, ya ce mata kusan kowa da take kallo a gidan, to fa ba yin kansa ne yasa yake yin wasu abubuwa ba, akwai wata gagarumar matsala a kasa, dan haka ba ruwanta da kowa, shi idan ya dawo, zai binciko koma mecece ainahin wannan matsala bakiɗaga. Hakan tasa sam bata ko ɗaga idanu ta kalli Dr William ɗin, ita ma ta nuna kamar bata san shi ba, uncle T kuma Lion ya aike shi Usa, ba da shi suka tafi Daular Mutuwa ba, Jay ya koma Washington abinsa, yanzu saura John kawai, suna rayuwarsu iya su uku, Dr William uncle Herry, sai John, sam basu shiga harkar su gwaggo, suma su gwaggon, basu shi ga harkarsu. Jehan ce kwance a saman bed ɗin gwaggo, dama idan baku manta ba, ɗakin da daddynta ya zauna, shi ne ɗakin gwaggon a yanzu, ta lafe shiru a saman bed ɗin tana tunanin duniya da kuma mijinta. Kamar daga sama tunanin gidan Hjyr daɗi ya faɗo mata cikin ƙwaƙwalwarta, a hanzarce ta miƙe zaune, cikin sauri ta fara leke leke a bayan gadon gwaggon. Jim kaɗan tasa hannu ta fito da wayoyi guda biyu da ta taɓa ajiyewa a wajen tun lokacin da ta zo gidan kafin ta ta fi prison. Ɗaya wayar Abubakar Salahuddeen ne, ɗayar kuma wayar Adiva. Ganin wayar Adivan nan ya sanya idanunta sun ciko tab da kwallah, tunaninsu ya dawo mata cikin ƙwaƙwalwarta, addu'a take yi Allah Ubangiji hasa Hjyr daɗi bata lalata masu rayuwa ba, Allah sarki Maryam baiwar Allah, yanda ta sha fama da wahalar rayuwa, idan dai Hjyr daɗi ta lalata mata rayuwa wlh sun gama zaluntarta, kuma da izinin Allah sanadiyar wannan marainiyar Allah Maryam, in dai suka cutar da ita duk da whalar da ta sha, wlh Allah ba zai barsu ba, zai yi mata sakayya cikin gaggawa. Ƙoƙarin kunna wayoyin ta fara yi, sai dai dukka sun ki kawowa, dan haka sai ta nufi waje da su, bedroom nasu ta nufa, chaji ta je ta sanya wayar tare da zama a gefen bed ta buga uban tagumi tana tunanin mafita. A haka Jelly ta shigo cikin ɗakin ta sameta, kusa da ita ta zauna tana faɗin "Aunty Jehan ina kwana?". A lallai Ammie ta gyara Jelly, har da su Aunty Jehan, duniya sabuwa, wato rashin mahaifiya babbar musifa ce kuma babbar barazace ga tarbiya da kuma rayuwar yaro gabaɗaya, yanzu dai daga ɗan zamanta da Ammie har ta koyi wasu abubuwa masu amfani, ta nutsu sosai, Allah Ubangiji ka karawa mahaifanmu daraja, ka kara masu lafiya, ka kuma kara masu nisan kwana, waɗan da suka rigamu gidan gaskiya, Allah ka jikansu da Rahman. "Lafiya lou Jalila fatan kun zo lafiya?". Ta bata amsa tare da mikewa ta nufi waje, dan ta je wajen daddynta, yau ta tuna da rayuwarta ta baya gabaɗaya, tana son ta je ta gayawa daddynta labarin su Sadiq ɗin Katsina, bata san cewa mum ta riga da ta gaya mashi ba, ya kuma ce idan su Lion suka dawo, komai ya dai'dai ta, zai taka kafarsa har izuwa Katsinar da kansa, zai je ya gaishe su, ya kuma yi masu godiya. A garden ta isko daddynta, daddyn Anaya Abba da kuma Abbi, sai gwaggo da Brr Naurat da daddyn Jelly, suna tattaunawa a kan abin da ya wuce a baya, Brr Naurat ne ta ce daddyn Rimsha ya basu labarin yanda ya yi bayan ya baro gida, da kuma yanda ya yi rayuwa, yanda ya haɗu da mummyn Rimsha da dai sauransu, to bai kai ga fara basu labarin ba Jehan ɗin ta shigo baki ɗauke da sallama, a tare suka amsa mata, sosai Brr Naurat ta zuba mata idanu, tana tsananin Kaunar Jehan ɗin, saboda kamanceceniya da daddynta da take yi. Kuma a duk cikin surukanta Brr Naurat ɗin ta fi kaunar mummyn Rimsha da kuma Aunty matar Abbi, saboda sun fi girmamata, sunfi ɗaukarta da daraja, musammanma mummyn Rimsha, ta ɗauki Brr Naurat ɗin tamkar mahaifiyarta, hakan yasa ita ma tafi kaunarta sosai ita da ƴaƴanta Rimsha da Jehan, dama kuma kunsan already shi daddyn Rimsha shi ne shalelen Brr. A duniya kowa yana son na gari, kowa yana son mutumin kirki, mai kyautata masa, ya Ubangiji kasa mu zama na kirki a koma wani irin hali muke ciki. Kusa da daddyn nata ta zo ta zauna tana faɗin "Daddy yau fa na tuna da rayuwarmu ta baya ne, ina son naje Katsina wajen maman Sadiq, wlh tana da kirki over daddy, ta taimakemu sosai, ina son nima na taimaka mata, ina son ka bani kuɗi dayawa in kai mata". Da yake daddyn nata yana zaune kusa da Brr Naurat ne, sai Brr ɗin ta kai hannu tana shafa kanta, a nutsu ta ce "Haka ake so Jehan, idan mutun ya yi maka alkhairi kada ka taɓa mantawa da shi, Allah ya yi maki albarka". A tare suka amsa da Amin, sannan daddyn nata ya ce "To shikenan my baby, jeki cikin gida muna tattaunawa ne a yanzu, idan Allah ya dawo mana da su Areef lafiya, mun huta, komai ya lafa, zamu je Katsina ɗin ni da ke". Okey ta amsa mashi da shi, sannan ta miƙe ta bar wajen, cikin bedroom nata ta koma, a in da ta ɗauki wayar Rimsha ta zauna a bakin bed kusa da Jellyn tana mai cigaba da kiran number Areef tamkar yanda ta saba a koda yaushe, sai dai kash a koda yaushe number tasa a rufe take, babu network sam sam. Su kuwa su Brr Naurat, daddyn Rimsha ne ya fara basu labarin yanda ya yi rayuwa bayan barowarsa gida, cikin nutsuwa ya fara magana kamar haka............. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 24/4/2024 E14 Su kuwa su Brr Naurat, daddyn Rimsha ne ya fara basu labarin yanda ya yi rayuwa bayan barowarsa gida, cikin nutsuwa ya fara magana kamar haka. "A lokacin da na fita gida, hotel na fara kamawa, ina shiga ɗakin nawa, na zauna na ci kuka na son ra'ina, a wannan rana na kwana ban yi barci ba, sai dai kuma na kudurci niyar duk wuya duk daɗi ba zan koma gida ba, ba zan sake waiwayar kowa ba, na kudurta a zuciyata zan yi rayuwata ni kaɗai'na, zan kuma tsaya tsayin daka na nemi ilimi, zan shiga siyasa, daga karshe kuma ina rokon Allah da ya bani iko da dama na samu na taimaki ƴan uwana a duk in da za su kasance, yin wannan tunani yasa ya sami karfin gwiwa, dan haka sai na tashi na yi wanka, na daura towel ɗin hotel ɗin na ɗan kwanta na huta, sai dai tunanin mummy da cikinta ya hanani sukunin, haka dai a daure ina yi mata addu'a. A washegarin ranar na nemi gida na saya, kuɗin da Mommy ta bani suna da mugun yawa sosai, da su na cigaba da yin rayuwata, na koma makaranta, na kuma fara sana'a, ko kaɗan bana tunanin komawa gida, a duk abubuwan nan da na saya kuma ko rabin kuɗin da mum ta bani ban taɓa ba, saboda kuɗin dollars ne, idan na canza kaɗan suna da yawa a kuɗin Nigeria, haka na cigaba da rayuwata ni kaɗai tsawon lokaci, ina zuwa makaranta, kuma ina juya kuɗina, akwai lokacin da ta kama dole na je gida, haka na shirya na je gidan, sai dai ban bari kunsan naje ba, takardun makarantata na je na ɗauka, a lokacin na sami mum tana zaune a garden, na tsaya tsawon lokaci ina laɓe ina ganinta, sai dai ita bata ganni ba, daga karshe na ɗauki abin da zan ɗauka na fita gidan, haka na kammala karatuna ni kaɗai na, ina kuma bibiyar ƴan uwana, ranar da aka ce daddy ya rasu, har gida nazo dan na tabbatar, amma babu wanda ya ganni, komai da yake wakana a gida ina sane da shi, har auren yaya babba duk ina sane da komai, kuma na tura mashi da gudumawata, sai dai bai san cewa ni ne na bashi ba, auren yaya Deen duk ina sane da su, har haihuwar Imran da matar yaya babba ta yi, duk ina sane, kafin haihuwar Imran ma korin Aunty Aisha da babban yaya ya yi daga gidansa duk ina sane, shi ne na je na ɗauketa, amma fa kafin na yi rayuwa da Aunty Aisha, na ruke Maik tukun nan, lokacin da naje gida dan tabbatar da mutuwar daddy, a lokacin na samu labarin cewa har da mum suka rasu, maganganun mutane ya kasu kashi biyu ne a lokacin, wasu sun ce ban da ita, wasu kuma sun ce har da ita, to ni dai da ban ganta a gidan ba, sai na ɗauko Maik muka dawo da shi gidana, ya yi rayuwa mai ɗan tsawo a wajena, ina ganin su baban yaya suka rinƙa nemansa, amma naki bayyana masu yana wajena, sai da ya ɗauki tsawon lokaci a wajena, sai tafiya ta kamani zuwa Dubai a kan harkar kasuwancina, bani da zaɓi dole na mayar da Maik gidan yaya babba, haka na shirya na ɗauke shi zuwa gidan, na bawa mai gadi shi, sannan na juya na koma, sam ban so rabuwa da Maik ba, na so na rene shi ne ya taso a hannuna, amma ba hali, da na tafi Dubai na ɗauki tsawon shekaru uku a can, a lokacin ne kuma Allah ya kara bunkasa mani arzikina, komai na taɓa kuɗi, har mamaki nake yi, abubuwa suka kara haɓaka, lokacin da Aunty Aisha ta baro gidan yaya babba ta suma a kan hanya, a lokacin ina Dubai, amma na sami labari ta hanyar security dana sanya yana yi mani gadin gidajen ƴan uwan nawa, dan ya gaya mani me yake faruwa, ina daga can nasa aka kai mani ita asibiti, satin ta ɗaya a asibiti na diro Nigeria, ni na cigaba da kula da ita na tsawon shekara ɗaya, bayan ta sami lafiya, sai na ɗauketa muka je har Washington, dan ta bani labarin abin da ya faru da ita, da muka je bamu sami waɗan da muke nema ba, sai na wuce da ita Dubai, a nan muka cigaba da rayuwarmu, ina sane da duk irin nemana da ƴan uwana suke yi, amma ko kaɗan ban ji cewa zan koma cikinsu ba, mun yi rayuwa mai tsawo a Dubai da Aunty Aisha, rabon auren Maryam ya dawo damu Nigeria, kafin mu dawo na sa an shifiɗa mana shinfiɗaɗɗen gini na alfarma, gini na gani na faɗa, muna dawowa na cewa Aunty Aisha zan je Niger in duba yanayin yanda ƙasar take, dan ina son buɗe company a can, a lokacin ina da wani aboki ɗan Niger ɗin, shi ne yake yawan bani labarin kasarsu, a makaranta muka haɗu, shi ne nace to bari naje ziyara na duba mu gani, ashe rabon auren Maryam ne ya kai ni, a hanyata muka haɗu da Shitu wanda ya kasance ɗan uwane ga ita Maryam ɗin, in takaice maku labari da na je ƙasar Niger, na so mu sauka a hotel, amma abokina ya nuna baya son hakan, ya nuna ba zai ji daɗi ba idan har ban sauka a gidansu ba, dan yana bawa ƴan uwansa labarina, iyayensa duk suna son ganina, yin hakan yasa na ce mashi to shikenan mu je gidan nasu, haka kuwa aka yi, lokacin kankanin na yi sabo da Shitu, muka zama kamar ƴan uwa, yana da kirki sosai, har muka karɓi number juna. Saukata a gidansu abokina naga karamci, suna da karamci sosai, mutanen Niger adilan mutane ne masu kirki sosai da sosai, suna da karamci over, haka suka karramani, suka mutuntani, a tare da abokina muka kwana, washegari da safe, bayan na yi wanka na shirya zamu je yawace gari da motar abokin nawa, muka shiga wajen mahaifiyarsa dan mu gaisheta, a nan na fara ganin Maryam, tana zaune kusa da mahaifiyar abokin nawa, da alama aikota aka yi, tana sanye da hijabinta har kasa, duk da cewa hijabin da kuma kayan jikinta duk a koɗe suke, amma ta yi shiga ta mutunci wanda duk wani ɗa namiji mai hankali zai sota, kuma zai yi sha'awar ta zama matarsa. Muna shigowa ta ɗaga mana gaisuwa cikin sanyin murya tana sunkuyar da kai kasa, kyakkyawar gaske ce sosai da sosai, sai dai alama akwai wahala sosai a tattare da ita, dan duk fatar jikinta a koɗe. A gaban idanunmu maman abokina ta bata sakon da ta zo karɓa a leda, ta tashi ta tafi abinta, mu kuma muka gaisa da maman abokin nawa, sannan ta zuba mana adduo'i tare da fatan alkhairi, daga nan muka fito, muna shiga cikin mota abokina ya kai mani duka yana faɗin malam ya naga sai kallon Maryam kake yi? Dariya na yi ina cewa kai kuma sarkin sa ido ba, dan Allah ƴar wacece? Ko kanwarka ce?. Bai yi kasa a gwiwa ba wajen gaya mani cewa ita marainiya ce, kuma ga in da take rayuwa, ya bani labarin komai da irin wahalar da take sha a hannun ƴan uwan mahaifiyarta da sauransu, na ji babu daɗi sosai, kuma na tausaya mata sosai, dan haka sai nace to muje gidansu, ko da muka je sai muka tarar da Shitu a gidan, shi ma ashe ya je dubata ne, ɗan uwanta ne ta gefen mahaifinta daga Nigeria kenan, na ji daɗi sosai na ganinsa, a lokacin yarinya ce sosai, dan ba zata wuci irin 13 to 14 years ba, hakan ce ta bani kwarin gwiwar naji cewa ina son na aureta, dan na tsamota daga wahalar da take ciki, kuma bata wuce shiga school ba, in takaice maku labari zuwana Niger dai shi ne silar aurena da Maryam, Aunty Aisha da kuma abokan arziki sune suka tsaya mani akan komai, da yake a lokacin ba wani ɗaukar Maryam ɗin da muhimmanci ƴan uwan nata suka yi ba, saboda rashin iyayenta, sai suka bani aurenta ba tare da bincike ko bin diddigin wanene ni ba, na auri Maryam, bayan ganina da ita na farko da wata biyar dai'dai, sannan na dawo da ita Nigeria, na kuma kaita har garin Maiduguri wajen ƴan uwan mahaifinta, dan naji labarin komai a kansa daga bakin Shitu, daga nan muka sake komawa Dubai da zama, ban yi zaman Nigeria sosai ba, mun yi rayuwa cikin tsananin farinciki, na sanya Maryam a makaranta, ta yi karatu sosai, dan tana da kaifin kwakwalwa da basira, kuma nima ina kara koya mata karatu sosai, Aunty Aisha ma tana kara mata wani duk da cewa ita ma tana zuwa ismaliya sosai a lokacin, aurena da Maryam ya ɗauki tsawon lokaci kafin mu sami haihuwa, cikin mu na farko yaron bai zo da rai ba, mun ji tsananin rashin daɗi, amma mun fawwalawa Allah komai, haka muka cigaba da rayuwar farinciki, cikinmu na biyu yana da wata bakwai ta haife shi, shima ɗa namiji ne, ya zo da rai, an saka shi a kwalba kasancewar bakwaini ne, kwanansa uku a duniya ya koma ga mahaliccinmu, munji babu daɗi, saboda mun ɗauki son duniyar nan mun ɗaura mashi, amma ba yadda zamu yi tun da haka Allah ya ƙaddaro mana, a cikin Maryam na uku ma yana da wata uku cikin ya zube, daga nan na fara shiga damuwa sosai a kan hakan, na ce sai dai muje asibiti, ko da muka je ma babu wata matsala, kawai dai Allah ne bai kawo mai tsayuwa ba, haka Aunty Aisha ta rinƙa kwantar mani da hankali, da har na fara tunanin shikenan ni ba zan sami magaji ba, a lokacin fa Hassan na ma ya yi aure, ɗansa Feroz har yana gudu ko'ina, ya girma, ga su Imran ɗin yaya babba duk sun girma, amma ni kuma shiru, abin kullum da shi nake kwana da shi nake tashi, ita ma Maryam tana cikin tsananin damuwa a kan hakan, sai dai bata bari na gane ba, kullum sai ta yi kuka, bata san ina sane da komai ba, damuwar da take shiga ne ma yake kara tsananta mani tawa damuwar, haka na cigaba da ƙoƙarin faranta mata rai ko dan maraicinta, in takaice maku sai da muka sami ciki har sau biyar dukka basu zama, wasu ta haifesu da rai su koma, wasu babu rai, a ciki na shidda ne muka haifi ƴan biyu dukka maza, kuma dukka Allah ya barɓi abinsa, shi na farkon, wato Hassan ɗin satinsa ɗaya a duniya ya rasu, na biyun kuma sai da ya yi wata biyar a tare da mu, sannan Allah ya karɓi abinsa, ni nasan mumini baya rabuwa da jarabawa ta Ubangiji, amma wlh wannan jarabawa ta ƴaƴa ya yi matuƙar girgiza mu, badan Aunty Aisha da take tare da mu ba, wlh da mun tabbaka babban kuskure, dan har cewa muka yi zamu sami wata mata mu biyata maƙudan kuɗaɗe, sai a sanya mata kwan haihuwata ta haifa mana yara ko uku ne, Aunty Aisha ce ta tsawatar mana sosai a kan hakan, a lokacin dai na bi umarninta ne kawai matsayinta na babba a kai'na, kuma ko ba komai Aunty Aisha ta nuna mana so da kauna nida Hassan fiye da tunanin kowa a lokacin da muke ƙasar Russia, amma banda haka wlh da a lokacin sam ba zan ɗauki maganarta ba, haka dai muka jure, ina ji ina gani dukka ƴan uwana daga mai yara uku sai mai yara biyu, shi babban yaya har matarsa ta haifi Imran, Akil, da kuma Akila, shi kuma yaya Deen, matarsa ta haifi Irfan, Aafia, and Umaisha har ma matar ta bar gidan a lokacin, ta bar Umaisha tana karama, Hassan matarsa ta haifi Feroz tana da cikin na biya, autanmu Maik dana rena da hannuna ma matarsa tana da ciki a lokaci, abin fa ba ƙaramin ɗaga mani hankali ya yi ba, Maryam da kanta ta ce na kara yin wani auren ko zamu sami ƴaƴan, naki yarda da zancenta, saboda bana son nayi mata kishiya, bana son kowa yazo ya takura mata, ina so ne ta yi rayuwar farinciki, ita kaɗai a cikin gidana, saboda mace ce ta gari, macece ƴar albarka, ta bani farincikin da ban taɓa tunani ba, tana da hankali da nutsuwa, ina tausayawa maraicinta, yanzu kuma ga rashin haihuwa, mun binne yara almost 7, amma shiru, a ƴan tsakanin nan muka sake samun ciki, a lokacin cikin matar Maik bai wani girma sosai ba, dan bai wuce 3 months ba, ita ma matar Hassan haka nata cikin bai fi wata uku ba, shiyasa ƴaƴan namu suka kasance shekarunsu ɗaya, sai dai ratan watanni, wato da Jalila, Anaya, da kuma Jehan kenan, sai dai fa ko da muka haifi Jehan ɗin, bamu wani jata a jiki sosai ba, dan muna ganin kamar ita ma mutuwa zata yi, amma da yake uwa da ƴa ba mai shiga tsakani, ita Maryam ta jata a jiki sosai, ni kam baya baya nake yi da ita, dan rasuwar Hussainin namu ya girgizani, na saba da shi sosai, ko ina zanje muna tare, yaro ɗan wata biyar amma ya san yawo, saboda fita da nake yi da shi, lokacin da ya rasu nasha wahala, har firgita nake yi a cikin barci ina kiran sunansa, to shi ne yasa na ki yarda na ja Jehan sosai a jikina, dan kada na sake shan wata wahala, sai da na ga Jehan ta cika shekara guda bata mutu ba, sannan ne na jata a jiki sosai, na fara nuna mata soyayya, mun so Jehan fiye da kanmu, baki ma ba zata iya faɗar adaddin soyayyar ba, haka muka cigaba da bata kulawa tamkar kwai a saman bajajjen faranti, Aunty Aisha ta fi mu nuna kula a kan Jehan, daga karshe ma haka muka hakura muka bar mata Jehan ɗin tana kwana a ɗakinta, dan ta kwace mana ita, shiyasa kuke gani a yanzu sun fi shakuwa, shakuwa ce da suka yi ta tun tile tile, ba ta yanzu bace ba, tun daga kan Jehan ɗin kuma bamu sake samun haihuwa ba har matar Hassan ta haifi Zaira, bayan haihuwar Zaira da wata ɗaya muma muka sami ciki, nan muka fara tattalin kayanmu, har Allah ya sauketa lafiya muka sake samun ƴa mace, a baya duk ƴaƴan da muka binne maza ne, yanzu kuma mata muka samu, ƴarmu ta biyu wato Rimsha, kama take da Maryam sak, while ita kuma Jehan kama take yi da ni sak, haka muka ɗauki son duniya muka ɗaurawa ƴaƴan nan namu guda biyu, muka cigaba da basu kulawa na wuce misali, sai dai sun fi shakuwa da Aunty Aisha, dan sun fi zama a wajenta, ni kuma ina kyale mata su ne dan su ɗebe mata kewar TRIPLETS nata da ta rasa, kullum maganar Aunty Aisha ɗaya idan tana yi wa su Jehan wasa, shi ne idan ta ga TRIPLETS nata, to sune mazajensu Jehan ba makawa, kuma zata yi ta addu'a a kan hakan, in dai tana raye ta gane ƴaƴan nata, to wlh ko sun yi aure sai sun auri su Jehan, kullum shi ne zancenta, a hankali hankali har ta zo ta fara dai'na zancen TRIPLETS ɗin nata, kamar wasa duk zancen ya bar bakinta baiwar Allah, haka muka rayu cikin farinciki, kullum muna waya da Shitu, shi ma ya jima da yin aure, suna da ƴarsu ɗaya Adiva, sa'ar Jehan ce yarinyar. Bamu tashi dawowa Nigeria ba har sai da su Jehan suka yi wayo, sai da Jehan ta kai primary 4 a school, wannan dalilin yasa sam basu jin Hausa, daga larabci, sai English da kuma yaren mamansu wato shuwa Arab, sai kuma kanuri da take yi masu kaɗan kaɗan, nima time to time ina yi masu fullanci, dan na koya wajen daddyna, sai dai Rimsha ce kawai ta ɗan iya fullanci, ita Jehan ko yaren mummyn nasu ma taki ta koya sosai, ita dai a barta da English, da shi kawai take magana, larabcinma sai taga daman yi, ga kafiyar bala'i, ga zafin rai, akwaita da iya tsare gida sosai, kuma dukka Aunty Aisha take zugata, ni dai bani da ta cewa, idan nayi magana Aunty Aisha ta hau surfa mani masifa, haka na zuba masu idanu, sai da muka dawo Nigeria ne na shiga harkar siyasa, da farko ina tsananin son siyasar, daga baya dana shiga cikinta, naga kazantar dake cikinta, sai naji ba zan iya ba, naso na barta, amma Maryam ta hanani, ta kuma kara mani kwarin gwiwa a kan lalllai na yi siyasa, lallai siyasa tana da bukatar mutun irina, zai tallafawa kasa ba kaɗan ba, ta dai nuna mani alfanonta sosai, na kuma gamsu, dan haka sai