𝐆𝐔𝐃𝐔 𝐍𝐀 𝒜𝒦ℯ 𝔂𝓲. 𝓐𝓼𝓱𝓪𝓷𝓽𝔂 𝓵♡︎𝓿𝓮 /Wannan labarin k'irk'irarren labari ne. Ba'a yishi don wani ko wata ba. Duk wanda yaga ya yi daidai da rayuwar sa arashi ne. بِسْمِ اللهِ الرَّحْمٰنِ الرَّحِيْمِ 1/5. Ruwa ne ake yi sosai kaman da bakin ƙwarya. Yau ranan ce ta litinin ,watan na August. Wata ne na ruwa abun sai godiyar ubangiji. Ƙaramar motace ƙirar pecanto mai ƙofa ɗaya fake gefen titi daidai gada ta kabuga. Tsananin ruwan da ake yasa mutane da yawa suka faka motocin su gefen titi ,saboda rashin gani da gudun faruwar wani mummunan hatsari. Cikin su harda Jaleela dake zaune cikin motar ta Pecanto jaa, wajen zaman direba. Bayan motar yarinya ce ƙarama da bata haura shakera bakwai ba. Tsakanin yarinya da Jaleela babu banbanci ,tamkar tayi ka ki ne ta tufar saboda tsananin kamar da suke da yarinya. Anees dake zaune tana ta zuba da ƴar muryar ta mai daɗi da zaiyi maka nuni da tabbas tana cikin nishaɗi, na wannan yanayi da ake ciki. Harshe Jaleela ta taune tana tura labbanta cikin baki daya zame mata kaman al'ada, musamman idan tana cikin stress. Numfashi ta sauke mai zafi takai hannu tana goge glass ɗin motar da ya yi naso sosai. Ranta gaba ɗaya a dagule yake. Hankalin ta gaba ɗaya ya karkata ne wajen aikinta data makara sosai ,ga makaranta da zata kai Anees. Yau gaba ɗaya bata fito daga gidan ba sai ƙarfe takwas saura, tana fitowa kuma hadari ya haɗu lokaci guda aka tsuge da ruwa mai ƙarfi gaske daya sata dole fakin gefen titi. "Kinji Mummy" Numfashi ta ƙara saukewa tare da lumshe ido ta buɗe ta juyo tana kallon Anees. Manyan Blue eye's nata ta watsawa y'ar tata dake da sak irin su. Muryar a hankali da tsananin taushi tayi magana tana ƙoƙarin ɓoye ɓacin ranta tace "Sorry, me ki ka ce?" K'aramin bakin ta Anees ta ƙara turowa da ƴar shagwaɓa tace "Mummy kullum nace miki ina Daddy sai kice ya yi tafiya. Ban taɓa ganin Daddy ba. Makaranta, Aunty mu kullum sai ta tambaye ni sunan Daddy ,amma kin ki gayamin Mummy " Wani irin dum ƙirjin Jaleela ya matsanancin bugawa. Lumshe ido tayi tana kiran sunan Allah cikin ranta. Saboda yanda ta tsani mutumin da duniya bata da maƙiyi kaman sa, Anees ke amfani da Baby Anees a makaranta babu sunan uba. Haƙiƙa tana tsananin tsoron ranan da sirrin data jima tana ɓoyewa zai tuno. Sirrin daya sa take ta guje-guje ta kasa samun mafaka. Tabbas yanzu ma lokacin barin ta Kano ya yi. A shirye take ta tsare ƴar ta daga dukkanin wani ƙalubale da hantara na rayuwa. "Kiyi haƙuri Anees. Nayi miki alƙwari mahaifin ki na nan zaki sanshi very soon inshaAllahu. " Cutely Anees ta harde hannu a ƙirji tana ɗan zumburo baki kaman mai shirin yin kuka. Furzar da numfashi Jaleela tayi mai zafi ta juya tana kallon waje. Babu laifi yanzu ruwan ya fara tsagaitawa don mutane har sun fara tafiya. Motarta itama ta tayar a hankali ta haura kan titi tana kallon agogon dake ɗaure tsintsiyar hannun ta. Ƙarfe tara da minti biyu ya nuna. Tasan da ace ba ruwa ake ba da tuni an nemeta daga gurin aiki. Maganan Anees ce ta katse mata tunanin da take taci wani mugun burki kan titi ,saboda mota data kusa bugewa. Kalman da Anees ta furta tayi masifar jefata cikin tashin hankali daya sai da idanuwan ta suka cika tab da hawaye. "Mummy ina naki Daddy da Mummy ɗin. Ko ƴan uwanki?. Ban taɓa ganin kowa yazo gurin mu ba sai kawayan ki kawai. Ko bamu da kowa ne?" Anees yarinya ce ƙarama amma tana da tsananin fahimta . Idan tayi wani abu wani lokacin sai kayi zaton ta haura shekarun ta. Akwaita da manyan ce gata da ɗaukan abu. Shi yasa Jaleela ke iya bakin ƙoƙari wajen ganin ta ɓoye dukkanin wani sirri nata, musamman ɗaya sana'ar ta da take. Rai a ɗan ɓace ta juyo ta kalli Anees tace "Tambayoyin menene haka? Bana hanaki idan ina tuki ki dameni da magana ba?. Kina kallo yanzu na kusa buge motar wasu. Ko kina so ranki ya ɓaci?" Shar hawaye suka biyo kuncin Anees a hankali tace "Kiyi haƙuri Mummy " Bata bata amsa ba sai kai data jinjina ta tada motar suka cigaba da tafiya. Harta sauke Anees a k'ofar makaranta tana sharar hawaye. Da ido ta bita harta shige kamartar mai suna Kamfa dake wajen BUk old side. Tanayin dukkanin wani bakin ƙoƙarin ta wajen ganin ta bawa Anees rayuwa da ilimi mai kyau a matsayin ta na Single Mom. Hawaye mau zafi suka biyo kuncinta. Haɗa kanta tayi da sitiyarin motar tana zubda hawaye. Sosai rayuwarta da dukkanin wasu abubuwa da suka gushe suke dawo mata kaman lokacin komai ke faruwa. "Abhie, Ammi. Ya Almu . Ku yafeni" Ta furta a hankali tana wani irin kuka mai taɓa zuciya. Haƙiƙa ta gogawa kanta bakin fenti da bazai zai taɓa gogewa ba a rayuwar ta ba. Ina ma dai ace ana dawo da hannun agogo baya data goge dukkanin wani fenti da tayi wa kanta. Ta nesanta kanta da wanda ya yi sanadin faɗawarta ciki wannan musiba da tashin hankali. Shine ya yi sanadin rabuwarta da gida. Ta baro gatanta, ta baro soyayyar ƴan uwa da kuma Iyaye. Ya gama cutar ta a rayuwa. Da ƙyar ta iya lallashin kanta ta, ta tada motar ta bar ƙofar makaranta. Tara da rabi daidai tayi fakin motar ta ƙofar office nasu na WOMAN RIGHTS HISBA .A hanzarce ta fito riƙe da yar jaka ta ratayawa dake lauke da waya da keys nata na gida dana mota. Sai abaya dake hannun tana ƙoƙarin ɗurawa kan damammiyar doguwar rigar dake jikinta. Tana ƙarasawa bakin ƙofar security ya buɗe mata yana mata sannu da zuwa. Kaman ko da yaushe murmushi tayi masa kafin ta shiga. Numfashi ta sauke bayan ta shiga. Kaman jira ake ta shiga kuwa dukkanin wani ma'aikaci dake gurin ya juyo yana kallonta. Idan da sabo ta saba da irin wannan kallo ,amma abun na yau sai taga kaman yafi yawa ,musamman yanda taga matan na jefan ta da wani irin kallo na izgilanci da ƙyama. Kai ta jinjina ta fara takawa a hankali don zama wajen tebir nata na chasier. "Dubeta da Allah. Kyau babu kyan hali sai shegen girman kan tsiya kaman yar sarki. Ai ni Jamila na gayamiki irin wannan masu Shiru-shirun munafukai ne. Ki duba kiga duk wannan shegen kyan, ashe ciki Fir'auna ne waje Musa. Kina ji ashe y'ar tata Shegi..." Jaleela tayi wani irin kukan kura ta d'auke ta da mari da gaba d'aya floor d'in saida ya amsa. Ihu da kururuwa Zainab ta sa ta riƙe kuncinta tana kallon Jalila da hargagi tace "Ni ki ka mara?" "An mare ki. Ki k'ara furta wata kalma kan y'ata yanzu kiga in ban chanza miki kamanni ba. Shiru ai ba tsoro bane. Nasan mutuncin kai na ne shi yas..." Wata irin dariya Zainab ta saki tana tana hannu. Dole Jaleela tayi shiru tana kallon ta ranta na suya. "Yoo wane mutunci kuma da an riga da an zubar dashi tuntuni a titi. Ko kin d'auka bamu san me ki ke aikatawa ba bane. Y'ar taki ai ba k'arya a kayi ba shegiya ce da bata da uba. Korarriya daga gidansu saboda tayi cikin shege. Kinzo nan kin fake mana da sunan salihar mace mai tsoron Allah. Ashe simimi kasau ce. Waje Musa, ciki Fir'auna. Babu fuss ,babu asss" Duk yanda Jaleela ke k'ok'arin wajen ganin ta danne hawayen da suka cika mata ido zuba, saida suka biyo kuncinta. Taune lebe tayi don bata da wani kalma da zata furta , dukkanin abun da Zainab ta fad'a gaskiya ne. Bata da wani abu da zatace ta kare kanta. "Mtswwwwww." Zainab ta k'ara jan wani irin dogon tsaki jikinta na tsuma kaman mai shirin yin dambe. Numfashi Jaleela ta sauke mai zafi ta d'an ja baya tana kallon mutanen gurin da sukayi shiru kaman ruwa ya cinye su. Yawancin su suna cikin nishaɗi n abunda ke faruwa. Tasan kuma yanda da yawa suke jin haushin ta sai sunfi kowa san ganin sunyi damben da Zainab. "Jaleela Mukhtar Bature" Babbar shugabar su ta Woman rights ta kira ta tsaye daga bakin k'ofar office nata. Hakan kawai sai taji gabanta ya tsananta fad'uwa. Da kyar ta iya taka k'afarta ta bita office d'inta. Bata yarda ta juya ta kalli su Zainab da take jin tashin dariyar su. A hankali ta tura k'ofar ta shiga bakin ta d'auke da yar siririyar sallama. Zaune ta sami shugabar tasu kan makeken kujerar ta dake d'auke da tebir. Da hannu ta nunawa Jaleela kujerar dake fuskantar ta. Jiki a sanyaye ta ja kujerar ta zauna tana kallonta. Bata ce mata uffan ba saida ta gama dube-dube cikin drawer ta fito da wasu takardu. D'agowa tayi ta kalli Jaleela take faman had'a zufa duk matsanancin sanyi da office d'in ke dauke dashi. Da murya mai kaushe tace "Jaleela. Nasan kina cikin fargaba na wannan kira da nayi miki. Tambaya d'aya ce nake sonyi miki." Shiru tayi tana kallon Jaleela dake sauke numfashi da a hankali. Kai ta d'an jinjina ta cigaba da cewa "Tambayar da nake sonyi miki shine. Kin tab'a aure ne?" Dum k'irjin Jaleela ya buga har H lami dake fuskantar saida taji yanda zuciyar ta ta ke bugawa. "Ki kwantar da hankalin ki. Ina so ne mu kawar da zargi da ake miki. Kwana biyu da suka wuce an kawo mana wasu korafi a kan ki. Saboda girman abunda aka kawo mana yasa muka k'ara yin bincike a kan background naki. A iya sanin mu kin sanar damu cewa baki da aure. To shin kin tab'a aure ne wata kaddarar ta sameki har ki ka rabu da mijin ki?" Gumi ne mai zafi ya karyowa Jaleela bakinta na rawa a mugun hankali tace "A'a " "Ikon Allah. To ya aka yi kuma ki ke da y'a dake da shekaru 7 a duniya. Kina so kice min yarinya taki bata hanyar Sunna aka same ta ba?. " Wani irin kuka ne ya kwacewa Jaleela ta danne shi, hawaye masu zafi suka biyo kuncinta ta. Kai H Lami ta girgiza rai a dagule tace "To maganan gaskiya Jaleela baza mu cigaba da d'aukan ki aiki a nan ba. Mu hisba ne da muke yak'i da mutane masu miyagun hali ,wajen ganin mun d'ora su kan turba mai kyau. Bayan haka mun samu labarin wani mummunan sana'a da ki ke aikatawa bayan wannan. Saboda haka mun yanke hukunci sallaman ki. Bazamu iya cigaba da zama dake ba. Ina so ki saka hannun a wannan takardar don mun kore ki " Hannun Jaleela na rawa ta karb'i takardar data mik'o mata ta saka hannu hawaye na diga kan takardar. Da wani irin sanyin jiki ta miƙe tayi bakin k'ofa zata fice. Lami tace "Amma naji mamakin wannan mummunan dabi'u da ki ke a b'oye Jaleela. Yanayin ki baiyi kama da mace mara daraja ba, mace mara sanin ciwon kanta na y'a mace. Mace data fifita duniya a kan lahirar ta. Yanzu me zaki ce da y'ar taki da ki ka haifa a titi a duk lokacin data buk'aci sanin waye uban ta?" A guje ta buɗe k'ofar ta fice tana wani irin kuka kaman mai shirin tada asmah. Zainab da sauran ma'aikatan dake jiran fitowar ta suna ganin yanda ta fito suka kwashe da mahaukaciyar dariya harda masu tafawa. A guje ta fice tayi wajen motar ta. Jiki na rawa ta buɗe ta shiga. Had'a kai tayi da sitiyarin motar tana kuka sosai kaman babu gobe. A karo na babu adadi nan ma sun Guje ta saboda kaddarar data same ta. 𝐆𝐔𝐃𝐔 𝐍𝐀 𝒜𝓀ℯ 𝔂𝓲. 𝓐𝓼𝓱𝓪𝓷𝓽𝔂 𝓵♡︎𝓿𝓮 6/10. Ta jima zaune cikin motar kafin tayi jarumta ta bar k'ofar office d'in. Maimakon tayi gida sai tayi inda take tunanin nan ne kad'ai zatafi samun nutsuwar zuciya. Kai tsaye tayi club dake can wajejen Suleiman crescent. Harabar gurin cike yake da motoci kace dare ne. Kowa yasan club yafi ci da daddare. Guri ta samu ta faka motar ta, bata fito ba saida ta cire abayar dake jikinta da d'ankwalin ta. Dogon gashinta dake nan har wanen hips nata ta sake shi wanda ta d'aure da ribbon . A hankali ta fito riƙe da waya da muk'ullin motarta a hannu. Rigar dake jikinta ba k'aramin kamata tayi ba wanda hakan ya bawa shape nata da k'irar ta fitowa muraran. Abun sai wanda ya gani tabarakalla Jaleela ba dai kyau. Akwai kyawu na fuska dana jiki amma babu na zuci. Daidaikun manyan Boy's dake gurin suna ganin fitowar ta suka bito da ido chaa kaman kura taga nama. Yanda take jinta a yanzu bata tunanin zata saurari wani namiji. Rai a dagule ta shige club d'in. Saida ta fara yiwa kanta order na drinks masu sanyi da y'an snack sannan ta wuce ta samu guri daga can b'angaren Vip ta lafe a bunta. Sosai tayi zurfi cikin tunanin rayuwar ta da irin kalubale da take fuskanta tun daga ranan data baro gida da gatanta, har zuwa yanzu da take iya bakin k'ok'ari wajen ganin ta bawa Anees rayuwa mai kyau. Duk wani namiji daya yunƙuro inda take zata watsa mata mugun kallo dole ya juya yana cije lebe. Yau sam bata marmarin kasancewa da wani namiji. Numfashi ta fesar ta d'aga lemonta na orange juices mai sanyi ta kora tana tunanin ,wai shin duk ina mutumin daya jefata ne cikin kangin rayuwa?. Mutumin da ya yi sanadin ta zama abun gudu da kyama?. Idan yasan cewa tana tare da y'ar sa zai k'arbe ta hannu biyu?. To wai shi d'in waye ne ma?. Menene asalin sa?. Haka tayi ta jerawa kanta tambayoyi har na tsawon wasu lokata. Hak'ika idan ta k'ara had'uwa da Mutumin nan bazata tab'a yafe masa uk'ubar daya jefata a ciki ba. Baza ta daina yi masa Allah ya isa ba da yi masa Addu'a, Allah ya gaggauta k'arban mata hakkin ta a duk inda yake a fad'in duniya. Ya hukuntashi kwatankwacin uk'ubar daya jefata a ciki. Ba ita ta baro Club d'innan ba saida ta daidaici lokacin tashin Anees ya yi daga makaranta. Tana fakin motar k'ofar makarantar su ana tashin su. Bata jima ba Anees ta fito a guje hango Mummyn nata datayi. Suna tafe a hanya tana bata labarin abunda yau sukayi a makaranta. Duk irin damuwar da take ciki haka ta daure tayi ta biye bata ko itama zata samu salama a zuci. Ta gama yankewa gobe inshaAllahu zasu bar Kano sai kuma wani lokacin bi'iznillahi. Saida suka tsaya nan Rufaida. Suka siyi yan snacks da fura sannan suka wuce gida. K'arfe biyu ta miƙa Anees makarantar Islamiya dake can gabn layinsu nan first gate. Kafin Anees ta dawo daga makaranta tuni Jaleela ta gama had'a musu kayansu da dukkanin wani abu da zasu buk'ata. Masu gidan ta kirasu ta sanar dasu zata tashi gobe inshaAllahu. Bayan dawowar Anees daga islamiya ta iske kayansu a fake guri d'aya. Ran Anees sosai ya soso dan ta gaji da wannan yawace yawacen da suke gari-gari. Yarinya ce ita k'arama amma tana da hankali. Yanzu idan suka koma wani garin shima haka zata fara komai sabo. Makaranta, kawaye. A guje ta shige ɗakin dake kallon na Jaleela tana kuka. Da yake gidan flat ne k'arami mai d'auke da d'aki biyu sai toilet daga tsakiyar sa inda ya raba dak'unnan. Sai falo da kitchen. Daga waje gidan nada y'ar relar da aka kawata da y'an bishiyu na furanni masu kyau. Babu yanda Jaleela batayi ba don ta rarrashe ta amma fafur tak'i ko abincin dare tak'ici ,k'arshe haka ta zuba mata ido har barci ya d'auke ta. Numfashi mai k'arfi Jaleela taja ta gyara mata kwanciya ta rufe ta. Tasan akwai gajiya, amma duk abunda takeyi tana yine saboda ita. Bayan tayi sallan isha zama tayi sosai tana rera kira'a mai tsananin dad'i kace Sudais ne a mace. Ni kaina mamaki ya kamani na zuba mata ido baki a sake ina kallon yanda take karatu a nutse babu gargada. Komai tana bashi hakkin sa yanda ya dace . Ikon Allah idan kaga Jaleela a yanzu koda wasa aka ce maka itace d'azu a club baza ka tab'a yarda ba. Kai k'arshe ma sai kayi fad'a da mutum don babu abunda zai hana kayi zaton sharri ne ko kage ake mata. Yanda take rera karatun zai tabbatar maka tayi sauka ba d'aya ba, bare biyu. Wai shin wacece ne Jaleela?. Awa guda cur ta d'auka tana rera karatun Qur'anin nan mai saka zuciya da kwanji cikin nutsuwa da annashuwa. A hankali ta rufe Qur'anin ta ajiye gefenta. Hannu ta d'aga tana rera Addu'o'i masu tab'a zuciya da bargon jiki. Sosai hawaye suke bin fuskarta tana rerawa Annabi salati da kiran sunanyen Allah, kyawawa ya kawo mata sauk'i cikin wannan rayuwa data tsinci kanta a ciki. Washegari misalin k'arfe bakwai na safe suka d'auki hanyar Abuja. Saida Jaleela tayi Addu'a sosai kafin ta shiga mota suka d'auki hanyar. Sosai Jaleela ta kware wajen tukin mota tana bin dukkanin wasu k'aidoji daya dace. Ga motar ta saki karatun Qur'ani na sheikh Sudais da Ali jabir. Bata cika tsayawa ba sai in Anees ta buk'aci yin fitsari. Wajen azahar suka isa Kaduna. Saida suka tsaya sukayi sallah ta k'ara cika musu mota da kayan abinci ,su tsire da y'an snacks da lemoka ,sannan suka d'auki hanya. K'arfe uku daidai suka shiga birnin tarayya. Kaman yanda kawarta Kainat tayi mata bayanin unguwar da take. Kai tsaye tayi Gwarunpha phase 2. Unguwar ce gwanin sha'awa ta manyan mutane harma da masu matsakicin rufin asiri. K'ofar wani k'aramin gate gida na bene tayi horn d'in motar ta. Maigadi ya buɗe ta danna kai cikin gidan. Tun kafin tayi fakin motar ta hango Kainat data fito a guje daga gidan sanye cikin riga da wando na jeans da t-shirt fara. Kannan nata yasha gashin doki har hips nata. Kainat irin black beauty d'in nan ce mai yar kiba. Bata da tsayi sam shi yasa koda yaushe cikin heels takarmi take ko a cikin gida. Kainat idon Naira kenan akwaita da san kuɗi da son jindaɗi na rayuwa. Murmushi Jaleela tayi hango Kainat d'in da tayi. A guje ta k'araso tana ihu ta kama murfin motar ta buɗe. "Wayyo Beauty wai kece yau a gida na da gaske?, wlh da ki ka yimin waya na d'auka wasa ki ke. Wayyo jama'a yau ga Beauty a gidana " Y'ar dariya Jaleela tayi tana girgiza kai ta juya tana kallon Anees data fara motsin farkawa daga barcin da take saboda ihun Kainat. A hankali yarinya ta buɗe manyan Blue eye's nata ta watsa su kan Kainat dake kallonta kaman ta had'iye. Da sauri ta matsa bayan motar ta d'auko Anees dake yunƙurin zama. "Kai gaskiya MashaAllah Jaleela. Wlh komai naki mai kyau ne. Yanzu dubi yarinya nan don Allah kaman ba mutum ba saboda kyau. MashaAllah " Da taimakon Kainat suka shigar da kayan su ciki. Gaba d'aya bakin Kainat yaki rufuwa duk ta rikice sai zuzuta kyan Anees take, gashi yarinya ita kuma tak'i sake mata sam. Duk da sunci abinci saida Kainat ta k'arayi musu order na take away. Ranan sam ta hana dukkanin wani aboki nata zuwa gidan. Itama Kainat kaman Jaleela zaman kanta take. Gidan da take ciki yanzu ma wani sugar Daddy nata ne ya bata. Dukkanin wani abu da take dasu daga mota har wayoyi dake hannun ta,abokan harkar ta ne suka bata. D'aki guda Kainat ta bawa Jaleela da Anees. Duk da cewa gidan k'aramine, an kashe masa dukiya ta kece raini. Babu abunda babu a ciki. Wanka Jaleela ta farayi kafin tayiwa Anees ta shirya ta cikin doguwar riga pink mara nauyi. Saida ta kwantar da ita tayi mata Addu'a ta kwanta nan gefen ta har tayi barci sannan ta miƙe ta jera musu kayansu cikin kwaba. Lokacin data gama an fara kiraye-kirayen sallan isha. Saboda haka ta koma ta d'auro alwala ta saka doguwar riga mara nauyi da katon hijabi daya kai mata har k'asa tayi sallah. Kaman yanda ta saba bayan ta idar zama tayi tana tilawa karatun Qur'ani. A haka Kainat ta shigo ta sameta. Mamaki ya rufe Kainat jin yanda Jaleela ke rera karatun Qur'anin. Ita dama tun ba yauba sun san Jaleela akwai ibada. To amma tana da wannan ilimin take irin wannan harkar?. Ko da yake ko wane bawa da sanadin kaddarar sa. Har yanzu basu san dalilin daya jefa Jaleela cikin wannan rayuwa da suke ba, don har yau tak'i sanar dasu komai. Guri ta samu gefen gadon ta zauna tana sauraran yanda Jaleela ke rere karatu. Tunawa tayi ita yaushe rabon da ma ta d'auki Qur'ani ta karanta?. Kai ko sallah idan zatayi Falak'i da Nas kawai take karantawa don tasan idan tace zata d'auko doguwar surata to tabbas zatayi kwaba, saboda babu karatun. Dama shi Qur'ani idan ka barshi ne da kwana d'aya ya barka da shekara guda. Tana jin Jaleela ta kai aya ta k'arshe tana 'Subhanakallahumma ashhadu an la'ilah illa'ant. Ashtagfurullahi wa'a tubu ilai'. Tace "Yauwa kin idar?. Ke nake ta jira tun d'azu. Na samo miki babbar harka...." Saurin katseta Jaleela tayi ta hanyar girgiza mata kai. Shiru Kainat tayi tana kallon Jaleela data nuna mata Qur'anin dake hannun ta. Miƙewa tayi ta fara ajiye Qur'anin a gefa cikin nutsuwa, ta cire dogon hijabin dake jikinta ta ninke shi ta ajiye cikin kwaba, sannan ta juyo inda Kainat ke zaune tana kallonta cike da mamaki. Saida ta nannade daddumar da tayi sallan a kai, sannan ta sami guri kusa da Kainat ta juyo tana kallonta tace "Yanzu ya dace kiyimin wannan maganan amma muje falo ,Anees tana barci" Baki Kainat ta buɗe amma babu abunda ya fito. Tsananin mamaki ya saka ta saki bakin tana kallon Jaleela. Wai Jaleela nada irin wannan addini take wannan mummunan dabi'u?. Ita kuwa wane irin mummunan iftila'i ne ya sameta haka take irin wannan rayuwar?. Duk abunda take haka, baisa ta manta da ibada ba. Falo suka fito Kainat ta wuce kitchen ta deb'o musu drinks da gashin kaza . Bayan sun nutsu take gaya mata kamun da tayi mata. DUBAI /ABU DHABI. THE PALACE. Katuwar masarautace da aka zuba mata dukiya kace baza'a mutu ba. Komai na masarautar tun daga wajen sa har cikin sa anyi sa da zenare da crystal stones. B'arin KING LK kuwa da daimons aka kerashi kace ruwan su ake. Kowa yasan Abu Dhabi shine b'angaren da dukkanin wani hamshakin mai kuɗi na duniya ke yada zango a Dubai ,wasu ma suna da gidaje na kansu a can, saboda Abhu Dhabi shine k'arshen gari na masu kuɗi. Kyakkyawar macece da bazata haura shekara 40 ba cikin wani tankamememen falo da aka k'awata da abubuwan more rayuwa. Tana zaune ne cikin wata lallausar kujerar mai tsananin taushi da akayi wa ado da zinare. Gefenta a tsaye,kuyangi ne wasu na mata firfita duk da cewa akwai Ac ta ko wane lungu da tsako na falon da girman sa ya yi wani k'aramin flat house d'in. Falon cike yake da bayi da suke tayi mata bauta. Gefenta yarinyace da bata wuce shekara 20 ba zaune k'asan lallausar kafet wajen kafar ta. Kaman yanda wannan babbar mata ke sanye cikin alkyabba ta sarauta data sha ado da zinare, haka itama yarinya. Daga gefen matar wasu manyan dattijai ne guda biyu zaune cikin kujeru dake fuskantar ta. Numfashi ta sauke mai k'arfi tana k'ara bin dattijan da kallo, kafin ta mayar da ido kan yarinyar dake zaune wajen gefen k'afar ta. Numfasawa ta k'arayi ta buɗe baki tana magana da muryar ta mai sanyi da dad'in sauraro da harcen larabci. "Anya kuwa wannan abu mai yiwu wane?. Kar ku manta irin kalubale da muke fuskata cikin wannan masarautar duk lokacin da wannan abu ya faru. Mata da yawa, rayuwar su ta salwata saboda wani sirri da mun kasa gane masa. Kuna ganin babu cutarwa cikin wannan LAMARI idan aka sake tafka wannan kuskure a karo na hud'u?" To fa wane sirrine wannan? Wannan tafiyar ta dabance. Kudai ku cigaba da bibiyar alkalamim Ashantylove. Kafin muyi nisa wannan littafin PAID BOOK ne. Zaki iya fara biya tun tafiyar bata fara zafi ba @ 500N kacal. Domin neman k'arin bayani ko tuntu'beni a wannan number 👇 08140754777 𝗚𝗨𝗗𝗨 𝗡𝗔 𝒜𝓀ℯ 𝓎𝒾. 𝓐𝓼𝓱𝓪𝓷𝓽𝔂 𝓵♡︎𝓿𝓮 11/15. Balaraben dattijan daya fi kusa da ita, wanda ke sanye cikin bak'ar alkyabba da rawani kaman yanda malamai suke. Hannun sa carbi ne kato mai d'auke da sunayen Allah. Saida yaja dogon salati da yin istigfari sannan yace da harcen larabci. "Hak'ika kin kasance Malika, sarauniya mai adalci da kuma tausayin talakawan ta. Kin kasance sarauniya dake sauke nauyi da Ubangijin sammai da kassai ya baku, bawai don kunfi sauran bayin sa ba, sai dan hakan yana daga cikin hikima irin tasa. Hak'ika Ubangiji bai hallici ko wane bawa ba ,saida ya rubuta masa kaddarar sa. Wannan kuma na daga cikin jarabawar ku" Shiru ya yi yana d'an jan fasali. Wani bafade dake gefen sa, ya yi maza ya zuba masa ruwa cikin wani irin glass cup mai kyan gaske ya miƙa masa cikin girmawawa. Karb'an ruwan ya yi ya d'an jik'a makogaro sa. Malika dake zaune tana sauraran sa, ta sauke numfashi. Allah kaɗai yasan abunda ke ranta. Juyowa mutumin ya yi sosai yana fuskantar ya cigaba da cewa "Tabbas Abu Sufyan da y'ar sa Aafiya sunsan kalubale da ake fuskanta cikin wannan masarauta. Ba suzo nan ba saida suka tabbatar da dukkanin wani jita-jita da ake yad'awa , walau gaskiya ne ko k'arya . A shirye suke wajen ganin sun tayamu yak'i da wannan b'oyyeyyen sirri da muka kasa gane masa. Sun kasance d'aya daga cikin dubbunnan Al'umma dake da burin ganin wannan masarauta mai Albarka ta had'a zuri'a dasu, du da sanin su na cewa rayuwar ya'yan su, ko su kansu ya'yan na iya salwanta. Yareema mai jiran gado dole yana buk'atar mace da zata taimaka masa kan wannan karaga ta MULKI. Lokaci na ja, lokaci na tafiya. Yanzu ne lokaci daya dace Yareema ya hau Mulki. Shine kad'ai ya cancanta domin shine ya kai wannan munzali ba kannen sa ba. Ya kamata Malika ta huta da dawainiya da dubbunnan Al'umma dake wuyanta. Ta sauka ta bawa Yareema mai jiran gado. Haka zamuyi hak'uri mu cigaba da kawaiwa Allah kukan mu har zuwa lokacin da zai yaye mana wannan musifa. Aafiya a shirye take don zama dashi da jure dukkanin wani kalubale da zata fuskata. InshaAllahu zamu samu nasara nan bada jimawa ba. Mu dage dayi masa Addu'a da yawanta sadaka har Allah ya kawo mana mafita" Shiru falon ya d'auka baka jin komai sai k'arar Ac da saukar numfashin sa. Manyan idanuwanta dake b'oye cikin farin glass Malika ta lumshe. Saida ta d'auki sama da minti biyu a haka tana tunanin da Allah kaɗai ya sani. Cikin nutsuwa ta k'ara gyara maza ta buɗe idan nata a hankali ta watsa su kan Aafiya dake zaune gefen ta. Magana tayi da murya mai taushi. Kai kanajin yanda tayi maganan kasan sarauta an gaje ta ciki da waje. "Aafiya " Ta kira sunanta. A hankali Aafiya ta d'ago kai da girmawawa har tana d'an yunƙurawa. Ido Malika ta zuba mata. Tabbas Aafiya yarinyace kyakkyawa san kowa kin wanda ya rasa. Bazata so ace yarinya k'arama kaman wannan ta had'u da wannan cruel fate ba da saura mtan da suka zo cikin masarautar nan, kaman dai yanda Aafiya sukayi da mahaifin ta. "Kina san ibni?"(D'a na?) Kai Aafiya ta k'ara d'agawa a kunyace. "Zaki iya zama dashi duk da sanin ki na abunda ke faruwa matsawar ki ka aureshi?. Duda da kinsa cewa zaki iya rasa rayuwar ki?" Nan ma dai kai Aafiya ta k'ara d'agawa. Ido Malika ta zuba mata cike da nazari. Hak'ika tana cikin mamakin yanda mata ke sadaukar da rayukan su a kan d'an nata shi kuma sam basa gaban sa. Tana burin d'an nata ya yi aure ya hayayyafa don cigaba da gina wannan masarauta data taso tun kakanni daga zuri'ar su. Kai ta d'an jinjina ta juyo da kanta wajen Abu Sufyan. "Abu Sufyan " "Na'am ya Malika" "Kaji ka aminci kuma kayi Na'am da wannan abu?, idan har kana da ja zaka iya magana. Aafiya y'ar kace babu wanda ya isa da ita kaman kai. Ka yarda ta kasance matsayin matar d'ana LAMEEN KHALELULLAH?. Sarauniya a wannan masarauta?" Da girmawawa sosai yace " Na'am ya Malika " Numfashi ta k'ara saukewa ta mayar da idonya kan Wazir dake gefenta. "Ayi shela da sanarwa cikin satin nan Yareema zai sake aure. Ayi sadaka ta Shanu da rakuma na dubu hamsin, da kuma sauka sau hamsin don samun nasara da kuma kariyar ubangiji" Murmushi ne kwance kan fuskar Wazir da Abu Sufyan har Malika ta miƙe don barin fadar. Kallon Wazir tayi da Abu Sufyan da suka rungume juna bayan sunyi musa baha na taya juna murna kaman yanda Larabawa ke yi. Kai ta d'aga musu ta wuce bayin ta da fadawan ta suka rufa mata baya. Wata had'addiyar lifter dake cikin falon ta glass da aka kawata da gwal ta shiga ita kad'ai sai wata baiwa dake binta duk inda tayi. Sauran suka shiga wata dake jikin wannan. Hannu ta kai a hankali ta dafe goshinta da take ji kaman zai rabe biyu ,sosai take cikin damuwa da tunanin kaman sun k'ara tafka wani kuskuren babba. Tana fargabar abunda ya faru da sauran matan da Yareema ya aura, ya faru ga Aafiya . Duk cikin yaran dake rububin zuwa ,bata san me yasa ba Aafiya tafi kwanta mata a rai. Ko dan hakan yana da nasaba da hankali da kuma tarbiyar da take tunanin yarinya na tare da ita ne?. A hankali ta furta a fili "Ya rabbil samawati, ya ubangijin sammai da kasai. Ya ubangijin dukkanin wata halitta. Mutum ko Aljan. Ya wanda ya halicci ruwa, ya halicci iska, ya halicci wuta da Aljanna. Ya Zuljalalu wal Ikram. Allah ka kawo mana mafita cikin wannan sark'arkiya da bamu da amsar ta. Allah ka kawo mana k'arshen wannan musiba. " Baiwar dake kusa da ita ta amsa da Amin cike da tausayin uwar d'akin nata. Hak'ika tun tasowar ta cikin masarautar nan taga irin gwaggwarmaya da SARKI KHALELULLAH ya yi da matarsa MALIKA, ARWA . Tasan dukkanin wani kalubale da jarumta da sukayi wajen ganin sun gina wannan masarauta mai Albarka. Taga irin jarumta da Malika tayi bayan k'asa ta rufewa SARKI KHALELULLAH ido. Irin dawainiya da take da ya'yan ta da mutane wajen basu kulawa da kariya daga dukkanin wani sharri da kalubale na rayuwa. Na ciki dana waje. To amma Yareema yana tare da wani sark'arken abu da an kasa gano masa. Anyi maganin sammu, anyi na aljanu. Amma an kasa samun nasara. A yanzu kam Addu'a ce kawai ake yi da yawan sadaka Allah ya warware koma menene. Ita kanta tana tausayin Aafiya. ABUJA. To Jaleela dai kam an zama mutanen Abuja. Duda dama Abujan ba bakon ta bane. Sai dai zuwanta yanzu ,Kainat tayi yawo da ita sosai cikin garin Abuja musamman clubs dake ci sosai na manyan yara. Tunda suka zo take ta fad'i tashi wajen ganin ta mayar da Anees makaranta. Yarinya har sukayi kwana biyu ta kasa daina kunci ,sam taki walwala. Abun tun baya damun Jaleela har ya fara damunta. Don haka yau ta d'auke ta suka dinga yawo Park,Parks da mall don ganin tayi walwala. Ai kuwa Anees tafi kowa farin ciki. Rabon da Jaleela taga farin ciki kan fuskar yarinya kaman haka harta manta. Sannu a hankali ta fara warwarewa musamman yanzu data fara zuwa makaranta tayi kawaye sosai. Kowa yana son ganin ya zama abokinta saboda kyau da Allah ya bata ga masifar k'ok'ari. A b'angaren Jaleela itama abun haka ne. Don yanzu dukkanin wani clubs da suke zuwa ita da Kainat tayi suna. Sunanta na clubbing shina LA REINA ,the cold Beauty. Ba ko wane namiji ne yake cire tuta a kanta ba sai ta zaba ta dirje kafin kace me,kuɗi sun fara zamarwa Jaleela tana wadaka dasu sai abunda taga dama. Nanny guda ta d'aukowa Anees dake kulawa da ita idan basa nan, duk da cewa basa fita sai ta tabbatar Anees tayi barci haka nan duk inda take, duk inda hud'u na asuba tayi zata dawo kafin Anees ta farka. Ciki kwana biyun nan ma basu cika had'uwa da Kainat ba saboda tayi busy sosai da wasu alhazawa da suka zo Nigeria. Ita dai Jaleela nata harkan bata bada kanta. Zatayi maka dukkanin abunda ka ke so amma baza ka tab'a ba tare da kasa ko yatsa a jikin ta ba. Wannan shine sharad'in ta. Abunka da mai kyau a guje mazan ke k'arban wannan offer, sudai indai zasu huta ai basu da matsala. Can k'asan zuciyarta tana kyamar wannan abu da take. Kai su mazan ma gaba d'aya ta tsane su , don namiji shine SILAH na fad'awarta cikin wannan halaka. A ganinta wannan abu da take shine kad'ai zai bata damar da zata bawa Anees rayuwa mai kyau. Dukkanin wani abu da zatayi gani take baza ta samu ba kaman yanda take samu haka ,bare har ta gina musu rayuwa mai kyau. (To amma kin manta kuɗi irin wannan basu da Albarka tunda ba ta hanyar mai kyau aka same su ba). Yau asabar daga ita har Kainat suna gida. Gaba d'ayan su suna falo ne. Jaleela na kwace cikin katuwar kujera sanye da riga da wando pink color. Anees na sanye cikin wata y'ar k'arama gown silver mai hoton unicorn a jiki. Kanta an rabashi biyu an kamshi gefe da gefe. Kainat kuwa n kwance kasan kafet tana mafa da waya daga ita sai y'ar doguwar riga mara nauyi. Ihu tasa ta miƙe tana zare ido a waje. A kasalance Jaleela ta kalleta ganin yanda duk ta rude riƙe da waya baki a hangame. Anees tace "Aunty Kainat, menene? Ko kinga dodo ne a wayar?" Dariya Kainat ta saki a hanzarce tace da Anees. "Baby jeki d'aki ki d'aukomin laptop d'ina kinji y'ar Albarka " A guje Anees ta ajiye Teddy da take wasa dashi tayi d'akin a guje. Da azama Kainat ta taso ta zauna kusa da Jaleela dake kallonta. Saida ta nuna mata wayar hannun ta tace "Gaskiya ke ko, ta dabance wlh. Labarin ki kawai yaji yake nemanki ruwa a jallo. Kinsa waye yake nemanki kuwa? Yanzu nan Khairat ta turo min. Kin san waye? ZAIN" Ta fad'i sunan da k'arfi. Tsaki mai k'arfi Jaleela ta yi tace "Waye kuma haka?" Ido Kainat ta waro harda d'aka mata duka "Zain ne baki sani ba?, d'an minister babban likita dake zama a turai. Ance yazo gari yaji labarin ki shine yace yana son had'uwa dake. Ko kinsan irin sa'ar da zaki taka idan ki ka kasance dashi?. Mata da yawa suna mafarki a kansa da burin kasancewa dashi kona rana d'aya ne. To ganin sa ma wahala yakewa mutane bare ka same shi. Kaman yanda ki ke juya mutane shima haka yake dan yaga yana da kyau. Ga kuɗi, ga kyau, ga aji, ga class. Haba wlh kedai kina da sa'a, manyan yarane kawai ke binki, ko da yake kin cancanci hakan ne don duk yanda mutum zai kiyasti ki kin wuce haka" Baki Jaleela ta tab'e cikin ko in kula tace "Bani da lokacin sa" Kainat ta buɗe baki zatace wani abu Anees ta fito a guje da laptop d'in datace ta d'auko mata. Dole ta taune harshe tayi shiru da maganan, amma ta kudurta a ranta dole nema ta had'asu. Itama ta yagi abunda zata yaga Jaleela baza tayi mata bak'in ciki ba. 𝗚𝗨𝗗𝗨𝗡𝗔 𝒜𝓀ℯ. 