na sake zage dantse sosai, ina da abokan hamayya sosai, amma ban taɓa mayar da hankali nabi ta kansu ba, kawai harkar gabana nake yi, a lokacin ne Allah ya haɗani da Abubakar Salahuddeen, muka fara takun saka da shi, in takaice maku labari shi ne ya zama sanadiyar rugujewar farincikina da ni da familyna bakiɗaya, saboda na kama shi yana dillanci kayan maye da kuma mata izuwa kasashen waje, ya yi ya yi na rufa mashi asiri, dan takarar da zai tsaya, naki yarda na rufa mashi asiri, sai ya bukaci da na shigo cikin tafiyar tasu, nan ma naki yarda, to shi ne ya nemi salwantar mani da rayuwata da ta familyna, a lokacin da na shiga siyasa sunana ya fito, kamar hauka haka su yaya Deen suka yi ta nemana, har gida sun zo wajena, amma sai nece masu ni ban sansu ba, bani da wata alaƙa da su, dan haka su kama kansu, shi ma Hassan yazo har gida, naki yarda da shi, kuma sarai na san komai ma da yake tafiya a rayuwarsu, dan ina aika masu da makudan kuɗaɗe tun ina Dubai, har na dawo Nigeria ban dai'na idan suna cikin matsala ta kuɗi na taimaka masu ba, wannan shi ne labarina da abin da ya faru da ni a takaice kenan, kun san komai ba zai faɗu lokaci guda ba, amma ku ruke wannan ɗin kawai". Ya kai karshen maganar yana mai gyarawa ya kwanta, tare kuma da tada kansa da laps na Brr Naurat. Ajiyar zuciya kowa dake cikin wajen suka sauke, Brr Naurat ce ta ce "Sannu ɗana, kasha gwagwarmaya kai ma". Tana magana tana shafa kansa. Abbi ne ya kai mashi duka yana faɗin "Kana ji muna nemanka a lokacin, amma sai ka sheremu ko?". Jinjina masu kai ya yi alamar e ɗin ya share. Nan fa kowa ya fara tofa albarkacin bakinsa, shiru ya yi masu kamar baya wajen. Haka suka kasance cikin tsantsar farinciki da kuma yi wa ƴaƴansu dake Daular Mutuwa addu'a. After some minutes gwaggo ce ta ce "Ni kam wai Aseef bai dawo daga shopping ɗin da ya ce mani zai je bane?". Daddyn jelly ne ya amsa mata da "Gaskiya fa kamar bai dawo ba, wata kila ya wuce wani wajen ne". Da mamaki Abban Imran ya ce "Kai ba Saif ya ce kada kowa ya fita daga cikin gidan nan ba? Ya za'ayi A'isha ki barshi ya fita? Suma sojojin ya za'ayi su karya maganar Saif? Ko da yake sun fi kusa da shi, kila ya ce masu idan Aseef zai fita su bashi hanya ne" "Hmmm yaya babba kenan, Aseef ɗan rigimar ne za'a hana fita, ai idan suka hana shi fita,to wlh gidan nan babu zaman lafiya, ni kai'na idan na ce ba zai je ko'ina ba, to babu ni babu zaman lafiya, shi ne yasa kawai na ce mashi sai ya dawo". Cewar gwaggo. "Gaskiya kam Aseef ɗan rigima ne wlh". Cewar Abbi. Abba ne ya tari nunfashinsu da cewa "Ni ne nan zan baku labarin rigimarsa, yaron da ya je ya tasani a gaba ya rinƙa kuka lokacin da na ce ba zan bashi auren AKILA ba, Irfan ya riga shi, hmmmm ni zan gaya maku rigimar Aseef wlh". Murmushi gwaggon ta yi, ita kaɗai tasan me take tunawa take sakin wannan murmushi. Haka dai suka cigaba da hirarsu na tsawon mintocin kafin nan a kira sallar azzahar kowa ya watse, dan suje su yi sallah. After some days. Abubuwa da yawa sun faru a cikin kwanakin nan da suka shuɗe, ciki harda neman Aseef da su gwaggo suka rinƙa yi, amma shiru babu shi babu labarinsa, hakan yasa hankulansu ya kara mummunar tashi, nan fa suka dukufa wajen addu'a babu kama hannun yaro, suma fa sauran sojojin da suke a bakin gate, hankulansu ya yi mummunar tashi ba kaɗan ba, dan idan har Aseef baya gidan, to ba shakka sun shiga uku da Lion idan ya dawo, dan sun karya mashi doka na barin wani daga cikin family ya fita, su kuma wlh sam basu ga fitar Aseef ɗin ba, ba su san time da ya fita ba, Allah ya gani, bayin Allan sun shiga tsananin damuwa na wuce misali. Daular Mutuwa. Sun shafe kwanaki a cikinta suna neman ƴan uwansu, amma san basu gansu ba, duk wani part da zasu faɗa a cikin Daular, sai su ga kamar sun bar duniya, ga shi su da suke rayenma sun raba hanya, Aseef ya yi gabas, Areef ya yi yamma, sun sha matukar bakar wahala, har shi kansa Aseef ɗin ya wahala, kuma bai gane ina Fadar Queen ɗin take ba. Areef ne ke a kan wata hanya yana tafiya, sai wuce ɗakuna da abubuwa na ban tsoro da tsafe tsafe yake yi, tunanin ina Lion yake kawai yake yi, wani irin azababben yunwa yake ji, akwai snacks and drinks a cikin jakar dake goye a bayansa, amma ya kasa saukewa ya samu waje ya nutsu ya ci ya ƙoshi, shi burinsa kawai yaga ƴan uwansa. Duk wannan wahala da yake sha, bai dai'na ambato sunan Allah ba, hakan yasa Queen ta kasa ganin wai shin a ina ma yake, ya ɓace daga idanun tsafinta, sai nemansu take yi shi da Aseef, amma ko alamar mai kama da su bata gani ba. Ya zo dai'dai wata mararraba, hanyoyi ne suka rabu gida biyu, ɗaya ta yi gabas ɗaya ta yi yamma. A dai'dai wajen ya tsaya yana tunane tunane ya zai yi a yanzu? Shi dai ko mutuwa zai yi wlh sai dai ya mutu, amma ba zai taɓa yarda ya bar cikin Daular nan ba tare da ƴan uwansa ba. Idan ma ya ce zai bar cikin Daular ta ina ne hanyar fita?. A hankali ya fara jin motsi ta hanyar dake kallon yamma, shiru ya surara yana son tantance motsin menene?. Jin kamar sautin numfashin mutane ne yasa ya nufi hanyar babu tsoro ko miskala zarratin a tattare da shi. Ko da ya isa wajen sai ganin su Mark ya yi gabaɗayansu da sauran sojojin a ɗaure da sarkoki masu karfin gaske, sai dai babu Lion a cikinsu. Hamdala ya yi ga Allah, ko ba komai ya ga wasu daga cikin tawagarsu, saura su Ayla da kuma Lion, sai Heartbeat nasu, wato Aseef shalele ɗan rigima. Ba tare da ɓata lokaci ba, cikin kwarin gwiwa ya fara ƙoƙarin buɗe kofar karfen, a rufe kofar take ruf da matakan tsaron Queen. Sai kuma me? Yana ƙoƙarin sakawa kofar karfi ya buɗe ta, kamar daga sama ya ji wani uban jijjiga da ginin ya fara yi, kafin nan ya yi wata yunkuri ginin ta rufta, kofar ɗakin ya toshe. Hakika a wannan karon ba ƙaramar tashin hankali ya shiga ba, ya shiga ruɗu ta yadda kwata kwata baya iya gane ina ya dosa. Da sauri ya bar wajen saboda wani irin turnukin kura da ya taso, dan ma Allah yasa kofofin ɗakunan irin na karafunan nan ne masu kama da prison, so kofar ta tare ginin bai ruguzo a kansa ba. Da sauri ya fito daga hanyar idanuwansa sun yi jajir tamkar wuta, sai wani huci yake yi, Hakika ya ji takaicin mutuwarsu Mark, har wani pat, pat, pat zuciyarsa take harba mashi, wani irin tukukin bakin ciki ne ya tokare mashi maƙoshi, da kyar yake haɗiyar wahalallen yawu, kansa sara mashi take yi tamkar zata fashi, har wani irin jiri ya fara gani. Yana fitowa daga wannan hanya ya faɗa cikin wata tapkekiyar waje, wannan waje kuma ba ko'ina bane face wajen da su Rimsha suka taɓa zama, already dama kunsan ya yanayin wajen yake, ga faɗi da girma, ga kuma ɗakuna da yawa a cikinsu. Zubawa wajen idanu ya yi yana kallon yanda yake, kamar daga sama ya ga dirowan mutane a gabansa. Jiga jigan matsafane masu ji da karfi, dama Queen ta turosu ne su nemo shi, tasbihi da yake yi ne yasa basu iya ganinsa ba, to a yanzu kuma ya dai'na ambaton Allah, saboda bala'in da ya shiga na ganin abin da ya faru da su Mark, a lokacin ne ma ya kamata ya ambaci sunan Allah da kyau, sai kuma tashin hankali ta hana shi, ya shiga ruɗu na ganin yanda wannan gini ta ruguzo. Ganin mutanen yasa ya kara shiga tashin hankali, dama already bai dawo dai'dai ba. Kafin ya yi wani yunkuri waɗan nan jiga jigan matsafa, ɗaya daga cikinsu ya sanya hannu ya sunkuce shi sama, wurgi ya yi da shi can gefe, ta fiya ya yi zai bugu da jikin wannan gunki na karfe mai kifiyoyin tsafi a jikinsa. Tamkar wani walkiya haka Aseef ya bayyana a wajen ya tare shi, a tare suka faɗi kasa ba tare da sun isa ga wannan gunki ba. Ash suka furta a tare. Shi Aseef da Areef ya faɗo a kansa ma yana a cikin hayyacinsa sosai, shi kuma Areef ɗin saboda already yana cikin ruɗani, sai hakan ta kara gusar mashi da hankalinsa daga jikinsa, hakan yasa ya kasa koda motsawa. Kwantar da shi a gefe Aseef ɗin ya yi tare da mikewa tsaye, a hankali ya ɗago da dara daran brown eyes nasa izuwa kan waɗan nan matsafa, sun kasance su biyarne cif, jibga jibga da su madaka karti. Kallon up and down ya yi masu kafin ya mai do da kallonsa a kan Areef dake motsi yana ƙoƙarin dawowa dai'dai. Wani irin taunan hakwara waɗan nan matsafan suka fara yi, tare kuma da wani lankwashe kasusuwan jikkunansu, tamkar wasu macizai. Shiru Aseef ɗin ya zuba masu idanu yana kallonsu, har suka gama duk abin da za su yi, sannan suka tunkare shi da nufin su yi kutsi kutsi da su, su cinyesu ɗanye. Dai'dai lokacin shi ma Areef ya mike tsaye, ya dawo cikin hayyacinsa bawan Allah, ga uban yunwa da yake ji. Wucewa gaba Aseef ɗin ya yi, ya tari waɗan nan matsafa gadan gadan suka fara faɗa babu kama hannun yaro. Areef ya so ya taimaka mashi, sai dai kuma faɗar tafi karfinsa, ta wuce tunaninsa, daga karshe sai ya rabu da su suna faɗar, shi kuma ya fara duba ɗakunan da suke wajen, a cikin zuciyarsa yana ta mamaki tare da tunanin a ina Aseef ya samu wannan karfi har haka, sai dai kuma a baki ya kasa furta hakan, ya kasa iya tambayar Aseef ɗin komai, sai dai kawai ya bishi da idanu, komai zai yi ba zai iya tambayarsa menene yasa ya yi ba....... E lallai da akwai cakwakiyar gaske kenan. Binciken ɗaku nan da ya fara yi ne, a nan ne ya cikaro da Dr Salman da kuma Ayla a ɗaki ɗaya suna zauna, sun buga uban tagumi, dama idan baku manta ba, Ayla mutuniyar Dr Salman ce sosai, sun saba tun zamanta a Daular a shekarun baya, dan haka ko da ta sake dawowa a yanzu, sai kawai ta koma ɗakinsa ma da zama tun da bata da abokan hira. Bayin Allan, da kallo ɗaya zaka yi masu kasan suna cikin tsananin firgici da tashin hankali, sun wahala over, duk sun yi wani tsuru tsuru da su. Da kallo ɗaya ya yi wa Dr Salman duk da tsufan da ya yi, ya gane cewa shi ne kakansu, dan babu in da Abbi ya baro shi a kamanni, akwai kaman ƴaƴansa a tattare da fuskarsa. Bai ɓata lokacin ba ya faɗa cikin ɗakin tare da yi masu bayani a tsaitsaye na cewa sun zo fitar da su ne, sannan ya ce su je ba ɓata lokaci, suma basu ɓata lokaci ba wajen mikewa su bi bayansa, saboda Allah ya gani sun gaji da wannan bakar gida ta bakaken azzaluman. Kafin su fito Aseef ya kashe waɗan nan mutane dukka, yana tsaye a harabar wajen yana aikin gyara agogon hannunsa da suka kwance mashi a wajen faɗa, ko a jikinsa, bai sha wahalar faɗa da su ba sam sam. Nunawa su Dr Salman Aseef ɗin Areef ya yi yana faɗa masu su je wajensa, shi kuma bari ya nemo sauran jama'ar da suka zo ɗauka. Ba musu suka amsa da to, suka wuce izuwa wajen Aseef ɗin, shi kuma Areef ya sake komawa yana leƙa ɗakunan. Suna zuwa Aseef ya rungumi Dr Salman yana faɗin "Welcome ɗan tsoho". Duk da cewa Dr Salman bai san su waye su ba a gare shi, bai hana ya rungumi Aseef ɗin ba shi ma. Yana ƙoƙarin yiwa Aseef ɗin magana ne suka jiyo muryar Areef daga ɗaya daga cikin ɗakunan dake wajen yana faɗin "Aseef come and see something". Kallon Dr Salman Aseef ɗin ya yi. "Ɗan tsoho ku jirani a nan kada ku motsa ina zuwa". Ya kai karshen maganar tare da sakin Dr Salman ɗin, da sauri ya nufi in da suka jiyo muryar Areef ɗin. Yana zuwa ya faɗa cikin ɗakin, sai kallonsa Dr Salman yake yi har ya kurewa ganinsa, ɗan tsoho yaga rayuwa iya ganin idanunsa, baki ma ba zai iya faɗar irin abin da Dr Salman ya fuskanta na kalubalen rayuwa ba, sai dai muce Allah ya kuɓutar da su. Aseef yana faɗawa cikin wannan ɗaki me zai gani? Heartbeat nasa ne a ɗaure cikin wasu sarkoki. Wani irin sanyi ya ji a ransa, da sauri ya karisa gareta, Areef yana ta ƙoƙarin yanda zai yi ya kwance waɗan nan sarkokin, shi kuwa Aseef ɗin yana zuwa ya rungumota yana faɗin ya yi missing nata over. Ita kuwa tana ganinsa ta sa mashi kuka, yi take yi babu kama hannu yaro, haka ya hau rarrashi, sai gaya mashi abin da ta gani da abin da suka yi mata take yi, baya sauraronta ma, shi dai burinsa kawai ta yi shiru, amma ta kiyi sam sam, shi kuma Areef yana ta ƙoƙarin yanke waɗan nan sarkoki. Can kuma ko me ya tuna, sai ya fara karantawa sarkokin karatun Alqur'ani mai girma, nan take suka fara kwancewa suna zubawa kasa, kan kace me sarkokin duk sun zama gari, hakan kuma tasa ɗakin ya yi wani irin haske, sannan kuma ya fara wani irin rugugi tare da surutai da wasu irin muryoyi marasa daɗin ji. Cikin hanzari Areef ɗin ya ce "Kai Aseef da matsala fa a dakin nan, ku wuce da wuri mu fita". Sam Aseef ɗin bai kula shi ba, ya rungume Heartbeat tasa suna kashe juna da shagwaɓa, su gabaɗaya ma sun mance a ina suke, har lokacin sai kuka take zuba mashi, shi ma ya biye mata suna wannan aiki dai da suka saba, wanda already kun san halinsu idan suka haɗu, shagwaɓa babu kama hannun yaro. "Aseef wai ba zaka barta sai mun fita daga ɗakin ba?". Ko ajikinsa, babu tsoro ko ɗigo a tattare da shi, cikin kwanciyar hankali ya ce "Kai Areef kasan tun yaushe ban yi kissing nata bane? Kai ba zaka bar mutun ya sakata ya wala ba, Allah ba zanzo ba sai na gama kissing nata har na ƙoshi". Girgiza kai Areef ɗin ya yi tare da nufarsu, Aseef sai ya sa an yi masu kisan walaƙanci sannan hankalinsa zai kwanta, ban da iskanci ma irin tasa, ana ta rai waye kuma yake ta wani kiss? Ya bari su rayu mana, daga baya ayi komai, yana ganin yanda komai yake ƙoƙarin lalace masu, ga shi har yanzu basu ma san ina Lion yake ba tukunna. Yana zuwa ya ja hannun Akilar yana faɗin "Idan kika biyewa Aseef duk sai mun mutu kamar dabbobi a nan, ke daɗi masoyi ko?". Janyota Aseef ɗin ya sake yi yana faɗin "Wai kai ka bari mana, ka sani ne ko kiss na karshe zan yi mata, idan bamu kai ga fita ba aka kashe mu kamar yanda aka kashe sauran fa? Ni ka barni na yi abinda zan yi Hai........" Bai rufe baki ba suka fara jin jijjigar ginin ɗakin, alamar suma ruguje ɗakin ake son yi da su a ciki, tamkar yanda aka yi wa su Mark kenan. Ihu Aseef ɗin ya kurma tare da shagwaɓe murya yana faɗin "Wayyo Areef mun shiga uku, shikenan zamu mutu ba tare da Heartbeat ta haifa mani baby's ba, wayyo ni Aseef naga ta kai'na". Wani irin harara Areef ɗin ya wurga mashi. Aseef ɗin nan mugun ɗan rainin wayo ne wlh, ji yanda yake kukan shagwaɓa kamar ba yanzu ya gama jibgan karti maza a waje ba!. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 25/4/2024 E15 Wani irin harara Areef ɗin ya wurga mashi. Aseef ɗin nan mugun ɗan rainin wayo ne wlh, ji yanda yake kukan shagwaɓa kamar ba yanzu ya gama jibgan karti maza a waje ba!. "Areef yanzu me abin yi, ni fa wlh bana son na mutu". Ko kallon arziki Areef ɗin bai yi mashi ba, bare ya sa ran zai amsa mashi, hannun Akilar kawai ya ja suka nufi kofar fita da gudun gaske, da ya ga ba zata iya gudun bama, sai ya ɗauketa cak, shi kuma Aseef ɗin yana tsaye yana zuba kukan shagwaɓa. Bayan Areef ya fita da Akila sun tsaya a waje ne, sai ya sauketa tare da dafa kansa yana faɗin "Dama na sani ai, Aseef our heartbeat kuma our headache, wato da gaske yana tsaye a cikin ɗakin kenan? Ya zan yi dole naje na lallaɓa shi ya fito, Heartbeat ki jirani a nan". Ya kai karshen maganar tare da juyawa da sauri ya koma cikin ɗakin. Gabaɗaya bangon ɗakin sai ruguzowa yake yi, amma Aseef yana tsaye yana zuba kukan shagwaɓa, shi dole sai Areef ya zo ya rike hannunsa shi ma, a kan me zai kama hannun Akila kawai, wato yanzu sun fi son Akila a kan shi kenan? Shi ne fushin da yake yi. Da sauri Areef ɗin ya dawo cikin ɗakin, hannunsa ya zo ya riko yana faɗin "Shikenan muje to". Bubbuga kafa ya fara yi yana faɗin "Yanzu ka dai'na sona, sai da ka fitar da Heartbeat shi ne ni zaka ce nazo daga baya, Allah ba zan yarda ba, ni babu in da zanje, kawai ka barni na mutu tun da kun dai'na sona........". Bai kai karshen maganar ba bangon ɓangaren hagu ta ruguzo. A dubu ɗari ya rungumi Areef ɗin yana faɗin "Wayyo daddyna, wayyo my Lion, na shiga uku zamu mutu, Areef ka ceceni bana son mutuwa". Gabaɗaya kan Areef ya kulle, wai shin Aseef ɗin nan wani irin mutun ne? Yanzu ka ganshi cikakken jarumi, anjuma kuma ya koma shagwaɓaɓɓe na kin karawa, ji yanda yake kukan baya son ya mutu, ya zo su fita kuma ya ce bai san wannan ba, shi ya yi fushi saboda an fara fitar da AKILA, yanzu kenan an daina son shi. Shi ma Areef ɗin rungume shi ya yi yana rarrashinsa a kan ya yi hakuri su tafi to. Bai kai ga rufe baki ba kamar daga sama ya ji Aseef ɗin ya sunkuce shi, ya ɗaga shi sama sun yi waje a guje. Suna fita ɗakin ya rufta mai gabaɗaya. Bai sauke ɗan uwan nasa a ko'ina ba sai a kusa da Akila dake tsaye tana faman sharar kwallah. Mamaki ya hana Areef ɗin yin wani kataɓus, yau kuma ko a ina Aseef ya samo karfin ɗaukarsa kamar ɗan baby kuma oho? Abin mamaki baya karewa. Shi kuwa Aseef ɗin yana sauke Areef ɗin sai ya faɗa jikinsa yana mai cigaba da kukan shagwaɓarsa kamar ba shi ne yanzun nan ya gwada wata zazzafar jarumta ba. Ture shi Areef ɗin ya yi ya nufi wajen su Dr Salman yana faɗin "Heartbeat dama kayanki ne, kin fi kowa sanin halinsa a yanzu, sai ku fama, ki rarrashe shi, ni bari na nemo maku hanyar fita daga wannan bakin kazamin gidan, ku fita, idan ya so zamu biyoku daga baya". Ya kai karshen maganar dai'dai lokacin da ya karisa wajen Dr Salman. Matsowa Akilar ta yi ta faɗa jikin Aseef ɗin tana mai cigaba da zuba mashi kuka babu kakkautawa. Rungumeta sosai ya yi tare da dai'na nashi kukan ya hau rarrashinta, ta tsorata sosai baiwar Allah, ta sha wahala, duk ta fita a hayyacinta, a haka ma fa dan tana matsayin jika ga Queen ɗin kenan, ba dan haka ba, da sai yaya? Taga kaɗan daga cikin abubuwan da Rimsha ta gani, a gaban idanunta aka fasa cikin wasu mutane biyu aka ɗebi wasu abubuwa, a gaban idanunta aka shanya gawa kamar busasshen kifi, a gaban idanunta aka yi abubuwa da dama, ita ma dan Allah yasa tana da tsawon kwana ne, da ita ce a kan layi yanzu, ba dan zuwansu Aseef ba, to da ba makawa ba zata kai gobe ba. Areef kuwa magana ya fara yi da Dr Salman a kan ko ya san wani abin dangane da gidan nan. Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Na shafe shakaru sama da talatin da uku a nan, amma har yau ba zan iya ce maka ga takamaimen abin da suke yi ba bayan kashe mutane da ɗibar jini da wasu sassa na jikin ɗan adam, sannan har yau ban taɓa ganin gini na farko ko kuma na karshe na wannan gida ba, sai dai kuma, na san da akwai wata hanya da Duna ya taɓa gaya mani, ya ce ko bayan sun ɗauke shi, idan zan iya na bi wannan hanya zan tsira daga wannan gida, sai dai kuma hanyar tana da haɗari, sannan tana da nisa sosai, kuma a karshen hanyar da kawai kofa da zata fitar da kai waje gabaɗaya, bayan hanyar da su Rimsha suka fita, wannan ita ce hanya ta biyu ta sirri a cikin gidan, sannan ya ce mani idan har ina tafiya a kan wannan hanya, to kada na juya baya, komai zan ji na tafi kawai, abin da yasa ban fita ba, saboda komai ya kare mani, ina jin ko nafita bani da kowa a duniya, kuma ya ce hanyar tana da tsawo sosai, so ba zan iya doguwar tafiya ba, ni kaɗai ne kuma, dan a lokacin, sun ɗauki mai taimaka mani ɗin, wato Mustapha, shi ne mai taimakona dama, to sun rabani da shi, sun mayar da shi cikinsu, suna can suna ƙoƙarin juyar da shi izuwa nasu, a halin yanzu ma ina ga sun mayar da shi ɗaya daga cikinsu ɗin, wannan dalili yasa na ce gara na cigaba da zama a nan ɗin kawai har ranar da rai zata yi halinta". Shiru Areef ɗin ya yi yana jinjina wannan al'amari na Dr Salman, abin gwanin ban tausayi, shekara ɗai ɗai har talatin da uku a cikin wannan bakin azzalumin gidan? Gaskiya Queen ta azabar da bawan Allah nan, ko da ace iya ajiye shi kawai ta yi, bata yi mashi komai ba, wlh masifar da yake gani wanda suke aikatawa kawai ya isa ya kashe shi idan da kwanansa ta kare, Allah sarki, da Allah ya ƙaddara kwanansa na gaba, shi ne har ya kawo iyanzu duk da irin masifu da yake gani, Allah ne kawai zai bi masu hakkinsu, dan kome aka yi wa Queen a yanzu, wlh ba'a biya ko mutun ɗaya abin da ta yi mashi ba, yanzu a kalla ba'a akasaraba wannan Daular Mutuwar ta haura shekaru hamsin da kafata, sai Allah ne kaɗai zai iya kiyaste rayukan da aka salwantar a cikinta, ya ilahi ya lillahi. Rugujewar sauran ɗakunan dake gefe da gefensu ne ya dawo da Areef ɗin daga duniyar tunanin da ya afka, da mamaki ya ɗago kai yana bin ɗakunan da kallo, sai rugujewa suke yi tamkar waɗan da ake jijjigewa. Anya lafiya kuwa? Areef ɗin ya tambayi kansa. Aseef kuwa kara kankame Akila dake kankame da shi gam ya yi, saboda tsoro, ta tsorata ne da ganin yanda gine ginen suke jijjigowa da kansu, sai ruguzowa suke yi, tamkar katafila ce take watsi da su. "Aseef let's go, saboda ina ganin gabaɗaya ruguje arean nan ake son yi, so tsayawarmu a nan babban haɗari ne, ka kawo Heartbeat ta tafi da su baba ta hanyar da ya gaya mani yanzu, zamu cin masu a hanya idan mun gane a in da Lion yake". Cewar Areef kenan. Kankameta ya kara yi yana faɗin "No Areef su baba ɗin su je kawai, ita Heartbeat tana nan tare da ni". "Aseef ba da wasa nake yi ba, kada ka yi ka salwantarwa da yarinyar nan rayuwa, ka barta ta bisu". "Nima ai Areef bada wasa nake yi ba, babu in da zata je, muna tare da ita". Dr Salman ne ya sa baki ta hanyar cewa "Jikana da ka bari mun yi abin da ɗan uwanka ya ce, dan wannan gida ya wuci tunaninka". "Baba ni fa ba zan rabu da Heartbeat ba, ai dama ta ce zata soni komai wuya komai daɗi, kuma idan ma aka bata zaɓi a kan mutuwa, to zata zaɓi mu mutu a tare, dan haka kunga ita already a shirye take da ta mutu a tare da ni, please kada ku dame mu, ko ba haka ba Heartbeat?". Tana daga kwance a saman kirjinsa ta amsa mashi da cewa "Haka ne, a tare zamu mutu". Girgiza kai kawai Areef ya yi, waɗan nan sun yi nisa, sam ba zasu ji kira ba, idan ka biyewa Aseef sai ya sanyaka hawan ruwa ba na jini ba. Tsananin jijjigar da gine ginen wajen suke yi ne yasa suka dawo cikin hayyacinsu, da sauri Aseef ɗin ya riko hannunta tare da raba jikinsu, cikin hanzari ya nufi su Dr Salman ɗin yana faɗin "Wayyo Areef menake ji da gani haka? Kada fa waɗan nan gine gine dukka su faɗo mana a kanmu, ya kamata mu gudu, dan ni dai gaskiya ban shirya mutuwa a yanzu ba, sai na sami magaji tukun nan........" Bai gama rufe baki ba gine ginen suka fara ruguzowa tamkar waɗan da karapila take jijjigewa. Cikin hanzari da zafin nama suka yi maza suka fara ƙoƙarin barin wajen. Dr Salman ne ya nuna masu hanya, a in da suka bi ta wata kofa dake ta yamma. Suna tafiya da sauri sauri, gine ginen ɗakunan bayansu na rugujewa kamar ba lafiya ba. Ganin Ayla zata basu matsala ne yasa Areef ya sauke jakar bayansa, a in da ya dawo da jakar ta gaba, sannan ya goya Aylar a bayansa, dan ba karya ta galabaita iya galabaita, ta sha bakar wahala, da kyar baiwar Allah take iya jan kafafunta, hakan kuma zai sanya har gine ginen su ruguzo a kansu ba tare da sun fita daga wajen ba, shi ne yasa Areef ɗin ya goyata, shi ma Aseef goya Akila a bayansa ya yi. Sun yi tafiya mai nisa kafin su cikaro da wani ɗaki, ƴan mata guda uku ne rufe a cikin ɗakin, buɗe masu kofa Aseef ya yi, duk da basu san su ba, amma sun taimaka masu. Haka suka cigaba da tafiya, duk wani ɗaki da zasu gani, in dai da akwai mutane a ciki, to sai sun buɗewa mutanen, su ce su biyo bayansu, tun suna su kaɗan, har suka kai kusan su 40 a wannan tafiya tasu, har a lokacin kuma basu cinma wannan hanya da Dr Salman yake son nuna masu ba, wanda kuma ta nan ne kawai za su bi su fita. A can gida kuma, abubuwa sai ƙoƙarin rikece masu yake yi, yau da wani irin azababben zazzaɓi Rimsha ta tashi, ga tsananin ciwon kai, tun safe take zuba barcin wahala, har misalin karfe 4, shi ma sai da gwaggo ta ga barcin ya yi yawa, sannan ne ta tasheta. Tana tashinta sai kuma me? Wani sabon tashin hankali suka afka, dan kuwa Rimshar tana tashi ta fara tambayar gwaggon wacece ita? Babbar magana. Zaro idanu waje sosai gwaggon ta yi, idanuwan nata tamkar za su faɗi kasa, cike da mamaki a samar fuskanta ta ce "Rimsha ni yau kuma kike tambaya wacece ni?". Wani irin harara ta watsawa gwaggon da waɗan nan dara daran fararen Sleeping eyes ɗin nata, ta ɗauki tsawon a kallah minti biyar kafin ta amsa mata da "E mana wacece ke? Kin wani zo ki zaunawa mutane a waje". Shiru gwaggon ta yi, ta rasa me zata sake ce da Rimshar. A haka Brr Naurat ta shigo ta samesu. Da mamaki take tambayarsu lafiya suka yi wani cirko cirko da idanu haka. Nisawa gwaggo ta yi tare da gyara zamanta, sannan ta ce "Mummy wai Rimsha ce take cewa bata sanni ba yau kuma". Murmushi kaɗan Brr ta saki tana faɗin "To kin dai san halin masu ciki, wata kila yau kuma da irin halin da ta tashi kenan, ai sai ki rabu da ita ki kama wani abin ko? Idan lokacin da ta dawo dai'dai ya yi, sai ki zo ki yi mata maganar da dama zaki yi mata ɗin". Ta kai karshen maganar tare da zama a gefen bed ɗin. Hakika dukkansu basu ɗauki zancen Rimsha na cewa da ta yi bata sannu ba da mahimmanci, gani suke yi dukka shirmene da kuma laulayin ciki, ita kuma ba wani shirme, har ga Allah da gaske take yi, bata sansu ba, gabaɗaya ƙwaƙwalwarta an ɗauke shi ne aka kifa shi, ta mance da komai na rayuwarta, da kuma kowa, ita kanta ma ta mance da ita wacece. Tashin sense!!. Komawa ta yi ta kwanta tana wani irin ɓata rai tare da ɗaure fuska sosai. Daga gwaggon har Brr Naurat ɗin babu wanda ya sake kulata a cikin ɗakin, da haka barci ya sake yin awon gaba da ita, yau tun da ta yi sallar asuba, bata sake yin wani sallah ba, dan ita kanta bata san wacece ita ba bare ta san cewa ita musulmace ko Kristar, wannan shi ne tashin hankali, to meyasameta kuma? Wanene ya juyar mata da tunani? Meyasa aka yi mata hakan?. Ku kasance da Alkalamin FATEEMA ZAHRA MUSA, PRINCESS TEEMA, alkalamina ne kawai zai iya warware maku wannan cankwakiyar. Hira Brr Naurat da gwaggo suka fara zubawa, ita kuma Rimsha ta mayar da barci. Baki ɗauke da sallama Jehan ta shigo cikin ɗakin. Saman bed ɗin ta haye tare da tada kai da laps na gwaggo, da kallo ɗaya zaka yi mata kasan cewa tana cikin tsananin damuwa, har ƴar rama ta yi, ta yi wani fiki fiki da ita, tamkar ba Jehan D.P.O kuma jarumarmu ba. Shafa kanta gwaggon ta fara yi tana faɗin "Babyn daddynta waye kuma ya taɓo mani ke?". Tamkar jira take yi a yi mata tambaya, sai kawai ta sa kuka, hawaye wani na bin wani, Allah mai iko, yai Jehan ce take kuka da hawayenta? A lallai abu ya yi tsamari. "Subhanallahi, Jehan lafiya kike kuka?". Cewar gwaggon. Brr Naurat ma dai abin da ta tambaya kenan, lafiya take kuka?. Cikin kuka ta fara magana kamar haka "Gwaggo ko na kira number Yah Areef bata shiga, kuma yau tsawon kwanaki fa basu dawo ba, babu wani zancensu ma, ni na rasa ya zan yi, wlh kirjina ciwo yake yi mani, please gwaggo ki ce ya dawo, ba zan iya ba..........." Kasa karisa maganar ta yi, saboda wani kuka daya kubce mata. Soyayya muguwar wasa, ta yi mata mummunar kamu, Allah sarki baiwar Allah, ba zata iya jurar rashin shi a kusa da ita ba. Rarrashinta gwaggo ta fara yi, yau ga uwar miji tana rarrashin matan ɗanta a kan matar tana kewar ɗan, Allah mai iko, abin mamaki dai baya karewa, sam babu kunyar gwaggo a tattare da Jehan, babu wani abin da ya sauya a yadda suke da, ita bata yi mata ma kamar gwaggonce ta haifi TRIPLETS ɗin ba, ita dai iya abin da ta sani shi ne, Gwaggo, gwaggonta ce, kuma abokiyar rigimarta, ta zuba mata shagwaɓa san ranta, ita kuma gwaggon ta biye mata, bayan haka ita bata wani san da cewa ana jin kunyar uwar miji ba. Da kyar da suɗin goshi gwaggon ta samu ta shawo kanta, da kyar ta yi shiru, ta hakura ta dai'na kukan, sai dai fa na ciki na ciki, kewar dai babu abin da ya ragu, har wani zazzaɓi take ji. Haka suka kasance har Anaya ma ta shigo ta same su, ita ma nata sabon babin kukan ta zo ta buɗe masu, yau dai suna ganin ikon Allah, haka suka fara rarrashinta ita ma, har sai da ta hakura ta yi shiru, daga haka kuma barci ne ya yi awon gaba da ita. Ba su suka farka ba har sai da gwaggo ta tashe su a kan lokacin sallar mangariba ta yi, su tashi su yi sallah su yi wa mazan nasu a addu'a. A nan ne Gwaggo ta ga abin mamaki abin al'ajabi. Wannan abin mamaki ba komai bane face Rimsha, tana tashi ta barci da aka ce ta je ta yi sallah, buɗar bakinta sai cewa ta yi menene kuma Sallah? Babbar magana. Zaro idanu suka yi, gwaggon zata daka mata tsawa, Brr Naurat ta yi saurin dakatar da ita, saboda ta lura tamkar da kawai matsala a tattare da Rimshar, abin ku da manya, ƙwaƙwalwarsu da tunaninsu ba irin na yara bane, har ta harbo da akwai gagarumin matsala a tattare da jikar tata, wanda su gwaggon kuma basu gane ba. Dan haka sai ta ce kowa ya je ya yi sallah, ita kuma Rimsha ta kwanta ta cigaba da yin barcinta, su kyaleta kada su sake yi mata magana. Da mamaki cike fal a fuskar gwaggon ta ce "Mummy sallah fa zata yi, kuma kice a barta kada ta yi? Ya haka kuma? Ai Rimsha yanzu idan ta ce ba zata yi sallah ba, to wlh da itace zamu karya mata kafa, dan ai ba yarinya bace tun da har da ciki a jikinta, uwa fa take shirin zama". Jama'a ina ganin ikon Allah, karfi da ya ji gwaggo ta mayar da Rimsha mai ciki, ko me ta gani a jikinta da har ta dage a kan lallai ciki ne da ita? Ku tayani dubawa my readers, ita dai Rimsha bata taɓa yin sunna da Lion ba, har yanzu virgin ce ita, amma an zage a kan tana da ciki, to koma me dalilinsu na cewa hakan, lokaci zai nuna mana komai. "Aisha tun da na ce ku bar Rimsha, to ku kyaleta kawai, idan kika cika matsawa, to ba makawa zaki tabka danasani mai girma, dan haka ku kyaleta ki je ki yi sallarki". Cewar Brr Naurat. Okey kawai gwaggon ta amsa mata da shi, sannan ta miƙe tsaye tare da nufar toilet, ita kuma Brr Naurat ta karisa tashin su Jehan a kan su je su yi sallah. In takaice maku wannan labari, Rimsha dai bayan wannan uban barci, to bata iya aikata komai, ko wanka bata yi, baiwar Allah, sai Allah ne kaɗan yasan menene matsalarta!. Haka Brr Naurat ta rinƙa lallaɓata tana ririta ta, sai dai kuma ba abin da take cewa face su gaya mata su waye su? Bata sansu ba. Abin ya ƙullewa gwaggo kai, ita kuwa Brr Naurat sam bata damu ba, dan izuwa yanzu ta gama yardanwa kanta cewa jikar tata ba lafiya take ba, da akwai gagarumin matsala a kasa, hakan yasa bata wani damuwa. Su Abba kuwa, suna can hankalinsu a tashe, sai adduo'i suke yi tare da bincikar ina Aseef, securitynsa Abban Imran ya kira a waya, ya sanyasu suka je suka shigar da report a kan ɓatar na Aseef, su kuma suna gida Lion ya hana fita. A ɓangaren Aafia dai babu wani sauki, sai ma abin da ya cigaba na rashin lafiya, duk ta kara ramewa, ta bushe sosai, ta yi wani irin duhu mai munin gaske, abin gwanin ban tausayi, kuma har yanzu bata amsawa kowa komai, daga ido sai ido. Akil, Imran da Irfan gabaɗaya tarewa suka yi a masallaci suna zubawa TRIPLETS addu'ar fatan nasara a tafiyarsu, Allah ya karesu ya dawo da su lafiya. A ɓangaren Katsina gidansu Sadiq kuwa, Allah mai iko, shagon Yusuf dai sai kara bunƙasa take yi, yanzu har da fridge ya sanya a ciki, yana sayar da kayan sanyi, abubuwa sun cigaba, shi ma Sadiq Alhamdulillah, abubuwa suna tafiya mashi yadda ya kamata, sai dai kuma kullum yana cikin tunanin Jehan, bawan Allah, yana tsananin sonta, bai san cewa matar wani ce a yanzu ba. Maman Sadiq a yanzu abubuwa sun saukaka mata, girkinta har da nama da kifi, sau uku take girki a rana, gabaɗaya ta fita daga harkar baban Sadiq ɗin, dan dama baya tsinana mata komai, yanzu Allah yasa ƴaƴanta sun fara tsayuwa gam da kafafunsu, abu dai sai dai muce Alhamdulillah, wani lokaci har kaji biyu Sadiq yake sayo mata, ya yanka mata, ta gyara masu, ta zuba mashi miya mai shegen daɗi, Allah ya taimaketa ya bata ƴaƴan masu zuciyar nema da kuma zuciyar taimaka mata dukka biyu, dan wani yaron yana da zuciyar nema, amma kuma kuɗinsa bata ciwuwa, ba zai taimaka ba, ita dai ta yi sa'a, daga Sadiq ɗin har Yusuf ɗin burinsu kawai suga sun yi mata abu, su ganta a cikin tsananin fariniki suna kyautata mata, shi ne muradinsu, kuma hakan ce tasa Allah yake taimaka masu, komai suka saka a gaba, sai sunga dai'dai, dan uwa ba wasa ba!!! Uwa ba wasa ba!!! Uwa ba wasa ba!!! Ku ruke wannan da kyau, duk mai son yaga dai'dai, to ya sanya mahaifiyarsa farinciki, ko da iya murmushi kawai kasanya mahaifiyarka a rana, to ba makawa wannan rana ba zata wuce ba har sai wani abin alkhairi da zai sanyaka farinciki ya wanzu a gareka, bare kuma ace ka yi wa mahaifiyarka abin da har zata buɗe baki ta zuba maka albarka da ruwan adduo'i, haba ai ranar abin alkhairi da zaka fuskanta sai Allah ne kawai zai san adadinsa, ina mai kara jan hankulanku ƴan uwa, a kula da uwa, abi umarninta koda babu daɗi matuƙar bai kaucewa dokar Allah ba, hakan zai sanya muga dai'dai a dukkan al'amuranmu, mu jikanta, mu tausaya mata, iyayenmu sun yi mana komai a duniyarnan, komai muka yi ba zamu taɓa biyansu ba! Sai dai mu kwatanta iya abin da zamu iya sanyasu farinciki kawai. To haka dai rayuwar su Sadiq take a yanzu, shi kuma baban nasu, gaula wanda ya rako maza duniya, yana can har iyanzu yana tare a gindin amarya, sai yadda ta ce haka za'ayi, yadda ta dama haka zai sha, naira na aiki, duk zaginsa da ƴan unguwa suke yi, wlh ko a jikinsa, haka Amarya zata yi mashi ɗinki, ko kunya baya ji zai saka kayan a jikinsa yana washe baki, Sadiq bakinciki kamar ya haɗiyi zuciya ya mutu, yana ji yana gani idan baban nasa ya yi wa Amaryar ba dai'dai ba, a tsakar gida zata kwashe mashi duk wasu albarka dake a tattare da shi, ta tsine mashi, ta yi mashi zagin kare dangi, amma dan rashin zuciya, zuciya ta mutu, haka zai yi ta bata hakuri, kuma bata hana shi ya sake komawa gindinta ya tare, abin dai ba'a cewa komai, Sadiq dai ba dan mamansa ba, da yaronnan ya haɗiyi zuciya ya mutu, saboda kunci da bakin cikin irin wannan hali na babansa, yarinya karama kamar amaryar nan da bata wuce sa'arsa a wajen shekaru ba, ta tsaya tana cin mutuncin mahaifinsa, ai kunsan dole zai ji zafi, dan fa uba uba ne komai lalacewarsa, Allah Ubangiji ka bawa kowa iyaye masu zuciya, masu sanin yakamata, masu sanin darajar kansu, masu sanin mutuncin kansu, ba masu kwaɗayin duniya ba, Allah ka karawa namu muku iyayen lafiya, ka kuma saka masu da mafificin alkhairi. Wannan shi ne rayuwar su Sadiq kuma. Idan muka dawo Kaduna kuwa, bayan sallar issha, Brr Naurat ce ta taka da kanta har izuwa part nasu daddyn Rimsha. A lokacin suna tare da mum suna hirar duniya. A palo ta zauna tare da yi masu sallama. Jin cewa ita ce yasa dukkansu har su Abba basu ɓata lokaci ba wajen fitowa. Da mamaki suke kallonta har suka kariso izuwa in da take, a saman sofa kowannansu ya zauna, sai binta da idanu suke yi, suna jiran karin bayani. Ta ɗan ɗauki mintina da a kallah za su kai biyar tana tunani ba tare da ta yi magana ba. Can kuma sai ta fara magana a nutse. "Nawazuddeen a gaskiya Rimsha tana cikin gagarumin matsala, kuma ga halin da muke ciki a yanzu, babu wanda aka yarjewa ya shiga gidan nan ko ya fita sai su Imran, Akil da kuma Irfan, suma dan tarewa da suka yi a masallaci ne, amma yana da kyau mu san matakin da zamu ɗauka, ba zai yi wu mu barta a cikin ciwo har haka ba, babban tashin hankalin ma shi ne rashin sallah, ba zai taɓa yiwuwa mu barta bata sallah ba har zuwa su Saif su dawo, dole kafin su dawo mu san abin yi". Ta kai karshen maganar tana jan doguwar numfashi tare da saukewa a hankali. Har suna haɗa baki wajen cewa "Me kuma yake damunta?". Nan ma shiru Brr ɗin ta ɗan yi, sai jinjina al'amarin a ranta take yi, abin ya bata mamaki kuma ya ɗaure mata kai. "To bana ce ba, amma yanzu abin da za'ayi kuzo muje ku yi mata karatun Alqur'ani mai girma, ko Allah zai sa a samu sassauci, dan fa ikirari take yi ma na cewa ita bata sanmu ba, mun ce mata to shikenan mun ji bata sanmu ɗin ba, kuma mun yarda, amma ta tashi ta yi sallah, shi ne ta ce bata san shi ba, kunga kuwa ai akwai gagarumin matsala, da farko ma na ɗauka dukka laulayin cikin nata ne yasa ta ce bata sanmu ba, amma da ta ce bata san menene sallah ba, sai na fahimci ba batun laulayin ciki bane, wata matsa ce ta daban". Shiru daddynta ya yi yana tauna zantukan na Brr, shi kuma Abban Imran cewa ya yi. "Gaskiya wannan matsala ce babba, bata san me sallah ba kuma? A dole mu nemi mafita, yanzu dai ina take? Muje sai muga me yakamata mu yi mata". Haka suka rankaya izuwa ɗakin gwaggon, suka baro su mum ko wacce a ɗakin mijinta, bama su san me yake faruwa ba. Har lokacin barci Rimshar take yi, tun abincin safe da ta ci, ƴar tahalikan nan bata sake sanya komai a cikinta ba, ko ruwa, da alama ciwon bayan ta yi breakfast ne ya bugeta, dan ba shakka ta yi sallar asuba lafiya lou. Tana barci basu tasheta ba, dan Brr ta ce kada a tashe ta, su yi mata addu'ar a haka, dan haka sai suka fara yi mata topi ta ko'ina, duk suka haɗu a kanta. Ko motsawa bata yi ba, tamkar wadda babu rai a jikinta, ba dan sauƙar numfashi kaɗan kaɗan da suke ji nata ba, to da sai su ce babu rai a tattare da ita. Sun ɗauki tsawon lokaci suna tofa mata addu'a, amma ko motsawa bata yi ba. Abin ya ɗan bawa daddynta mamaki, sai dai bai bayyana hakan ba, ya dai cigaba da yi mata topin kawai. Daga karshe Brr Naurat ta ce su barta kawai, zuwa gobe da safe In Sha Allah sai a kirawo su Imran a waya, su dawo gida a san abin yi. Okey suka amsa mata, shi dai daddynta ya amsa ne kawai saboda mahaifiya ba wasa ba, basu ja da maganarta, amma ba dan haka ba, a daren nan ya so ya ɗauketa su je neman magani, dan abin ya ɗaga mashi hankali!!, Barema yanda ya ga fuskarta ta kara wani irin haske, ita da take chocolate color, to ta kusa kai Jehan haske a yau, ga face ɗin nata ya ɗan kunbura kaɗan, abin dai ba'a cewa komai, tana a cikin matsala ainun. Da haka suka koma ɗakunansu, ita kuwa Brr Naurat ta gyarawa Rimshar kwanciya tare da rufa mata bargo, sannan ta ce gwaggo ta koma ɗakinsu Rimshar ta kwana da Jehan, su barta da Rimshar a nan. Okey gwaggon ta amsa tare da cewa "Zan je ɗakin Saif na kwana kawai, kyale Jehan ɗin nan, ba zan iya rigimarta ba yau ɗin nan, dan sam yau bana jin daɗi". Ta kai karshen maganar tare da nufar kofar fita. Kiranta Brr ɗin ta yi a kan ta dawo. Ba musu ta koma ta zauna, nasiha mai ratsa jiki Brr ɗin ta yi mata, dan tasan cewa ba wani rashin jin daɗin jikinta da take ji, kawai tunanin TRIPLETS nata ne ya sakata a gaba, ba dan Brr ɗin ma tana yi mata faɗa da nasiha a kullum ba, ai da abin sai ya fi haka. Sosai ta ji nasihar mahaifiyartata, ta kuma yi alkawarin In Sha Allah zata cire damuwar a ranta, za kuma ta kara tsananta masu addu'a sosai. Da haka suka yi sallama, ta wuce ɗakin Lion dan ta kwanta, ita kuma Brr Naurat ta gyara ta kwanta a kusa da Rimshar, baiwar Allah sai barci kawai take ta zubawa ba ci ba sha. A ɓangaren Daular Mutuwa kuwa. Sunci bakar wahala na kin karawa, sun azabtu kafin nan su kai wajen da Dr Salman ya ce masu hanyar take. Sai dai kuma ko da suka je wajen babu wata hanya a wajen, wayam wajen take. Jugum jugum suka tsaya suna mayar da numfashi, ga kuma gine ginen gidan cigaba da rugujewa yake yi, idan har basu hanzarta nemo hanya ba, to har in da suke ma sai ya ruguje ya rufta da su. Sauke Ayla daga bayansa Areef ya yi, sannan ya fara kewaye a wajen yana nema masu ko da akwai wata makama da zata nuna da alamar hanya ta sama ko ta kasa a wajen. Ita kuwa Aylar, yana sauketa ta zube kasa a saman gwiwowinta, cikinta ne yake wani irin murɗa mata, tamkar cikin yana son fita daga jikinta ne, ta wahala ne aihun. Sauke Akila shi ma Aseef ya yi, ita ma yana sauketa ta zuba kasa a saman gwiwowinta, tana mai da numfashi. Shi ma Dr Salman zama a wajen ya yi, saboda wajen tiles ne fari tas da shi, babu alamar kazanta a wajen. Ganin hakan yasa duk sauran jama'ar da suka biyusu, suma sai suka zauna a kasa a wajen ɗin kawai. Wasa wasa cikin Ayla na kara tsananta mata ciwo, tun tana dannewa har ta fara ruwan hawaye, sam Areef ko Aseef babu wanda ya lura da halin da take a ciki, sun tafi dubawa ko za su ga hanya a wajen. Da AKILA ta ga yanda ta dafe cikin nata tana murkusoso, sai ta daure ta matso kusa da ita, cike da kulawa ta rungumota, daman kunsan ita Akila akwaita da son ƴan uwanta da dangi, tana da tausayi sosai. Haka ta rungumo Aylar tana tambayarta meyake damunta take kuka. Kasa yin magana ta yi, Dr Salman ma matsowa kusa da ita ya yi, sun zaci wahalar hanya ce, sai suka fara ƙoƙarin rarrashinta. Sai kuma me, jini suka fara gani ya fara bin kafafunta. Sosai Akila ta tsorata, hakan yasa ta zunduma ihu tana faɗin "Heartbeat jini, jini matar bappa Maik take zubarwa sosai". A tsananin rikice ta yi maganar, saboda bata taɓa ganin jini na fita dayawa daga jikin mace har haka ba, shi ne abin ya tsoratata. A tare Aseef ɗin da Areef ɗin suka juyo da kallonsu a kansu, da yake shi Areef ya fi su tausayi, a dubu ɗari ya nufo in da suke, dan ya duba me matsalar. Sai dai kuma bai kai ga karisowa ba, a dai'dai tsakiyar wajen, filin ta ɓurma da shi ya zurma kasa. Tashin sense, shikenan Areef ya rufta!. Kafin Aseef ɗin ya yi wani yunkuri, ilahirin wajen gabaɗaya ya fara wani irin jijjiga yana ƙoƙarin ruftawa da su......... ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 26/4/2024 E16 Kafin Aseef ɗin ya yi wani yunkuri, ilahirin wajen gabaɗaya ya fara wani irin jijjiga yana ƙoƙarin ruftawa da su. Da Aseef ɗin ya ga haka, sai ya yi amfani da nasa tunanin, cikin ƙanƙanin lokaci ya binciko ƴar hanyar da take a wajen, a hanzarce yasa karfi ya buɗe kofar hanyar, ta cikin kasa take. Ya sha bakar wahala kafin ya buɗe masu, sannan ya ce su zo su fita ta wajen. Ayla ba zata iya miƙewa ba, dan haka sai ya kamata ita da Akila da Dr Salman, ya ce da sauran mutane kuma su bi ta hanyar su tafi. Da sauri suka fara dira a hanyar, shi kuma sam bai ji kyamar jinin dake jikin Ayla ɗin ba, ya ɗauketa cak, ya goyata a bayansa, da kyar ta iya ruke wuyarsa, saboda tsananin azabar da take ji. Haka ya riko hannun Heartbeat tasa, sannan ya ce da Dr Salman ma ruke ɗayar hannun Heartbeat, komai zai faru kada su yarda su sake hannun juna. To suka amsa mashi da shi. Da ɗan ɗaga murya ya ce duk su rufe idanunsu, dan yasan halin AKILA sarai, yanzu idan taga ta in da zasu faɗa, to haukace masu zata yi, ga shi ba damar ya goyata, saboda Ayla tafita bugatar taimako a halin yanzu. Suna rufe idanunsu, ya jasu da karfi, gabaɗaya suka tafi suka faɗa ta in da Areef ya faɗa. Suna faɗawa bai fi da minti biyu ba, gabaɗaya ginin dake wajen ya ruguje ruguzum. Suna faɗawa basu sauka a ko'ina ba sai a ainahin cikin fadar Queen da suka kwashe tsawon kwanaki suna ne ma, ashe su suna a sama da fadar ne ma, fadar tata tana a cikin kasa. Suna dira a tsakiyar fadar, cikin hanzari ya sauke Ayla dan su dubata, su ceci rayuwarta, bai ma lura da cewa a fadar Queen suke ba. Sai bayan ya sauke Ayla ɗin ne ya ɗago kansa da nufin ya ce da Akila ta bashi ɗankwalin kanta. Yana ɗago idanu suka yi ido huɗu da Lion da yake zaune a saman kujerar mulkin Queen ɗin. A dubu ɗari ya ɗago kan nasa da kyau, dan ya kalli shin abin da yake gani gaskiya ce. Ba shakka Lion ɗin ne yake zaune kamar yanda ya gani tun farko, gabaɗaya jikinsa duk jini, da alama ya sha gwagwarmaya ba kaɗan ba, ya jingina kansa da jikin head na sofar, sai sauke numfashi yake yi a hankali hankali, yana wani irin nishi, alamar ya gaji over, daga hannunsa, kirjinsa, fuskarsa wajen kumatu, dukka jini ne ya ɓata shi, babu riga a jikinsa, ainahin kakkarfa kuma kyakkyawan surar jikinsa na cikakkun jaruman maza a bayyane, sai binsu da blue eyes nasa kawai yake yi abinsa. A dubu Aseef ɗin ya miƙe tsaye yana kallonsa da kyau, a hankali ya fara bin cikin fadar da kallo. Can ya hango ƴar Queen ɗin a ɗaure da sarka, Lion ya yi mata ɗaurin goro, ita kuma Queen ɗin tana kwance flat a tsakiyar fadar, tamkar gawa, ko motsawa bata yi, da alama rai ya yi halinsa ne, ga kuma hannunta ɗaya babu shi, da alama Lion ya sare mata hannu ɗaya ne, alamu sun nuna ba karamar faɗa suka gwabza a tsakaninsu ba, dan kuwa sun ruguje komai na cikin fadar, babu abin da ya rage mai amfani a cikin fadar. A hanzarce ya nufi Lion ɗin, tsabar a galabaice Lion ɗin yake ya kasa tambayarsa meya kawo shi nan? Ya aka yi kuma ya zo? Ya sha mamakin ganinsa sosai, sai dai ba zai iya yin wani magana ba. Bai kai ga karisawa wajen Lion ɗin ba, sai ga Areef ya fito daga wata ɗaki dake a cikin fadar, hannunsa na ruke da wasu kyallaye farare guda biyu. Wajen Lion ɗin ya kariso yana faɗin "Saif bari na ɗaure maka hannun nan naka dake zubar da jini da wannan tsummar, sai na ɗaukeka mu fita daga wajen nan, idan ba haka ba, duk zamu mutu, kasan dai gabaɗaya gidan nan rugujewa zai yi ko? Tun da dama mafiya yawan ɓangarorin gidan ba ginasu aka yi ba, da tsafi aka yi su, to yanzu mai tsafin ma ta mutu, kaga suma dole ne su mutu, dan haka ka yi sauri muje". Ya kai karshen maganar yana karisowa kusa da Lion ɗin sosai. Ɗaga mashi hannu Lion ɗin ya yi, alamar baya da bukatar a ɗaure mashi hannun nasa, ya bar mashi abinsa. Bai yi ja in ja da shi ba, sai ya bar mashi, dan yasan ba zai ce a bar mashi hannunsa jininsa na zuba haka kawai a banza ba. Da kyar Lion ɗin ya yunkura ya miƙe, wani irin jiri yake kallo, yau tsawon kwanaki bai ci komai ba, sai gwabza yaki yake yi da mukarraban Queen har ya iso gareta, shi ne yasa ya galabaita sosai, kuma ko da ya iso gareta, ba ƙaramin yaki suka yi da ita ba, ta wahala shi ma ya wahala kafin ya samu ya kasheta. Na san zaku so jin ya akayi hakan ta faru, to ku saurara. Shi Lion already ko da ya shaki kamshin turaren da Queen ɗin ta shaka masu a gidanta, to shi bai suma ba, saboda askar na safe da ya yi, askar na safe idan ka nutsu ka yi shi, Ubangiji ya yi alkawarin Mala'iku ne zasu kula da kai, babu abin cutarwa da zai sameka har izuwa maraice, idan ka yi na maraice, to Mala'ikun zasu sake kulawa da kai har izuwa gobe da asuba, wannan faɗar Allah da manzonsa ne, kuma ya yi karatun Alkur'ani mai girma sosai kafin ya baro gida, sannan ya yi adduo'i ba kaɗan ba, dan yanda yaga Rimsha ta rikice, sai ya ɗauki abin serious, shi kuma Areef da yake bai san ya Daular Mutuwa take ba, tun da Rimsha ba matarsa bace, bai san halinta ba, sai bai ɗauki abin serious ba, bai yi wani addu'a ba, shi dai ya saɓi jaka kawai, ya lodi kaya kamar wanda zai je honey moon da matarsa, to a takaice dai shi Lion ko da ya shaki kamshin turaren, bata yi mashi komai ba, ya kwanta ne shiru kawai tamkar ya suma, dan yana son shigowa cikin Daular Mutuwar ta kowace hali, a tunanin Queen, ita ce ta yi wasa da kwakwalwarsu, ta kuma kafa masu tarko, ta yi nasara suka faɗa, bata san cewa ita ta faɗa tarkon ba, ba ita ta kamasu kamar yadda take tunani ba, Lion ne ya kamata a cikin tarkon nata da ta kafa masu da kanta, wasa da tunaninta sosai ya buga, bata taɓa tunanin hakan zai faru ba. Lokacin da ta rufe shi a ɗakin duhu, ta kuma daure shi, duk yana jinsu, yana a cikin hayyacinsa, ya yi masu abin da zaki yake yi idan zai farauci abinci ne, kwanciyar ɗaukar rai ya yi masu, abin da basu taɓa zata ba. Waɗan nan sarkokin da suka ɗaure shi dai, already kun san sarkokin tsafi ne, dan haka yana karanta masu Alqur'ani mai girma, duk suka ruguje, suka zama gari, sai dai ya sha bakar wahala sosai kafin ya fita daga cikin ɗakin duhun. Yana fita kuma bai nemi kowa ba, sai ita Queen ɗin, sam bai nemi ina su Areef suke ba, dan yasan idan ya kamata to tamkar ya gano dukkan in da ƴan uwansa suke ne, saɓanin shi Areef da ya tashi sai ya fara neman Lion ɗin, da yake kowa da irin kaifin kwakwalwarsa da tunaninsa, kuma babba kam ko da minti ɗaya ya fika, to ko yaya babba ne, ya fika, shi ne yasa Lion ɗin ya fisu hangen nesa, dan ya fisu a komai. Yasha bakar wahala sosai a wajen neman Queen ɗin, ya yi faɗa da mukarrabanta sosai. Tsawon kwanaki yana nemanta, a hanyarsa na neman nata ne ya kashe su barbushi, ya yi nasarar kashesu ne da taimakon Allah. Haka ya yi ta fama har ya gano in da shegiyar fadar tata take. Time da ya shigo fadar, babu kowa a ciki sai ita da ƴarta, duk ta tura mukarrabanta domin su kamo mata su Areef, bata san shi ma Lion ɗin ya fito ba, da taimakon sunan Allah ya ɓacewa idanuwan tsafinta, hakan tasa bata ga fitowarsa ba. Tana ganinsa ta miƙe, da tsafinta ta yi ƙoƙarin damko wuyarsa ta janyo shi, dan ta hallaka shi. Already kafin ya shigo cikin fadar tata da bismillah ɗauke a bakinsa ya shigo, dan haka sai ta kasa kama shi ɗin, ta yi ta faman gwadawa, amma ina takasa. Shi kuma yana tsaye gam, kamar wani jarumin sadaukin yaki. Ganin ta kasa saka hannunta a jikinsa ne yasa ta fara ƙoƙarin tura mashi kayan tsafe tsafenta, dan su illatar da shi, to a nan ne aka samu wannan fashe fashen kaya da suka rinƙa yi a cikin fadar, sai da ta fasa komai nata da kanta. Da ƴarta ta ga haka, sai ta yi ƙoƙarin tayata yakin, shi kuma Lion ya ɗauko wani wuka dake a wajen ajiye wukakensu, wuka ce mai tsananin kaifin gaske, ya yi amfani da ita ya sarewa Queen ɗin hannunta na dama ba tare da ta ankara ba, ya cire mata hannun tun daga sama wajen shoulder ta. Yana datse hannun nata ya kai hannunsa ya cire zobben dake a jikin babbar yatsarta, wannan zobbe ba komai bane face karfin tsafinta, shi ne karfinta da komai nata, idan babu shi, to ita ba koman komai bace, already dama yasan da irin wannan zobbe, duk wasu cikakkun matsafa suna amfani da wannan zobbe, duk matsafan da basu da shi, to da sauransu, har yanzu basu kai shegu ba, akwai wata kungiyar matsafa da ya taɓa tarwatsawa a New York, suma haka ya datsewa shugabansu hannu, ya ɗauki wannan zobbe ya jefata a cikin wuta, daga nan alkadarin tsafin ta karye. To ita ma Queen haka ya yi mata, yana cire zobben ya zura a aljihunsa, da ta ga haka, sai ta fara ƙoƙarin yin faɗar hannu da shi da hannu ɗaya, ga bakar azaba tana ji a hannun nata, amma saboda karfin hali, sai bata karaya ba, ta fara faɗa da shi, dan ta kwaci zobben. Bugu ɗaya ya yi mata a bayan kunne ta wajen wuyarta, daga haka bai kara na biyu ba rai ya yi halinsa, dama kunsan ta tsufa, ta kai shekaru 45 zuwa 50 a duniya, to bugu ɗaya mai lafiya Lion ya yi mata, shikenan ta ce ga duniyarku. Already dama shi Lion kun sani, zaratan maza ma ya suka kare da shi? Da duka ɗaya yake kai mutun in da zai yi danasani har ƙarshen rayuwarsa, bare kuma ita Queen da take mace, macen ma tsohuwa, ai dukansa ɗaya ma ya yi mata yawa. Ita kuma ƴarta Lion ɗin ya kamata ya ɗaureta, a cewarsa, bai yi tunanin irin hukuncin da yakamata ya yi mata bama tukun nan. Yana kashe Queen ɗin kuma wasu zaratan maza suka shigo cikin fadar, matasan igbo ne, kyawawa da su majiya karfi, su goma sha biyu cif. Ganin abin da yake faruwa ne yasa suka fara ƙoƙarin kashe Lion ɗin, to da sune ya yi faɗar nan da suka ji mashi ciwo, jikinsa duk jini, sun ji mashi ciwon ne kuma ta hanyar dogayen faratunan yatsun hannunsu da suke da shi, kun san soft skin nasa kuma, tana da laushi tamkar fatar jariri, ya ji hutu ya ƙoshi, to shi ne idan suka yagushe shi sai wajen ta yi jini, hakan yasa suka sami kalaba ta ji mashi ciwo sosai a jiki. A garin dukansu kuma ya yanke da wuka sosai a hannu, shi ne wajen da Areef ya ce zai ɗaure mashi yaki yarda. Wannan shi ne a takaice abin da ya faru, abin da yasa gine ginen wajen kuma suke ruguzowa da kansu, saboda already da tsafi aka yi su, to kuma tsafin dake a cikin gidan a halin yanzu ya karye, komai ya lalace, dole gidan ta ruguje.......... To kun ji yadda aka yi, har kullum PRINCESS TEEMA ce taku ta amana mai abin ban mamaki🤙. STORY. Cikin wata iriyar kasalalliyar murya, can kasa kasa Lion ɗin ya ce "Areef ka ɗauko Mark mu tafi, ya sami karaya a kafa, he can't walk by himself". Zaro idanu sosai Areef ɗin ya yi yana faɗin "Lion what are you saying? Mark fa ka ce?". Jinjina mashi kai kawai ya yi ba tare da ya sake yin magana ba, saboda idan ma ba dan yana da taurin zuciya ba, Allah ko mikewa ba zai iya yi ba, dan tsananin yunwa, kuma dama already kun san shi baya da jumuriyar yunwa sosai, Areef ya fishi jure yunwa, amma shi da Aseef, sam basu shiri da zancen yunwa sam sam, sai dai kuma, basu cin abinci dayawa, idan sun ci kaɗan Alhamdulillah sun ƙoshi. "I think Mark he already dead?". Ya faɗa fuskarsa ɗauke da mamaki ƙarara a bayyane. Ko sannu Lion ɗin bai sake ce masu ba. "Where is he?". Cewar Areef ɗin. Da kyar Lion ɗin ya iya nuna mashi wata hanya da take a cikin fadar. Da sauri ya nufi hanyar, shi kuma Lion ɗin ya fara takowa a hankali yana nufo su Aseef. Ganin yanda yake tafiya da kyar da kyar ne yasa Aseef ɗin ya kariso wajensa da sauri. Yana zuwa ya taimaka mashi suka karisa wajen da su Dr Salman suke tsaye. Ayla baiwar Allah azaba tasa ta sume, har lokacin kuma jini take zubarwa. Kallo ɗaya Lion ɗin ya yi mata ya kawar da kansa gefe guda, wani iri yake ji a cikin zuciyarsa, ga tunanin Meeshansa, ga bakincikin da yake ciki na cewar Aseef ba ɗan uwansu bane, ga bakin cikin abin da su Josephine suka yi masu na cin amanar mahaifinsu, sannan suka ci amanarsu suma, abubuwa sun taru sun yi mashi yawa a cikin zuciyarsa, ba dan yana da dakiya da juriya ba, da ya jima da faɗuwa kasa, da makiya sun yi galaba a kansa, sai dai ya rigasu ya ce Allah, dan haka Allah yake dafa mashi a koda yaushe, hakan tasa a kullum sai dai ya kara tsayuwa da kafafunsa gam, ba dai ya je kasa ba. Areef ne ya fito daga wannan ƴar siririyar hanyar ɗauke da Mark ɗin a saman kafaɗarsa, baya ko motsi, da alama a sume yake. A kusa da Dr Salman ya kwantar da Mark ɗin yana faɗin "Ina sauran sojojin kuma?". "The already dead, remain 2". Lion ɗin ya bashi amsa a takaice tare da wucewa ya nufi kofar fita daga fadar, dan fadar dab take da ta ruguje. Sake ɗaukar Mark ɗin Areef ɗin ya yi, shi kuma Aseef ya ɗauki Ayla dake sume gwanin ban tausayi, duk sun jigata na kin karawa, duk wanda ya gansu a wannan hali, babu shakka sai ya tausaya masu, yau Lion da kansa da kyar yake tafiya, ko daga nan kun san bala'in Daular Mutuwa ta wuce tunanin mai tunani. Sun ɗan yi tafiya mai ɗan nisa kafin su kai wata kofa dake fuskantar gabas. A tab bakin kofar Lion ya tsaya ba tare da ya buɗeta ba. Sai kuma ya duƙa kasa a wajen, a hankali ya buɗe wata kofar kasa dake a wajen, sannan ya miƙe tsaye. In a cool voice ya ce masu su zo su shiga, nan ne kawai kofar da ta rage ta fita a gidan, duk saura sun ruguje, su yi sauri dan in da suke ɗin ma, dab yake da rugujewa, abu kaɗan ya rage. Da sauri suka karisa wajen, ɗaya bayan ɗaya suka shi ga. Lion ɗin ne ya sake ce da Areef ya koma ya ɗauko sojoji biyu da suka saura da ransu. A tare suka koma da Aseef, bayan Aseef ɗin ya sauke Ayla a cikin wannan hanyar kenan. Da sauri suka ɗauko su. Suna fita daga cikin fadar ginin ta ruguzo a kan ƴar Queen ɗin da ita kanta Queen ɗin. Daga in da suke suna jiyo sautin ihun ƴar Queen ɗin, amma babu wanda ma ya ji cewa tamkar mutunce take ihun neman taimako, ga shi ba halin ta gudu, dan Lion ya ɗaureta, haka gini ya ruguzo a kanta, da haka ta mutu. Sai dai fa sun sha ruwan mamakin jin ihun mutane sosai a lokacin da ginin yake rugujewa, hakan na nufin da akwai sauran mutane a cikin gidan, Allah sarkin ginin nata rugujewa a kansu, dan kofofin ɗakunan duk a rufe suke, ba halin su gudu, sai dai wasu daga cikinsu, sun samu sun iya buɗe kofar sun gudu, sun nufi sauran ɓangarori na cikin gidan, fatan mu dai Allah yasa su sami hanyar fita, suma su tsira, ko ina Mustapha da Kausar?. Bayan sun shiga cikin wannan hanyar dukkansu, Lion ne na karshe da ya shiga, sai da ya tabbatar dukkansu sun shiga, bayan ya shiga, sai ya janyo kofar ya rufe. Bayan ya Rufe ne ya tsaya ya tsare Aseef da dara daran idanuwan nan nasa. Ƴan kame kame Aseef ɗin ya fara yi, dan wlh idanun Lion mugun rikita mutun suke yi, musamman idan ya tsareka da su ba tare da ya yi magana ba, duk sai ka ji ka tsargu, ko da kuwa baka yi laifi ba, sai yasa ka rasa nutsuwarka, haka shi ma Aseef ɗin ya yi, duk sai ya rasa nutsuwarsa, ya kama ƴan kame kame kamar wani tsohon munafuki. Ko sannu Lion ɗin bai ce mashi ba, ya sa kai ya nufi wajen da Ayla take kwance, ɗan duƙawa ya yi a kusa da ita, a hankali ya kai hannunsa ya saɓeta a saman kafaɗarsa, sannan ya ruke hannun Dr Salman da hannunsa ɗaya, bai ce da kowa komai ba ya kama hanyar fita. Ganin haka yasa Aseef ya ɗauki soja guda ɗaya, shi kuma Areef ya ɗauki Mark, suka bar soja ɗaya a wajen. Kasancewar tafiyar Lion yana da sauri, hakan yasa ya yi masu nisa sosai. Can saman wani dutse ya kwantar da Aylar, sannan ya juyo ya dawo dan ya ɗauki sojansa ɗayan da yake a bakin kofar shiga hanyar. Duk sojojin suna a sume, kuma babu ruwan da za'a zuba masu su farfaɗo. Duk da ciwon da yake jikinsa, da wahalar da yasha, hakan bai sa ya ji cewa zai iya barin wannan sojan nasa a wajen ba, saboda amana da kuma sanin darajar rai irin nasa. Har cikin ransa yana jin zafin jikinsa, amma haka ya ciza laɓɓansa gam ya saɓi sojan nan a saman shoulder ɗinsa. A hanya bai kai ga karisawa wajen da ya kwantar da Aylar ba, ya ci karo da Areef, karɓa mashi sojan Areef ɗin ya yi, ba musu ya miƙa mashi sojan suka cigaba da tafiya. A takaice a haka sai da suka yi tafiyar kwana ɗaya da wuni ɗaya cur a cikin wannan hanyar, ba dan Allah ba, da ba zasu taɓa kai labari ba, sun sha wahalar da ko makiyinka ba zaka yi mashi fatar ko makamancin irin hakan ta faru da shi ba. Da yake hanyar yana da faɗi, kuma yana da reshuna, ma'ana hanyar ta rabu kashi kashi. Kun tuna hanyar da su Rimsha suka bi suka fita? To ɗaya ne daga cikin reshen wannan hanyar, ta kasu ne kashi kashi, to suma haka suka cigaba da tafiya a cikin wannan dutse, har Allah yasa suka fita. A wajen fita ma ba karamar gwagwarmaya suka sha ba, dan an rasa wanda zai iya jijjige masu kofar ya buɗeta su fita, duk sun galabaita fiye da tunanin mai tunani, shi kansa Aseef ɗan dirama, yanzu ya yi laushi, bare Heartbeat nasa da Dr Salman, ai ba'a magana bayin Allah. Daga karshe dai Lion ɗin ne ya daure ya cije ya buge masu kofar tare da taimakon Aseef, shi kam AREEF ya zama tamkar Aseef a baya yau, ya yi laushi over, ga bala'i yunwa. Suna buge kofar wani irin hasken rana ne ya haske masu idanu, dukkansu sai da suka datse idanuwansu, kafin daga baya su sake buɗewa a hankali. Lion ne ya fara sako kafafunsa waje, dan shi ne babba, shi ne yakamata ya fara fita, dan yaga ya yanayin hanyar take. Kungurmin dajin nan ne da su Rimsha suka fita ta wajen, sai dai su Rimsha ta baya suka fito, su kuma ta gaba suka fito, dama kunsan hanyar tana da reshuna. Ganin wannan dajin ne yasa ya ce su fito kawai su tafi, zasu cinma gari a gaba ai. Wahalar dai su fita gari ne, suna fita gari koma ina ne komai zai saukaka masu, dan su ko'ina suka je, to dole masu ruke da mulkin garin su tarbesu hannu bibbiyu, dan ko a kasar America da kanta moryiyinsu tana da matuƙar kaifi fiye da tunanin