𝓐𝓼𝓱𝓪𝓷𝓽𝔂 𝓵♡︎𝓿𝓮 16/20. Tsawan kwana biyu Kainat nayin dukkanin iya bakin k'ok'ari wajen ganin ta shawo kan Jaleela sunje club d'in da take tunanin Zain na zuwa, fafur Jaleela tak'i kwana biyu ma babu inda taje ta mak'ale a gida wajen Anees. Duk hanyar da Kainat ta biyo Jaleela zata toshe dole tayi shiru ta zuba mata, amma k'asan ranta tana had'a plan. Saida tasan yanda zatayi ta samu number Zain. Da farko tayi masa kiran duniya yak'i d'agawa saboda isa. Haushi kaman ya kashe Kainat. Batayi k'asa a gwiwaba ta tura masa sak'o cewar ita tasan yarinya da yake nema La REINA, the cold Beauty. Zata had'ashi da ita amma sai ya bata kaso mai tsoka. Lokacin da sak'on ta ya shigo wayarsa yana kwance ne cikin tamfatsetsen d'akin sa da aka kashewa dukiya. Gajeren wando ne a jikinsa da single. Zain kyakkyawan mutum ne irin handsome black beauty d'in nan. Yana da manyan lumsheshshun idanuwa da dogon hanci ,bakin sa irin full d'innan ne dake nan jazur dashi ,kuma very oily kaman wanda ke shafa masa man leb'e. Zain yana daga cikin irin mazannan da za'a kira tsaka-tsaki a fannin tsayi. Yana da murdadden jiki burin ko wace mace. K'irjinsa kuwa cike yake da gashi yala-yala daya kwanta tsam gwanin sha'awa. Haka fuskar sa kewaye take da dan siririn gashi daya zagayo har zuwa bakinsa. Ana kiran irin wannan gyaran fuska da kwata million. Zain kan abun MashaAllah don ya gama had'ewa ta ko wanne fanni. Bak'ar fatarsa da taji hutu da kuɗi sai shek'i take irin ta aje butters. Ga fatar tasa da mugun laushi kaman mace. Bashi da gashi sosai a kansa don gashinsa irin namu ne na malam bahaushe, amma saboda gyara da mai da kan kesha gashin ya kwanta lum kansa, ya nannade kace hula ya d'ura. Hankalin sa da nutsuwar sa gaba d'aya yana kan laptop nashi ne yana duba wani file da aka masa transfer na wata mata da tayi mummunan had'ari a can CALIFORNIA. had'arin ya yi muni da dole ake buk'atar manyan likitoci surgeon's don su dukafa a kanta, wajen hatsarin da tayi ne wani irin rodi mai tsananin k'arfi ya huda ta kasan habarta ya bullu ta saman kanta. Kana ganin kwakwalwarta dake motsi ga jini dake fita ta kan nata yana tsartuwa kaman fanfano. Likitoci sun had'u sosai a kanta wajen ganin an bata taimakon gaggawa, duk da cewa da yawa suna tunanin bazata kai ko ina ba. Sai akayi rashin sa'a Zain baya k'asa lokacin da abun ya faru. Da za'ayi mata aikin sai Zoom call akayi dashi yana ganin yanda abun ke gudana yana bada taimakon da yake ganin ya dace. Cikin ikon Allah kuwa aka cire k'arfen amma saida aka kwana aka wuni sunayin. Yanzu matar tana kan bed rest ne don ta shiga coma. Bayan samun nasara na wannan babban aiki da akayi. Tun dawowar sa bai fita ba sai ranan ya shirya don samun fresh air. Bayan zuwansa club d'in ne yaji maza na magana kan Jaleela, da yanda suke buri ganin sun samu lokacin ta kona awa d'aya ne. Amma ita d'in wuyar samu take sai ka ajiye kwalitis da take so. Yanda yaga mazan na hauka a kanta duk inda ya wuce maganan The Cold Beauty suke. Hakan yaji shima yana da interest a kan wannan yarinya. Baiyi zaton zataki amsar tayinsa ba duba da matsayin sa da yanda mata ke hauka a kansa. Saboda wannan ja masa class da take yaji interest nashi a kanta ya kara picking. Murmushin gefen baki ya yi bayan ya gama karanta sakon Kainat. A take ya bata amsa yace ta turo account nata zai saka mata kuɗi. Yana ajiye wayar aka buga k'ofar d'akin nasa aka shigo. Yarinya ce ta shigo da bata wuce shekara 18 ba. Kyakkyawace ta gaske Black beauty. Kallo d'aya zakayi mata kasan sun had'a alaka da Zain. Manyan idanuwansa ya d'ago ya watsama mata ta shigo rik'e da tray dake d'auke da wani bowl na fruits da shawarma sai zuba kamshi take. A kunyace ta ajiye kayan kan tebir saboda irin kallon da Zain ke jefanta da shi. Kusa da gadon ta samu guri ta zauna tana murmushi tace "Barka da rana Ya Zain. Ga fruits na kawo maka nasan kayi aiki ka gaji" Wani irin killer look ya bata yana murmushin gefen baki ya ajiye laptop din dake cinyarsa. Murya so sexy yace "Thank you my dearest, yaushe ki ka zo?" D'an far tayi da ido a dan shagwaɓe tace " ba tunda ka dawo ka ki zuwa mu gaisa ba?, to ni na biyoka har gida" "Sorry tunda nazo ban zauna bane. How is Uncle?" Tana wasa da yatsun hannun ta tace "Yana nan lfy. Tare muka zo" Kai ya jinjina ya d'auko abincin yana ci . Sosai suke jefin juna da wani shirtaccen kallo kai kana gani kasan ko wanne da matsayin daya ajiye d'an uwansa. Ayush y'ar k'anin babansa ce. Kaf family na mai tangaran. Wato minister an san yanda Ayush da Zain suka shaku da juna tun suna yara. Saboda wannan dalili yasa iyayen suke yanke had'asu aure. To amma daga Zain har Ayush babu wanda yasan da wannan batun. Dukkanin su ,su biyun babu wanda ya furtawa d'an uwansa kalman so. B'angaren Kainat tana ganin sak'on ta daka wani tsalle da ihu. A gaggauce ta tura masa account number nata da kuma ranan da zata kawo masa Jaleelan har inda yake. Kaman yanda Kainat d'in ta shirya Plan nata. Yau rana ta juma'a da safe misalin k'arfe takwas ta fito cikin shiri. Falo ta sami Jaleela da Anees na karyawa. Anees shirye cikin kaya na makaranta. Kaman yanda Jaleela ta koyar da ita yarinya da ladabi ta gaisar da Kainat. Murmushi Kainat tayi ta shafa kanta tana tambayar yanda ta tashi. Zama itama tayi suka karya tare suna gamawa suka fito gaba d'aya don kaita makaranta. Bayan sun sauketa Kainat ta juyo ta kalli Jaleela data maida hankali kan tuki tace "Yau fa ina da wani babban event." "Na me?" Jaleela tace ba tare data juyo ba. Kainat ta cigaba da cewa "Ina wata kwata Cele?. Yau birthday nata za'ayi party a nan club da muke zuwa. Don Allah badan niba ki daure kizo kinga musamman ta gayyace ki" Shiru Jaleela tayi tana tunani. Itama dai tana san ta d'an fita tasha iska. Kwana biyu babu inda ta leke. Ko wayarta kashewa tayi don bata san damuwa. Saida ta d'an tura harshen ta wajen kuncinta kaman wanda ke hura iska tace "Zanje" Ihu Kainat tayi harda d'an rungume ta ta gefe. Tace "Kai amma na gode. Ga Vip card naki idan kinzo kai tsaye zaki shiga " D'an k'aramin card ta mik'awa Jaleela . Karb'a kawai tayi ta ajiye bata duba ba. Ran Kainat fari tas ta ajiye ta hanya inda zata had'u da wani sugar Daddy nata. Itama Jaleela wani had'edd'en restaurant tayi ta kebe guri d'aya tana cigaba da tunanin rayuwarta da iyayen ta. Misalin k'arfe goma na dare ta gama shiryawa cikin wata arniyar doguwar riga mai hannu d'aya. Rigar kaman net take tabi dukkanin wani sassan jikinta ta ta kwanta. Gashin kanta ta sake shi ya zubo gadon bayanta. Dogon takarmi ne a k'afarta mai igiya. Kan rigar ta d'ura wata y'ar jacket mai hula dake da gashi. Sosai tayi bala'in kyau ta fito sak baturiya. D'an k'aramin bak'in daya sa janbaki ta motsa tana k'ara kallon kanta cikin mudubi. Kai ta jinjina kanta ta matsa gadon da Anees ke kwance ta k'ara tofeta da Addu'a kafin ta fito daga d'akin. Zaune falon ta sami LAMI dake kula da Anees idan bata nan. Dattijowar mata ce . Mata tana da kulawa sosai ga tsabta. Bacin haka akwaita da ibada. Murmushi Jaleela tayi ta ciro y'ar k'aramar waya ta mik'a mata kaman yacce take duk ranan da zata fita. "Gashi Mama. Idan kuna buk'atar abu sai ki gaggauta yimin waya koda Anees zata farka" Kai Lami ta d'aga ta karb'i wayar cikin girmawawa. Sallama Jaleela tayi mata ta wuce Lami ta bita da kallo ciki da mamaki da Allah wadai irin wannan rayuwa. Tana mamakin rayuwar da Jaleela ke yi. A haka kana kallonta kallon salihar mace zakayi mata. Don tana da hankali ga nutsuwa da tausayi, bayan haka kuma ga tsananin ibada. Dazu tana jin yanda take rera karatun Qur'ani kaman wata Sudais. Amma yanzu ji irin shirgar da tayi ta fice da wannan tsohon daren. Ita kuwa wane iftila'i ne ya sameta haka harta jefa kanta cikin wannan halaka? Kai ta girgiza ta miƙe ta shige d'aki da Anees ke kwance. Saida ta k'ara gyara mata kwanciya tayi shimfiɗa nan kasan kafet ta kwanta cike da tausayin yarinya da irin rayuwar da uwarta take. Don ma taga Jaleelan na sauke dukkanin wani nauyi da Allah ya d'ura mata na uwa .itace uwa itace kuma uban. Tana kuma yin bak'in k'ok'arin ta wajen ganin ta ginata bisa tarbiya mai kyau. Har yau bata tab'a kawowa ranta cewa Anees bata hanyar sunna aka same ta ba. Sha d'aya daidai tayi fakin motar ta harabar club din. Tun daga wajen sa mutane keta kai da kawo kace safiya ce. Club din yau a cike yake tam da manyan yara,maza da mata. Kota ina fitilune kaman rana. Guri ta samu wajen su dank'ara-dankaran motoci da ganin irin su a nan sai a kashashen waje. Haka nan kawai taji k'irjinta ya d'an buga tana k'arewa motocin kallo. Juyawa tayi yaga yanda da yawa duk ji da kuɗin su motocin suke kallo suna musu hoto, babu wanda ya iya matsawa jikin su saboda wasu shegun Bodyguards dake jikin motocin da suit a jikinsu fuskar su rufe da mask ,baka gani komai sai idanuwansu. Harta hannunsa bakaken safe ne. Kana ganinsu kasan ba hausawa bane don yanda suke a murde. Idanuwan su kad'ai ya isa ya saka fitsari a wando saboda yanda suke jefan mutane da wani deadly glare. Kana gani kasan wannan Bodyguards abun tsoro ne. Ji tayi kaman ta juya,amma ita tana daga cikin mutanen nan da suka d'auki alkwari da muhammaci. Numfashi ta fesar a hankali ta buɗe murfin motar ta fito. Ai kuwa ido ya yi caa a kanta bata bari kallon ya dameta ba ta taka a hankali ta shige club d'in. Saida ta fara zuwa gurin Bartender ta nuna masa katin. Da d'an mamaki ya nuna mata hanyar da zatabi ta wuce mutane dake kallonta. Wasu na rawa ,wasu na zaune suna shaye-shaye. Y'ar corridor tabi mai dan tsayi sai gata ta bullo wata k'ofa da samanta aka rubuta VIP LOUNGE. Babu tunanin komai ta kama k'ofar ta kutsai ciki. Abu na farko daya fara dukan fuskata shine wani irin kamshi da tsananin sanyi daya ratsa ta. D'akine hadadden gaske da aka kwata da kayan more rayuwa. Kana ganin d'akin kasan ba kowa ke iya book nashi ba sai d'an wane da wane shima sai ya kai ya wuce. Da d'an mamaki take bin d'akin da kallo sam bata kula da wasu tsumammun deep black eyes kaman midnight da suka kafeta ba. Baki ta d'an buɗe da mamakin ina mutanen kuma nan babu kowa. Sannu a hankali ta fara yin k'asa da idonta har suka sauka kan wannan black eyes d'in daya d'aga gira cikin matuƙar confusion yana kallon ta. Dukkanin wani noti dake kanta kuncewa ya yi numfashi ta ya tsaya cak lokacin da idanuwan su suka sarke da juna. Idonta ya yi wani irin buɗewa so wide da sai ka tsorota. Kace mutuwa ta gani.Shima nashi b'angaren matsanancin mamaki ya rufesa yana kallonta. Da wani irin mugun slow gefen bak'in sa ya yi wani irin coiling da wani irin creepiest way ya saki Smirk. Cikakkayar girar sa ya d'aga guda d'aya murya so ,so deep and husky yace "You" ...... 😁finally ooo. Kina so a tallata miki Hajar ki @ affordable price?. Chat me up 👇 08140754777 𝗚𝗨𝗗𝗨 𝗡𝗔 𝒜𝓀ℯ . 𝓐𝓼𝓱𝓪𝓷𝓽𝔂 𝓵♡︎𝓿𝓮 21/25. Yanda ya kira ke d'in sai tsigar jikin ka ta tashi kaji kaman ka buga kai jikin baango tsaban creepiness. Jaleela bata san sanda ta juya da wani bala'in gudu ba har tana yarda wayarta da jakarta dake hannun ta. A guje ta fice wani irin kuka ya kwace mata. Yanda ta fito kaman mahaukaciya ya bawa mutane mamaki suka bita da kallo. A guje ta fice daga club d'in ko takan motar ta bata bi ba. Haka tayi ta shek'a gudu kan titi tana kuka kaman hauka sabon kamu. Duk wanda ya tsaya don taimakon ta idan yaga yanda duk ta firgice sai ya tsorata ya kasa mata magana. A guje zasuja motar su. Da yawa ma suna tunanin ko gamo sukayi. Gabas kawai ta saka a gaba bata tsaya ba saida ta ganta k'ofar gida. B'angaren wannan mysterious mutum wani irin miƙewa ya yi majestically ya tako inda ta tsaya. A hankali ya sunkuya ya d'auki jakarta data yasar yana juyata cikin tafin hannun sa dake sanye da safa. Sunkuyun da ya yi lallausan gashin kansa ya zubo ya rufe masa ido. Mugun smirk ya saki murya so husky yace "So..... finally after all those year, we meet?. Who could have thought The world is too small" ya k'arasa yana wani irin chuckling. K'ofar banɗakin da aka buɗe yasa ya d'aga ido a kasalance ya watsawa Zain daya fito yana goge hannu da d'an k'aramin tawol. Gira ya d'aga yana kallon Zain ta gefen ido. "What?" Zain yace yana k'ok'arin zama. Wani irin chuckling ya yi ya miƙe rike da pose d'in ya dawo ya zauna kusa da Zain yana kallon sa. "Your Babe. She just left" "What?" Zain yace yana zare ido ya yi saurin warce jakar daga hannun sa. A hanzarce ya fice daga d'akin ya bishi da manyan black eyes nashi yana mugun murmushi. Da saurin Zain ya fito har harabar gurin amma ko kurar ta bai gani ba. Baki ya cije rai a b'ace ya koma lounge nasu. Yanda ya barshi haka ya same shi zaune lazy kan kujera ya d'ura hannuwansa kan kujerar ya kafe k'ofar da sexy eyes nashi. Mugun kallo Zaid ya watsa masa "Me kayi mata?" Y'ar gira ya d'aga kafin ya saki y'ar deep dariya da dimples nashi suka lotsa. Oooh wannan mutum is a very sight to see. Baza kasan sanda ka ke dilalar yawu ba idon kana kallonsa. Da deep voice nashi yace da hausar da bata fita sosai "Ni kuma? Ask her mana. Me yasa daga ganina ta tsorota ta gudu, kaman wacce taga wani mugun abu? " Smirk d'in daya saki zaka san akwai meaning bayan maganan da ya yi. Numfashi kawai Zain ya sauke. Duk lokacin daya d'auka yana jiran wannan rana in the blink of an eye komai ya wargaje. Zama ya yi gefen sa yana kallon yanda ya koma ya kwanta ido a lumshe, har zuwa lokacin da murmushi kan fuskar sa. Tunanin abunda ya kawo shi Nigeria ma yau d'in nan yake. 2 DAYS BACK . kwana biyu da suka wuce. ABU DHABI. Kaman yanda Malika tasa ayi shela, hakan ne ta kasance. Cikin d'an k'ank'anin lokaci labarin auren LK da Aafiya ya baza Abu Dhabi. Da yawa suna cikin jimami da tunanin yanda makomar Aafiya ita ma zata koma. Kaman sauran matan da Lk ke aura, itama Aafiya gagarumin biki Malika ta fara shiryawa. Dukkanin wasu dangi na b'angaren Aafiya da Lk sun hallara cikin wannan katuwar masarauta. An fara shagali bikin irin nasu na larabawa ta ko wanne fanni. To amma shi wanda ake abun domin sa yana can MALIBU baisan abunda aka be. Sai bayan an d'aura aure Malika ta tura kannan sa da suke twins. Aizak da Aryan suka je suka tisoshi a gaba. Bai san da zancen bikin ba sai da daddare ya kebe cikin d'akin sa. Had'addiyar black suit dake jikinsa yake cirewa a hankali cike da kasala. Wani irin ingarman namiji ne majiyi karfi. Koya ya motsa jiki sai kaga damtsen nan sun motsa. Dogon gashin sa dake tufke a tsakiya kansa ya kai dogayen yatsun sa ya cire band d'in. Kaman ruwa gashin ya biyo ya kwanta wuyansa luf mai tsananin laushi da tsantsi gashi bak'i sid'ik. K'ofar d'akin sa da yaji an buɗe alamun an shigo baisa ya juyo ba saida ya kama farar rigar dake cikin suit d'in ya fara cirewa. Jin shirun ya yi yawa ya wani irin juyowa a hankali yana balle ragowar botirin rigar da ya yi saura. Numfashin Aafiya ya wani irin tsarkewa lokacin da kwayar idonta ta fad'a cikin midnight Black nashi. Kut ta had'iye yawu. Hak'ika waya da labarai basa masa adalci sam. Don yanda ta gansa haka a zahiri , Sam ba'a kwatanta irin matsanancin kyau da Allah ya bashi. Mutum kaman shi ya yi kansa. Jan wani irin numfashi tayi sanda kwayar idonta ta sauka fatar cikinsa dake uban shining ga wasu uban 8packs kace zanasu a kayi. Kut ta k'ara had'iye wani yawun. Sannu a hankali ta ke yawo da idonta dukkanin wasu sassan jikinsa kafin idonta ya sauke kan kyakkyawar fuskar dake d'auke da wani irin full lips pink masu matuƙar shek'i. Hancin nan kaman biro tsaban tsayi ya tafi da manyan idanuwan da ko ita Albarka. Tsananin bak'in kwayar idan nasa da girman idon nasa idan yana kallon ka sai kaji kaman mai kallon ruhin ka. "Min ant?" Taji kakkausar murya sa kaman saukar aradu. D'an firgita tayi saboda yanda tayi nisa wajen bege. Saida ta lashe leb'en ta daya bushe kamas ta buɗe baki zatayi magana , kaifin idonsa da yanda ya kafeta da manyan idanuwan sa, fuskar nan babu wani emotion yasa taji fitsari na neman kwace mata. Had'iya ta k'arayi ta k'ara buɗe baki amma ko kalma d'aya ta kasa fitowa. Gaba d'aya a firgice take da tsananin kyawun sa da kuma kwarjinin sa . Dif,dif ya nufota kaman wani bijimi. Aafiya batasan sanda ta juya da wani bala'in gudu ba tayi waje. Turus ya tsaya inda ta bari ya kafe k'ofar da ido. Wacece ne kuma wannan harta samu ikon shigo masa d'aki haka kai tsaye. Duk cikin masarautar nan ansan yanda baya son mata suna masa aiki. Why Malika zata turo masa ita don yasan bazata wuce wata Baiwar ba. To amma anya Baiwa ce? Yanda ta chaba ado haka. In har bai manta ba harda gwala-gwalai ya gani a wuyanta da hannun ta. Wacece ne wannan?. Kafin ya sake wani yunƙuri an sake buɗe had'addiyar k'ofar tasa an shigo kai tsaye. Wacce ta shigo yasa ya d'an saki ajiyar zuciya yana binta da kallo. Sanye take da alkyabba da aka Chab'awa ado da zinare. Alkyabba mai hula ce data rufe fuskatar ta ruf kaman rariya. Sannu a hankali ta maida k'ofar ta rufe saboda bayinta dake bakin k'ofar. A hankali ta juyo ta tako har inda Lk ke tsaye. Hannu ta kai ta yaye hular alkyabba data rufe mata fuska. "RAINHA" (ma'ana Sarauniya da harshen PORTUGAL). Kyakkyawan murmushi tayi masa ta d'ago hannun ta daya sha ado da gwalgwalai ta shafa fuskar sa. Tsananin kyawun ta saiya firgita duk wanda ya ganta. Saboda haka ne take rufa fuska. MATILDA baturiyar k'asar Portugal ce. Sanadin had'uwar ta da Sarki KHALELULLAH ta musulunta har sukayi aure shekara takwas da suka wuce. Matilda ta girmi MALIKA nesa ba kusa ba don tayi shekara 50, amma zakayi mamaki idan ka ganta baza kace tayi shekara 25 da biyar ba. Kullum yarinya take k'ara zama ga wani irin shirtaccen kyau da take dashi mai firgita maza da sasu zama bayinta. Tunda ta shigo masarautar ABU DHABI ta shiga jikin LK sosai ta zame masa tamkar uwa. Kusan a yanzu yafi amfani da maganan ta akan ta Malika. Sosai sun samu sabani Saboda hakan, amma duk yacce Malika tayi LK baya tab'a daina bin umarnin Matilda. Da yaranta na Uwa wato Portugal tayi masa magana don sosai ta koya masa yaren. "Quem é aquela garota que acabou de sair do seu quarto?" "Wacece naga ta fito daga d'akin ka yanzu?" Kafin ya bata amsa suka tsinkayi muryar Malika data shigo ita da Aafiya basu kula ba. "Matar sace" Da azama suka juya suna kallon Malika dake takowa cikin izza da Mulki Aafiya b'oyenta. A tare suka maimaita. "Mata?" "Wife?" Ran Matilda sosai ya b'aci. Wato Malika saboda taga bata nan taje garin su can Portugal wajen iyayen ta shine tayi masa aure bata sani ba?. Wato Malika bata tsoron abubuwan da suke faruwa duk lokacin da LAMEEN ya yi aure. Ido cikin ido suke kallon juna ita da Malika kafin ta maida idonta kan Aafiya. Wani irin kallo ta watsawa Aafiya da Allah kaɗai yasan abunda ke cikin ranta. Rai a b'ace ta rab'a ta gefensu ta fice daga d'akin. Lameen ji ya yi kaman ya rushe da kuka yana kallon mahaifiyar tashi dake kallonsa babu alamun wasa tattare da ita. "Samu guri ki zauna Aafiya " Babu musu ta zauna kan wata had'addiyar kujera . Hannun sa Malika ta kama ta zaunar dashi kusa da Aafiyan. Baki ya taune ya k'ara matse rigarsa da bai gama cirewa ba. Zama tayi kujerar dake fuskantar su tace "Ga Aafiya matar ka dana aura maka ita yau da safe. Dukkanin wani tunani dake ranka ka ajiye sa gefe don bata amince da auren ba saida tasan kome ke faruwa. Du da haka tace tana son ka a haka zata zauna dakai. InshaAllahu zamu cigaba da Addu'a har Allah ya kawo mana sauki. Yanzu lokaci ya yi daya kamata ace ka ajiye iyali. Girma ka ke Lameen ba yaro ka ke komawa ba. Lokaci ya yi daya kamata ka hau kan kujerar mahaifin ka duk rashin sonta da ka ke" Miƙewa tayi tsaye tana kallonsa ya sunkuyar da kai ya kasa cewa komai tsabar bak'in ciki. Wai sai yaushe Malika zata gane shifa mata ya tsanesu ne in general, saboda wata yarinya data tab'a shiga rayuwar sa wani lokuta da suka shud'e.Numfasawa tayi ta k'ara cewa "InshaAllahu auren ka da Aafiya babu komai sai alkhairi. Zansa yanzu a kawo muku abinci. Ina mai umarta ku, ku fara yin sallah don neman tsari daga dukkanin wani sharri na b'oye dana fili. Naga kaman wanka zakayi Aafiya ki had'a masa ruwa ya yi wanka. Allahumma barikum" Kai Aafiya ta d'aga cikin girmawawa duk irin matuƙar tsoron dake cinta. Kallonsa Malika ta k'arayi ganin har zusa lokacin kansa na k'asa ya kafe kafet da ido. Girgiza kai tayi ta juya ta fice rai a dagule. Shiru ne ya ratsa d'akin bayan ficewar Malika. Aafiya ta cigaba da kallon sa a kaikaice ta k'asan ido tana k'ara kistima matsanancin kyau da yake dashi. Gefe tana shak'ar daddadan kamshi da jikinsa yake na vanilla and flowers. Tsaban yanda kamshin ya game jikinsa ,ya yi wanka ko baiyi ba, yasa turare ko aa. Koda yaushe kamshi yake mai sassanyan dad'i. Sama da minti d'aya suka d'auka haka babu wanda ya yi motsi sai bugun k'irjin ta dake k'ara tsannanta. Can ya miƙe bai kalli inda Aafiya take ba ya nufi wata arniyar glass door. Ko ba'a fad'a mata ba tasan hanyar banɗaki ne. A hanzarce ta miƙe ta bishi cikin banɗakin daya shige. Sarkewa numfashin ta ya yi ganin tamgamemen banɗakin data shiga dake d'auke da wani irin jacuzzi kaman swimming pool. Bata tsaya tunanin Lameen ba daya juyo yana kallonta da b'acin rai ya taune leben sa na k'asa. A hanzarce ta had'a masa ruwan wanka ta fice da sauri don ji take kaifin idonsa na neman shek'ata barzahu. Da ido ya bita harta fice kafin yaja wani dogon tsaki kaman mace ya hau cire ragowar kayan dake jikinsa. B'angaren Aafiya d'akin ta dawo tana binsa da kallo. Tabbas duk kuɗin iyayenta. Duk fice fice da take kasashen duniya buɗe ido, wani abun ma b'ata taba ganinsa ba sai a nan. D'akin Lameen yaci sunan sa Aljanna duniya. K'ofa aka kwankwasa ta matsa da sauri ta buɗe. Wata baiwa ce ta shigo da wasu a bayanta riƙe da kayan abinci. Da girmawawa suka jera kayan suka fice. Guri ta samu ta zauna tana jiran fitowar sa. Sama da minti ashirin ya d'auka cikin banɗakin duk ta kotsa. Finally taji motsin tab'a k'ofar sa. A hanzarce ta daga kai ta kafe k'ofar da ido. Sai gashi ya sanyo kai in all his glory sanye da tawol dake d'aure k'ugunsa. Sai d'an k'arami dake rataye a wuyansa yana goge jik'akk'en gashinsa dashi. Wani irin had'iyar yawu tayi tana binsa da kallo tun daga k'afafuwansa harzuwa k'irjin sa. Tsabar yanda ta shagala da kallonsa bata lura da yanda ya ke mata wani irin kallo ba. Saida ta d'aga idonta zuwa fuskar sa. Lokaci guda ta saki wani irin mummunan ihu da saida gaba d'aya masarautar ta d'auka. Kafin Lameen ya yi wani yunƙuri ta zube k'asa a sume. Numfashi ya fesar mai zafi cikin ransa yace. 'Here we go' A hanzarce ya yi k'ok'arin numfar inda take yashe a k'asa, amma kaman wanda aka kafe ya kasa motsi. Lokaci guda kuma ya kai hannu ya rik'e wuyansa da yake ji kaman an shake shi. Kakari ya fara yana wani irin tari daidai yaji muryar Malika na magana da bada umarni a b'alla k'ofar. Dazun ma daya sa suka shigo saboda yabar muk'ullin a jiki ne. Bayan an kawo abincin Aafiya ta ciresa ta dawo dashi ciki. Luu shima nashi idon suka fara rufewa numfashi ya masa wahalar fita. A take fuskar nan tayi jazur da ita na tsaban wahala . Har zuwa lokacin kokawa yake da koma menene yake tunanin ya shakeshi ta baya. To amma baiji komai a wuyan nasa ba sai hannun sa kawai. Gaba d'aya ya yi k'asa shima daidai Malika ta dannu kai d'akin. Ihu tasa da kiran sunansa tayo kansa a guje kafin ta k'araso tuni ya zube gurin a sume. A tare Malika da Matilda suka k'araso inda ya zube a sume. Da k'araji Matilda ta bada umarni a kira family doctor nasu. Aizak da Aryan suka fad'o d'akin suma a guje don tuni labari ya riske so. Saidai Matilda ta k'anannade shi kan cinyarta ta hana kowa ya tab'a shi sai Dr ya shigo. Tsaban taikaci Malika ta zuba mata ido ta kasa cewa komai. Rai a b'ace tasa aka d'auko Aafiya akayi waje da ita. Sosai gabanta yake mugun fad'uwa duk yanda take k'ok'arin danne wasu zafafan hawaye da suka cika mata ido saida suka zubo. Kan gadonta tasa aka kwantar da Aafiya da bata ko motsi. Duk a tunanin su itama ta mutu kaman sauran matan. Amma na Aafiya yafi ko wanne sauri don su alamu sun suna sai ya fara kusantar su hakan ke faruwa dasu. Yanda taga Aafiya da kayanta batayi tunanin wani abu ya shiga tsakaninsu ba tukun. Tanajin Aryan ya rungume ta ta baya. Hawaye ne kebin fuskarsa shima. Aizak yana can tare da Lameen da Matilda ta kafa ta tsare a kansa. Likitane ya shigo a guje ya yi kan Aafiya. Kallo d'aya ya yi mata ya yaga yanda take numfashi kad'an sai ka zuba ido sosai zaka kula. Numfashi ya sauke a hankali yace da Malika tana da rai. A gaggauce ya bata taimakon gaggawa. Malika ta sauke numfashi mai k'arfi tana kiran sunanyen Allah. Wai wannan wane irin abu ne?. 𝗚𝗨𝗗𝗨 𝗡𝗔 𝒜𝓀ℯ. 𝓐𝓼𝓱𝓪𝓷𝓽𝔂 𝓵♡︎𝓿𝓮 26/30. Saida Lameen ya kwana biyu a sume sannan ya farfaɗo. Matilda ta kafa ta tsare ko nan da can bata matsawa. Malika ta kasa jurewa tayi mata tas ganin yanda k'arfi da yaji take neman rabata da d'an ta. Sosai sukayi fad'a Matilda tayi fushi wunin ranan ko hanyar Lameen batayi ba. A daren ranan ya farfaɗo twins dake d'akin a guje suka rungume shi. Da ido yake binsu yana son tambayar su ko Aafiya ta mutu. Aizak daya fuskanci abunda ke cikin ransa yace. "Ya akhie. Ka kwantar da hankalin ka wannan karon koma menene ke bibiyar rayuwar mu bai samu nasarar kashe matar ka ba" Numfashi ya sauke a hankali ya koma ya kwanta. Aryan dake waya ya mik'o masa da sauri yana cewa 'gashi' da ido yabi wayar kafin ga k'arata a kunne. Wani irin numfashi ya ratso wayar mai k'arfi murya Zain ta ratsa dodon kunnensa cike da damuwa yace "Alhamdulillahi ka farfaɗo?" Lameen bai bashi amsa ba yace "I'm coming " "Dude ina Nigeria. " "I know gani nan zuwa" Baijira Lameen d'in ya k'ara cewa komai ya kashe wayar. Yana buk'atar guri da zaiyi breathing air. Away from all this. Malika ta fad'a d'akin cikin sauri. Kai tsaye ta rungume shi tana masa ya jiki. Rabonda ya kebe da mahaifiyar sa haka shi kanshi ya manta. Don haka ya yi luff a k'irjin ta. Ita ta sahi a gaba yaci abinci ya yi sallah. Da kanta ta had'a masa ruwa ya yi wanka ya fito. Saida ya gama shiryawa a taushe yace mata zai tafi Nigeria don ya samu salama a zuci. Bata musa ba ta amince masa tana son ta kwato d'anta daga hannun Matilda dake nemanyi mata k'ak'anakayi. Aafiya dai har zuwa lokacin bata farfaɗo ba saidai numfashinta ya daidaita. Idan ka ganta kaman wacce ke bacci. To sanda ya diro Nigeria baiyi tunanin Fate zai k'ara had'ashi da macen da yake nema ba ruwa a jallo saboda wani unfinished business dake tsakanin su. Present . Numfashi Zain ya sauke yana cigaba da kallo Lameen da harzuwa lokacin idonsa ke a lumshe. Tabbas Lameen na tare da sirri mai ban aljabi. Ga dai kyau iya kyau Allah ya bashi, amma yana neman tashi a banza. Duk sanda ya yi arba da wata mace sai wani mummunan abu ya faru. A yanzu ma yasan babu tantama Jaleela taga wani abu tattare dashi da ya yi sanadin firgitar ta harta fice haka a guje. Wayarta k'irar iphone x ya juya a hannun sa da tunanin hanyar da zaiyi ya buɗe ta. "Let me help you with that " D'agowa ya yi ya kalli Lameen daya mik'o masa hannu. Kai ya d'an jinjina ya mik'a masa wayar. Wato Lameen ba despite duk wannan abun da yake faruwa dashi, he's a damn genius and hacker. Ya iya hacking na ko wane abu sai dai in baiga dama ba. Wayar ya juya a hannun sa ya yi d'an murmushi. Dan danne danne ya yi saiga wayar ta buɗe. First abunda ya fara cin karo dashi jikin screen d'in wayar shine hoton ta da Anees. Suna sanye da k'ananan kaya kansu babu d'an kwali daga ita har Anees gashin su a sake ya bazo ta ko ina ga iska da take kad'ashi. Hoton da sukayi ne wani amusement Park data kai Anees. Ta d'agata suna dariya akayi hoton. Sunyi bala'in kyau kaman wacce suka zo daga wata duniyar. Ido ya zubawa hoton yana jin wani irin abu na ratsa shi yana kallon Anees. 'She has a daughter?' (Tana da y'a?) Ya furta a fili ya d'ago yana kallon Zain daya zuba masa ido. Cikin rashin fahimta yace "What. Wacece take da y'a?" Fuskar wayar Lameen ya nuna masa yana tunanin . Idan har tana da y'a? Ta tab'a aure kenan? Ko kuma a hanyar prostitution(karuwancin) ta sameta?. Haka nan kawai yaji wani abu ya chake shi a zuciya ya yi saurin kawar dashi yana d'an girgiza kai. Why do i care?. Tunda Allah ya sake had'amu, zanyi making sure life nata is a nightmare har sai ta durkusa ta bani hak'uri. Smirk ya saki daya sa Zain shan jinin jikinsa yace "Me ka ke tunanine?" "Nothing " Bai bari Zain ya k'ara cewa komai ba ya miƙe ya fice daga d'akin rike da wayar a hannun sa. Yana fitowa kuwa guards nashi suka kawaye shi. Duk inda ya wuce ya zama abun kallo. Mata duk sun mutu a kansa maza kuma suna burin ina ma dai sune. Suna kallo ya shige shegun motocin sa dake fake a gurin. K'aramar motar Pecanto dake kusa da tashi ya zubawa tsumammun idanuwan sa. Motar waye wannan har ta iya fakin kusa da motocin sa?. Hmm. "Find who's car is this" (ka nemo motar waye wannan) Yace da right hand Bodyguards nashi. Da girmawawa yace " yes, Boss) Har suka fice daga club d'in yana juya wayar Jaleela tafin hannun sa. Despite all the burika dayaci yanda zaiyi making life nata he'll, bazai ignore na kyau da sukayi ba ita da Anees. Yana son ya yi finding out y'ar waye wannan. Yarinya is so beautiful to be true. Tsintar kansa ya yi da shiga gallery nata ya cigaba da kallon hototun nan su ko Allah zaisa yaga wani clue da zai nuna uban Anees. But baiga komai sai hoton Jaleela kawai da Anees. Baya son zarginsa ya zama gaskiya. In dai kuwa har Anees bata da uba, oh life na Jaleela is about to get much worse. Wani irin zafi zuciyar sa yaji tanayi hakanan kawai. Abubuwa da suka shude shekarun baya suna masa yawo cikin ido. A fili yace "She's a liar. Duk son Allah nata da Manzon sa. Har take iya kiran wasu da sunan y'an iska. At the end ita ce y'ar iskar ashe?. What a snake" " you will pay for what you did. Just wait am coming for you miss Aleeyna " Smirk daya saki sai ya matuk'ar bawa mutum tsoro. Bodyguards nashi mai suna James dake zaune gefen zaman mutum banza ya had'iye yawu kutt yana shivering. Haka ya yi ta bincike a wayar . Duk wasu mutune da take hulda dasu ya d'auke su cikin d'an k'ank'anin lokaci. To Jaleela da rawar jiki ta shige gida bayan Lami ta buɗe k'ofar. Mamaki ya cika Lami ganin yanda ta shigo a firgice babu takalmi bare d'an kwali. Hankali a tashe ta fara karanta Auzubillahi da dukkanin wasu ayoyi da suka zo bakinta. A tunanin ta ko Jaleelan tayi gamo ne. Yaraf Jaleela ta zube k'ofar d'akin ta. Had'a kai tayi da gwiwa tana wane irin kuka mai ban tausayi. Sai a lokacin Lami ta sauke ajiyar zuciya saboda wani irin tsoro daya rufeta. D'an nesa da ita kad'an ta tsaya a tsorace tace "Hajiya lfy? Wani abu ya faru ne?" Jaleela ta kasa cewa komai sai kuka kawai da take. Jikin Lami ya yi sanyi sosai a hankali ta matso ta durkusa kusa da ita. Rungume ta tayi tana d'an buga bayanta. Da ace tabbas Jaleela na tare da uwarta tasan cewa tabbas abunda take buƙata kenan. Aikuwa ta shige jikinta ta cigaba da kuka sosai tana kiran Ammi kaman wata k'aramar yarinya. Jikin Lami ya k'ara sanyi sosai. Menene ya yi sanadin daya sa Jaleela ta bar gida?. Sun d'auki sama da minti goma a haka kafin Jaleela ta janye ta yunƙura ta miƙe tsaye ta shige d'aki. Kai tsaye gadon da Anees ke kwance tayi ta jata ta matse a k'irjinta kaman wani zai kwace ta. Sosai take fad'a da zuciyar ta. Wani sashen nace mata ta gaggauta barin garin Abuja tun baiyi tracking d'in ta ba, wani sashen na cewa. And so what kuma. Ya kamata mu daina zama so weak. This is our chance to fight. Yanzu ya dace mu sashi regret na kangi rayuwa daya jefamu. Mu daina nuna masa weakness namu. Saboda shi muke ta guje-guje. Enough is enough. Allah shi kad'ai yasan ikon sa daya k'ara had'amu bayan mun fidda ran sake ganin sa. Yanzu ya dace shima ya d'and'ana d'acin daya saka mana a baki. Ya yi kuka kaman yanda mukayi shekaru d'ai-d'ai har bakwai. We have to show him we are strong and ready to fight, just like before. Numfashi ta sauke da wannan tunanin ta yanke hukunci. Zatasan duk yanda zatayi bazai gano Anees ba. Tana tsoron ya kwace ta. Anees ita kad'ai ce duniyar ta a yanzu. Tana kuma rayuwa ne saboda ita kad'ai. Duk da begen ta nason komawa gida wajen iyayenta, bazata iya ba. Tana kunya ta koma musu bayan shekaru da yawa. Addu'arta a kullum Allah yasa su yafe mata ko inta mutu ta samu saukin cikin kabari. Tunda Lameen ya fice ya yi zurfi cikin tunani. Wai wacece ne wannan yarinya ne?. Me yasa duk wanda ya had'u da ita baya iya rabuwa da ita ne?. Yasan waye Lameen and what hid capable of doing. Sosai yaga interest na yarinya cikin kwayar idonsa. But shima yana da interest a kanta and he's going to have her. Hoton ta daya gani yanzu ya k'ara jefashi cikin wani yanayi. Yarinya is so beautiful. To amma wannan y'ar way'e?.Numfashi ya fesar mai zafi ya ciro wayar sa ya dannawa Kainat kira. Tsawon kwana biyu Jaleela tayi mak'ale a gida. Daga ita sai Anees. Ko k'ofar gida bata lek'o ba. Sam bata damu da motarta ko wayarta data bari ba a club d'in. Ita damuwarta karta sake had'uwa dashi. Yau ya kama Monday k'arfe bakwai suka fito ta gama shirya Anees. Yarinya tayi kyau sosai cikin uniform nata na kamaranta. Yar doguwar riga data tsaya iya kugu sai wata a ciki mai necktie. Kanta hulace da Jaleela ta nannade gashin kanta ta turashi kaman gammo. Bayanta jakarta ts makaranta ce peach mai gashin kaman ta mage. Lunch box nata da jakar kalansu d'aya. Ita kuma Jaleela duguwar rigace a jikinta mai fad'i wacce aka raba daga kugu. An tattare ya matse kaman sket. Rigar darka blue ce da mayafin ta data rataya a wuya. Duda cewa batayi kwalliya ba, tayi kyau sosai. Hannu Anees ta riƙe suka fito tana riƙe da Lunch box d'in. Saida ta tofeta da Addu'a sannan suka fito. Bakin gate suka tsaya saboda layin nasu akwai kwalta. Motoci na wucewa sosai na haya. Wata arniyar BMW M5 2025 ce wajen gudu biyar fake daga can d'aya b'angaren d'an gaban gidan kad'an. Jaleela sam bata kula dasu ba ta tari keke nape daya shigo layin da wasu mata. D'aya daga cikin motar aka buɗe masa ya fito in all his glory sanye cikin bak'ar suit daya dura musu katuwar coat ash colour. Gashin nan yasha gyara sai shining yake. Tsayawa ya yi yana kallonta gefen bakinsa a d'age da smirk. Suna can suna magana da mai nape sam bata lura ba sai da Anees taja hannun ta tana cewa "Mummy kinga wani