mai tunani, ga shi kuma su taurari ne na faɗin Washington DC da kewayenta, ta ko'ina ana ji da su fiye da tunanin mai tunani, so wahalar ta dai a yanzu su fita gari ne. Cigaba da tafiya suka yi ta yamma maso arewa, bama su iya gane gabas ba bare yamma, su dai in da ya fi yi masu, in da suke ganin zai fi masu sauki, nan suka bi. Da yake rani ya shigo, damuna ta tafi, sai ya zamana ƴaƴan itatuwan dake a dajin sun fara ƙarewa, haka dai suka cigaba da tafiya. Sun yi tafiya mai nisa sosai daga in da suka fito, sannan ne Lion ya zauna a kasar wata bishiyar mangoro mai matukar girma, kusan kamar bishiyar kuka. Abin mamaki a kasar wannan bishiyar su Rimsha suka fara zama time da suka fito, dan hanyar da su Lion ɗin suka biyo, ya zo ya haɗu da hanyar da su Rimsha suka biyo, dan idan baku manta ba, ta yamma su Lion ɗin suka juya suka bi, hankan ce ta mayar da su ta wancan hanyar. Dukkansu zama suka zo suka yi a kusa da Lion ɗin, sauke Mark Areef ya yi, sannan ya shiga cikin dajin, dan ya nemo ruwa, su samu su yayyafawa sojojin nan su faffaɗo, idan suka farfaɗo, komai zai zo masu da sauki, zasu rage wahala ta ɗaukarsu. Jingina kansa da jikin itacen Lion ɗin ya yi, a hankali ya lumshe idanuwansa, wani barcin wahala ce ta ɗan ɗaukesa a wajen, ita ma Akila kwanciya ta yi a kasar, tare da tada kai da laps na Heartbeat nata, tana kwanciya sai barci, shi ma Dr Salman kwanciya ya yi, ya yi barci bawan Allah, ita Ayla, dama already a sume take. Kafin Areef ya dawo, duk sun yi barci, ya ɗebo ruwa a cikin wata gora da ya gani a wajen, sai a lokacin ya tuna da jakarsa da ya barota a fadar Queen, har ruwa da akwai a cikin jakar. Ajiye ruwan ya yi, sannan ya zauna dan ya mike kafafunsa ya ɗan huta, shi ma ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi. After some hours. Can cikin barci Lion ya ji motsi a kusa da su, duk da ya san suna da yawa a wajen, amma wannan ba motsin mutun bane, mutsin wata dabba ce, kunsan shi dama already bashi da nauyin barci, dan haka sai ya farka. A hankali ya buɗe idanuwansa. Wata zabgegiyar kunama ce a kusa da Aseef dake jingine da jikin itacen yana barci shi ma, ga Heartbeat ta yi barci a saman cinyarsa, shi Lion already dama ya saba da irin wajen nan, wanda ya fi haka haɗari ma sun zauna a ciki kafin ya taka matsayin da yake a kai yanzu, ai dama soja bai kamata ya ji tsoro ko kuma ace waje irin wannan ta zamar mashi bakuwar waje ba, musamman ma sojoji irinsu na Usa. Dan haka sai ya kai hannunsa ya kama kunamar, tana ƙoƙarin kai mashi harbi, ya yi maza ya damki karin nata, da karfi ya tsige daga jikinta ya gefar gefe guda. Yana gefarwa sai ya ji wani motsi daga ɗan nesa da su, alamar tafiyar mutane ne. Lumshe idanuwansa ya yi yana mamaki mutane kuma a wannan dajin?. Bai buɗe idanu ba har sai da ya ji isowar mutanen kansu. A hankali ya waro idanuwansa a kansu. Mutanene sun kai su 10, kaɗan ne daga cikin mutanen da su Areef suka taimaka a cikin Daular Mutuwar, su ne waɗan da Aseef ya buɗewa kofa suka fita. Sannu suka yi wa Lion ɗin cikin harshen yarabanci. Mayar da idanuwansa ya yi ya lumshe, a cewarsa basu ishe shi kallo ba, ba zai ɓata idanuwansa wajen ganinsu ba. Wata daga cikinsu ne ta yi magana cikin harshen turanci, a in da ta ce "Laaa kuga abin mamaki, ga shi yana zaune a wajen, ga kuma zanen face nasa a jikin itacen da yake zaune ɗin! Ko dai shi ne ya zana? Amma kuma kamar zanen ya jima!". Jin sun ambaci sunan zane ne yasa ya waro idanuwansa, dan shi dai yasan Meeshansa ce kawai ta iya zana shi, kuma ba shakka ya ga tulin zanensa da ta yi a cikin Daular Mutuwar, a hanyarsa ta zuwa neman Queen, a lokacin ya ci karo da wani ɗaki, yana shiga ya tatda zanen face nasa da yawa a ciki, duk tabi jikin bango ta zana, wannan ɗakin kuma ba ko'ina bane face ɗakin da Rimshar ta zauna, idan baku manta ba dama ta yi zanensa sosai a wajen. A hankali ya juyar da kallonsa izuwa kan in da matar take nunawa, dan ya kalli zanen da idanunsa. Bai yi mamaki ba, kuma da kallo ɗaya ya yi wa zanen ya gane tabbas zanen Rimsha ce, saboda zanenta baya ɓuya mashi, tana barin alama guda ɗaya a jikin zanenta idan ta yi, wannan alama kuma ba komai bane face a duk in da ta zana face nasa, to sai ta zana mashi lips nata a saman kumatunsa, alamar ta yi kissing na zanen, so a dukka zanensa da ta yi a rayuwarta, da akwai wannan alamar ta kiss ɗin. Mai da idanuwansa ya yi ya lumshe yana tunani yanzu duk irin wannan wahala ta wannan hanya haka Meeshansa ta biyo? Yanzu haka ta keta wannan kungurmin daji haka? A gaskiya Queen ta cuce shi dayawa, ta wahalar mashi da pleasurensa, dole Rimsha ta ce ba zata dawo Daular Mutuwa ba, ashe azaba ta sha na kin karawa baiwar Allah, ya zama dole idan ya koma gida ya kula da ita sosai....... Yana tsaka da tunanin ne mutanen suka katse mashi tunanin da cewa sun zo su taimaka masu ne, da akwai abinci da ruwan sha a masaukinsu, su zo suje sai su ci.................Lallai rashin sani yafi dare duhu, basu san wanenen Lion ba, da sam bama za su zo in da yake ba bare suce ya zo ya ci abincinsu da suka girka da ita ce duk hayaki, abincin ma a dajin suka samo shi, sai Allah ne yasan menene ma, sai kuma su da suka girka, to shi Lion da ma bai iya cin abincin Nigeria ba! Ai ko sau ɗaya bai taɓa gwada cin abincin Naija ba, bai iya ba, baya ma son kamshinta, ina da tabbacin ko yunwa zata kashe shi ba ci zai yi ba, komai haɗin da za'ayi wa abincin Naija da wuya ya iya ɗanɗanawa, abinci mai rai da lafiya wadda ta amsa sunanta abinci ma kenan, ina ga kuma wannan abincin nasu na ƴan gudun hijira? Ai ko kallo ma ba zai yi ba bare ci, zai ce datti ce, kuma kun san shi da bala'in kyankyani, ai idan ya gani da ido ma, ya rinƙa sheka masu amai kenan har sai abin da hali ya yi kuma. Ko kallon in da suke bai sake yi ba, tamkar ma babu shi a wajen, da suka ga bai amsa ba, sai suka yi tunanin bai ji su bane, sai suka sake yi mashi magana. Wani irin tsawa ya daka masu na su tashi su bashi waje, dan sun ishe shi. Bayin Allah har wani firgita suka yi, su da suka zo taimako, dama sun ga cewa Areef da Aseef sun taimaka masu ne, shi ne suma suna ganin a yanzu sun sami dama, bari suma su taimaka masu, basu san waɗan nan ba'ayi masu goninta ba, ai TRIPLETS barsu kawai a yanda ka gansu, dan sun wuce tunaninka, sai kana tunanin yau zaka gansu a fari, sai ka gansu a ja, haka suke, baka gane ina suka dosa, sam su ba'a yi masu goninta, kuma ba'a burgesu, idan ba yanzu ma da suka sami mata bane abin ya ragu, da a baya ne ai ba'a ma magana. Tsawar nan da ya daka masu ne yasa su Areef suka farka daga barcin da suke yi. Kallon sama da kasa Areef ya watsawa mutanen, a lokacin kuma already sun juya zasu koma wajensu. Miƙewa ya yi ya ɗauko robar ruwan da ya ajiye, a gaban sojojin ya dawo ya tsugunna, a hannunsa ya tarbo ruwan tare da fara yayyafa masu a face nasu. Kusan a tare bayin Allah suka farka, ganin sun farka ne yasa ya ajiye ragowar ruwan, ya koma kusa da Ayla dake kwance bata ko motsi. Shiru ya ɗan yi yana tunanin, shin ya dubata ne? Ko dai ya barta kawai sai sun isa gida? Dan ko ya ce zai dubata ma, sam babu kayan aiki, babu komai a tattare da su, ga shi kuma cikin jikinta ne ya fita, aiki take bukata na musamman. Daurewa dai ya yi ya kyaleta ba dan ya so ba, bawan Allah yana da tausayi sosai. Mikewa Lion ya yi ya nufi cikin dajin, dan ya duba ya wajen yake, bayan ya karɓi Jacket ɗin dake jikin Aseef. Shi kuma Areef ya fara ƙoƙarin tattare kansu, dan su tafi, ya yayyafawa Mark ma ruwa, bayan ya farfaɗo, sai ya saɓesa a saman kafaɗarsa, kasancewar ya sami karaya a kafar tasa, da haka suka mike suka fara tafiya, Lion kuma ya shige cikin daji, Areef ya ce su je Lion ɗin zai samesu a gaba ai, ya san halinsa sarai, ga sauri a wajen tafiya, zai yi saurin cin masu. Haka suka cigaba da tafiya, Lion bai sake haɗuwa da su ba har sai da rana ta kusa faɗuwa, a can gaba da nisa sosai ya cin masu, ya wanke jikin dake jikinsa, ya wanke face nasa sosai, ya yi salloli dake a kansa da sauran abubuwa, ya saki dark black cuirly hair nan nasa, ga shin ma yanzu ta kara tsawo sosai, ya jima bai rage tsawonta ba. Ya sha ruwan mamaki yanda ya rinƙa ganin zanen face nasa a wannan daji, abin ya yi matuƙar burge shi, wani irin azababben kaunar Meeshantasa ya kara ji a ransa, burinsa kawai ya je gida ya ganta, yana tsananin kewarta, ji yake yi kamar a kan kaya yake da bata nan a kusa da shi, baiwar Allah, duk ta bi ta zane face nasa abinta, ba shi kaɗai ya yi mamaki ba, har da sauran abokan tafiyar tasa, kowa ya yi matuƙar mamaki na ganin zanensa a jikin itatuwan dake a dajin, ga zanen ya fito ɓaro ɓaro gwanin birgewa, kamar ka kira shi ya amsa, sai dai babu wanda ya yi gigin yi mashi magana a kan zanen, ko Areef bai yi mashi maganar ba, dan bai ga fuska ba, ya bari sai sun je gida, idan suka huta zai yi mashi tsiya a kan zanukan, sojojinsa sai kallon zanen suke yi suna satar kallonsa, Meesha ta ja mashi, Allah ma yasa sojojin kwara biyu ne kawai suka gani, sai Mark wanda already ya san komai. A haka suka kwashe kwanaki suna tafiya a cikin wannan dajin, banda ƴaƴan itatuwa babu wani abin da suke ci. Da kyar suka iya kaiwa cikin wani ɗan ƙaramin kauye dake kusa da dajin. Tun da suka sako kafafuwansu a cikin wannan kauye, kowa dake cikin kauyen ya zuba masu idanu, sai kallonsu suke yi tamkar sun ga bakin halittu daga wata duniya ta daban, su kuwa ko kallon mutanen kauyen basu yi ba, suka cigaba da tafiya a galabaice. Duk cikinsu babu mai ko raina biyar, haka suka cigaba da tafiya har suka fito cikin babban gari. Kai tsaye shagon sai da wayoyi Lion ya fara nufa, dan already dama basu zo da wayoyinsu ba, sun barosu kashe a gida. Sai ya ce su Areef ɗin zauna su jirasa, kada su bisa wahalar zata yi yawa, bari shi ya je, daga baya zai zo ya ɗaukesu. Abin hawa ya tara, wato mai mashi, ya hau ya ce da mai mashin ɗin ya kai shi katafaren shop na sai da wayoyi, su kuma suka zauna a wajen wani babban masallacin suna jiransa. Sun yi tafiya mai nisa kafin su kai challenge, wani kasuwar waya ce a cikin Ilorin state ɗin. A tare da mai mashin ɗin suka shiga cikin wani katafaren shagon sai da wayoyi. Kun san yarabawa da shegen son kyawawan kuma fararen mutane, sai kallon shi suke yi kamar zasu cinye shi, haushi tamkar ya kwakwale masu idanu yake ji, dan ya tsani kallon nan da suke yi mashi. Amma ba yadda zai yi, dole ya yi abin da yake a gabansa kawai. Yana zuwa ya zaɓi irin wayar da yake da bukata, sannan ya tambayi mai shagon suna karɓar transfer? E guy ɗin ya amsa mashi, da yake katafaren shago ne, akwai yaran gida dayawa a ciki, idan ka zo sayan abu, to za'a sami ɗaya daga cikin yaran shagon ya kula da kai, ainahin Managernsu kuma yana zaune a ciki, gabansa da tarin computers. Tambayarsa Lion ɗin ya yi a kan zai tura masu 2 million Naira, sai su ɗauki kuɗin wayarsu, su bashi sauran kuɗin, sun yarda za su karɓar?. Kasancewar babban shop ne, akwai kuɗi sosai a ciki, sai Manager ya ce ba damuwa ya tura kuɗin. Kum san eƴamurai da bala'in son kuɗi, da kuma daraja costumers, sun iya business over, to shagon na eƴamuri ne bana yarabawa ba, shiyasa suka yarda cikin aminci. Shi ma Lion ɗin cikin mutunci ya ce da guy ɗin da ya yi attending ɗin nasa, ya ɗan ara mashi wayarsa na minti biyar bari ya yi kira. Kun sansu akwai daraja costumers, dan haka ba musu guy ɗin ya ara mashi wayar. Karɓa ya yi, number Imran ya saka ya kira, dan ya haddace number a kansa, sama da shekarun 8 suna a tare da Imran ɗin, kunga kuwa dole ya haddace numbersa, bare ma shi da yake da kaifin kwakwalwa sosai, duk wata number da take a wayarsa idan ka tambayesa zai zayyano maka ita. Bugu ɗaya Imran ɗin ya ɗauka, a tsananin kasale ya ce da Imran ɗin zai turo mashi wata account number ya saka mashi 2m a ciki yanzu. Jin muryarsa yasa Imran ɗin bai san time ɗin da ya miƙe tsaye zubur ba, a hanzarce ya fara tambayarsa suna lafiya? A ina suke yanzu? Kuma yaushe za su dawo?. Cikin ƙaguwa ya rinƙa jefo mashi tambayoyi. Kasancewar a galabaice over yake, sai kawai ya katse kiran, dan ba zai iya biyewa Imran ɗin ya tsaya amsa mashi tambayoyin ba. Yana katse kiran ya ce da guy ɗin ya bashi account number shop ɗin nasu. A hanzarce ya kira mashi, ya yi typing ya turawa Imran ɗin. Ko minti biyu ba'ayi ba sai ga kuɗin Imran ɗin ya turo. A takaice haka suka gama ya biyasu kuɗin wayar ya karɓi saura chanjinsa, daga nan ya tambayi mai mashin ɗin ina hotel nasu mai tsananin kyau take. Mai mashin da kuɗi yake so, sai ya ce su je ya kai shi, ba ɓata lokaci suka nufi hotel ɗin. Katafaren hotel ne mai matukar kyau da kawatuwa, sai da suka tsaya a hanya ya sayi kayan sakawa a wani katafaren super market, sannan suka karisa hotel ɗin. Duk rana ɗaya ra'ina dubu ɗari biyu za su biya kowani ɗaki ɗaya. Ɗaki biyar ya kama masu, 1 million a rana kenan, Imran ya sake kira da number ɗaya daga cikin ma'aikatan wajen, sannan ya saka shi ya tura masu kuɗin ɗakunan. Daga nan ya karɓi keyas dan ya shiga ciki, mai mashin ɗin zai tafi, sai ya ce a'a ya jira shi bari ya zo zasu koma wajen da su Areef suke a tare, daga nan sai ya sallame shi. Okey mai mashin ɗin ya amsa mashi. Sama wajen ɗakunan da ya kama ya nufa, ɗaki ɗaya ya zaɓa ya buɗe ya shiga. Ɗaki ne aljannar duniya, tamkar ɗakinsa na gidan nasa na Kaduna, haka ɗakin take, sai tashin kamshi air freshener mai daɗi take yi, komai very clear. Wayar da ya saya ya sanya a charji kasancewar da akwai wutar nepa, yana so ya yi charjinta dan ya saka sim card ya kira his excellence a turo masu jirgi su bar garin nan. A hanzarce ya yi wanka, sannan ya shirya sosai cikin ƴan mintocin da basu fi 30 ba, ya fito suka tafi da mai mashin ɗin, dan ya je ya taho da su Areef. A hanya sai da ya tsaya ya saya masu ruwar roba mai bala'in sanyi da yawa, dan yasan suna jin kishin ruwa. Ganin yanda yake pacaka da kuɗi ba karamin mamaki ya bawa mai mashin ɗin ba, kasancewar shi ba wani sanin kan kuɗin Naija ya yi ba, ida zai sayi abu, ɗibar kuɗin kawai yake yi ya basu, ko sun bashi canji kuma baya karɓa, ko kallon canjin ma baya yi, hakan ce ta yi mugu mugun bawa mai mashin ɗin mamaki, duk da ya gan shi Bature jajir da shi, amma dole ya sha mamaki, dan akwai Turawa mazauna Nigeria sosai, so a tunaninsa irinsu ne, bai san Lion kam wannan karon ce zuwansa Naija ta farko ba, sai kuma ya haɗu da jarabawa, in ba haka ba ai before bai ma san Naija ba, bare kuma ya san ya take ko ya kuɗinta yake da sauransu! Shi ne yasa yake kashe kuɗin tamkar bai san ta yaya ake nemosu ba. Kai tsaye wajensu Aseef ɗin mai mashin ɗin ya mayar da shi, shi kansa mai mashin ɗin sai satar kallonsa ta cikin mirror gaban mashin ɗin yake yi, saboda ba karya Lion fa duk wanda ya gan shi, in ma mace ko na miji, to sai ya saki baki ya yi ta kallon shi babu gajiyawa, saboda tsananin kyan da Allah ya yi mashi! Ga uban farinjini da kwarjini, bugu da kari ga waɗan nan dara daran idanuwan nasa masu rikitar da mutun idan ya kallesu. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 27/4/2024 E17 Kamar yanda ya baro su Areef ɗin, haka ya dawo ya samesu. Ruwan ya fara basu, a hanzarce suka karɓa, Areef shi kaɗai sai da ya shanye roba biyu na ruwan, sannan ya kama mayar da numfashi, shi ma Aseef roba biyu ya sha, Akila rabin roba, Dr Salman ya shanye sauran rabin nata, sojojin Lion guda biyun nan kowannansu sai da ya sha roba ɗaya da rabi rabi, shi ma Mark roba biyu ya sha. Daga haka Lion ya ce su tashi su karisa hotel ɗin, daga nan su yi wanka su huta kafin ya kira His excellence. Ya kai karshen maganarsa tare da juyawa ya hau bayan mashin ɗin da suka zo, sanna ya ce da mai mashin ɗin ya tara masu taxi su hau, ba musu ya tara masu taxi guda biyu, da yake a bakin babban hanya suke, sai aka yi saurin samun taxi ɗin. Rayuwa kenan, ba ta yanda bata juyawa mutun, wai yau TRIPLETS ne da shiga taxi? Idan ba ƙaddara ba, babu abin da zai kawo su Naija ma da kanta bare har wata Ilorin state, amma da yake kana naka Allah na nashi, sai ga su har ma Daular Mutuwa ba iya Naija kawai ba. Haka suka shiga taxi ɗin, Mark da sojojin nan taxi ɗaya, Areef da Akila da Ayla suka shiga ɗayar taxi ɗin a gidan baya, Aseef kuma ya shiga gidan gaba na taxi ɗin su Areef, Dr Salman ya shiga gidan gaba na taxi ɗin su Mark, haka suka kama hanya. Gaba mai mashin ɗin Lion ya yi, masu taxi ɗin suka rufa mashi baya, bayan su Areef ɗin sun gama shiga kenan, har lokacin Areef ne yake ruke da Ayla baiwar Allah, ko motsawa bata yi ba har izuwa yanzu, ba dan zuciyarta na bugawa ba, to da sai ma su ce rai ya yi halinsa. Suna isa hotel ɗin Lion ya ɗebo makudan kuɗaɗe da a kallah za su kai 200k, ya bawa mai mashin ɗin nasa, shi fa bai san nawa ya bawa mai mashin ɗin ba, dan ko da ya bashi ma sai da ya tambaye shi ya isa haka? Ya biya shi hakkinsa ko dai sai ya kara mashi?. Bawan Allah bai san kan kuɗin Naija ba, mai mashin ɗin da yake yana da tsoron Allah, sai ya ce "Sir this money is too much, is pass my, I think this money pass 200k, my own money is only 5k, so I will going to carry my own and return the remaining change to you". Ya kai karshen maganar yana ƙoƙarin cire 5k nasa. A takaice Lion ɗin ya ce mashi kada ya damu, ya tafi kawai, dan shi bai ma san 5k a kuɗin Nigeria ya take ba, da ma dai dollars ce, ya santa a ido, ya santa a baki dukka. Kun san yarabawa da iya zuba godiya, ai kuwa wannan mai mashin ɗin yana jin Lion ya ce ya bashi kuɗin, a dubu ɗari ya diro kasa daga saman bashin ɗin nasa, cikin hanzari ya zube gwiwowinsa a kasa a gaban Lion ɗin, nan take ya fara zuba ruwan godiya, adduo'i, tare da zallar ruwan albarka da fatan alkhairi. Ko sannu Lion ɗin bai sake ce mashi ba, ya wuce ya je ya bawa masu taxi ma makudan kuɗaɗe da a kallah za su kai 100k ke. Haka suma suka fito daga cikin taxi ɗin tare da zube gwiwowinsu a kasa, suka hau engine zuba godiya. Sam bai kula su ba, bai ma bi ta kansu ba ya sa kai ya wuce cikin hotel ɗin, Areef ya ɗauko Mark ya rufa mashi baya, shi kuma Aseef yana ɗauke da Ayla, haka suka shige ciki, suka bar masu taxi zube a saman gwiwowinsu suna zuba godiya. Suna shiga Lion ya wuce bedroom nasa abinsa. Da Ayla da Akila bedroom ɗaya, Aseef da Areef bedroom ɗaya, Dr Salman shi kaɗai, su kuma sojoji da Mark nasu ɗaya. Haka suka kasa ɗakunan nasu, amma fa sun sha gwagwarmaya wajen diramar Aseef, dan ya ce babu mai raba shi da Heartbeat nasa, a tare za su kwana, Areef kuma saboda mugunta, saboda shi matarsa bata kusa, sai ya kafe a kan lallai Akila da Ayla za'a barta, dan ciwon ƴa mace ta ƴa macece, dan haka Akila zata kuka da Ayla. Kuka sosai Aseef ɗin ya rinƙa zuba masu, amma suka ki kula shi. Daga karshe dai sai ya hakura ya wuce bedroom nasu shi da Areef ɗin. Lion yana shiga cikin bedroom nasa, wanka ya sake yi, saboda tsananin zafi da rana da ake narkawa. Bayan ya shirya cikin ɗaya daga cikin kayan da ya saya, sai ya ɗebi baya kala biyu ya kaiwa su Aseef ɗakinsu, sannan ya wuce ya fita daga hotel ɗin. Su kuwa, wanka suka yi, kowa ya tsabtace jikinsa, suka sanya kayan da Lion ɗin ya kawo masu. Suna gama shiri sai ga masu karɓar order abinci sun shigo. Kasancewar su sun saba cin abincin Naija, sun ci shi a wajen Rimsha, sai suka bada order fried rice, and pepper chickens, sai ruwa da Maltina. Mai karɓar order ya amsa da okey sannan ya fita, yana fita ya faɗa ɗakinsu Mark, bayin Allah su basu taɓa cin abincin Naija ba, amma a yau basu da zaɓin da ya wuce dole su ci, kada yuwa ta illatar