mutum mai kyau?" K'irjin Jaleela ya wani irin harbawa, da sauri ta kalli inda Anees ke nuna mata. Saida zuciyar ta ta kusa tarwatsewa sanda idonsu ya had'u. Wani irin fisgar Anees tayi ta fad'a cikin motar a guje tana cewa muje malam. Ai tuni mai adaidaita da matan dake ciki cikinsu ya duri ruwa. Irin wannan abun da suke gani a American films na Mafias da suke sace mata suna sana kaisu prostitution ko wani abu makamci haka. Shine suka tunanin yake shirin faruwa a zahiri. Don duk wanda yaga Lameen da irin shirgar sa ga Bodyguards nashi da suka rufe titin dole kayi tunanin wani Mafia boss ne. Malam bahaushe da tsoro. Da yawa motoci sunci birki daga can nesa sun kasa k'arasowa kowa tsoro ya kamshi ganin turawa sun danno musu gari haka. Mai nape bai jira ta k'ara cewa su tafi ba ya tashi mashin a guje zasu hau titi Bodyguards nashi suka rufe titin. Tuni ciki ya d'uri ruwa. Jaleela ta zuba masa ido kaman yanda shima ya kafeta da nashi black eyes d'in. Sosai k'irjint yake bugawa amma fuskarta ta hana nuna wannan tsoron ya nuna. Blank take kallonsa kaman yanda yake mata. Murmushi ya k'arayi da dimples nashi suka lotsa ya fara takowa a hankali cike da izza. Zagayowa ya yi inda take zaune ya d'an sunkuyo abunka da mutum mai tsayi. Anees dake ta kallonsa tana murmushi ya kalla kafin ya maida ido kan Jaleela data k'ara matse Anees kan cinyarta tana rufe mata fuska da hannu. "Hmm. What with the rush?" (Menene na saurin?) Shiru tayi bata bashi amsa ba sai mugun kallo data watsa masa tanaji kaman ta kifa masa mari. Murmushi ya k'arayi ya kalli Anees. "What is your name Beautiful?" A hanzarce Anees tace " Baby Anees" ita kanta ta rasa farin ciki me takeyi haka. Hannu ya mik'a mata da d'an murmushi yace "Come. Zona kai ki makaranta ko Baby?" A guje Anees ta kai hannu zata kama nashi, Jaleela ta wani irin buge hannun saida Anees ta saki kuka. Rai a bace tace "Me nace miki akan kula wanda baki sani ba?" Tana kuka sosai Anees tace " Sorry mummy ". Mugun tsaki Jaleela taja ta kalli mai nape da mugun b'acin rai tace "malam mu tafi " mai nape dai tsoro ya hanashi tafiya ya kalli Lameen daya kafe Jaleela da ido Allah kaɗai yasan abunda ke ransa. Kwayar idonnan ta kara zama wani irin black. "Kinga Hajiya kawai ki sauka" "Eh wlh ki sauka kawai, kar ki shafa mana kashin kaji bamuji bamu gani ba" Matan dake zaune cikin motar suka saka baki. Baki Jaleela ta cije kaman tayi bindiga. Wota yanzu ana cikin wani yanayi da ba'a taimako. Koda yake bayau ne ta fuskanci irin wannan kalubale ba. A fusace ta fito daga motar Lameen ya d'an ja baya yana kallonta da wani irin creepy smile kan fuskarsa. Mai nape tuni yaja mota a guje yabar gurin. Da azama ta juya zata koma gida ganin babu wasu motoci dake k'ok'arin shigowa. Batayi tunanin zai biyota ba saida ta kama k'ofar ta buɗe tana k'ok'arin shiga ta juyo taga mutum tsulum bayanta kaman zai shige jikinta. Wani irin ihu tayi tayi tsalle ta koma gefe taja k'ofar da sauri ta rufe bata shiga ba. Kama Anees tayi ta b'oye bayanta kaman mai shirin rufeshi da duka tace da k'araji. "Uban menene ka ke bina kuma?" "Language. Kinsa yanda na tsani zagi" "Naci uban Language d'in na bishi da gudu. MENENE ka ke bina?" Ta fad'a da k'arfi da kaf compound d'in saida ya d'auka. Ido ya zuba mata cike da nazari sai kuma ya saki y'ar dariya yace "Har yanzu kina nan da wannan feistyness naki. After all shine sanadin komai " Kaman bashi ne ya yi dariya ba lokaci d'aya ya wani irin had'e fuska kaman bai taba dariya ba. Ita kanta Jaleela duk kurinta saida tasha jinin jikinta. Wani k'aramin card ya fito dashi ya mik'a mata. Wulaƙantaccen kallo ta watsawa hannun nasa da katin bata karb'a ba. Gira ya d'aga kafin yace "Take it or you will not like what am going to do next "( ki karb'a baza kiji dad'in abunda zanyi ba idan ki ka k'i) Yanda ya yi magana saida wani tsoro ya ratsa ta . Ka kalli fuskar ta maida ido kan Anees dake kallon su. A guje ta warce katin kaman mai k'arban kashi. Murmushi ya yi ya d'an ja baya kad'an yace "Ki same ni wannan address bai 7pm Sharp. Don't be late" "Who the he'll are you da ke ke tunanin zaka bani unarni nabi" Wani irin kallo ya yi mata taji kaman ta saki fitsari. "Do not come. And see what happens " K'arasa maganan ya yi da kallon Anees. A guje ta k'ara b'oye ta a bayanta. Ya d'ago ya kalleta da murmushi kan fuskar yace "Exactly" Daga haka ya juya ya bar gurin. Da ido Jaleela ta bisa k'irjinta na wani irin suya. Tsana, kiyayer sa sunyi mata katutu a rai har makogaro take ji. Tana kallo ya shiga mota suka bar gurin. Ga mamakin ta sai ga motar ta an shigo da ita an faka. Wani Bodyguards nashi ya fito daga cikin motar bai kalleta ba ya juya ya fice. Tsaban takaici ji tayi kaman ta saki ihu. Numfashi kawai ta fesar mai zafi ta kama hannun Anees suka shiga motar ta kaita makaranta. A mota tayi tayiwa Anees fad'a na kulashi da tayi harda gaya masa sunanta. Ji take kaman ta rufe yarinya da duka tsabar takaici. Data dawo gida kuwa taita ihu tana jifa da kaya kaman mahaukaciya. 'Sai kayi dana sanin kara dawowa rayuwata a karo na biyu. Mu zuba nida kai shege ka fasa. Ahhhhhhh" Ta suri filon kujera tayi jifa dashi. 𝗚𝗨𝗗𝗨𝗡𝗔 𝗔𝗞𝗘 . 𝒜𝐬𝐡𝐚𝐧𝐭𝐲 𝐥♡︎𝐯𝐞. Masu tambayar books nawa akwai. SULTANAAH SAUYIN LAMARI MULKI KAIDIN MACE ZUBAR HAWAYE Da sauran su. Mutanena a dinga share na GUDUNA AKE sauran groups da ku ke pls. I can't do this ni kaɗai kullum sai kayi share from the beginning. Pls a dinga share fisabilillahi 🙏🏻👌🏻 31/35. Shabiyu da rabi daidai ta d'auko Anees daga makaranta. Tunda daga safe har zuwa wannan lokacin ta kasa yanke hukunci kan taje kaman yanda ya bata umarni?, ko ta share shi?. Haka zatayi ma bai isa ya yi mata abunda Allah baiyi ba don haka baza taje ba. Idan ya isa shi wani ne yasa azo a fito da ita k'arfi da yaji. Magriba nayi ta gark'ame gida ta ko ina. Window da kofofi. Tariga da tasan Kainat ganinta yanzu kuma sai sanda Allah ya yi don bata ma nan garin Abuja tana can Emo wajen wani Sugar Daddy nata soja. Duk yanda take nuna jarumta kan fuskarta amma zuciyar ta abun yasha banban sosai. Tana cikin fargaba duk sakan d'aya daya wuce idonta nakan agogo tana irga lokaci. Lokacin da agogon ya nuna k'arfe bakwai daidai saida k'irjinta ya harba. Tsoro sosai ya darsu cikin ranta. Tabbas tasan koma wanene wannan mutum hatsabibi ne na gaske. Saboda lokaci kad'an yasan inda take har yasan kuma motarta data bari a club d'in. To in har yasan hakan tabbas babu abunda bazai iya aikatawa ba. Wai shin shidin waye ne?. Me yasa ne tun farkon had'uwar su babu alkhairi ne a ciki?. Numfashi ta fesar mai zafi ta gyarawa Anees da tayi barci kusa da ita kan kujera kwanciya. Fuskarta ta shafa ta k'ara tofeta da Addu'a. Ajiyar zuciya ta k'ara saukewa ta maida hankali TV da take kallon wani series na Korean, QUEEN OF TEARS. Duk yanda take tsananin son kallon series d'in gaba d'aya batajin dad'in sa. Kallon kawai take amma bata da nutsuwa koya taji motsi zata kalli k'ofa ko window. Gani take kaman zai aiko d'inne a fita da ita k'arfi da yajin. Tanan nan zaune har k'arfe gome babu wani motsi. Sai a lokacin ta sauke wata katuwar ajiyar zuciya ta miƙe ta suri Anees sukayi d'aki. Wanka ta shiga bayan ta kwantar da ita ta fito sanye da rigar wanka data tsaya mata a gwiwa sai d'an k'aramin tawol da take goge gashin kanta dashi. K'aramar riga tasa mara nauyi ta barci. Saida ta feshe jikinta da turaruruka taja hijabi ta shimfiɗa dadduma. Sallan isha tayi da nafila. Ta jima tana Addu'a da neman tsari wajen Allah na wannan mutum kafin taja Qur'ani ta fara tilawa. Daran ranan dai Jaleela haka tayi barci da ido d'aya. Washegari a daddafe ta shirya Anees suka fito zata kaita makaranta. Sosai gabanta ke fad'uwa tunda suka fito. Koda suka shiga mota ma tanayi tana waige waige. Kusan kaff week en Jaleela tayi shi ne cikin fargabar abunda zaije ya dawo. Sannu a hankali kuma komai ya wuce had'uwar su ta k'ara zama kaman labari. Ganin har an d'auki wannan lokacin bata k'araji motsin basa, ta tarkatashi ta ajiye a gefe. Sannu a hankali ta soma dawo da rayuwar ta. Waya ta sake mai kyau k'irar Samsung. Tana buɗeta ta fara kiran Kainat. Saida kunnenta ya yi ciwo saboda ihu da hargagi da Kainat d'in ta dinga yi mata cikin wayar. Bata tsaya sunyi wata doguwar magana ba ta kashe wayar. Kai ta girgiza tana kallon tsirarun mutane dake ta wucewa k'ofar makarantar su Anees. Agogon hannunta ta kalla baifi saura minti biyu su tashi ba. Lokaci na cika kuwa aka buga k'ararrawa. Shiru-shiru Jaleela na jira taga bullowar Anees amma shiru ka ke ji kaman wacce ta aikate garinsu. Tana kallo yara nata fitowa iyayen su na d'aukan har suka k'are sai malamai. A yanzu wani irin zufa ta fara had'awa cikin motar. Jiki na wani irin rawa ta buɗe motar ta fito tayi cikin makarantar. Sama ko k'asa babu Anees bare labarin ta. Jaleela tun tana ganin abun wasa sai gata ta zama kaman mahaukaciya tana neman Anees lungu da tsako na makarantar da kiran sunanta. Sauran malamai da suka rage a makaranta aka bazama ko ta shiga wani gurinne. Ana cikin neman nata saiga malamar su da data fito daga office na principal. A guje Jaleela tayi kanta tana ihu "Ina Anees, ina Anees ina ki ka bari ta tafi ba'a tashi ba?" Da tsananin mamaki Auntyn tace "Yanzu abunda ya fito dani daga office na principal kenan. Yau tsawon sati guda kenan Anees batazo makaranta ba" Idan kaga yanda idan Jaleela ya fito sai ta baka tsoro ta wani irin dafe k'irjin tana cewa "Ban gane abunda ki ke cewa ba? Anees d'ince tayi sati bata zo makaranta ba? Wa nake saukewa kenan nake d'auka idan an tashi?" Tayi maganan kaman zata rufeta da duka. Da sauri malaman dake kusa suka shiga tsakani suna bada hak'uri. Jaleela ta cigaba da bala'i "Wane irin maganan banza. Yarinya da nake kawowa kullum nake d'auka kice tayi sati batazo ba. Ciwon hauka ne ya kama ki ko makamcewa ki ka yi. Ina y'a take? Haushi ya kama Auntyn itama a zafafe tace "malama kinga kar ki cimin mutunci. Saboda me zanyi miki k'arya?. Biyana akayi na kula da y'ar ki na bata ilimi mai kyau. Kulawa na d'aya daga cikin abunda nake bata, badon kulawa da nake ba bazan damu da rashin zuwanta ba bare har na kai office. Saboda haka babu abunda zaisa nayi k'arya. Yau sati guda kenan batazo ba " Dumm k'irjin Jaleela ya buga. Innalilllahi wa Inna'ilaihi raji'un. Hannu ta d'ura aka ta rushe da wani irin kuka da ihu. "Wayyo Allah na shiga uku" Ihuce-ihucen yaja hankali mutane suka shigo makarantar harda shi principal ya fito. Yanda take ihu ana bata hak'uri sai abun ya baka tausayi. Gaba d'aya ta fice daga hayyacin ta. Sosai tayi musu bayani kullum sai ta kawota ta ajiye kuma idan an tashi zatazo ta d'auke ta. Ya akayi babu wanda yake kula da zuwanta da kuma fitarta?. Wannan abu dai akwai d'aure kai. Kaman wacce aka tsikara ta miƙe da bala'in sauri daga kasan da tayi zaman dirban. A guje ta fito daga makarantar. Turus ta tsaya bakin k'ofar kaman wacce aka kafe a guri ta zubawa Motar dankareriyar Motar PRADO dake fake gefen ta ta motar ido. Ba motar ce ta sata tsayawa ba sai wanda yake jingine jikin motar. K'ananan kayane a jikinsa blues Baggy Jean's da wata ashe d'in riga data kwanta jikinna ta kamashi tsam kaman baya iya numfashi. Ya d'ura mata jacket irin ta Biker's d'in nan Leather bak'a. Gashin sa ya tufke tsakiyar kansa yan silli sun zubo gefen fuskar sa dake d'auke da farin glass. Wayyo kyawun da ya yi abun bazai kwantatu ba. Komai na Jaleela tsayawa ya yi chak bata ganin kowa da komai sai shi. Zuba masa manyan Brown eyes nata tayi k'irjinta na wani irin boiling kaman wacce ake zubawa tafasheshshen ruwan zafi. Wani irin karkatar da kai ya yi gefe yana k'are mata kallo tun daga sama har k'asa sai kuma ya saki Smirk. A hankali ya kama murfin motar ya buɗe. Y'an k'afafuwan Anees suka fara fitowa daga cikin motar ya mik'a hannun ya d'auko ta . Numfashi da Jaleela ta sauke kai k'arfi shima saida yaji k'irjinta ya wani irin harbawa kaman an kwad'amata guduma har saida takai hannu ta dafe tana wani irin haki. Wani iri relief ya saukar mata da wasu hawaye masu matuƙar zafi suka biyo kuncinta. Jiki na rawa ta nufeshi ta fisge Anees daga hannun sa da k'arfin gaske. Kafin ta gama sauke ta daga jikinsa ta d'auke shi da wani mahaukacin mari saida fuskarsa ta koma gefe. Haka ya tsaida fuskar tashi yana kallon gefen bai juyo ba. Allah ne kad'ai yasan irin zafi da zuciyarsa take. He was so piss off da kwayar idonsa a take ta rikid'e ta koma jaa. A karo na biyu ta k'ara maimaita thesame mistake. Yanda ya juyo ya watsa mata manyan idonsa da sukayi jazur kaman garwashi saida ta tsorata taja da baya. Amma zuciyarta dake zafi da tafarfasa baisa tayi backingdown ba ta fara zagga masa masifa tana zagin sa da gaya masa dukkanin wani abu daya zo bakinta. Uffan baice ba saida ta gama ruwan bala'i ta k'arasa da cewa "InshaAllahu yanda ka shiga rayuwarta ka hanani samun nutsuwar zuciya da kwanciyar hankali, sai Allah ya jarrabeka da kwatancin uk'ubar rayuwa daka jefani. Duk wani hali dana shiga kaine sanadi kuma bazan tab'a yafe maka ba. Ka fita daga rayuwata dana y'ata " Leb'ensa na k'asa ya wani taunewa yana kallonta da wani irin strange look. Menene take ta babatu haka? Shine ya yi sanadin shigar ta me?. Fuu ta juya ya bita da kallo da jajayen idonsa. Saida ta saka Anees cikin mota ta zagaya zata shiga ta tsinkayi maganan. "You just make thesame mistake da ki ka yi before. So watch out for me" Sosai maganansa ya bata chill har cikin bargon jikinta, bata juyo ba ta fad'a cikin motar da sauri ta fisgeta a guje ta bada masa kura da sauran mutane da suka tsaya kallo. Yanzu wannan mutumin tsoro yake bata. Maganan gaskiya bazata iya cigaba da zama nan ba matsawar yana nan. Mutum kaman aljani. To wai taya yake iya shiga yake d'auke Anees da zarar ta ajiyeta? Kuma yake dawowa da ita ta d'auke ba tare da kowa ya lura ba?. Anya kuwa mutum ne?. Numfashi ta k'ara saukewa ta kalli Anees dake rungume da wata katuwar pink Teddy Bear. Yarinya tayi wani irin shiru kaman mara lafiya da alamun bataso rabuwa da Mutumin ba. Bazaiyiwu ba dole ma ta gaggauta nesanta Anees dashi. Tanaji tana gani bazai kwace mata yaba. To yanzu ina zataje?. GIDA . Zuciyar ta ta bata amsa. Hawaye suka wanke mata fuska ta k'ara maimaita GIDA kan leb'enta hankali . Shikam ya jima a tsaye kafin ya buɗe motar ya zauna a baya. Jingina ya yi kujera ya maida idonsa ya lumshe yana wani irin numfashi a hankali. 'InshaAllahu yanda ka shiga rayuwarta ka hanani samun nutsuwar zuciya da kwanciyar hankali, sai Allah ya jarrabeka da kwatancin uk'ubar rayuwa daka jefani. Duk wani hali dana shiga kaine sanadi kuma bazan tab'a yafe maka ba. Ka fita daga rayuwata dana y'ata ' Maganganun ta suna tayi masa yawo a kunne. What did she mean by that?. Zain dake zaune wajen direba ya juyo sosai yana kallonsa. Yau daga shi sai Zain ne suka zo saboda ya sasu suna investigate na wasu da yake tunanin suna bibiyar Jaleelan da bata sani ba. Target d'in nasu kuma yaga kaman kan Anees ne. Abunda Jaleelan bata sani ba tun ranan dukkanin wani motsin ta a tafin hannunsa yake. Yasan dukkanin wani abu da ita kanta Jaleelan bata sani ba. Wasu mutane ya gani suna binta kullum zata kai Anees makaranta. Idan ta sauke ta zasu faka motar suna tunanin yanda zasu shiga su karbo Anees. Ranan daya tabbatar da zarginsa ya shirya Plan nashi perfectly. Da zarar ta sauke Anees kafin kowa ya ganta yaronsa da yake ciki yana jiranta zai fito masa da ita. So she kansa baisan why yake protect na yarinya daya tsani uwarta ba. But he can't help the feeling da strange connection da yake ji duk sanda yaga Anees ko ya yi kusanci da ita. Ya barwa kansa yana protect nata ne saboda yarince dake so innocent and pure koda kuwa bata hanyar Sunna aka same taba. Jan numfashi ya yi ya kai hannu a hankali ya shafa fegen fuskarsa data mara. 'But hannun ta is so soft ' 'What?, dude no' Murmushi ne ya kufce masa jin yanda yake fad'a da zuciyar sa shi kad'ai. "King ka sani a duhu. What is going on ne ? Dama ka santa ne har ta iya daga hannu ta mareka and you did nothing?" Idonsa dake lumshe ya ware su kan Zain dake kallonsa cikin rashin fahimta. Zubawa juna ido sukayi yana karantarsa sosai yake hango damuwa cikin kwayar Zain d'in. Kaman bazai bashi amsa saida ya maida idonsa ya lumshe sannan yace "She's that girl 7years ago" Sosai zain ya ware ido waje. Itace wannan yarinya data tab'a marinsa shekarun baya da suka wuce tasa ya yi abunda ba halinsa ba. This life is so scary wlh. A hankali ya sauke numfashi yanajin wanj irin nauyi a k'irjinsa. Yanzu daya k'ara ganin Jaleelan a fili he can't deny da sudden attraction da yake a kanta. "Follow her" Bai musa ba ya tada motar ya harbata kan titi. Jaleela na fakin motar ta harabar compound na gidan Zain ya danno da Prado tasu ciki. Saida k'irjinta ya buga ta fito da sauri ta suri Anees zata shige gida a guje. Saidai tana buɗe k'ofar shima ya kawo hannu jikinta. Bai jira ta juyo ba yace "Ki same ni address dana baki yau By 7p.m. " Bai jira tace komai ba ya juya ya koma mota. Numfashi ta sauke mai zafi ta k'ara matse Anees jikinta. Tana kallo suka fice ta buɗe gidan ta shiga. Tayi decide by seven suka fito da kayanta ta saka cikin booth na mota. Doguwar riga ce a jikinta k'irar Dubai maroon Colour. Anees kuma y'ar kanti ce pitch da tayi mata kyau sosai. Maigadi taba keys na gida suka fice. Address daya bata tayi kai tsaye. Wani tamfatsetsen gida ne Address d'in daya bata nan Maitama. K'ofar gidan cike yake da masu tsaron sa. Abun mamaki tun kafin ta k'arasa aka buɗe mata gate alamun sun san da zuwanta. Wajen fakin ta faka motar ta da already wani yake jiranta. Rik'o Anees tayi suka fito har zuwa bakin k'ofa da zai sadaka da ciki. Bugu d'aya ya yi ya wuce ya barsu a gurin. Saida sukayi sakan biyu a tsaye kafin taji an buɗe k'ofar. Ido suka had'a lokacin daya buɗe sanye da white shirt da black wando. Kansa a jiki yana digar ruwa da alama daga wanka ya fito. Fuska babu wani emotion yace "Come in" K'ofar ya buɗe sosai ta rab'a ta shiga riƙe da Anees . Bakin k'ofar taja tungs ta tsaya kai tsaye tace masa "Gani nazo what did you want?" A hankali ya juyo ya watsa mata tsumammun idonsa ,maimakon ya bata amsa yace "Me zaki sha?" Kaman ta haushi da duka a zafafe ta k'ara cewa "Kana batamin lokaci. Ka gayamin dalilin da yasa ka ke son ganina anan" Anees ya kalla dake kellonsa alamu ya nuna tana son zuwa gurinsa. Hannu ya mik'a mata da d'an murmushi yace "Come here baby " Ai a guje ta fisge hannun ta daga na Jaleela tayi wajen sa ta d'ane tana dariya. Matuƙar mamaki da aljabi ya saka Jaleela sakin baki tana kallon su. Sumbatar Anees ya yi goshi kafin ta ajiye ta a hankali yace "Go and play OK. Zanyi magana da Mummy " Kai Anees ta d'aga da sauri tana cewa to "uncle" sai kuma ta kwasaa guje tayi wata k'ofa kaman ta san inda zata. Baki Jaleela ta saki tana kallon ta harta b'ace. What? . "Sit down" Taji muryar sa data dawo da ita daga shock datayi. Tabbas dole ta guje masa as soon as possible. "Ba zama ya kawo ni ba. Ka gayamin abunda yasa ka kawoni nan" Ido ya zuba mata na y'an minti baicr komai ba sai kuma ya jinjina kai. Wasu takardu dake kan glass tebir ya d'auko ya yi inda take tsaye ya miƙa mata. "Hold this" Kaman bazata karb'a ba ta warce azafafe tanajan tsaki. Tana duba takardun ya k'ara da cewa. "Ina so muyi aure " Chak ta tsaya da duba takardun ta d'ago ta watsa masa manyan idonta. Can kuma ta fashe da wata irin dariya kaman mahaukaciya. Baice komai na sai ido daya zuba mata tana dariya harda hawaye. D'an murmushi ya yi dashi kad'ai yasan ma'anan sa. She thinks am playing. Yace a zuci yana murmushi. "Wayyo Allah " tace tana goge hawaye tsaban dariya kafin ta nunashi da hannu ta nuna kanta. "Amma dai wannan kan ba d'aya yake ba ko? Ka buga kan naka ne ko ciwon hauka ne ya kama ka? Dawa zakayi auren" "Hmm" Ya saki d'an murmushi kafin yace " Kinga wata ne a nan?. See, kar kiji nace muyi aure ki d'auka your something special. Kedin ba komai b'ace sai a desperate prostitute. After all babu wani namiji dazai aure ki in his right mind. So ki dauka favour ne nake miki badan ke ba saidan saboda y'ar ki." Zafin maganganun sa ji take kaman mashi yasa yake sukanta dashi. Batasan hawaye sun zubo mata ba saida taji digar su. Mutumin daya jefata cikin wannan kaddarar shine yanzu ya yi sanadin da taji ta k'ara tsanan karuwanci da take. Murya na wani irin rawa ta nunashi da yatsa "Kana ganin laifin waye?. Kaine sanadin dana fad'a cikin wannan halaka. Kai ka lalatamin rayuwa. Da ace ana maida hannun agogo baya dana mayar na goge ranan da zaka shiga rayuwata. Ni karuwance naji amma ina so ka sani ko zan mutu banyi aure ba, da dai na aure ka gwanda na gama rayuwata a titi" Fuu ta wuce shi tana kuka sosai tayi k'ofar da Anees tayi. Ace katon play ground ne babu abunda baby aciki. Ranan da yafa kawo Anees washegari yasa aka had'ashi saboda ita. Can kan wata mota ta hangota tana yi masu tsoro tsaye lungu da tsako suna bata kariya. A guje ta yi wajen ta d'auko ta fito. Yarinya ta saki kuka dan ko kad'an batasan abunda zai katse mata wasan da take. Haushi ya kama Jaleela ta daka mata tsawa. Kiga daga had'uwa da mutum soyayya da shukuwa mai k'arfi na neman shiga tsakaninsu.? Wai a haka ma don bata san cewa shine ubanta ba?. To da sake. Yana nan tsaye inda ta barshi ta wuce bai motsa ba tayi bakin k'ofa ta buɗe. Saida ta tura Anees waje sannan ta juyo ta kalleshi da wani irin tsana ta sakar masa bomb "Kuma ina so ka sani. Anees y'ar kace. Flesh and blood. But she's my daughter tun daga farkon haihuwar ta har zuwa yanzu. Nice ubanta nice kuma uwarta. Stay out of our lives." A hanzarce ta fice ta barshi a tsaye cikin matsanancin mamaki. 'Anees y'ar kace. Flesh and blood' What?. Tsaban yands maganan ta dake shi ya kasa motsi sai k'ofar daya kafe da ido. Magana d'aya ce cikin ransa. But how? Bazai manta ba clear as a day ko a wancen ranan bai kusance ta ba so how is this possible? .sai a yanzu ya yi snap daga shock d'in daya Shiga a guje ya fito daga gidan amma tuni Jaleela ta fice da matsanancin gudu. Numfashi ya fesar mai zafi bazaiyi k'arya ba ya yi abubuwa da ita sosai ranan but he did not go all the way in. Jaleela dai maimakon tayi gida sai tayi hanyar wajen Abuja kaman yanda tayi kuduri. Sosai take shek'a gudu kan titi don ta tsere masa. Tasan yanzu tunda yaji wannan bomb dole zai biyota gida, inshaAllahu ita kuma ta gama zaman Abuja. Koman dare a yau d'innan ba gobe ba zata koma Gida .zata koma wajen iyayenta. UNKNOWN Wani irin d'aki ne mai tsananin duhu da ko tafin hannun ka baka iya gani. Babu windo ko k'ofa a d'akin da wata iska ko haske zai shigo. Haske guda d'aya ka ke iya hangowa kaman dot. Wasu irin eerie red glowing eyes ne masu matuƙar ban tsoro da tsananin hasken su yake dan reflecting a d'akin. Blinking idon sukayi don su kad'ai ka ke iya gani saboda duhu. Direct suka kalli bango sai ga wani irin round mudubi ya nuna a jikinsa. Hasken idon ya yi reflecting mudubin a take wani irin hayaki ya fito daga cikin sa sai kuma ya koma ys rufe mirror d'in gaba d'aya. Wata irin murya mai amo da ban tsoro ta fara magana kaman mai chanting abu. Abun mamaki saiga hoton Jaleela da Lameen tsaye jikin mudubin suna magana tsakiyar d'akin kaman mai kallon TV. Dukkanin wani abu daya faru tun daga inda Jaleela ke dariya na cewa suyi aure har zuwa sanda ta fice tana gaya masa Anees y'ar sace. Kaf ya yi playing a jikin mudubin. Wannan bakin hayakin dake zagaye da mudubin ya rikid'e lokaci guda ya yi shaping kaman mutum. Gaban wannan jan idon ya tsaya da har zuwa lokacin baka ganin mamallakinsu. Maganace ta fara fitowa daga cikin sa kaman iska "The fairest of all ta kara dawowa shugaba. Idan mukayi sakaci zata zama mukulli da zata kawo k'arshen mu" "A'a. " Muryar tayi amo mai k'arfi saida d'akin ya jijjiga. Tana wani irin gurnani mai ban tsoro tace "Wannan karon babu tantama idan ta kara shiga gonar daba tata ba zata mutu. Allahn ta da take bautawa shine yake bata kariya mun kasa samun nasara a kanta. Amma karfin ikona da magic nawa wannan karon zan samu nasara. Zamu fara da y'ar. Babu wani shamaki da zai shiga tsakanin da KING . Da nasan cewa tun wancan ranan tana d'auke da cikin sa dana hallaka shi tun baizo duniya ba. KING nawa ne ni kaɗai. A shirye nake na kashe duk wanda zai rabe shi." WACECE JALEELA? Shekara BAKWAI (7YRS) da suka wuce. Seven years back. ...... Next page. 𝗚𝗨𝗗𝗨𝗡𝗔 𝗔𝗞𝗘 . 𝒜𝐬𝐡𝐚𝐧𝐭𝐲 𝐥♡︎𝐯𝐞. A/N. Wannan page naku ne masoya littafin GUDUNA AKE. bazaiyiwu na kira suna ba don Allah kaɗai yasan yawan yaku. Ashanty tana godiya da kauna ❤. 36/40. WACECE JALEELA? Jaleela Mukhtar Bature ko nace ALEEYNA. Iyayenta Mukhtar Bature cikakken Kanuri ne ya yinda Ammi , Zulaikha Abdulaziz Bature sadaka yalla ce. Mutanen Niger ne sudin kuma y'an uwane. Sunyu aure ma zumunci da kuma kauna. Allah ya azurta Bature da ya'ya da jikoki. Sai ya kance suna aure tsakaninsu da wuya kaga sun auri bare. Bayan auren Mukhtar da Zulaikha suka bar cikin dangi da y'an uwa suka dawo nan Jihar ADAMAWA state Saboda aiki. Abhie yana da buri ganin ya buɗe makaranta ta yana yana koyar dasu ilimi na addini. Saboda haka suna dawo ya fara tara yara nan k'ofar gidan sa yana d'an koya musi hadithi da fikihu. Shekarar su biyu da auri Ammi ta haifi AL'MUSTAPHA. Almu dana Shekara guda cif Ammi ta fuskanci tana d'auke da wani cikin. Sosai ta shiga damuwa ga ciki ga kuma goyo. Haka tayi ta hak'uri da kukawar Abhie ta rani cikin da Almu da take shayarwa. Wata tara cif ta haifi Amnah. Almu da Amnah sun taso cikin gata da soyayya da kuma tarbiyar. Daga kansu Allah sa ikon sa Ammi bata sake ko b'ari ba. Saida Almu da Amnah suka shekara bakwai da y'an watanni saiga wani ciki. Wannan karan kam ciki mai matuƙar laulayine da saida ta kai Abhie ya aika can Niger aka turo kanwar Ammi ,Fareeda tazo tana taimaka mata. Sosai Ammi taci wuya wannan cikin kaman bazata kai ba. Yanda ta saba haihuwa wata tara cif wannan saida ya cika wata goma. Ranan da nakuda ta tashi kuwa wuni tayi tana fama. Makota da unguwar zoma sunyi k'ok'ari a kanta sosai. Cikin ikon Allah wajen asuba ta sankaco baby girl mai tsananin kyan gaske don tafi su Almu da Amnah kyau nesa ba kusa ba. A take Abhie ya yi mata hud'uba da rad'a mata sunan ALEEYNA wato ma'ana ( BEAUTY AS THE MOON). Babu wanda yakai Almu da Amnah farin cikib samun kanwa. Y'an uwa da abokan Arziƙi suna ta turuwa zuwa barka kace haihuwace ta farko. Duk wanda yazo yaga ALEEYNA saiya tanka ta. Saboda haka ne Abhie ke yawan sawa ana mata rubutu ana bata basu gaba d'aya saboda bakin mutane. ALEEYNA ta taso cikin kauna gata da soyayyar iyaye da kuma yayye. Lokacin data shekara goma sha d'aya cif a duniya sukayi sauka gaba d'aya ita dasu Almu wajen Abhie. Ya dage sosai a kansu wajen karatu gasu yara ne masu matuƙar hazaka da kwakwala. Allah da ikon sa kuwa makarantar Abhie ta habbaka sosai almajirai ta ko ina suna tururawa wajen ganin sunzo sun samu ilimi mai kyau. Nan k'ofar gidansa Abhie yasa aka buge akayi siminti da kuma rufi na kwano. Kangon da yake jikinsa kuma ya siya aka gina masa makaranta da kuma dakuna na almajirai da suka kwana. Shekarar Almu ashirin cif lokacin ya yi sauka har bazata ta kirguga ba. A lokacin kuma ya gama secondary shida Amnah suna shirin wucewa Jami'a ta ABU dake can zaria. Aleeyna tana shekara goma sha uku. Idan kaji yanda take karanta maka hadithi da nahawu, sai ka riƙe baki. Abhie saboda ganin ta fara tasawa yasa ya sakata nan makaranta ta islamiya da take can gaba dasu. Tana fara zuwa makaranta saboda hazakar ta duk wani abu daya danganci musabaka ko taro da za'ayi itace a gaba. Wani lokacin haka zaka ganta y'ar mitsitsiya a aji tana koyarwa. Sosai Aleeyna tayi suna ga kyau ga ilimi. Qur'ani kuwa idan ta fara karatun sai kaji kaman karta daina. Tana shekara goma sha biyar kyawunta ya fara fitowa sosai da sosai. Don Aleeyna irin yarannan ce mai garin jiki saffa-saffa musamman daga kirji da kugunta. Komai nata irin na Ammi ne. Lokacin da girma ya fara zuwa zai ya kasance koda yaushe cikin hijabi take ko a gida. Kai ko barci zatayi bata cire Hijabi ,gata yarinya mai tsananin kunya da girmama mutum. Hakan ya jawo mata soyayya ta mutane lungu ta tsako. Ko baka santa ba kanajin labarinta sai ta shiga ranka. Tana shekara goma sha shida akayi auren Aunty Amnah da Zubair. Yasha wuya sosai kafin ya sameta don Amnah da Zubair jirginsu ba d'aya ba. Zubair dan gidan attijaran mutum ne, maihaifin sa kansila ne a nan garin ADAMAWA. Acan ABU d'in ya ganta sanda yaje raka wani abokinsa. Tun daga lokacin ya haukace yana binta ita kuma sam taki bashi fuska. Saida ya had'a hannu da Almu ya shige jikinsa ya zame masa aboki na k'arfi da yaji. Cikin ikon Allah ya fara samu kan Amnah. Babu b'ata lokaci duka iyayen sukayi Na'am da batun. Lokaci kad'an akayi aure babu wata haniya sai yar walima da sukayi da y'an al'adu irin nasu na kanuri da sadaka yalla. A nan ne dan gidan wan Abhi , wato Lukman yaga Aleeyna ya rikice shifa yaga mata. Da yake ba wani zuwa Niger din take ba shi yasa dangi ba kowa ta sani ba. Saida kowa daya halacci bikin yasan Lukman na son Aleeyna. Sosai ya rikice ya zama abun dariya cikin y'an uwa. Kowa yana cikin murna da farin ciki saboda an jima ba'ayi auren zumunci ba. B'angaren Aleeyna kam sam bata son auren zumunci saboda haka tun abun Lukman baiyi nisa ba ta gaya masa ita bata sonshi. To da yake Lukman ya yi nisan da bayajin kira sam yaki haka ya yi ta bibiyar rayuwarta. Tun tana wulak'antanshi har ya fara samun kanta. Lukman ya iya soyayya da kulawa. Baya cikakken sati biyu zaizo ADAMAWA ba. Uwa uba ga kyau ga rufin asiri daidai gwargwado Family na Bature suna dashi. Don Alhaji Bature irin tsohon attajirin nan ne. Duk cikin su babu mummunan saidai ace wancan yafi wannan kyau. Ganin yanda Lukman ke zarya Abhie ya shirya da kansa yaje can Niger ya samu wansa IBRAHIM BATURE. Bai bar Niger ba saida ya tabbatar an saka rana na Aleeyna da Lukman. Kai ranan Lukman kaman wanda aka bawa Aljanna. B'angaren Aleeyna kwana tayi taba kuka bawai bata son Lukman bane, ita tana da burine taga ta gama makarantar book tukun kafin tayi aure. Kuma tasan can Niger Lukman zai kaita tunda nan yake zaune. Ita kuma bata son abunda zai rabata da Ammi sam. Babu yanda zatayi haka ta cigaba da zuwa makaranta boko da islamiya lokaci kuma na k'ara matsowa sosai na bikinta da Lukman. FAITHFUL DAY. A hanzarce ta fito sanye da Hijabi na islamiya dayazo mata har k'asa. Nikaf dake hannunta ta warware tana k'ok'arin daurawa a fuska, Ammi ta fito daga kitchen rike da kula a hannun ta. "Har kin fita Leeyna? Bazaki bari ki karya ba?" Da muryarta maitsananin dad'i tace "Ammi na makara. Musabaka za'ayi kuma nice zan farayi. Tun dazu Aina'u ke kirana a waya. Idan naje bazan rasa abunda zanci ba" Kai Ammi ta girgiza tace "To shikenan ai Allah ya taimaka ya bada sa'a " A hanzarce tace 'Amin Ammi' ta suri jakarta ta fito daga gidan da sauri. Kaman koda yaushe Abhie na zaune baranda ya almajiransu suna karatu. Da sauri ta zagaya ta durkusa kusa dashi tana gaisheshi. Albarka ya shimata da fatan samun nasara. Tana mike motar taxi ta faka k'ofar gidan. Almu ya fito daga motar goye da jaka . A guje ya rungume shi tana dariya ya shafa kanta dajan kumatunta. Sannu tayi masa da zuwa tayi saurin wuce ta tafi makaranta. Daga can b'angaren. Numfashi ya sauke mai zafi ya kalli agogon hannun sa. Wani irin tsaki yaja ya d'ago manyan black eyes nashi ya watsa kan Zain dake duba wata patient. Wani tsakin ya k'ara ja. Zain ya juyo ya watsa masa harara "Ai saida nace kar ka biyoni ka biyoni kazo ka dameni da tsaki ina aiki" Kaman zaice wani abu sai kuma ya fasa da sauri ya miƙe ya suri coat tashi daya ajiye kan kujera. Murya a kausashe yace "Am going out" "Kasan garinne dazaka fita?" "No. Babban gari ne ai. Ina buk'atar fresh air ne" Yana gama fad'in haka bai jira abunda zaice na ya juya ya fice Zain ya bishi da ido. Kai ya girgiza yana d'an murmushi wato Lameen ya zame masa jela. Duk sanda yake son guduwa daga masarauta musamman idan yaji ana zancen aure ko hawansa kan kujerar Mulki direct gurinsa yake zuwa ya b'oye. Shida Lameen abokaine sosai da suka zama tamkar yan uwa. Tun had'uwa da sukayi suna shekara goma sha shida a makaranta ta Oxford suka d'inke. Shiya koya masa hausa sosai ya kuma kawo sa Nigeria mahaifarsa. Tsakanin sa da Lameen soyayya ce daga Allah kawai. Zamansa da Lameen yasan abubuwa da dama da mutane basu sani ba. All this top guy da yake nunawa da bad boys duk facade ne. Inside mutum ne so soft ga tausayi . Yana fitowa masu tsaron sa suka rufe shi. Mota suka buɗe masa ya shiga suka bar asibitin. Jingija ya yi jikin glass na motar yana kallon waje da yanda mutane ke mu'amala. Life nasu na birgeshi matuƙa. Kowa yanayin abunda yake so ne babu wani daya tsaya yana juya masu rayuwa sai yanda akace suyi. Daidai danger suka tsaya data tsaida su. Kaman ance ya d'aga kansa ya hangota tsaye bakin titi da alamun tsallakawa zatayi. Tsintar kansa ya yi ya zuba mata manyan idonsa duk da cewa baya ganin fuskatar saboda nikab data sa. But baisan abunda yasa ba idonya ya yi drawing d'insa in hakanan kawai yaji yaja son ganin fuskarta. Yana kallo ta tsallaka da sauri ta wuce mutane suka bita da kallo. Ware idonsa ya yi sosai yana kare mata kallo dason gani koda wnai inch ne na jikinta. Chak idonsa ya tsaya kan babban stain