da su, haka suka bada order pepper cikin, dan suka ganin kamar shi ne zai fi masu. A ɓangaren Akila kuwa, order jolof rice and chips ta bada. Haka mai karɓar order ya tattara kan order tasu ya koma abinsa. Cikin ƙanƙanin lokaci ya kawo masu duk abin da suka saka order. Dukkansu babu daɗi bakunasu, amma haka suka daure suka tsakuri abincin, dan kada yunwa ta kayar da su. After some minutes, Areef ne ya fito daga bedroom nasu, ɗakinsu Akila ya shiga bakinsa ɗauke da sallama, da yake shi ya fisu tausayi, Ayla tana a cikin ransa, yana ta tunanin halin da take a ciki, ya kasa samun sukuni, burinsa kawai ya zo ya dubata, ya kuma sa Lion ya nemo likitar da zai bata taimakon gaggawa da zai taimaki rayuwarta kada ta mutu kafin su karisa gida. Kamar yanda ya kwantar da ita, haka ya shigo ya sameta. Yana shigowa bai kai ga karisawa cikin bedroom ɗin ba, Aseef ya shigo shima bakinsa ɗauke da sallama, hannunsa ruke da wata jibgegiyar leda da Lion ya sayowa su Akilar kayan sakawa a ciki. A bakin bed ɗin dukkansu biyu suka zauna, Areef ya kai hannu ya taɓa Ayla, dan ya ji har yanzu akwai sauran rai a jikinta ne. Shi kuma Aseef ya miƙawa Akila ledar kayan yana faɗin "Yanzu Lion ya dawo ya kawo maku, ya ce ku shirya da wuri, helicopter zata zo ta ɗauke mu zuwa gida". Ya kai karshen maganar tare da miƙa mata ledar. Karɓa ta yi tare da fara buɗe kayan, Abays ne a ciki, sai takalma. "Heartbeat zaki iya yi wa matar uncle wanka idan na kai maki ita cikin toilet?". Cewar Areef. Da sauri ta gyaɗa mashi kai alamar e zata iya, dan tun ɗazun take yi wa Ayalar kuka, Allah sarki, ba shakka Akila tana da tsananin tausayi kamar Areef ɗin, halinsu kusan ɗaya, dukkansu, kuma babu in da suka baro daddyn Rimsha a kamannin hali, kunga shi ma duk abin da ƴan uwansa suka yi mashi a duniyar nan bai sa ya ji cewa ba zai iya taimaka masu ba, to haka Areef da Akilar ma suke, shi Aseef yana da zuciya gaskiya, idan ka yi mashi abu ya taɓa mashi zuciya, to yana wahala ya mance da wannan abin, kuma shi ruwa biyu ne, wani lokaci yana da zafi sosai, wani lokaci kuma yana da sanyi, kun tuna time da suke Washington? Har su Uncle T bai kyale ba, to haka yake, idan ka yi mashi laifi, to ba zai yafe ba sai ya rama, ko kuma ya fita harkarka, ya zubaka a kwandon shara, shi kuma Lion ai ba wata zancen fita harka, hukunci zai baka mai kyau, daga nan kuma shikenan komai zai wuce, bashi da riko kamar Aseef. Ɗaukar Aylar Areef ɗin ya yi ya kaita cikin toilet ɗin, already Akila ta haɗa ruwa mai zafi a cikin jacuzzi, yana zuwa ya sanyata a cikin jacuzzin, sannan ya fito ya fice daga ɗakinma gabaɗaya. Yana fita wajen Lion ya nufa. Bakinsa ɗauke da sallama ya shiga bedroom ɗin, Lion ɗin yana zaune a bakin bed nasa yana aikin latsa waya. Kusa da shi ya zo ya zauna yana faɗin "Ka yi magana da su momma ne?". Bai amsa ba, kuma bai ɗago ba, ya cigaba da abin da yake yi na tsawon lokaci, kafin nan ya ɗago kansa tare da kai kallonsa a kan Areef ɗin. "Where is your phone?". Yana gida ya bashi amsa. Shiru ya ɗan sake shi kafin ya ce "A wajen waye wayar take? Momma or your wife?". Girgiza kai ya yi yana faɗin "In my room, kuma switch off nata ma na yi". Okey ya amsa mashi da shi, sannan ya mayar da hankalinsa a kan wayar tasa, tun ɗazun number Rimsha yake kira, amma taki ɗauka, hasalima wayar tana a cikin bedroom nasa, ita kuma tana tare da Brr Naurat, dan taki yarda kowa a gidan ya taɓata sai Brr Naurat, ƙwaƙwalwarta sai kara birkice masu yake yi, abu kamar wasa yana neman ya zama babbar case, sam yanzu ta dai'na magana ma, idan ka tambayeta abu, sai dai ta zuba maka idanu kawai taka kallonka, Allah mai iko yau harta daddynta da mummynta bata sansu ba, abin ya yi mugun ɗaga masu hankali ba kaɗan ba, sun shiga damuwa na wuce misali, dan ma Brr Naurat tana kwanta masu da hankali ne, da abin sai ya fi haka, a takaice dai Rimsha bata leƙawa ko palo, ko da yaushe tana kwance a saman bed ɗin Brr Naurat, wanka ma Brr Naurat ɗin ce take yi mata, yanzu ta zama tamkar jaririya, wanka ma bata iya ba, in short ba wani abin da Rimsha ta iya a yanzu, common abinci Brr Naurat ce take bata a baki, duk taurin zuciya irin ta Jehan, sai da ta zubarwa da kanwar tata kwallah ba kaɗan ba, ta sha kuka sosai, saboda Rimsha dai ita kaɗai ke gareta, ita ce kawai kanwarta, duk wannan dirama da suke yi suna tsananin kaunar junansu na wuce misali, kawai Jehan ɗin ce dama da shegen iya tsare gida yasa Rimshar bata kusantar ta sosai, amma suna kaunar juna over. Lion ya kira wayarta har ya gaji ya hakura. Hakika yana son yin magana da ita, saboda a jikinsa yana jin cewa bata da lafiya, ba lafiya take ba, dan duk lokacin da ya tuna sunanta, sai zuciyarsa ta harba, abin ya ɗan ɗaga mashi hankali, hakance ma tasa ya ce da His excellence ya sanya a turo masu jirgin helicopter kawai su koma gida da wuri, sannan da akwai abubuwansu da suka bari a airport na Enugu state, dan haka his excellence yasa ya mayar masu da shi gida. Burinsa kawai ya koma gida, da gwaggo da Rimsha sun tsaya mashi a cikin tunaninsa fiye da tunanin mai tunani. A ɓangaren su Akila kuwa, Areef yana fita daga toilet ɗin Aylar ta farfaɗo, saboda ruwa da aka sanyata a ciki. Tana farfaɗowa ta fara zuba kuka babu kakkautawa, rarrashinta Akilar ta rinƙa yi, amma taki ta yi shiru, hakan tasa Akilar ta kyaleta ta yi mata wankar kawai, bayan ta gama ta tallafa mata ta fito, sannan ta ɗaura mata towel daga kirjinta, da kyar Aylar take iya jan kafarta har suka fito izuwa cikin bedroom ɗin. Ko da suka fito basu sami Aseef a ɗakin ba, ya fice abinsa. A bakin bed ta zaunar da Aylar, ta ciro kayan da Lion ya saya masu, tare da tallafa mata ta sanya a jikinta, sannan ita ma ta wuce toilet ɗin dan ta je ta yi nata wankar. Baiwar Allah Ayla, har kumbura face nata ya yi, ta yi wani iri da ita, gwanin ban tausayi. A takaice dai sai misalin karfe 3 na yamma, sannan jirgin helicopter ya iso, basu ɓata lokaci ba wajen tafiya, Ayla dai sai ruwan hawaye take yi, cikinta tsananin ciwo yake yi mata, baiwar Allah bata taɓa jin azaba irin haka ba, dan cikin nata ba ƙaramin ciwo yake yi mata ba, shiyasa ma ta kasa daurewa har take kuka. Areef bawan Allah shi ya yi ta fama da ita, ya yi ta rarrashinta har suka dira a cikin Kaduna. Already su Imran suna airport suna jiransu. Basu ɓata lokaci ba suka fito suka nufi gida, dan akwai majinyata sosai a tattare da su, shi kansa Lion ɗin kamata ya yi ace yana kwance a gadon asibiti, amma saboda dakiya da taurin zuciya tare da karfin imani, yasa ya dake, ya ki yarda ma kowa ya duba shi, ya ce sai ya dawo gida kawai. Gabaɗaya family suna tsaye a harabar gidan suna jiran isowarsu, Rimsha, Jehan, Anaya, su ne kawai basu a cikinsu, suna ɗaki suna barci, Jehan da Anaya sun ci kuka sun ƙoshi ne har barci ya yi awon gaba da su, ita kuma Rimsha already kun san matsalar da take a ciki, an yi mata ruƙiya ma, amma shiru, farko sun ɗauka aljanu ne suka shafeta, sai da aka yi ta yin ruƙiya aka ji shirune yasa suka fahimci ba aljanu bane, wata matsala ce dai ta daban, dan haka sai suka kyaleta sai Lion ɗin ya dawo, dan sun san halinsa, kada su kira malami ko a kaita wajen magani ya dawo ya sauke masu kwandon aradu a kansu, dan ba ƙaramin aikinsa bane ya ce uban waye ya ce a taɓa mashi matarsa? Waye ya ce wani ko wata ya zo ya dubata? To gudun kwandon bala'insa ne yasa suka bar mashi kayarsa, ya zo ya san yanda zai yi da ita. Suna dira a gida, Lion ne farkon da ya fara fita daga cikin motar, tun motar bata gama tsayawa a parking space bama ya fice abinsa. Sam bai bi ta kan kowa dake tsaye a wajen ba, cikin gida ya wuce abinsa, kai tsaye bedroom nasa ya wuce. Yana shiga ya nufi toilet, wanka ya yi a gurguje, sannan ya fito ya shirya cikin three cuter sky blue da singlet, singlet ɗin fara ce tas, tamkar yanzu ya cirota daga ledarta, abin da ya sanya ya saka singlet ɗin kuma, saboda ciwukan dake a kirjinsa. A box ya ɗauko tare da zama a gefen bed nasa, dan hannunsa in da wuka ta yankar nan ba ƙaramar ciwo take yi mashi ba, hannun ta kumbura, kun san wuka da akwai dafi a jikinta, hakance tasa hannun ta kumbura sosai. Family kuwa, cikin tsananin murna suka fara rungumar juna, kowa baki ya ki rufuwa, saboda tsantsar farinciki. Areef yana ɗauke da Ayla a saman kafaɗarsa, bai wani tsaya a wajensu ba, sai ya wuce izuwa cikin gida kawai, dan ya kwantar da ita, ta huta. Gabaɗaya family sun sha matukar mamakin ganin Aseef a tare da su, sai dai kuma sun kasa iya tambayarsa ya aka yi hakan? Ga tambayar a cikin ransu, amma ta kasa fitowa fili, abin ya ɗaure masu kai, amma haka suka hakura suka daure. Sai rungumar Dr Salman suke yi tamkar za su mayar da shi cikinsu, Brr Naurat har da ruwan hawaye, sai tsiya su Imran suke yi mata. Shi ma Dr Salman ɗin ya sha kuka ba kaɗan ba, dan bai taɓa tunanin familynsa suna a raye ba, ya yi zaton komai ya kare ya lalace masu, ashe dai sunanan, sun zama taurari zakarun gwajin dafi ma a cikin al'umma, wannan abin ya yi mugun sanya shi farinciki wanda baki ba zai iya furtata ba. Haƙiƙa farincikin da wannan family suke ciki a yau, sam baki ba zai iya furtata ba, ya wuce misali. Haka Dr Salman ya rinƙa yin kuka yana faɗin kowa ya yafe mashi, ina Nawazuddeen ɗinsa? Dan Allah Nawazuddeen ya yafe mashi. Anyi anyi ya yi shiru yaki yi, ya ce har sai Nawazuddeen ya yafe mashi. Haka daddyn Rimsha ya rungume shi yana faɗin. "Daddy ni baka yi mani laifin komai ba, idan ma kayi, to ni na yafe maka, ban taɓa ji a ra'ina kamar ka taɓa yi mani laifi ba, kullum cikin yi maka addu'a da fatan alkhairi nake yi, dan Allah ka dai'na kukannan kada ka saka muma muyi kukan". Sosai Dr Salman ɗin ya rubgume shi yana mai cigaba da matsar kwallah. Da kyar suka samu suka lallaɓa shi ya yi shiru, a tare suka rankaya izuwa cikin gida, kai tsaye bedroom na Lion suka nufa, while shi kuma Areef ya kai Ayla ɗakin gwaggo ya kwantar da ita a kusa da Rimsha, sannan shi ma ya fito izuwa bedroom ɗin na Lion ɗin. Lion yana zama a bakin bed ɗin nasa yana ƙoƙarin fara duba hannunsa, sai ga family gabaɗaya sun shigo cikin ɗakin, duk sun biyoshi, gabaɗaya fuskokinsu ɗauke yake da tsantsan annuri da farinciki, yau Dr Salman ya dawo cikinsu, ga shi ba su rasa ko mutun ɗaya ba a cikin ƴaƴan nasu, abin ba karamar daɗi ta yi masu ba. Sun shigo ne dan su duba lafiyar Lion ɗin, dan kunga shi bai tsaya a wajen nasu ba, suna sauka ya wucu bedroom nasa kawai. Kallo ɗaya Lion ɗin ya yi masu ya kawar da kallonsa gefe guda, ya cigaba da aikin da yake yi. Ganin abin da yake ƙoƙarin yi na yiwa kansa magani ne yasa gwaggo da Areef suka kariso kusa da shi da sauri. A tare suka zauna a gefe da fefensa, suka sanya shi a tsakiya kenan. Gwaggo ce ta fara karɓar A box ɗin tare da kama hannunsan tana dubawa, ba shakka ya ji ciwo sosai. A hankali ta ɗago da kallonta a kansa, hannu ta kai ta shafa lallausan kumatunsa kafin ta ce "Let me do something". Shiru ya yi bai yi mata magana ba, ya dai zuba mata idanu, shi ya mance da cewa ita ma babbar likita ce kamar daddynsu, sai da ta ce bari ta yi mashi wani abin ne yasa ya tuna ashe ita ma babbar likita ce sosai, dan haka sai ya miƙa mata hannun ya bita da idanu kawai. Cikin ƙanƙanin lokaci ta fara yi mashi aiki, duk wani magani da zata zuba mashi sai ta ɗago kai ta ce mashi sannu, dan tasan da akwai bala'in zafi ba kaɗan ba, bare kuma yanda hannun ta ɗauki lokaci, ta jiƙa sosai ciwon, dole zai sha zafi, sai dai kuma shi wayarsa ma ya ɗauko yana latsawa da hannu ɗaya, a cewarsa duk zafinta bata kai harbin bullet zafi ba, dan haka shi bai ga abin cewa da zafi a nan ba. Haka gwaggo ta yi mashi treatment na wajen da kyau da kyau, sannan ta ce ya kwanta bari ta duba lafiyar jikinsa gabaɗaya. Sai sannu family suke yi mashi, sam bai ɗaga idanu ya kalli ko mutun ɗaya daga cikinsu ba, dan yana cikin wani irin yanayi wanda shi kaɗai yasan me yake ji bawan Allah, da yake shi kullum a siffa ɗaya yake ne yasa sam sam ba wanda ya gane cewa yana cikin tsananin damuwa, kullum face nasa a haɗe take, baka gane farincikinsa bare bakin ciki, harta TRIPLETS nasa ma basu iya rabe yana cikin farinciki ko bakin ciki, saboda kullum dai yanda yake a haka yake babu canji. Bai yi wa gwaggo musu ba, ya miƙe ya kwanta a saman bed ɗin da kyau, dan a agajiye sosai yake. Duba lafiyar jikinsa ta fara yi ita da Areef, ya rufe idanuwansa yana tunanin duniya. "Momma where is Meesha?". Kamar daga sama su gwaggo suka ji sanyayyar muryarsa ya gefo masu wannan tambayar, ya yita kuma idanuwansa a lumshe. Kallon kallo jama'ar cikin bedroom ɗin suka fara yi, ita kanta gwaggon sai da gabanta ya faɗi na jin tambayar nan tasa. Ganin yanda suke kallon kallo a tsakaninsu ne yasa Aseef da Areef har suna haɗa baki wajen cewa "What is happening? Where is our Rimsha? Ya naga kuna ta kallon juna, is there any problem?". Kamar abin haɗin baki suka jera masu tambayoyin, Areef kam har da mikewa tsaye yana binsu da kallo, dan wlh idan wani abin ne ya sameta yau za'ayi yaki ba kaɗan ba, saboda ita ɗin tamkar bugawar zuciyar TRIPLETS ɗin take, dukkansu ukun suna tsananin sonta fiye da tunanin mai tunani, akwaita da mugu mugun shiga rai na wuce misali ne. Kara datse idanuwansa gam Lion ɗin ya yi, kansa na yi mashi ciwo sosai, yana jin duk abin da suke faɗa, amma ya kasa buɗe idanuwansa, dan ƙwaƙwalwarsa ba zata iya ɗaukar wani abin ya sami Rimsha ba, shiyasa ma ba zai buɗe idanu ba bare ya ga fuskokin family su kara jefa shi cikin wani raɗaɗin. "Areef nothing happened to her, just she is not feeling well, tana ma cikin bedroomna tana kwance, she is sleeping now". Cewar gwaggon kenan. Kusan a tare Aseef da Areef ɗin suka sauke nauyayyar ajiyar zuciya, da sauri Aseef ya ce bari ya je ya ganta ya tabbatar. A tare suka fita da Areef ɗin dan su je su dubata. Ita kuma gwaggo, sai ta cigaba da duba ɗan nata, Dr Salman ne ya ce su fita su bar Lion ɗin ya huta, dan ya gaji matuƙa. Haka kuwa aka yi, duk suka fita, ita ma gwaggon da ta gama yi mashi duk abin da ya dace, sai ta fita ta kyale shi, yana jin fitarta, amma bai ce mata komai ba, saboda yana da bukatar ya huta ɗin ne, ga salloli na la'asar da mangariba a kansa bai samu ya yi ba. Ransa cike da tunani barci ya yi awon gaba da shi, bawan Allah ya yi matuƙar gajiya na wuce misali, dole ne ma barci ta ɗauke shi. A ɓangaren Aseef da Areef kuwa, da suka je suka tabbatar yes Rimsha tana nan tana zuba barci, sai suka ji wani irin sanyi da salama ya lulluɓesu. Hakan tasa suka zauna a bakin bed ɗin na gwaggon suna ɗan tattaunawa a tsakaninsu. A gabaɗaya cikin family an rasa wanda zai iya tambayar Aseef ya aka yi ya je shi Daular Mutuwa? Ga dai tambayar a cikin ran kowa, amma sun kasa fito da ita fili. To meye dalili? Alƙalamin PRINCESS TEEMA ce kawai zai iya rubuta maku dalilai, dan haka ku biyoni!! A nan family suka shigo suka samesu. Da mamaki ɗauke a fuskar gwaggo take tambayar Areef ɗin me ya sami Ayla kuma?. Kallon daddyn Jelly Areef ɗin ya yi tare da miƙewa tsaye, cike da tausayi ya ce "Sorry uncle, ta yi loosing pregnant nata ne, momma ki bata taimakon gaggawa, dan babu abin da muka yi mata, babu wani drugs or injection da yake a tare da mu, so tana cikin mawuyacin halin, help her". Ya kai karshen maganar tare da sa kai ya fice daga ɗakin, a lokacin ita ma Jehan ita da Anaya duk suna bedroom nasu suna barci, sun ci kuka ne sun ƙoshi, har barcin wahala ta yi awon gaba da su bayin Allah. Haƙiƙa gwaggo ta tausayawa Aylar na ganin halin da take a ciki, dan haka sai ta ce Aseef ya kawo mata kayan aikinsu bari ta dubata, daga nan kuma ta yi wa daddyn Jelly ban hakuri. Kowa daga cikinsu Abba sai da ya bashi hakuri. Ba shakka ya ji zafin fitar cikin na Ayla, dan yana tsananin son yara, Jelly kaɗai gare shi, ita ma ta yi aure, so yana tsananin kaunar yaga ya sake samun yara, amma kuma farincikin dawowar Aylar ta fi yawa a cikin zuciyarsa sama da zubewar cikin, kuma shi dama mutun ne mai yarda da ƙaddara, dan haka ya yarda da ƙaddararsa, ya kuma rungumeta hannu bibbiyu, ya ce babu komai, haka Allah ya ƙaddara, dama ai ba su suka bawa kansu cikin ba, Allah ne ya basu, dan ya karɓi abinsa ba zasu ji babu dadi ba, shi ya godewa Allah ma da yasa ta dawo gida da ranta, iya wannan ma ya ishe shi murna, kuma dole ya godewa Allah da yadawo mashi da ita da ranta. Da haka Brr Naurat ta ce kowa ya je ya yi sallar issha, tun ɗazun aka yi sallah su suna nan suna zaune. Haka suka watse kowa ya nufi bedroom nasa, dan su je su yi sallah, Dr Salman kuma suka tafi tare da Akil, ita kuma gwaggo Aseef ya kawo mata kayan aiki ta fara duba lafiyar Aylar, dan ta lura sai anyi mata wankin ciki ma. Bayan ta gama sai ta yi mata alluran barci dan ta sami hutu. Daga nan ita ma ta mike ta fita izuwa bedroom nasu Jehan dan ta yi sallah, ta bar Brr Naurat tare da Aylar da Rimshar. Tana shiga bedroom ɗin ta tarar da Areef zaune a saman bedside drawer kusa da Jehan, ya zuba mata idanu yana ta kallonta, ita kuma tana zuba barci, ya yi wanka ya canza kayan jikinsa izuwa na barci, da alama ya yi sallah ya ci abinci. "In tasan maka ita ne Areef?." Cewar gwaggon, ta yi maganar tana nufar hanyar toilet dan ta yi alwala. "A'a momma ki barta, i want to see her ne ma kawai yasa na zo dubata, na yi missed nata over, yau ina gajiye sosai, ba zan iya da rigimarta ba, dan haka kyaleta sai da safe". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa, ko kunyar gwaggon bai ji ba ya ɗan duka ya sumbaci Jehan ɗin a kumatu, sannan ya juya ya fice, ita ma gwaggon ko a jikinta ta shige cikin toilet abinta. After some hours, gabaɗayansu sun yi barci, dan a tsananin gajiye suke, family kowa yana cikin bedroom nasa yana zuba barci, masu aikin dare suna yi, yau suma family za su yi barci a cikin salama, dan tun da TRIPLETS suka tafi basu samun barci mai kyau, a kaikaice suke yin barcin, to yau za su sami barci mai cike da daɗi. Misalin karfe biyu yunwa ta farkar da Jehan, dan bata ci abincin dare ba ta yi barci, fitowa ta yi izuwa palon kasa, abinci ta ɗebo a plate, sam bata da labarin mijin nata ya dawo, komawa palon sama ta yi ta zauna a saman sofa, cikin nutsuwa ta fara cin abincinta tana yamutse fuska tamkar mai cin magani, ita kuwa Anaya sai zuba barci take yi, ita bata farka ba. Kamar daga sama ta ga Lion ya fito daga cikin bedroom nasa sanye da farar jallabiya a jikinsa, sai yanzu ya samu ya biya bashin sallolin dake a kansa, tun da ya yi barci sai karfe 1 ya farka, wanka ya yi tare da ɗauro alwala ya zo ya fara biyan bashin sallolin dake a kansa, bayan ya kammala ne ya fito dan ya je ɗakin gwaggo wajen Meesha. Ba karamar tsorata Jehan ɗin ta yi da ganinsa ba, da farko ma ta ɗauka aljani ne, saboda dare ne kuma ga shi da farar jallabiya, bugu da kari bata san sun dawo suna gidanba, sannan ya saki dark black cuirly hair nan nasa bai ɗaure ba, ga shi da tsawo sosai dama, ai dole ya bata tsoro. A dubu ɗari ta miƙe tsaye tana ƙoƙarin kurma ihu, sai gani ta yi ya shige ɗakin gwaggo bai ko kalli in da take bama, hakan yasa ta fahimci lallai sune suka dawo, dan haka sai ta ajiye plate ɗin abincin nata, da sauri ta sauka kasa izuwa bedroom na Areef. Babu ko sallama ta faɗa cikin ɗakin, wani irin duhu ne a cikin ɗakin, kun san shi baya shiri da haske dama, idan zai yi barci a duhu yake yi, hakan tasa bata iya ganin komai, lallaɓawa ta yi a hankali ta nufi wajen switch, da kyar ta gano switch ɗin ta kunna wutar, nan take haske ya gauraye ko'ina a cikin bedroom ɗin. Cike da tsohon abin da zata iya cin karo da shi a saman gadon ta ɗago kanta, a hankali ta kai kallonta wajen. Yana kwance cikin kyawawan kayan barcinsa yana zuba barci abinsa, ya rungumi pillow a kirjinsa, ya kuma ɗaura kafafunsa a saman pillow ɗaya. Wani irin nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke, ta kasa motsawa daga wajen, ta zuba mashi idanu sai kallonsa take yi. Saboda wannan haske da ta kunna mashi ne yasa ya ɗan fara motsawa yana son farkawa, ganin hakan yasa ta yi maza ta kashe wutar tare da juyawa ta fice daga ɗakin da sauri tana hamdala ga Allah. Shi ma Aseef duk rigimarsa na son ya yi dis virgin ɗin Akila, to yau dai ya shafa mata lafiya, dan dukkansu a tsananin gajiye suke, sai barci suke zubawa babu kakkautawa, sun wahala ne over. Jehan na fita ta koma palon saman, abincinta ta ɗauka ta cigaba da ci, tsabar murna na ganin mijin nata, sai ta ji abincin ma ya kara daɗi, haka yasa ta ci sosai ta ƙoshi, tun ranar da suka tafi rabonta da ta ci abinci dayawa haka, bayan ta ƙoshi ne ta ɗaura plate ɗin a saman dining table dake a cikin palon, sannan ta wuce cikin bedroom nasu, yau barcin nishaɗi zata yi, ranta fes mijinta ya dawo. Shi kuma Lion bakinsa ɗauke da sallama ya shiga ɗakin gwaggon. Gwaggo na a saman dadduma tana sallah, Brr Naurat tana kwance saman bed tana barci, ga Rimshar a kusa da ita tana barci. Ɗakin nasu da akawai hasken wuta sky blue. Saman bedside drawer ta ɓangaren da Rimshar ke kwance ya je ya zauna. Hannu ya kai ya ɗan janye bargon da Brr Naurat ta rufa mata. Da kallo ɗaya ya yi mata ya fahimci bata da lafiya, dan ta yi muguwar rama sosai. Shiru ya zuba mata idanu yana tunanin to me yake damunta?. A hankali ta fara motsawa, alamar tana son farkawa, hannu ya kai ya shafi face nata, hakan yasa ta farka mai gabaɗaya. Tana waro idanunta kai tsaye sai cikin nasa idanun. Turo baki ta yi tare da kawar da kallonta tana faɗin "Kai kuma waye? Daga ina da zaka zo ka tashe ni, kuma ka wani tsareni da wasu shegun idanu kamar na wancan mutumin da yake zama a palon kasan nan (Dr William)". Dama kunsan ciwon nata yasa tana ji da bala'in masifa, duk zafin Jehan sai da ta sarara mata, to yanzu ma tana tashi ta hau surfa masifa, ba gaira ba dalili. Da farko Lion ɗin ya zaci magagin barci ne, sai daga baya ya fahimci babu magagin barci a tattare da ita, tana nan normal, hakan yasa ya fahimci wannan shi ne rashin lafiyar da take fama da shi kenan. Ko kaɗan bai ɗaga hankalinsa ba, dan shi ya fahimci menene matsalar tata, dama kuma already ya dawo da nufin ya yaki wancan matsalar, dan haka sai bai damu ba, godiya ga Allah ma ya yi da ya sanya ya dawo ya sameta ba'a dauketa ba, dan haka sai ya riko hannunta ɗaya, kasa kasa ya ce "Zo muje ki rakani to, sai na gaya mani wanene ni da kuma abin da yasa na tsareki da idona". Kallon sama da kasa ta yi mashi kafin ta ce "Ni ka sake mani hannu hai, babu in da zanje, kuma ka bar mana ɗakinmu". Dama kunsan bata yarda kowa ya raɓeta sai Brr Naurat, duk wanda ya zo kusa da ita bala'i ne yake tashi ya tsaya gam, to shima surfa mashi bala'i ta rinƙa yi a kan ya bar masu ɗakinsu. Nisawa ya yi tare da kai ɗan bakinsa ya sumbaci lallausan kumatunta, sannan ya miƙe ya nufi hanyar fita, yana jiyo muryarta tana faɗin "Mugu da zaka wani taɓani, ina ruwanka da ni?". Bai kulata ba ya fice abinsa, duk abin da suke yi gwaggo dake saman dadduma tana jinsu, hakan yasa ta kara tsananta masu addu'a na samun lafiyar Rimshar. Shi kuma Lion yana fita ya koma bedroom nasa, ainahin wayarsa ya ɗauko, ba wanda ya saya a Ilorin ba, na ainahin ya ɗauko tare da kunnata. Duba time ya yi, karfe 2:40am dai'dai. Number his excellence ya kira, wayar ta yi ringin har ta kusa yanka sannan ya ɗaga. A takaice Lion ɗin ya ce mashi "Zan shigo Usa gobe, ina da bukatar lokacinka at least 1 hour, so sai ka shirya". Yana gama faɗar hakan ya katse kiran, duk da ciwon dake a jikinsa, hakan bai hana shi ya tashi ta fara shirin tafiya ba, acewarsa, gara kawai ayita ta kare. Duk wani abin da zai buƙata ya shirya a cikin trolleynsa, sannan ya fito ya nufi bedroom na gwaggo, ita kaɗai ya gayawa zai tafi yanzu ba sai anjuma da safe ba, ta so ta dakatar da shi, ta so ya bari ya huta, amma ya nuna mata yana sauri, dole ne ya isa Washington gobe goben nan, dan haka kawai ta bishi da addu'a. Ko TRIPLETS nasa bai gayawa ba, a cikin wannan dare ya fita daga gidan tare da Donal, a hanyarsu ta zuwa airport ne ya sanar da Donal ɗin cewa zai turo likita dan a ɗaura kafar Mark, so ya kula da shi sosai, bawan Allah ya azabtu matuka, baki ma ba zata iya faɗar azabar da Mark yake a ciki ba, kowa dai yasan yanda karaya take, idan baka taɓa karyewa ba, to an taɓa yi a kusa da kai, tana da matuƙar raɗaɗi na azaba. A takaice dai Lion da private jet nasa ya bar Nigeria, dama tun da su TGA suka zo jirgin tana airport babu wanda ya taɓata, to da yake yanzu tafiya ce ta ujila, sauri yake yi, sai bai tsaya yin booking na jirgin kasuwa sun ɓata mashi lokaci ba, kawai ya yi amfani da nasa. Ya bar Nigeria karfe 4:30 na asuba, sai addu'a gwaggo take zuba mashi sosai da sosai, su kuma TRIPLETS sai barci suke zubawa a tsananin gajiye, basu da labarin Lion ya bar kasar!. Yana dira Washington Tga ya zo ya ɗaukesa, kamar yanda babu wanda ya san ya bar Nigeria sai gwaggo, haka babu wanda ya san ya dira a cikin Washington sai his excellence, ko Tga ma sai da ya kusa sauka ne ya kira shi a kan ya zo airport ya ɗaukesa, so babu wanda ya sani. Kai tsaye gida suka wuce da Tga ɗin, yana zuwa ya yi wanka tare da shiryawa, sannan ya samu ya zauna ya nutsu ya ci abincin mai yawa sosai, tun daren jiya yake jin yunwa, amma wannan matsala ta tsaya mashi a rai da har ta hana shi cin abincin, ji yake yi idan bai dira a cikin Washington ba, to ba zai iya samun sukuni ba, shi ne yasa bai iya zama ya ci abinci a gida Nigeria ba, ya daure sai da ya dawo nan, amma fa ya wahala matuƙa a cikin jirgin, dan ma dai ya yi ta shan Maltina ne. Bayan ya ci abinci ya ɗan huta na ƴan mintoci, sai ya sake shiri tare da sanya face mask a fuskarsa ya fito, Tga ya so ya raka shi, amma ya hana kowa binsa, ya ce shi kaɗai zai tafi, basu da zaɓi, dole su hakura su kyale shi, amma sam basu so hakan ba, sojojin dake jibge a gidan nasu ba ƙaramin mamakin ganinsa suka yi ba, sun jima rabonsu da shi, sun yi kawarsa. Da kansa ya ja mota, bai tsaya ko'ina ba sai white house wajen His excellence. Abu ne da kuka riga da kuka sani, baya neman permission a wajen kowa idan zai ga his excellence, kai tsaye ma yau palon gidan ya nufa, sam bai je fadar shugaban kasa ba, da yake already his excellence ɗin ya san da zuwansa, sai ya bar duk abin da yake yi, ya tashi ya je ya samesa a cikin babbar palon nasa kawai. Sannu da zuwa His excellence ɗin ya yi mashi tare da fara tambayarsa ina su Michael nasa? Dakatar da shi Lion ɗin ya yi, a takaice ya ce mashi "Where is Anderson?" A tsananin razane his excellence ɗin ya ce "Romeo what... What... What are you saying? Anderson is already died you know that... And now.......". Yana magana yana samun sarkewar word. Dakatar da shi Lion ɗin ya yi ta hanyar ɗaga mashi hannu ba tare da ya barshi ya kammala maganarsa ba, ya sake cewa mashi "Uncle i said where is Anderson?." Tashin hankali!. "Romeo i told and you already know that Anderson is d......" Katse shi Lion ɗin ya yi ta hanyar ɗaga mashi hannu a karo na uku tare da miƙewa tsaye. Bai sake cewa da shi komai ba ya nufi waje abinsa. A tsananin firgice his excellence ɗin ya miƙe tsaye, kana ganinsa kaga zallar mara gaskiya, nan take wata zufar wahala da shiga ruɗu ta fara tsastsafo mashi daga gefe da gefen fuskarsa, idanuwansa duk sun raina fata, ya yi wani wiki wiki da shi, duk wata alama ta rashin gaskiya tare da shiga tsananin tashin hankali sun bayyana a tattare da shi, a kiɗime ya nufi saman bene dan ya kai ga isa bedroom nasa. Shi kuma Lion yana fita daga gidan bai zame ko'ina ba sai gidan kanin his excellence ɗin, mai sunan Michael kenan. Yana shiga palon bai sami kowa ba, kai tsaye ya haura sama izuwa bedroom ɗin na kakan nasu, rabonsa da ya taka kafa ya zo wannan gida yau ya kai tsawon shekaru takwas zuwa goma, yanzu ma ko da yazo securityn gidan basu gane shi ba, har sun nemi su ɓata mashi lokaci ta hanyar dakatar da shi, sai da ya cire masu face mask na face na shi sannan suka gane shi, cikin girmamawa suka barshi ya wuce, ya cire masu face mask ɗin ne kuma saboda baya son hayaniya, aikin da ya kawo shi kawai yake da bukatar yi ya fita. Kamar yanda kuka sanine, dukka ilahirin familyn Roshan shahrarrun masu kuɗaɗene ta duniya, duniya na damawa da su, suna da karfin faɗa a ji a duniya bakiɗaya, ko'ina ka je ka ambaci sunansu an sansu, dan haka shima wannan kakan nasu shahrarren biloniya ne ta duniya, tsayawa zayyana maku kyan gidansa ma ba zai yiwu ba, saboda baki ba zata iya zayyana adadin dukiyar familyn Roshan ba, sai daidai kawai ku ƙawata a ranku. Lion yana hayewa sama kai tsaye ya nufi bedroom ɗin na kakan nasu, yana shigowa ya fara jin sautin karar tapi rap, rap, rap, tamkar jiransa ake yi ya shigo dama. Ba kowa ne yake wannan tapi ba face kakan nasa, da alama yasan da zuwan nasa, sam Lion ɗin bai yi mamaki ba, sai ma karisa shigo cikin bedroom ɗin da ya yi ba tare da ya jira an yi mashi izini ba. A bakin katafaren bed na kakan nasa ya zauna tare da zubawa kakan nasa idanu yana yi mashi wani irin kallo wanda babu wani mahaluƙi da ya isa ya fassara ma'anarta sai shi da kansa, kallo ne mai cike da abubuwa da dama a cikinta. Dama daga ganin idanuwan Lion ɗin a halin yanzu kasan da akwai gagarumar abu a kasa. "Romeo' Romeo Romeo' you are so special our Lion, you really try". Cewar kakan nasa. Mai da kallonsa a saman yatsun hannunsa ya yi, sannan ya yi kasa da kansa, cikin sanyin murya ya ce "Why uncle? Why? Why you people did all that to us? Ina cikon TRIPLETS na? What happened to him?" And lastly where's Anderson?". Cike da izza kakan nasa ya fara magana. "Romeo the time is out! And the game is over! Bari ka ji mu bamu ɗauki ɗaya daga cikin TRIPLETS naka haka kawai bisa raɗin kanmu ba, ina son ka sani mahaifiyarku ita ce da kanta ta sadaukar mana da cikonku, ita da kanta ta ɗauke shi ta bayar, meyasa baka tambayeta ba? Ai ita zaku zarga! Mu a tsarin mu bamu amfani da yaron da ba iyayensa ne suka ɗauke shi da kansu suka bamu ba, idan ma mun ɗauki yaron da iyayensa basu bamu ba, to yaron ba zai yi mana amfani ba, dole sai wanda iyayensa suka bamu ne yake yin amfani a wajenmu, kamar yanda William ya gaya maku tun farko na cewa mahaifiyarku ta badaku, to hakan ce gaskiya! Mahaifiyarku ta bada guda ɗaya ne daga cikinku, William ɗin ma bai faɗi dai'dai ba, guda ɗaya ta bada ba dukkanku ba, shi ne yasa Anderson ya ɗauki wanda ta badan, dan haka ka dai'na neman Anderson, dan bashi da laifi, idan kuma kana ganin ba haka bane, ka koma Nigeriar ka je ka tambayi mahaifiyar taka, zata gaya maka ai, kada ka matsa a cikin wannan al'amari, idan ka matsa to ba shakka zaka fara danasanin zuwanka duniya, ka koma wajen mahaifiyarku ta gaya maka gaskiya!!".................... Tashin hankali, wannan wani irin azababben cakwakiya ce? Gwaggo ce da kanta ta sadaukar da cikon TRIPLETS kenan? Kenan kila shiyasa bata yi maganar yaro ɗaya mai blue eyes ɗin ba tun da ta ganesu? Kenan dama tasan baya nan? Meyasa to zata yi hakan? In dai haka ne kenan tana da sa hannu a ciwon Rimsha? To wai meyasa? Menene dukka wannan abin? Wanene shi wannan Anderson ɗin? Abin da ɗaure kai! Ya ake son Lion ya yi da ransa? Kashe shi suke son yi ne? Wannan bala'i ai sai ta sa zuciyarsa ta buga, uwa fa! Ya ilahi ya lillahi. Ni kai'na PRINCESS TEEMA a wannan gaɓar ka'ina ya yi wani mummunar bugawa, zazzaɓi nake ji my peoples 🥺🥲💔 littafin TRIPLETS wan kill me with more cakwakiya and sarkakiyar. HAR WA YAU TAKUCE FATEEMAH ZAHRA MUSA PRINCESS TEEMA TAKU TA AMANA MAI ABIN BAN MAMAKI🤙❤️ ASHA KARATU LAFIYA🥲💔 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 28/4/2024 *Page na yau ban samu na yi editing nasa yanda ya kamata ba, saboda rashin chaji, so zaku iya samun typing errors, amin afuwa.* E18 Nisawa Lion ɗin ya yi ba tare da ya ce komai ba, dan yana tattauna maganganun ne ma tukunnan. "Haƙiƙa babu wasa a wannan al'amari, tun kuna cikin cikinta, tun cikinta yana da wata biyar aduniya ta bayar da ɗa ɗaya daga cikinku, wannan dalilin yasa da aka haifeku muka ɗauki guda ɗayan, wannan zance haka take, kuma duk in da zaka je ka zo hakan ce! Babu makawa kuma babu tantama a cikinta, muna da shaidu a kan hakan, na san dama zaka zo, zaka zo garemu Romeo, saboda tun da ka fara girma muka fahimci ka ci sunanka da WILLIAM ya sanya maka wato Lion, so our Lion already we know that you're special! Hakan yasa muka ajiye maka tarin hujjoji da zaka gansu a aikace, sai dai bamu yi tunanin zaka zo garemu da wuri haka ba, bamu yi tunanin zaka gane mu da wuri haka ba, anywhere mu bamu cutar da ku ba, ku tuhumi mahaifiyarku da kuma Josephine, sune suka yi komai!!". Haƙiƙa a maganar kakan nasa babu karya a cikinsu, tabbas duk abinda ya faɗa gaskiya ce, gwaggo da bakinta tun cikinta yana da wata biyar, tun bata ma san me zata haifaba, ta bada guda ɗaya, to su kuma basu mantuwa, shiyasa da ta haihu suka ɗauki ɗayan, sai dai da akwai abin da ya saɓa a cikin maganar, wanda kuma dole a wajen Josephine da Cherish ne kawai za'a san ainahin menene wannan!. Wannan shi ne cakwakiya, Lion dai yana tsaka mai matuƙa wuya wanda fitarta sai Allah ya ƙaddara. Nan ma dai shiru ya yi mashi bai yi magana ba. Gabaɗaya kakan nasa ya shiga ruɗu, saboda yin shiru Lion ba alkhairi bane, sun san shi tun yana ƙarami, idan ya yi shiru, to wani abin yake ƙullawa a cikin ransa, so haka har ya girma, shirunsa musiface a wajen marasa gaskiya masu cin amana da tauye haƙƙin ƴan adam. Ganin yanda ya yi shirun ba ƙaramar ɗaga mashi hankali ya yi ba, dan haka sai ya sake cewa "Ni zan je office ana jirana". Ya ɗauki tsawon lokacin da a kallah zai kai 10mins kafin ya sake nisawa tare da ɗago idanuwansa ya sauke a kan kakan nasa, cikin tsananin nutsuwa ya fara magana. "Ni ban tambayeka waye ya baku cikon TRIPLETS da kuka ɗauka ba, ni kawai na ce maka ne ina yake? Me kuka yi da shi? And lastly where's Anderson? Wanda ya baku wannan duk daga baya ne, zamu zo kan zance, for now dai amsa this two questions that i asked you! Where is my TRIPLETS? And where is Anderson?". "Anderson is already died, you know that, so i don't know what do you want us to tell you again kuma". Jinjina kai ya yi tare da faɗin "Okey Anderson is already died, wow this is so nice, agreed, amsa me da remaining question, where's my brother?". Ya kai karshen maganar yana miƙewa tsaye. "Romeo your brother has gone since that time". Sake jinjina mashi kai ya yi kafin nan ya fara takawa a hankali ya nufe shi, dama yana tsaye ne ta wajen mirror, ba halin yin baya baya, bashi da zaɓin da ya wuce ya tsaya kawai har Lion ɗin ya iso gare shi. A hankali ya iso in da yake, hannu ya ɗaga cikin nutsuwa ya shafi lallausa kuma jajir ɗin kumatun kakan nasa, cikin sanyin murya ya ce "Okey let me try something, let me send you to the place that you send my brother!". Ya kai karshen maganar yana gangaro da hannunsa izuwa wuyar kakan nasa. Da karfi sosai ya shake ɗan tsohon, ransa a tsananin ɓace over, amma saboda ya gane suna neman hassala shi ne, sai ya ki bari ɓacin ran nasa ta yi tasiri, sai ya danne kawai. Cikin kwanciyar hankali kakan nasa ya sanya hannu a saman hannun Lion ɗin, tamkar wanda ya kama hannun ƴar baby haka ya ɓanɓaro hannun Lion ɗin daga jikin wuyarsa tare kuma da murɗe ta baya da karfi, nan take yanayin kakan nasa ya fara sauyawa, cikin tsawa da wata iriyar murya wadda da ka ji ta kasan ba nasa bane, dan murya ce ta irin kartin mazan nan, da ita ya dakawa Lion ɗin tsawa, sam Muryar bata da daɗin ji, tamkar an tada injin jiƙa lalatatce. Ba shakka abin mamaki ne canzawar kaka nasa da kuma irin karfin da yake da shi a matsayinsa na dattijo, sai dai kuma ko kaɗan Lion ɗin bai yi mamakin hakan ba, dan ya san fin hakan ma zasu aikata. Kasancewar yana da ciwo a hannun, sai murɗe mashi hannun da kakan nasa ya yi ta yi mashi muguwar zafi, hanan tasa ya kai ɗayar hannunsa yana ƙoƙarin sake shako wuyar kakan nasa, dan tsananin zafi da yake ji. Sam kakan nasa bai bari hannunsa ya sake taɓa jikinsa ba, sai ya yi ƙoƙarin haɗe hannayen nasa dukka biyu ya ruke da hannu ɗaya. Da Lion ɗin ya fahimci wannan karfi fa ba na kakansa bane, dan haka yana da kyau su yi fito na fito, idan ba haka ba, idan ya zuba masu idanu to zasu yi mashi illa mai girma. Tuna hakan ne yasa bai bari kakan nasa ya kama ɗayar hannun nasa, sai ya yi ƙoƙarin kaucewa, hakan ya bawa kakan haushi ba kaɗan ba, sai ya yi wani irin kurma kururuwa kamar kukan giwa a dawa, nan take ya canza halittarsa izuwa wata halitta mai matuƙar girman, tana kama da ɓauna, wato saniyar dawa, ga wasu kawo guda biyu a kai. Ko kaɗan Lion bai ji tsoro ba, sai ma nishaɗi da abin ya bashi, shi da ya yi faɗa da su barbushi jibga jibga mutane masu kama da samudawa, dan haka sai ya gyara tsayuwa tare da dakewa, shi hakan ma ta fi mashi, ya fi jin daɗi su yi fito na fito da su, ya ci ubansu Roshan babu sirki, ya kuma sanyasu su duka su gaya mashi gaskiya!!. Gadan gadan wannan halitta da kakan nasa ya koma ya tunkarosa. Yana zuwa Lion ɗin ya furta kalmar bismillahi tare da fara kokawa da shi. Sai dai ina ya riga da ya ambaci sunan Allah, babu wata tsafi da zata yi amfani a wajen, haka yasa suna fara yin faɗa kakan nasa ya koma ainahin halittarsa, sarai Lion ɗin yasan da hakan, amma sai bai kyale shi ba, ya jibge shi da kyau da kyau, wani irin wawan mari ya kai mashi a kumatunsa wanda har sai da ya sanya shi ganin wani haske ya gilma mashi ta cikin idanuwansa, bai barshi ya dawo dai'dai ba ya kwashe kafafunsa, sai ga ɗan tsoho ya zube kasa wargajam. Guntun tsaki Lion ɗin ya ja, ya so ace da matashin mai jini a jika zasu gwabza, dan ya ci ubansa, ya sauke mashi duk wata haushi da yake ji a kansa, ya jibgi banza, amma sai ya zamana da tsoho ne ba matashi ba, wannan tsohon idan ma ya ce zai dake shi, ai sai dai ya karisa gawar da ba tasa ba, dan wannan idan ya yi mashi duka ɗaya lafiyayyiya ba makawa sai dai a ɗauki gawarsa. Wayar makekiyar Tv dake a ɗakin Lion ɗin ya tsinko, da karfi ya ja har sai da Tv ta faɗo kasa ta tarwatse, ko a jikinsa ya zo ya ɗaure kakan nasa ɗaurin goro, ta baya ya ɗaure hannayen nasa, sannan ya ɗaga shi cancak, bai sauke shi a ko'ina ba sai a saman tsakiyar bed nasa. Ya sauke shi tare da zama a saman bedside drawer, kasa ya ɗan yi da kansa yana ɗan murza ƴatsun hannunsa, ya ɗan ɗauki lokaci da a kallah zasu kai 10mins kafin ya ɗago kai tare da kai kallonsa izuwa kan ɗan tsohon, a takaice ya ce "Are you ready to tell me the truth or not?". Murya a tsarke, cike da tsoro ya ce "Zan faɗa maka komai". Yana magana yana zare ash eyes nasa, haƙiƙa ya tsorata na ganin tsafinsa taki yin aiki a kan Lion ɗin, ya ji matuƙar rashin daɗi, sam ba haka ya so ba, ya so ne ya jibgi Lion ɗin har sai ya yi laushi, sannan ya ɗaure shi kansa a kasa kafafuwansa a sama, sai dai bai san cewa ta Allah ba tasa ba, bai san cewa shi Lion ya rigada ya ruke Allah hannu bibbiyu ba, wanda kuma ya ruke Allah, tabbas babu shi babu taɓewa, wanda ya ce Allah shi ne komai nasa, to babu shakka Allah ba zai taɓa bashi kunya ba, Allah zai kula da lamuransa ba zai taɓa bashi kunya ba, ya Allah ka iya mana da iyawarka!. Jinjina mashi kai Lion ɗin ya yi tare da yi mashi alamar ya yi maganarsa yana jinsa. "Magana ta gaskiya dai, na farko a nan shi ne, da gaske mahaifiyarku ce ta bamu yaro ɗaya, babu wasa a cikin wannan maganar, shi kuma maganar Anderson, ba shakka Anderson yana raye kamar yanda ka yi hasashe, maganar ɗan uwanka cikon TRIPLETS naka kuma, i don't know har yanzu yana raye or not, wannan shi ne iya gaskiyar da na sani". Shiru Lion ɗin ya ɗan yi na ɗan lokaci kafin ya sake cewa "Tun ainahi menene matsalar, and meyasa kuka karɓi cikon TRIPLETS nawa?". A tsananin razane tare da kiɗima kakan nasa ya fara magana "Please Romeo don't ask me this questions! I don't want to die, i have alot of things da nake son cinmawa, idan har na gaya maka gaskiya, to ba shakka zan mutu a yau, please save my life, leave me like that!". Ya kai karshen maganar yana zare idanu kamar an tare ɓera a tarko. Nisawa ya yi nafin a takaice ya ce "I don't want all this miscellaneous excuse, just amsa me, meyasa suka ɗauki cikon TRIPLETS nawa? Me kuka yi da shi?". Allah sarki Lion bawan Allah, yasan cewa baba shakka gwaggo da bakinta ta bada ɗaya daga cikinsu, amma shi ba hakan ce a gabansa ba, dan ya san wlh gwaggo ba zata bayar da su haka kawai ba, dole da kawai kwakkwaran dalili, shi yanzu so yake yasan menene yasa aka yi hakan dukka, ba damuwarsa wanda ya bayarba, a gaskiya sai mai karfin Imani mai kuma tawakkali da yarda da ƙaddara ne kawai zai iya ɗaukar abin da Lion yake ɗauka, bugu da kari shi duk abin da zaka gaya mashi sai ya yi doguwar nazari a kan maganar, shiyasa yana da matuƙar wahala kaga ya yanke kuhunci ba dai'dai ba, saboda aiki da kwakwalwa da basira, a yanzu da wani ne ya ji abin da kakan nan nasu ya ce, to ba shakka da ba zai yi wani dogon tunani ba, kawai zai ɗauki karan tsana ne ya ɗaurawa gwaggo ɗin, alhalin kuma dole da akwai dalilinta na yin hakan, Allah ka bamu ikon yin amfani da kwakwalwarmu wajen yin tunani a koda yaushe. "Romeo it's a long story, please and please let me go........" Kasa karisa maganar ya yi saboda wani irin kallo da Lion ɗin ya wurga mashi, hakance tasa ya haɗiye maganar. "Uncle you know that bana repeating na word ko? And them bana cancel na magana idan nayi ko?". Jinjina mashi kai kakan nasa ya yi, ba shakka yasan da cewa Lion ba zai canza maganar nan ba, ya gaya mashi gaskiya shi ne kawai zai zama mafi a'ala a garesa, idan ba haka ba, wlh Lion zai gana mashi azabar da sai ya gwammaci mutuwa a kanta, dan haka sai ya fara magana cike da iya gaskiyar da ya sani kamar haka. "Romeo ainahin wannan matsala ta samo farko ne daga kan kakanku Jacob mahaifin William, shi ne makasudin shigarku dukka wannan matsala, Jacob wato mahaifin William shi ma member ne na kungiyarmu, kuma shi ne mataimakin shugaban kungiyarmu wanda ya kasance shi ne Anderson, Anderson shi ne shugaba, Jacob mai take mashi baya, to dama a ƙa'ida ta kungiyarmu kowa dole zai kawo yaro daga cikin yaransa wanda ko ya mutu wannan yaro zai gajesa, hakan ce kawai zata sanya kungiyar ta cigaba da haɓaka, so shi Jacob sai ya bada yaronsa Herry, daga baya sai ya sake bada Josephine, saboda yana son zama shugaba, a ƙa'idarmu dama hakance, wanda ya fi sadaukarwa uwargijiyarmu, shi ne zai zama shugaba, kai baka yi mamakin meyasa Jacob ya fi kaunar William a cikin ƴaƴansa ba? Saboda yasan cewa William ɗin shi ne kawai ɗansa, a lokacin sam ba'a san za'a haifi Tga ba, to a takaice dai da Herry da Josephine Jacob ya bayar da su, ya rage saura mashi William kawai, shiyasa ya fifita William ɗin sama da su, ya kaunace shi sosai, dan yasan shi ne kawai zai gajesa a duniyar mutane, su Josephine ba nasa bane, nan da ɗan lokaci za'a ɗaukesu, haka muka cigaba da tafiya a kan tsarukanmu, nima na bada yaro ɗaya daga cikin yarana, dan ya zama magajina a kungiyar, kowannanmu dai ya bada na shi, kwatsam sai William ya zo da batun auren mahaifiyarku wadda ta kasance musulma, shigowar musulma gidan Jacob zai iya zama barazana ga gariyarsa a kungiya, dan haka sai ya tsaneta, na nuna baya goyan bayan tarayyar ɗansa da ita, to da yake abin ya zo da karar kwana, shi William kaifi ɗaya ne, ba'a isa a tankwara shi ba, ai kaga yadda suka kare, William ya zama sanadiyar mutuwar Jacob ɗin, to mukuma abu ne da ka rigada ka sani cewa bamu yafe jininmu, dan haka ba zamu iya yafewa William wannan laifi da ya yi na kashe mana ɗaya daga cikin member kungiyarmu mai karfin faɗa aji ba, bugu da kari kuma yayanmu na jini, hakan yasa muka fara shirye shiryen yadda zamu ɗauki fansa a kan William, a dai'dai lokacin ne kuma muka fuskanci babban barazana da ya yi ƙoƙarin rugujemu, wannan barazana kuma ba komai bane face musuluntar William da su Josephine, mun shiga tsananin tashin hankali na wuce misali, saboda Josephine da Herry namu ne ba naku ba, idan aka ce sun musulunta mun shiga uku, zamu iya rasa rayukansu a kan hakan, ga shi lokacin ya zo a dai'dai Herry zai maye gurbin Jacob tun da ya mutu, kuma suna matsayin musulmai ba ta yadda za'ayi su kasance a cikinmu, saboda suna yin sallah da sauransu, duk musulman da zaka gani a ire iren kungiyarmu, to basu yin sallah da sauran ibadunsu ne, dan tsafi baya haɗuwa da sunan Allah, to su Josephine bayan sun musulunta suna sallah har da karatu, hakan ba ƙaramar ɗaga mana hankali da jefamu cikin bala'i ya yi ba, a wannan lokacin ne Anderson ya fuskanci mummunar ukuba daga wajen uwargijiyarmu, dan shi ne shugaba a wajen, komai ya faru za'a ga laifinsa a matsayinsa na shugabanmu, dan haka sai uwargijiyarmu ta hukunta shi a kan musuluntar su Josephine, wanda hakance tasa duniya take ganin kamar ya mutu, dan ya sha bakar wahalar da kowa ya bashi mutuwa, bayan ya dawo cikin hayyacinsa, uwargijiyarmu ta saukaka mashi ne sai ya koma cikin kungiya da zama mai gabaɗaya, kuma a lokacin ne uwargijiyarmu ta ce ta bamu lokaci ƙanƙani mu ɗauki mataki a kan abin da yake faruwa, kuma mu san yanda zamu yi mu dawo da Josephine da Herry cikin sauri, a takaice hakan tasa muka yi ƙoƙarin dawo da su cikinmu, hakan kuma ba zai taɓa yiwuwa ba har sai mun rabasu da mahaifiyarku, dan tana koya masu abubuwan addini, (Addu'a da karatun Alqur'ani mai girma) idan kuma suka karanta wani abin ma (addu'a) da mu bamu san menene bane suna iya ɓace mana daga idanun tsafinmu, hanan tasa muka fara ƙoƙarin rabasu, sai muka fara da WILLIAM, dan munfi jin haushinsa sama da kowa, shi ne sanadiyyar komai da ya faru, shi ya kawo mahaifiyarku a cikinmu, ya yi mana laifi dayawa, shi ne ya zama sanadiyar mutuwar Jacob, sannan ya janye su Josephine daga garemu, ya kuma kawo mana mahaifiyarku ta zo da addininta tana ƙoƙarin ruguzamu, wannan dalilin yasa muka yi iyaka bakin ƙoƙarinmu wajen cusawa William tsanarta, kuma a lokacin sai muka yi sa'a yazo dai'dai tana da ciki, sai muka cusa mashi tsanar cikin da ita kanta, to hakan ce tasa muka yi nasarar nesanta ta da William ɗin, ta koma gefe guda tana rayuwa, sai mukuma kuka kama William ɗin muka ɗaure shi, sai muka kawo wani mai kama da shi muka yi replacing, a takaice dai William da kuke tare da shi a yanzu ba naku bane, ba shi ne mahaifinku na gaskiya ba, namu ne, naku har wa yau yana ɗaure a kungiyarmu, dan ya yi mana laifi dayawa, Anderson ya ce kada a kashe shi, a barshi a ɗaure har ya mutu, to har yanzu dai bai mutu ba, yana dai shan bakar wahala, sai dai babu wanda ya san da cewa William da yake tare da ku ba naku bane namu ne. Bayan mun ɗauki William na ainahi, sai muka koma kan Josephine, munyi munyi mu juyar da tunaninta, amma da yake ita ta yi sabo sosai da mahaifiyarku, tana tare da ita kullum, sai muka kasa, hakan ba ƙaramin ɓatawa Anderson rai ya yi ba, sai ya yanke shawarar dole ita ma mahaifiyarku mu hukuntata, dan ita ma ta kawo mana barazana a cikin harkokinmu, hakan yasa muka yanke shawarar karɓar ɗanta idan ta haifa, wannan shawara da muka yanke yasa sai muka barta a tare da Josephine ɗin, shi kuma Herry muka juya mashi tunani, muka kife ƙwaƙwalwarsa ma gabaɗaya, sai ya zama bai ma san menene addinin musulunci ko kuma mahaifiyarku ba, muka mantar da shi komai kamar yanda muka yi wa Rimsha a yanzu, haka muka cigaba da saka idanu a kan mahaifiyarku da Josephine, cikin dabara muka fara controlling na Josephine ɗin ita ma, mun sami nasarar yin hakan ne kuma a lokacin da take jinin haila, babu tsarki a tattare da ita, shiyasa muka yi nasarar aikata hakan, daga nan sai muka cigaba da amfani da ita dan muna son mahaifiyarku ta aihu mu ɗauki yaron, ita Josephine ita ce ta sanya mahaifiyarku ta bada yaro guda ɗaya, da bakinta ta ce ta bamu ɗaya, ban dai san ya suka yi da Josephine ɗin har ta yarda ta bada yaron ba, abin da na sani shi ne ta yarda ta bada babban ɗanta, so ba kai bane babba, wanda muka ɗauka shi ne yayanku, shi ne aka fara haifa, tun cikinta yana da wata biyar a duniya ta yarda ta bada ɗan da zata fara haifa, wanda zai fara faɗowa duniya, to shi ne yasa bayan ta haihu muka turo Herry ya karɓi yaron, a lokacin ita ma Josephine ɗin bata isa ta yi mana musu ba, ba a cikin hayyacinta ta bada yaron ba, sai dai abin mamakin shi ne, Bayan Josephine ɗin ta bada yaron, lokacin da mahaifiyarku ta koma gidanta tana kuka, idan baku manta ba Josephine ɗin ta bita ai, a lokacin sun sake zama na ƴan kwana biyu a tare, wannan zama da suka yi ne yasa Josephine ta sake kubce mana, dan mahaifiyarku ta sake ɗaurata a kan turbar musulunci sosai, kuma time da mahaifiyar taku zata bar kasar nan, akwai wani littafin adduo'i da ta bawa Josephine ɗin, ta ce kada ta yi wasa da shi, ta rinƙa karantawa, hakan yasa Josephine ta kubce mana mai gabaɗaya, dama ita sau biyu ta taɓa halaktar kungiyarmu, a lokacin muna controlling nata ne, to tun da mahaifiyarku ta bata wannan littafin, sai muka rasata, wannan dalilin kuma yasa da William namu dake wajen ku, da kuma Herry basu kaunarta, sun tsaneta sosai, saboda idan ta kusancesu, za su iya konewa, William dake wajenku mun sanya shi ya reneku kamar uba, sai dai mun sanya shi ya cusa maku tsanar Josephine ɗin, dan saboda kada ku kusanceta ta gaya maku gaskiya, bamu son ku zama Musulmai, idan kuka zama hakan za'a sami gagarumin matsala, kuma ita Josephine musulmace, to kusantarta a gareku babban haɗari ne a garemu, hakan yasa muka shiryawa William abin da zai gaya maku yasa ku tsaneta, da Josephine ɗin ta fahimci hakan, sai ta yi amfani da wasu abubuwa nata na tsafi da ta koya daga wajen wata kawar mamanku mai su na Cherish yar kasar China, kasan chinawa da iya tsafi, to ita ma Cherish ɗin ta iya, sai ta koyawa su Josephine, mahaifiyarku dai ta ce bata son koya a lokacin, dan babu kyau, ita kuma Josephine ta ce zata koya dan zai yi mata amfani, ai kuwa ya yi mata amfani, dan lokacin da ta farga muna son cutar da rayuwarku, mu tauye ku, bamu son gaya maku gaskiya, sai ta yi ƙoƙarin zuwa ta yi magana da kai, a lokacin kana da 15 years a duniya, amma saboda already William ya cusa maku tsanarta, sai kaki ka saurareta, har ma kayi yunkurin kasheta, to data ga hakan, sai ta fahimci me matsalar, shi ne sai ta yi amfani da ɗaya daga cikinku, wanda kuma mun rigada mun fara yin tsafi da shi a baya, wato Michael, sai ta yi amfani da shi da nata tsafin da ta koya a waje Cherish, sai tana baku kariya sosai, abin ya ɗaga mana hankali matuka, sai muka yi ƙoƙarin kasheta kawai mu huta, amma muka gagara, da muka matsa ma, sai kungiyarmu ta jijjiga tana neman rugujewa, bamu da zaɓi dole muka hakura muka kyaleta, muka kuma fita harkarku, dan mun lura idan muka matsa zamu iya jawowa kanmu gagarumin matsala, Josephine tana shirya maku abubuwa da dama da zai sanya ku zo in da take, dan ta gaya maku gaskiya, amma sai abin ya ci tura, kun rigada kun tsaneta tun farko, shi ne yasa komai zata yi ba zaku je in da take ba, sai dai kai Romeo mutun ne mai sa'a, duk shirin da muka yi wa William namu, duk kula da ya yi daku, kaki ka yarda ka ɗauke shi a matsayin uba, ka fi son Josephine sama da shi, tun daga nan muka gane cewa kai ɗan baiwa ne, kuma idan bamu yi da gaske ba, zaka iya kawo mana gagarumin matsala, mun yi niyar juyar maka da tunani sosai, sai wani gagarumin aiki ya taso mana a kungiya, hakan yasa muka mai da hankulanmu a kan aikin, kafin mu dawo shi ne muka tarar ka musulunta, abin ya yi mummunar ɗaga mana hankali, mun shirya maku abubuwa da dama da baki ba zai faɗe shi ba a kan kada ku kusanci musuluncin nan, amma mun rasa ya aka yi ka musulunta, abin fa ya jijjigamu ba kaɗan ba, daga nan muka fara neman ta yanda za'ayi mu kaika kasa koma ta yaya ne, dole mu kasheka dan zaka iya zama mana babban baraza wanda baki ba zai iya fadarta ba, Amma mun kasa yi maka komai, saboda taimako da kuke samu daga wajen Josephine da kuma mahaifiyarku, duk da bata a tare da ku, amma kullum sai ta yi maku addu'a, wani lokaci muna ganinta tana rabawa al'umma kuɗi sosai, duk a cewarta Allah ya kare ku a duk in da kuke, sau ba adadi muna kawo maku hari dan mu kasheka, amma Josephine tana shiga tsakaninmu da ku ta hanyar Michael, to a yanzu ne muke ganin mun sami dama da zamu kaika kasa ta hanyar matarka da ta kasance ita ce rauninka, a baya bamu iya gane menene rauninka ba, amma a yanzu ya fito karara matarka ita ce rauninka, munsan idan wani abin ya sameta dolenka ka shiga damuwa na wuce misali, idan ka shiga damuwa kuma, hankalin kowa zai karkata a kanka, hakan ne zai bamu damar kasheka cikin sauki ba tare da Josephine ko mahaifiyarka sun shiga tsakaninmu ba, sai dai kuma abin da ya bamu mamaki, duk halin da muka jefa matar taka a ciki, hakan bai sa ka ɗaga hankalinka ba ma bare har ka shiga damuwa, yanzu dai halin da ake ciki Anderson ya ce mu kashe matar taka, yin hakan shi zai sa dole ka shiga damuwar da zai sa hankalin kowa ya dawo kanka, kai Romeo ka bamu ciwon kai na wuce misali, ka sanya mu cikin bala'i ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba, shi ne yasa Anderson ya ce mu kasheka kawai, wannan shi ne ɗan takaitaccen abubuwan da suka faru, saura amsa zaka samu a wajen Anderson.........". Ya kai karshen maganar yana mayar da numfashi....... Nasan ko a iya haka my readers kun fahimci in da aka dosa, tsayawa nace zan yi dogon jawabi na bada labarin komai dallah dallah ba zai yiwu ba, dan haka ga shi nan a takaice na baku ta yanda zaku gane in da aka dosa. Nisawa Lion ɗin ya yi kafin ya fara magana a nutse "Ni babu wanda ya kare ni face Allah da ya halicce ni, addu'a kuma bata faɗuwa kasa banza, koda kun sanya na faɗi kasa, to ba zaku iya yi mani komai ba, koda hankalin su Josephine ya bar kanmu, ba zaku iya yi mani komai ba, saboda Allah ne yake kareni ba kowa ba, Allah kuma baku isa ku karkatar da hankalinsa ba, kunsan meyasa cutar Meesha bai ɗaga mani hankali ba? Saboda already nasan Allah yana sane da komai, and them nasa evil eyes suna kewaye da mu, sannan na san so kuke ku ga na shiga ɓacin rai da har zata iya sanya zuciyata ta buga, already na san shirinku, shiyasa ban bari na ɗaga hankalinna ba, kai baka yi mamakin ya aka yi ban tunkari Josephine da wannan magana ba na tunkareku kai tsaye? Saboda already na jima da sanin cewa Josephine musulma ce ba krista ba, kuma a duk lokacin da zan yi addu'a a tsakanin iyayena, a kan Josephine ne kawai nake samun kwanciyar hankali ba William ba, tun daga nan na fahimci William ba shi ne ubanmu ba, shiyasa kaga ni ban kula shi ba, saboda bani da time nasa, yanzu duk ba ma wannan ba, ina son ka gaya mani wani yaro ne kuka sanya a cikinmu time da kuka ɗauki cikon TRIPLETS nawa?!". "Yaron da muka sanya a cikinku muka ɗauki wancan ai ɗayan ku ne!". Ya bashi amsa yana wani irin jan numfashi tamkar wanda aka shake yake ƙoƙarin fito da numfashin nasa. "How comes zai zamana ɗayanmu? Ban gane ba". "Romeo kamar yanda na gaya maku ɗayanku ne, hakan yake, ku ba TRIPLETS bane, QUADRUPLE (Ƴan huɗu) ne Aisha ta haifa, to dama kasan ɗanta na fari ta ce ta bamu, kuma na gaya maka uwargijiyarmu bata karɓar ɗan da ba a bayar da shi ba, a lokacin da mahaifiyarku ta haifeku, sam bata a cikin hayyacinta, kuma a gida ta haihu ba a asibiti ba, dan ta ce ba zata je asibiti ba, sai dai a ɗebo mata likitoci a gida, Cherish ce ta jagoranci likitocin da suka karɓi haihuwar tata, so a lokacin mun yi amfani da Cherish ɗin da Josephine ne muka ɗauki yaro ɗaya, dama kasan idan aka haifi TWINS, TRIPLETS or QUADRUPLE ana ɗaurawa wanda ya fara faɗowa duniya wata ƴar agogo launin fara a hannu, alama ce da take nuna shi ne babba, shi ma na biyu haka, har dukkansu, to a lokacin Josephine ɗin sun kiɗime, sai suka bamu ɗan autanku a maimaƙon ɗan farin, har mun fara yin tsafi da shi, sai Uwargijiyarmu ta ce ai wannan iyayensa basu bada shi ba, ba shi ne aka bada ba, dan haka ba zai yi aiki ba, already kuma mun fara taɓa ƙwaƙwalwarsa, hakan yasa muka dawo da shi muka ɗauki babban yayanku wanda har lokacin yana ɗaure da white agogonsa na nuna cewa shi ne babba, yaro na farko da muka ɗauka Mahaifiyarku bata cikin hayyacinta, da zamu dawo da shi kuma tana a cikin hayyacinta, tun ɗaukarsa da kwana biyu muka so mu dawo da shi, amma ba dama, dan kullum tana a tare da ku, ganin hakan ne yasa muka ɗan hakura muna jiran wata dama da zata zo sai mu ɗauke shi. A lokacin da ta kaiwa William yaran, mune nan muka sanya William ɗin ya daki JAMES da sanda a kai, hakan ne ya bamu damar ɗaukar babban yayanku, muka dawo maku da ɗan autanku da muka ɗauka da farko wato Michael, so mu ba wani canza ku da muka yi, ita ma Josephine da wannan taɓa ƙwaƙwalwar Michael ɗin da muka fara yi ne ya bata damar samun hanyar baku kariya ai, so a takaice Michael shi ne wanda muka fara ɗauka, daga baya muka dawo da shi muka ɗauki yayanku, wannan dalilin yasa kaga Michael ƙwaƙwalwarsa ba'a dai'dai take ba, mun rigada mun birkita kwakwalwar mun fara yin tsafi da shi ne, kai baka yi mamakin idan kun tambayi William menene ainahin musabbabin ciwon Michael sai ya ce maku haka aka haife shi ba? Ai shi yasan komai, a gabansa aka yi komai, kawai yaki gaya maku ne, dan ma kada ku gane ba shi ne ainahin mahaifinku ba, William na ainahi yana kungiyarmu! Shiyasa ko wani asibiti da kuka je suka kasa gane me matsalar kwakwalwar ta Michael ɗin...........". Shiru Lion ɗin ya yi yana mamakin yanda waɗan nan tsofaffi suka zauna suka shirya abu tiryan tiryan babu mistake a ciki, lallai sun cika shahararrun ƴan duniya, musamman shi Jacob Uban William ɗin da ya mutu, ya fi kowa iya tantiranci da haɗama, har da bada yaransa guda biyu, Allah mai iko, yanzu wani irin hukunci ne ma ya dace da waɗan nan azzaluman? A kan neman duniya kawai?.........Sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba, shi Lion yana nan, su gwaggo kuma suna gida Nigeria, kada kuma ku manta suna a tare da Uncle Herry da William na karya wanda kuma dukka sun kasance mambobine na kungiyar su His excellence ɗin, kuma ga Lion ya tirke kakansa a nan ya tonawa kungiyar tasu asiri, kuna ganin ƴan kungiyar za su barsu kuwa? Kuna ganin ba za su yi amfani da William da Uncle Herry su cutar da su gwaggo ɗin da suke gida ba kuwa? Kun dai ji Anderson ya yi umarnin a kashe Rimsha! Ga kuma garkuwanta Lion a nan ya taho ya barta, ga shi sun juya mata kwakwalwa ko sallah ma bata sani ba bare ace zata yo askar Allah ya kareta. My peoples PRINCESS TEEMA naku ta amana yau bana jin daɗi, saboda cakwakiyar TRIPLETS har wani zazzaɓi zazzaɓi nake ji! Na barku lafiya❤️