dake jikin hijabin nata wanda hakan shi ya yaja hankalin mutane sosai ta zame masu abun kallo. (Malam bahaushe kenan) . Baisan ya akayi ba sai ganin ya yi ya fito daga cikin motar. Aikuwa yoo ido ya yi kansa kace sabon halitta aka gani. Taku d'aya biyu ya yi ya rik'o hannun Aleeyna dake neman haurawa d'aya b'arin. Da wani irin matsanancin mamaki da shock ta juyo kwayar idonsu suka sarke da juna. A take zuciyoyinsu suka harba lokaci guda. Wani irin ware manyan ido Aleeyna tayi k'irjinta ya wani matsanancin harbawa cikin matsanancin tsoro da tashin hankali tayi k'ok'arin fisge hannunta daya riƙe. Innalilllahi wa Inna'ilaihi raji'un. Wane irin tashin hankaline wannan kana tafiya katon gardi ya riƙe ka kan titi cikin mutane?. Gardin ma Arne don wannan ba bahaushe bane. Hankali a tashe ta cire hannu ta kifa masa mari. Tsananin mamaki da shock yasa ya saki hannun nata ya zuba mata manyan idonsa yana kallonta idon nan sunyi jazur. "Allah ya isa daka tab'a min jiki mai tsarki. D'an iska kawai. Ka d'auka nan irin k'asarce da mata ba komai bane sai riga?" Shar hawaye suka biyi mata fuska inda ta samu sauk'i ma babu wanda zaice wacece ita. A guje ta k'arasaa tsallakawa ganin yanda suka had'a uban go slow kan titi. Kowa ya fito daga mota yana kallon wannan abu. Ga masu tsaronsa daya k'ara saka tsoro zuk'anta su sun kasa taɓuka komai. Saida ta shige wani lungu ya juya da wani irin zafin rai ya cukwukwuye rigarsa daya cire zai bata ta d'aura. A zafafe ya fad'a mota zuciyar sa na wani irin zafi dashi kansa ya rasa dalilin da yasa hakan. "Follow her" Ya bada command. A guje suka tashi mota suka kutsa layin da Aleeyna ta shiga don tayi yanke. Babu wasu gidaje ko mutane sosai a layin saboda yanzu yake d'an tashi. Tana tafe tana kuka tsabar bak'in ciki da sai tsini masa take koma waye . Babu zato shegun motocin sa suka fakaa gabanta. K'irjinta ya k'ara bugawa da k'arfi ta juya da bala'in gudu zata bar layin. Woof taji ya d'auke ta wulla cikin mota. Ihu da kururuwa Aleeyna ta saki na neman taimako da agaji tana dukan glass. Amma da yake glass na motar soundproof ne ga tint babu wanda yaji bare ya ganta. Tana kallo suna ta shek'a gudu kan titi duk ta haukace. Ganin babu sarki sai Allah ta juyo inda yake zauje ya kafeta da ido fuska babu emotion ta bara bashi hak'uri. Wani irin smirk ya saki murya so husky yace "Did you know who you just slap? Big mistake ki ka aikata you most get punish. Babu wanda ya tab'a daga hannu ya mari KING ,not know not ever. And I will show you how dirty nake" "Wayyo Allah na shiga Uku. Ammi ,Abhie, ya Almu ku taimaka min" Ta cigaba da kururuwa cikin motar. Free pages na gab da zuwa karshe my people. A hanzarta a shiga sawun wanda suka fara payment nasu. Show me the love and support da nake gani. Chat me up 👇 08140754777 𝗚𝗨𝗗𝗨𝗡𝗔 𝗔𝗞𝗘 . 𝒜𝐬𝐡𝐚𝐧𝐭𝐲 𝐥♡︎𝐯𝐞. A/N: kuzo ku hanzarta ku shiga sawun wanda suka fara payment nasu na GUDUNA AKE. It's just 500N . Basai mun gama free pages ba da suna gabda zuwa k'arshe. Kar ku bari ayi wannan zazzafar tafiyar babu ku. A cigaba da bawa Ashanty ,love da support da ake bata. Chat me up 👇 08140754777. 41/45. K'aramin Estate suka shiga mai kyan gaske. Bakin wani flat house suka faka motocin. Har suka isa Aleeyna na zuba ihu da kururuwa na neman taimako. Fita ya yi daga motar ya zagaya b'arin da take ya fisgota da k'arfi tana ihu da kai masa duka. Ganin zata b'ata masa lokaci ya wullata k'afad'ar sa ya yi cikin gidan da ita. Saida ya wuce can kariyar d'akin na master bedroom ya watsa ta kan gado. A guje Aleeyna ta tashi taba ihu ta haura can d'aya b'angaren. Bakin gadon ya tsaya ya zuba mata tsumammun idonsa yana k'ara accessing nata. So yake yaga fuskarta yaga wace yarinya ce ita haka har ta keda jarumta ta d'aga hannu ta mareshi saboda zai taimaka mata?. Hannu yakai a hankali ya fara cire suit d'in jikinsa lights blue. Wani irin ihu Aleeyna tayi ta kwasa a guje tayi bakin k'ofa. Da dukkanin k'arfin ta take buga k'ofar tana jijjiga abun hannunta amma k'ofa taki buɗewa don ya riga da yasa mukulli. Hucin numfashinsa dataji bayanta ta wani irin juyo da sauri daidai ya kai hannu ya fisge nikaf dake fuskantar. Saida numfashin ya tsarke sanda ya yi arba da kyakkyawar fuskarta. Manyan idanuwansa ya zuba mata kaman yanda itama ta zuba masa nata ido dake d'auke da matsanancin shock baki a buɗe. Kallo ta yake tun daga d'an k'aramin pink lips nata zuwa dogon hancinta da manyan idanuwan ta dake d'auke zararan gashin ido. 'She is so beautiful ' zuciyar sa ta furta. Kai kawai ya jinjina yana cigaba da kallonta. Da zafin rai takai hannu zata fisge nikaf d'in ya d'aga shi sama. Kuka ta k'ara saki mai k'arfi tana cewa "Me ka ke so dani ne?. Don girman Allah kayimun rai ka kyaleni na tafi gida. Kayi hak'uri don Allah. Na taso gidan tarbiya da Addini in kana kaunar Allah da Manzon sa karka lalatamin rayuwa. Kaje can inda ka samu lalata rayuwar wasu yanda ka sab amma don Allah kyale ni." Da gaske dai kallon d'an iska fasiki take masa?. Shi da fari duk so yake ya tsorata amma yanzu data k'ara gayama haka ransa ya k'ara zafi. OK zai fara lalata ya'yan wasun amma kanta zai fara. Wani irin zafin rai ya fisgota ya yi kan gado da ita. Matsanancin dambe suka suke da kokawa tana d'aukan dukkanin abunda taci karo dashi ta kwad'ama. Shi kanshi ya yi mamakin k'arfi da yarinya take dashi. Gata y'ar mitsitsiya amma sai k'arfin tsayi. Lokaci d'aya ya dagata ya kama kan gadon kafin tayi wani yunƙuri ya danneta da katon jikinsa. A wahalce ta saki wani irin tari idonta suka k'ara fitiwa waje don gaba d'aya ya sake mata nauyin sa. Numfashi ya fara mata wahalar fita. Hannnta ya had'a saman kanta ya riƙe da nashi guda daya. Ido ya zuba mata yana k'ara kyestima irin kyau da yarinya keda shi. Dama a Nigeria bakaken fata akwai mata masu kyau haka?. ( Nace malam Lameen. Ai babu irin matan da babu a Nigeria. 😂). Mamakin yanda yake jin tudun k'irjinta yake. Yarinya is to small to have doe's things. Nan da nan yaji wani irin urge da son ganin gaba d'aya jikinta. Yana kallonta fuskarta da hawaye ke gudu kaman an buɗe fanfo ya kai d'aya hannun ya fara tattare dogon hijabin dake jikinta. Wani irin ihu tayi tana k'ok'arin fisge hannunta amma k'arfi ba d'aya ba. Saida ya tattare hijabin har wajen cinyoyinta dake b'oye cikin dogon wando na islamiya. Dan sunkuya ya yi ya kai kallonsa gurin. Sosai yaga yanda wandon ya b'aci don har ya fara bushewa ma. Akwai maza da yawa da idan matansu na al'ada basa son iya tab'a su saboda suna kyankami sai a daukewa mace wuta sai ta gama jini kaga an dawo ana rawar jiki da ita. To ai ubangijima bai hana ka samu nutsuwa da matar ta kaba idan tana al'ada. Saidai an haramta ka kusance ta. Idan mace tana Al'ada akwia hanyoyi da dama da zaka samu nutsuwa da ita ba sai ka kusance ta ba. Ko kad'an baiji wani kyama ko kyanmi ba ya kai hannu ya Jane wando da k'arfi ya yi wurgi dashi. Kaman wacce ya zarewa rai haka ta k'ara sakin wani irin ihu da kici kicin gani ta kwace kanta. Manyan idonsa ya zubawa fararen cinyoyinta dake wani irin shining tas-tas dasu babu ko silin gashi guda d'aya. Wani irin kankancewa idon nasa sukayi yaji wani irin urge nason tabu su. Hannunsa na dan shaking ya kai hannu ya nutsa cikin naman k'afarta. Laushi da sulbi da yaji wa wajen gaba d'aya notin kansa ya kuce. Dukkanin kukanta da ihunta sai ya daina jinsu. For the first time in history nashi yaji yana sha'awar mace. Duk mata dake hauka a kansa bai tab'a ganin mace data sashi yaji sha'awa bare har yaso kasancewa da ita. But this girl. She is so different. A karo na farko yaji ya zama so alive har wani gumi ne yake karyo masa. Burinsa da kuma mission nashi yaji ya rage mararsa data wani irin daurewa lokaci d'aya. Jiki na wani irin rawa ya koma jikinta ya kwanta yana kallon fuskar da hawaye suka wani iri gudu ta runtse ido kaman mai shirin kashe kwayar idon nata. Numfashi ya sauke gefen wuyanta ya k'ara tura wuya yana shak'ar kamshin saloon wanka na Dove da fatarta take wanda ya game mata jiki. She is o heavenly. D'an k'aramin bakinta dake ta rawa ya zubawa ido yanajin urge nason kissing nasu. Wai yau shine yake son kissing mace. Wai what magic yarinya take amfani dashi ne. Lashe nashi jajayen leb'en ya yi kafin ya kawo hannu a hankali ya riƙe habarta sosai karta kwace. Da zalama ya kawo harshe ya lashi leb'en ta na kasa kafin ya wani irin jashi very slow and sexy ya tura cikin bak'in sa. Hit da kamshin da bakinta suke dake shi dan rogowar notin sa daya rage ya kwace. Saidai baije ko ina ba ta dartse harshen dake neman hanyar shiga bakinta da hakoranta. Har kwakwalwar kansa saida yaji wata irin zaba amma na lokaci kad'an don a take zabarta maye da wani irin pleasure dake neman birkita masa lissafi. Wani irin gurnani ya saki ya kama habartata ya matse da hannunsa dole ta sakar masa harshe da yaji jini ya fara biyowa. Da zafi zafi ya kara tura bakinsa cikin nata yana bata wani irin zazzafan kiss ,so deep da har makogaronta take jin harshen sa. Saida ya sumbeta sosai ya kusa duk wani lungu da tsako na bakinta. Da ace wace macece yake wa wannan abun da take so kaman yanda yake yi sai taji ta a wata duniyar daban. But for Aleeyna ji take tamkar wutar Lava yake d'ura mata cikin baki. Sanda ya cire bakin nasa daga cikin nata har wani irin pop sound ne ya fito yawunsa da nata ya biyo gefen bakinta. Idan Aleeyna ya yi wani irin ja tsabar kuka sai neman sai numfashi take mai matuƙar wahala. Harshe ya kawo ya lashe gefen bakin nata da yawo ki bi. He needs more. K'irjinta dake ta up and down ya kalla yana jin wani irin urge ya tab'a su, but wannan bashine top priority nashi ba yanzu. Yana buk'atar release. Don haka da zama ya fige pant dake jikinta. Murya a dashe Aleeyna ta k'ara sakin wani ihu da kuka jikin na jijjiga. Tana ji ya had'a kafafuwanta guri d'aya ya matse da k'arfi kafin ya kwanto jikinta. Idonta dake runtse ta ware so da karfi kaman saucer saboda wani abu dataji tsakanin cinyoyin nata daya masifar firgita ta matuƙa. A d'ure ta kalli Lameen for the first time tunda ya fara mata wannan abun .shima idon sa kan nata sun rikid'e sun kara zama wani irin black. Irises na idon har wani girma suka k'ara. Murmushin daya sakarmata saida taji kaman ta sume tsabar tsoro. Tanaji ya fara goga jikinsa cikin kafawuwanta yana wani irin gurnani da kallo idonta. Saurin maida idon tayi ta runtse sosai ,kukan kam yanzu har ta rasa wane iri zatayi. Saitin kunnenta yake ta nishi da gurnani har tsawon minti biyar kafin taji ya tura hannunsa karkashinta ya d'ago ya matse jikin k'irjinsa yana wani irin nishi mai k'arfi. Lokaci d'aya kuma taji wani irin sanye kan mararta daya saita sosai yanda zai taba k'ofarta. Firgice da ban tsoro yanzu yasa ta yi irin suman nan na wucen gadi ta zubawa silin d'in d'aki ido. Tana jin ya gama sakin Seeds nashi kan mararta lokaci d'aya kuma taji kaman wanda aka fishe daga jikinta da k'arfin gaske. Tsananin mamakin abunda ya faru bai tashi daga zaunen da ya yi tsakiyar falon ba sai ido daya zubawa Aleeyna data ke wance bata motsi sai idonta kawai dake blinking. What? Bayansa ya juya ya k'ara juyowa inda take. Menene kuma ya faru. Zai iya rantsewa da Allah alamun hannu yaji kan wuyansa sanda yake kawowa kan mararta. Ji ya yi kana an shakeshi kafin yaji an fisgoshi da nugun k'arfi saida ya wantsala ya fad'o tim k'asan d'akin. Tsananin mamakin abunda ya faru yasa ya miƙe zaune yana fuskantar Aleeyna dake kwance harzuwa lokacin bata iya motsi. WTF?. Yanda akayi watsi dashi gefe kaman wani force ne da baya iya ganinsa. K'ara juyawa ya yi bayansa ya k'ara kallon lungu da tsako na d'akin but nothing. Babu komai dagashi sai ita kawai. What is this?. Shiru d'akin ya d'auka har na tsawon awa d'aya kafin yaga ya yunƙura da kyar ta miƙe zaune tana kuka sosai. Ido ya zuba mata yana tunanin why is she crying kuma?. Ai baiyu rape nata ba. He just find his release. She should be thankful ma. Mata da yawa suna so ko romance d'inne ya yi dasu but basa gabansa. Hannu ya kai kan leb'ensa yana shafawa har zuwa lokacin yana jin gard'inta cikin bakinsa. Yana kallo ta d'auki wandonta daya jefar . Dan tsayawa tayi tana kallon wandon sai kuma ta saka a haka. Sosai take kuma mai ban tausayi .harta gama sa wandon, ta gyara kayanta bata kalli inda yake ba ta wuce shi tayi k'ofa. Tsayawa tayi kawai jikin k'ofar bata juyoba. Kallonta ya cigaba dayi sai kuma ya miƙe a hankali yana gyara nashin wandon da bai gama cirewa ba. Tana jin motsin ya nufo k'ofar tayi saurin matsawa kaman zata shige bango. Buɗe k'ofar ya yi ya kalleta ta ya yi waje. Har tasa kai zata fita sai taji kaman wani irin pressure ne tsaye a bayanta. Kaman ana kallonta. Tsananin tsoro da yanda take son ganin ta fita daga wannan fit hole baisa ta juya ba fice da sauri daga d'akin. Da ace Aleeyna da Lameen za suga irin red glowing fury eyes dake kallonsu cikin wani irin black shadow sai zuciyoyinsu sun buga a take lokaci guda. Wani irin iska ce ta kad'a mai tsananin k'arfi cikin d'akin bayan fitar Aleeyna kafin wani iri gunji ya ratso dakin mai tsananin ban tsoro saida bangon d'akin ya tsage. To abunka da abun b'oye babu wani mahaluki dazaiji ko yaga yanda bangon d'akin ke tsagewa. Tana fitowa kai tsaye tayi hanyar gate. Da ido Lameen ya bita tsaye jikin mota. Yasan taurin kanta don haka ya biyota shima a kafa Bodyguards nashi suka rufa masa baya. Har ta fito bakin titi suna biye da ita. Nikaf nata ta sauke gaba d'aya har ido saboda sanin da tayi na stain da tayi ga kukan. Allah ya taimake unguwar babu mutane sosai .tana tsayewa wani dan sahu ya shigo layin. A hanzarce ta tsayar dashi ta fad'a batama yi masa bayanin inda zata ba. Shi kuma tsorone ya kamasjo ganin Lameen da dakarunsa tsaye bakin titi. Tunanin d'aya ya bashi ita suka biyi zasu sace saboda haka babu jiran baasi ya fisge adaidaita a guje ya juya ya bar layin. Da ido Lameen yabi mitar har ta bace daga idansa. Kai kawai ya jinjina ya kalli yaronsa guda d'aya yace "Follow her ,and find who is she" "Yes KING" A guje ya juya wasu suka rufa masa baya suka shiga mota. Saida yaga wucewarsu sannan ya juya ya koma ciki. B'angaren Aleeyna kai ta had'a da gwiwa tana wani irin kuka mara sauti. Tausayi ya kama mai nape yace "Hajiya kiyi hak'uri. Yanxu duniyar ce ta zama abun tsoro. Duk inda ka ke baka tsira ba. Ko meya kawosu kuma Nigeria har suke son sace mana mata kuma oho. InshaAllahu Allah yafi k'arfi su." Ita dai Aleeyna batace komai ba sai kuka kawai da take. "Hajiya ina zamuj?" Sai a lokacin ta tsagaita da kukan ta d'ago da kyar ta gaya masa inda zai kaita. Basu jima ba ya faka motar k'ofar gidansu. Abhie yana nan zaune da Ya Almu sai yan tsiraran yaran da suke karatun hadda. Ya Almu na hangota cikin motar ya taso da suari ya nufota. Wani irin kuka ya k'ara kwacewa Aleeyna. Yanzu taya zatayi musu bayanin abunda ya sameta. Da mamaki ya kamata ya fito da ita. Kuɗi ya cire ya bawa mai nape ya rungume ta tsam kan kirjinsa yana cewa "Auta. Menene? Baki da lfya ne?" Ta kasa cewa komai sai aikin kuka da take. Mai nape kam kaman wanda aka kullewa baki baice ga daga inda ya d'aukota ba yaja motar sa yabar k'ofar gidan. Sai bayan Almu ya rungume tane yaga yanda hijabinta ya b'aci. D'an murmushi ya yi ya girgiza kai ya kamata suka shige gida. Ahbie ya bisu da kallo cike da damuwa. Tsakar gida suka samu Ammi tana jin wa'azi cikin radio data kunna. Ganin yanda ya suka shigo ya rike ta d'ago da sauri tana cewa "A'a Leeyna Lafy har kin dawo? An tashi daga musabakarne?" Jikin Ammi tayi a guje tana kuka murya a shaƙe tace "Ammi na manta yau watane. Naje makaranta ya batamin jiki mutane sai kallona suke" Kai Almu ya girgiza ya juya ya fice yana murmushi. Aleeyna akwai ta kunya. Saboda wannan abu take kuka haka kaman wacce aka kashewa uwa. Murmushi Ammi tayi itama " shine ki ke kuka haka?. To akwai wanda ya wuce hakan ya faru dashi ne? . Shi tsautsayi ai yana kan kowa. Yi shiru haka tashi keje kiyi wanka kizo kici abinci " 'A ace kunsa abunda ya sani wannan kukan da sai kunyi wanda yafi wanda nake' Aleeyna ta furta a zuci. Da kyar ta iya yin wanka ta kimtsa kanta.shige d'aki ta kwanta. Tanajin Abhie ya shigo Ammi tana masa bayani. Saida ya k'ara dubata sannan ya fice. Tana kududdune cikin bargo Almu ya shigo da leda ya ajiyr ya fice baice komai ba . Ranan wuni Aleeyna tayi tana kuka har saida ya saukar mata a zazzaɓi. Rashin zuwanta islamiya yan aji suka fara turuawa zuwa don Aleeyna abun son kowace. Haka Lukman ya wuni yana kiranta a wuya hankalin sa duk ya tashi burin ransa na kwance babu lfy. Kallo Zain ya watsa masa yana k'ara bin k'irjinsa da kallo. Satin farce da jan da jikinsa ya yi ya bashi mamaki. Dagashi sai tawol don daga wanka ya fito. "Wai menene ya sameka haka jikinka duk yakushi da cizo?" Bai bashi amsa ba saida ya matsa bakin mirror da tawul rataye a wuyansa. Jik'akk'en gashin daya zubo fuskarsa ya kai hannu ya tura shi baya. Kallon kansa ya yi cikin mudubin tana tuna irin dambe da sukayi da ita. At one point harta cije shi a fegen wuya bata sani ba. Murmushi ya k'arayi ya kai hannu ya shafa gurin. Daga wani point of view na wani zaiyi tunanin ko satin soyayya ne ta bashi kaman yanda turawa suke wato HICKEY. Saida ya gaka shafe jikinsa da turaruruka masu tsananin kamshi da dad'i sannan ya juyo ya zauna gefen Zain dake kallonsa da tarin tambaya cikin idonsa. Kaf ya kwashe komai ya gaya masa bai b'oye ba. Mamaki da shock ya kama Zain. "What King? Kai ne ka kusa rape ta mace? , are you kidding?" Fuska ya b'ata murya a kausashe yace masa "When did i ever lie to you?, it's all her fault da take kirana Names. Da zace ta tsaya taji abunda yasa na riƙe ta da duk hakan bai faru ba." "But King. Kamanta nan da DUBAI ko kasashen da kake zuwa ba d'aya bane. Akwai tarbiya da kamun kai. Ko kaine hakan ta sameka zaka bada thesame reaction. Someone you dont happens to hold in a busy road. Kasan irin suna da backlash da hakan zai haifar mata?" Wani irin tsk sound ne ta fito daga bakin Lameen yace "Kana nufin na barta tayi ta roaming gari haka with huge stain na period a jikinta saboda your people are cowards bazasu iya gaya mata abunda ya sameta ba?. Saidai ta zame musu abun kallo ko abun zagi?, is that what you want me to do?" Shiru ne ya ratsa d'akin an rasa wanda zaice komai sai kafe juna da sukayi da ido. Numfashi Zain ya sauke don bashi da abun cewa. Tabbas al'umman malam bahaushe yanzu abun babu taimako ko tausayi. Saida a dinga kallo da zundenka. Kalilan ne masu taimako yanzu. This all thing ya chaja masa kyau. Muryar Lameen yaji yace "Exactly. That's what i thought" Baice masa komai ba sai ido daya bishi ya shige cikin kwaba. Baijima ya fito sanye cikin suit three pieces dark Ash. "Zan koma Dubai yanzu. Urgent matter ne ya taso" Bai jira Zain yace komai ba ya juya ya fice daga d'akin. Yana zaune ne cikin yana tunanin. 'Miss Aleeyna ' kaman yanda yaronsa ya binciko masa. Sunan ya k'ara maimaita kan leb'ensa. 'Miss Aleeyna. I'm coming back for you. Our story is just getting started.' Wani irin smirk ya saki da zai bawa mutum chill idan yana kusa dashi. 𝗚𝗨𝗗𝗨𝗡𝗔 𝗔𝗞𝗘 . 𝒜𝐬𝐡𝐚𝐧𝐭𝐲 𝐥♡︎𝐯𝐞. A/N: kuzo ku hanzarta ku shiga sawun wanda suka fara payment nasu na GUDUNA AKE. It's just 500N . 👇 08140754777. Last free pages. Not edit. 46/50. Tsawon satin gaba d'aya Aleeyna ta k'ara zama wata so silent da ita. Ya sawa kanta damuwa zazzab'i saida ta kwana biyu tanayin. Sosai Ammi,Abhie da Ya Almu suka shiga damuwa. Harta Amnah saida tazo gidan ta kwana biyu saboda soyayya Aleeyna data game musu jini da tsoka. Ko kaɗan basa son abunda zai kwantar da ita. Ga Lukman dake ta sintiri shima babu kwanciyar hankali tattare dashi. Ita kam Aleeyna bata san me zatace ma su Ammi ba kan abunda ya sameta da damuwa da suke nunawa a kanta. Sabida haka ne tafa k'ok'arin wajen ganin ta d'an rage rashin walwala a gida ko a makaranta. Lukuta suka shude. Kwana ya koma sati, ya koma wata. Bikinta da Lukman na k'ara matsowa. Bata da wani zabi daya wuce hak'uri a wannan lokacin da fawwala Allah. Shi kuwa wannan mutum bata daina sashi cikin Addu'a ba a koda yaushe ta kafa goshinta gaban Allah. Allah ya bita hakkin ta a kansa . Sosai Ammi suke ta shiri Hajjo ,kakar Ammi ana saura sati guda ta dire Higgi da mai gyaran jiki aka. Zuwa wannan lokacin Aleeyna ta d'an warware ta ajiye komai cikin bak'in littafinta. To alhamdulillah an fara hidimar biki duk da ba wani abune za'ayi ba, y'ar walima ce sai dinner da Lukman ya dage shi sai ya yi. Ance ta rana bata k'arya saidai uwar diya taji kunya. Yau aka tashi da hidimar biki a yau rana ta alhamis. Tun safe Aleeyna ke gidan mak'otansu da y'an tsirarun kawayenta ana musu kunshi. Tayi wani irin ta k'ara fresh fatar sai shek'i take. Ga gashinnan daya sha matsanancin gyara ya k'ara sulbi da laushi. Idan ka kalleta sai ka k'ara. To a b'angaren Aleeyna tunda ta tashi yau take cikin matsanancin fad'uwar gaba da ita kanta ta rasa dalilin hakan. Koyaya ta motsa ko akayi magana kusa da ita sai gabanta ya yanke ya fad'i. Duk yanda take k'ok'arin ganin wajen ta saki ranta abun ya gagare ta. Saida Hajjo ta sata a gaba da tambaya meke damunta, amma ta kasa furta komai. Dangi dake gurin sanda Hajjo ta sata a gaba suka fara yi mata tsiya wai dan taga zatabar Ammi ne shine duk ta zama kaman mara lfy. Itadai bata iya tankawa. To a washegari juma'a aka tashi da shirin d'aurin aure da za'ayi idan an sakko daga masallaci. Abun yau yafi na kullum don har wani zazzaɓi ta tashi dashi. Tun bayan anyi sallan asuba babu wanda ya k'ara runtsawa kowa ya tashi ana ta dinima. Aleeyna tun k'arfe 8 na safe bayan sun karya Amnah suka shige da ita d'aki da mai kwalliya ana tsantsarata. To a b'angaren ango abun ba'a cewa komai. Suma dai kaman sauran mutane ana yin sallah asuba suka d'auko hanyar ADAMAWA. Bakin Lukman ya kasa rufuwa shida manyan abokansa da guda biyu. Du da cewa kafin ya fito cikin b'acin rai yake son Mahaifiyar sa Sam bata son auren. Tana da burin ganin ta had'ashi da y'ar aminiyarta Najla ya aura, to shi kuma Lukman hankalin sa na kan Aleeyna. Ko irin d'an taron nan batayi ba ace uwa guda na Aurar da d'a. Sai daga b'angaren Mahaifiyar tashi ne da Baffan nashi sukayi taron da babu yanda ta iya. Karfe d'aya daidai suka faka harabar masallaci da za'a d'aura aure. Burinsa yaga sanyin idaniyar sa ko zaiji sauk'in rashin ganinta da ya yi na kwana biyu. Yana k'ok'arin fita daga motar ganin ana shirin shiga masallaci. Bakinsa Sam ya kasa rufuwa, saidai yana kai hannu jikin murfin motar zsi buɗe sak'o ya shigo wayarsa. Bai buɗe ba saida ya fito daga motar ya kai hannu cikin aljihun wandon na riga ya zaro wayar daga aljihu yana murmushi. Khamis da Isma'il dake tsaye kusa dashi sai murmushi suke taya abokin nasu saboda wannan rana ta farin ciki ce a garesu baki d'aya. Ya Almu dake tsaye bakin masallaci da Zubair suna jiran isowarsu ya taho da sauri cikin manyan kaya. Sosai Almu ya yi kyau cikin babbar riga ash datash surfani. Shi kansa bakin nasa ya kasa rufuwa saboda farin ciki. Fuskar Lukman yake kallo da murmushi kan fuskar sa. Lokaci guda yaga yanayi Lukman din ya chanza wannan fara dake kwance kan fuskarsa ta chanza zuwa wani irin matsanancin b'acin rai har rawa jikinsa yake. Wani irin jiri ne ya kwashu Lukman bayan ya yi arba da mummunan abunda yasa zuciyars kusan tarwatsewa. A take ya yi luu zai kifa Isma'il dake kusa dashi ya yi hanzarin taro shi yana "Subhanallahi, lfy?" A hanzarce Almu da Zubair suka k'araso suna tambayar Lukman meke damunsa haka yanzu-yanzu. Kasancewa komai ya yi sai wasu irin hawaye masu zafi da radadi da suka biyo kuncin sa. Jiki na wani irin rawa ya d'ago zaice wani abu, Baffa ya kwala musu kira daga k'ofar masallacin suyi maza su shigo ayi sallah . Baice komai ba ya wuce da sauri yana k'ara k'ank'ame wayar dake hannun sa da yake ji kaman wuta aka bashi. Har akayi sallah Lukman baya cikin nutsuwar sa. Haka ya zauna zuru kaman mutum mutumi baya fuskantar komai. Bayan an idar anyi hud'uba, babban limami da zai d'aura auren ya juyo yana neman magabata. Abhie da Baffa suka matso kaman yanda shari'a tace. Kafin Abhie ya Baffa suyi wani yunƙuri wajen wani abu Lukman ya miƙe da wani irin sauri kaman wanda aka mintsina. Jiki na rawa ya yi maganar data girgiza mutane dake cikin masallaci suka zuba masa ido cikin matsanancin mamaki. Baffa ya b'aci sosai a zafafe yace "Kana da hankali Lukman. Kasan me ka ke furtawa kuwa? Ko kasha wani abune?" Shar hawaye suka wanke masa fuska murya na rawa ya girgiza kai yace "Kayi hak'uri Baffa amma na fasa aurenta. Babu abunda nasha Allah ne kuma shedata. Ina son Aleeyna amma bazan iya aurenta yanzu ba bayan abunda na gani" Yana gama furta hakan ya juya da sauri zai ya fice daga masallacin baima bari wani ya k'ara cewa komai ba. Wani iri shiru masallaci ya d'auka daga Abhie har Baffa matsanancin mamaki da tashin hankali ya hanasu motsi. Liman ne ya yi gyaran murya yace "Meke faruwa ne Alhaji. Akwai wata matsala ne da ba'a sani ba? Ko kuma dama baisan auren ne?" Da wani iri sauri Baffa ya girgiza kai zufa nan karyo masa yace "Ko kad'an Malam. Kasan Yaran yanzu na zamani. Wlh lfy lau ya taho wajen d'aurin auren nan. Wata k'ila y'ar matsalace suka samu yake neman d'aga mana hankali. A d'aura kawai ai nini waliyin sa" "A'a yaya. Muje dai muji meke faruwa tukun" Abhie ya katse Baffa da sauri. Kai liman ya jinjina na gamsuwa sa maganan Abhie haka sauran mutaje dake gurin. A hanzarce suka tashi suka fito wanda Almu tuni ya rigasu yin waje. Da wani irin zafin rai ya tare Lukman dake k'ok'arin shiga mota. "Kana da hankali. Kasan abunda ka ke yi kuwa? Dama kace zaka auri Auta ne don ka tozarta ka wulak'anta cikin mutane da dangi. Menene ribarka na aikata hakan da kayi?" Shar hawaye suka k'ara wankewa Lukman fuska ya fara kuka kaman k'arami yaro. "Na ranste da Allah iana son Aleeyna, har yanzu kuma ban daina santa ba, amma bazan iya aurenta ba. Niba fasikin mutum bane saboda haka bazan auri fasika...." Kafin ya gama kai zancen Almu ya d'auke shi da wani irin b'arin makauniya. Ai a take dambe mai k'arfi ya kaure tsakanin su. Sosai gurin ya chabe da kyar aka raba Lukman da Almu. Shidai Lukman banda kuka babu abunda yake. Tsananin bak'in ciki da tsanan Aleeyna ya darsu cikin ransa da yake ji kaman ya harbeta. Duk abunda za'ayi ayi amma wlh ya fasa auren. Ran Baffa a b'ace ya kifawa Lukman d'in dake ta muzurai yan maimaita bazaiyi auren ba idan ana dole sai a sashi ya yi ,mari. "Ni zaka tozarta? Nace ni zaka tozarta? Idan wani abune ya faru ka bari ayi cikin sirri mana. Wato na lura uwarka ta fara maka tasiri wajen ganin ka raba kan zumunci ko?" A zafafe ya ciro wayarsa ya mikawa Abhie dake tsaye yana kallon Lukman d'in ya kasa cewa komai. Jiki babu kuzari Abhie ya mik'a hannu zai k'arbe Almu ya yi wuff ya kwace wayar. Abunda yaci karo dashi jikin wayar ya yi masifar d'aga masa hankali da jiri ya debeshi ya yi taga-taga zai fad'i. Zubair ya yi saurin tashi. "Innalilllahi wa Inna'ilaihi raji'un. Allahumma ajirni fi musibati wa aklifni khairan min ha" Almu ya furta da k'arfi. A yanzu kan k'irjin Abhie wani irin matsanancin bugu yake yana kalin Almu daya damke wayar da Baffa ke k'ok'arin kwacewa yaga ko Menene haka a jiki, amma Almu yaki bayarwa. Da wani iri bala'in gudu ya juya a guje ya Zubair ya bishi. Mota ya fad'a jikinsa har wani irin tsuma yake. Ganin haka Abhie da Baffa suka tabbatar lallai koma menene wannan babban abune. A hanzarce suka bi bayan sa Baffa ya saka Lukman a gaba suka shiga mota. Wani wawan fakin Al'mustapha ya yi kofar gida ko motar bai kashe ba ya fito a guje sai Zubair ne ya kashe motar . Kaman mahaukaci ya shiga yaja kwala kiran Aleeyna. Mata duk akayi cirko-cirko ana kallon Almu daya shigo kaman mahaukaci. Amnah ta fito da sauri tana cewa "Lfy ya Almu an d'aura auren ne?" "Ina Auta" "Tana d'akin Ammi" A guje ya fad'a d'akin can kuryar gado ya sameta ta nannade cikin bargo Hajjo da wasu mata a kanta suna yi mata sannu. Wani irin fisgota ya yi ya jiki na rawa ya nuna mata fuskar wayar dake hannun sa. Yana tsuma hawaye tab cikin idonsa yace "Menene wannan? Ki gayamin bake bace a cikin video danan Auta, ki gayamin" Wani irin dum kanta ya Sara ta kwalao ido tana kallon kanta dake jikin video da Almun ke nuna mata. Gata nan a kwance da wani namiji yana sex da ita haihuwar uwa. Blue film ne sosai. Tsananin kidima da tashin hankali da Aleeyna ta gani ta kasa motsi. Aikuwa Almu ya d'auke da wani irin mari da a take ta sume a guri. Da ihu ya yi kanta zai rufe da duka yana cewa "Kiyi kun magana" Dan sam bai lura ta sumen ba. Su Abhie suka riƙe shi da sauri. D'akin duk ya kacame da ihu-ihuce. Wani irin komawa gefe Almu ya yi ya durkusa ya had'a kai da gwiwa yana kuka kaman karamin yaro. HAJJO sai bala'i take kaman zata rufeshi da dukan itama. Ammi kuwa ta kasa ceea komai tsaban mamakin wannan abu. Jikin Abhie a matuk'ar sanyaye ya kai hannu ya kwace wayar dake hannun Almu. Kallo d'aya ya yiwa wayar ya yanke jiki ya fad'i. Ai zo kaga ihu. Hankula suka k'ara dugunzuma. Sai koke-koke da d'akin ya kaure dashi. Cikin tashin hankali aka kwashe su zuwa asibiti. Lukman kuwa babu wanda yasan sanda ya sulale ya bar gurin. Taimakon gaggawa aka basu . Saida Aleeyna tayi awa biyu cur bata farfaɗo ba. Abhie kuwa tun kafin su k'arasa asibitin ya farka yana ta nanata Innalilllahi cikin ransa. Abu dai duk ya dagul an shiga cikin damuwa da tashin hankali. Duk suna zaune jugum jugum Hajjo ta d'ago ta kalli Almu dake tsaye jikin bango duk ya fice hayyacin sa tace "Wai me yake faruwa ne? Kai Mustapha ka samu a duhu. Ka warware mana abunda yake faruwa gashi ance ba'a d'aura auren ba har yanzu. Ina ma Lukman d'in ne?" K'irjin Abhie dake wani irin zafi ya taune harshe yana kallon k'asa saboda idan Baffa da yake ji a kansa. Kafin Almu yace wani abu likita ya fito yana cewa su biyoshi office. Abhie, Baffa da Ammi sai Hajjo ne suka shiga. Saida bayan sun zauna yace "Sakamakon bincike da mukayi ya tabbatar mana da yarinya na d'auke da juna biyu wata d'aya da sati biyu. Ya kamata a dinga kula da Lafiyarta ita da abunda ke cikinta. Saboda early stage na pregnancy babu abunda bazai iya haddasawa ba. A daina bari tana yawan shiga damuwa saboda mun fuskanci tana cikin depression hakan kuma had'ari ne sosai a gareta dan zai iya janyo wa cikin jkinta ya zube. A dinga bata cika mai kyau saboda lfyr ta da kuma abinda ke cikinta." Wani irin shuuu sukaji gaba d'ayan su kafin suji Tim Ammi ta zube k'asa a sume. Jikin Hajjo na wani irin rawa tace "Likita wacece take da cikin harna wata guda da sati biyu? Badai jikita ba ko? Yarinya da ko aure batayi ba yau d'innan ne za'a daura auren sai kuma y'ar matsala ta faru. Ka k'ara dubawa da kyau dai ko kayi kuskuren wajen sunan" Kai ya girgiza " A'a Hajiya. Ita dai wannan yarinya da aka kawo itace nake miki bayani ga file din nata ma ki duba " Kasa motsi Abhie ya yi sai Baffa ne karb'a jikinsa na rawa. Takardun sukayi ta zubewa yana d'aukowa saida ya yi haka har sau uku sannan ya iya riƙeta a hannun ya buɗe yana karanta report d'in a fili. Innalilllahi wa Inna'ilaihi raji'un. Hak'ika wata masiba da tashin hankali ta ratso cikin family nasu kuma babu ta yanda za'ayi su iya guje mata. Wani irin gunjin kuka Hajjo take taba salati da sallami. Shi kuwa Abhie kai ya sunkuyar hawaye na diga daga idansa. Innalilllahi wa Inna'ilaihi raji'un. Firgigit Ammi ta farka ta kaman wacce aka mintsila. A guje ta fice daga d'akin tana kuka sosai mai tab'a zuciya. Kai tsaye d'akin da aka kwantar da Aleeyna ta kusa inda ta tarar da duk yan uwan da dangi a ciki saboda farkawarta. Ratsu kawai tayi daidai Amnah da Bagira K'awar Aleeyna na k'ok'arin kamata ta zauna.babu zato ta rufeta da matsanancin duka tana wani irin kuka. A guje aka rike Ammi ana bata hak'uri cewa kawai take "Ku kyaleni na kasheta na huta da wannan bak'in ciki data jefamu. Ku kyale" Da kyar aka janye Ammi daha jikin tana kuka sosai. Baffa ya shigo yace kowa da kowa ya fita zaiyi magana da Aleeyna. Saboda yanda Baffa keda kwarjini babu wanda ya musu duk suka fice suka barshi da ita. Wani irin kuka take ta had'a kai da gwiwa abun gwanin tausayi. Numfashi ya fesar mai zafi ya zauna kan kujera yana fuskantar ta ya kira sunanta. "Aleeyna " Bata iya amsawa ba sai kai data d'ago ta kalleshi da idanuwan ta da sukayi jazur . "Ki gayamin tsakani da Allah. Waye ya yi miki ciki?, nasan tarbiyar ki Aleeyna nasan wacece ke. Tarbiyar gidanmu abun alfahari ne a garemu nasan cewa hakan kawai bazaki bari wannan tarbiyar ta lalace ba. Ki gayamin wayene ya lalata miki rayuwa ?.waye sanadin da yaja tarbiyar wannan ahali take k'ok'arin wargajewa?" Dumdumdum. K'irjin Aleeyna ya wani iri bugawa da saida Baffa yaji. Suman zaune tayi ta kafe Baffan da ido kaman wadda ke ganin kai hud'u a tare dashi. Ita ce take da ciki? Mafarki take ko me? Taya zatayi ciki ita da bata tab'a sanin wani namiji ba? Ko wancan ranan ma tana al'ada kuma bai keta mata haddiba. Innalilllahi wa Inna'ilaihi raji'un. Luu ta koma ta k'ara zubewa a sume. End of free page. Chakwakwayi da gwaramar yanzu ta fara. Yar uwa kar ki sake ayi wannan tafiyar babu ke. GUDUNA AKE it just @ 500N. A turo payment wannan account number 👇 3078293347 Aisha sani danjuma First Bank. A turo shedar biya wannan number. 08140754777. Sai na jiki masoya Ashantylove na kwarai. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels