Showing 1 words to 3000 words out of 5998 words

Chapter 1 - Addini Na Complete Hausa Novel

12 Jul 2025

634

*ADDINI NA*
*KAINUWA WRITER'S ASSOCIATION*
*BY MARYAM ISMAIL*

*NOTE* *labarine ba wanda aka saba yiba, akan addininmu da yadda ake hukunci da alqur'ani da sadaukarwa zai taba zuciyar duk wani mai imani, don Allah ba mace ba namiji ina rokon kowa ya karanta inka karanta ka turawa wasu inaso ya bide duk social media da kukasan ana kai novels cos amfaninmu ne ku daure ku fahimci labarin*.

*Ban yarda wani ko wata ta juyamin labari ba ko ta dauki wani abuba ko a siyarmin da labari ba tare da izinina ba*
09030953294.
*TRUE LIFE STORY*

*YA ALLAH INA ROKONKA KA BANI DAMAR ISAR DA SAKON DA NAYI NIYA, KA SAMIN ALBARKA A CIKIN WANNAN RUBUTUN NAWA KASA YA ZAGAYE KO INA, KUMA MU AMFANA DA DUK ABUNDA KE CIKI, NA FARA DA SUNANKA BISMILLAHI RAHMANUR RAHIM*

*SADAUKARWA GA DUK KOTUN DUNIYA MAI HUKUNCI DA ALQUR'ANI DA HADITH YADDA SHARI'A TA TANADA*

1

Bakajin komai sai ihunsu da suke magana da caca a wurin ga kwalaben giya a warwatse ga mataye da keta yawo da shigar banza duk wani rashin da'a da laifi marar kyau na hangosu a wurin wasu zina ce sukeyi wasu karta wasu shan abubuwan maye, wani babban mutum na hango wanda shekarunsa ba zasu gazawa 40 ba jin an kirasa da suna *JABEER* yasa na gane shine sunansa daka gansa kaga usulin bafillace kyakyawa da Shi saidai duk bakinsa yayi bakikirin saboda shayeshaye kwalbar giyarsa ya daga yana kwankwada yake magana cikin maye"akwai dan iskan daya isa yace bani na cinye kartar nan ba? ".

Dariya suka kwashe da ita suna fadin"waya isa yaja dakai, makiyanka takalminka duk wanda yaja dakai to tabbas wahalarsa da rashin sa'arsane suka tsaya".

Shima dariya yayi sosai yaja wata budurwa dake gefansa ya rungumeta yayi cikin wani daki da ita.


Kyalanta ta dauka tare da yanawa saman doguwar rigar tata baka ta koma balarabiyar tata Jakarta ta saba ta dafa wata kyakyawar yarinya da bazata wuce shekara 10 ba tace" *Khadija* ki tsare gida bazan dadeba zan dawo kinji"

Ko kadan khadija bata damuba tunda dama bashine karona farkoba da iyayen nata ke barinta a gidaba, saidai ta kalli masu aekin gidansu ga dukiya iya dukiya saidai ko kadan bata samun kulawa ko tarbiyya gatadai musulma gaba da baya. Cikin rashin ko inkula tace"saikin dawo Ummi".

Dariya *AYSHA* tayi ta shafa kan y'ar tata ta fita tare da yiwa mota dinta key tayi gaba.

Khadija kam daki ta shiga ta soma kallo babu abunda ke damuwarta don shine kawai abun yinta a rayuwarta sai'in ta takaici idon mai gadi tayi gaba abunta.


Masu aekin gidan kam abincin sukayi suka jera a dianing suka koma part dinsu basu kuma fitowa sai girkin dare.

Aysha na isa kofar wani tankameman gidan karuwai tayi burki ta shige abunta kirari suke mata sosai sannan ta fada bisa wani katon nata da ake Kira ALHAJI, sosai suke soyewa tare dashan kwayoyi da giya.


Wannan shine rayuwar ma'aurata biyu *JABEER da AYSHA*

Sai kusan 11 na dare sannan Jabir ya kunno motarsa cikin gidan fitowa yayi yana tangadi ga wata kwalbar wine a hannunsa, bankado kofar yayi ya shigo tare da fuduwa, Khadija dake zaune da sauri ta mike ta tallafo Abi din nata tana masa sannu ko kadan bata kyamatar rayuwar iyayen nata gani takeyi shine abu mai kyau da kowa ke aekatawa, shafa kanta kawai yayi ya mike yakai kansa daki da kyar itama ta wuce dakinta tabi lafiyar gado, sai lokacin Aysha ta shigo gidan, dakinsu ta shiga itama bata jiraba ta watsa ruwa kawai ta kwanta gefan Jabeer tuni bacci yayi awan gaba dasu.

Kullun haka suke rayuwa, sai lokaci lokaci Khadija ke zuwa makarantar boko ba laifi ta iya fannin boko amma bangaren ADDINI ko oho don batama tabajin kalma irin Wannan ba, a kwana a tashi har tayi weac da neko, ta zama budurwa mai cikar zati shekarunta 17 a duniya, tuni Khadija ta kware fannin shaye shaye naduk ko wacce irin kwaya kuka sani cikin duniya, saidai ko kadan bata taba aekata zinaba amma ko yaushe tana like da maza zasu zauna kamar yacce zata zauna da y'ar uwarta mace, tana kazamar rayuwa zina da lesbian kawai ke bata aekatawa a cewarta bata taba ganin iyayenta sunyi Wannan ba saidai tana ganin ana rungumarsu da kuma shayeshayen da sukeyi.

Zaune take tsakiyar Abbas da Aliyu a club dare yayi rabi shaye shaye sukeyi ba kama hannun yaro, kallon Sadeeq tayi daya dora hannunsa saman breast dinta, tsuke fuska tayi tace a yanayin maye"kai baka ganewa ne, bance karka kuma tabamun jikiba, ka kiyayeni"ta karashe maganar tare da figan bag dinta tayiwa motanta key duki take ta ganganci ikon Allah ne kawai ya kaita gida ko kula iyayenta dake parlor batayiba ta shige dakinta a kasa ta fadi ta soma baccin asara.


*Don girman Allah in yazo wurinka ka tura zuwa wasu groups din don kowa ya amfana*

Emmm Iyyyy



*ADDINI NA*


*KAINUWA WRITER'S ASSOCIATION*
*BY MARYAM ISMAIL*

*DON GIRMAN ALLAH NA ROKA INKA KARANTA KA TURA WASU GROUPS, KO WANI SOCIAL MEDIA DA SAKON ZAI ISA*
*TRUE LIFE STORY*
2
Rai bace Nura ya dubi Sadiq yace"kanada matsala friend kasan me Khadija ke aekatawa so nawa kasan batasan zina ba, kai kuma kaki ganewa ya kamata inma kudiri gareka kabita a hankali"

Murmushi Abbas yayi yace"ya zaka bashi shawara akan abunda kasan tamkar budewar rigima ne a tsakanin abokananmu tun yarinta zako kusa ta tabu damu"

"Saime to"Sadiq ya fada.

Buga table din gabansu yayi yace "haba waime ya shiga kanku ne, ko kun manta tunda na kawo Khadija cikinmu na baku labarin rayuwarta da asalinta meye na batawa kanku lokaci, kadaiyi da wata but ka fita harkan Khadija cos nasan me zata iya aekatawa"Aliyu ya fada da nufin shawara.

Tsaki Sadiq yaja yace"nuna mana kaika kawota to Dan iska kawai".

Dariya suka kwashe da ita tare da rungume juna su duka hudun, Abbas, Aliyu, Nura, Sadiq, abotarsu babu abunda ke batata ko bacci baya rabasu gidansu daya suna matukar son junansu rawa suka ci gaba dayi da shaye shayensu a bige suka koma gida.

Next day

Fitowa tayi parlon sanye take da jeans black iyakarsa rabin cinyarta blue rigace mai hannun vest jikinta ko cibinta bata rufeba ga hills a kafanta gashin kanta sake yake a bayanta, zama tayi tana kurbar copee tare da tsare wadanda ta iske a parlor ALHAJI ne UMMINTA yana rungume da ita sai holewarsu suke, ajiye mug din hannunta tayi ta figi jakanta da key din mota tayi gaba ta fice zuciyarta cike da farinciki don bata ganin abunda Umminta ke aekatawa a matsayin laifi.

Tsayawa tayi da mota ganin wurin da cinkoso da sauri ta karasa inda akayi accident din kama matar tayi aka sakata mota, mutan wurin kowa daka gansa kaga cikkun larabawa donko shigarsu ta nuna.
Wasu matane ke gulmarta daya tace"asara daya ko biyu yar larabawa amma a haka"
Daya tace "karkuga laifinta waye besan JABEER da AYSHA ba dukiyarsu ta hana a hukuntasu da ADDININsu wanda kunsan hukuncin jiya ya wajaba a kansu amma yanzu shara'ar kudi da son rai akeyi ina za'aga daidai"

Itako batasan sunayi ba tayiwa motarta key kai tsaye gidansu Aliyu ta nufa cos duk yawanta daga club sai nan, sai in kuma su suka jata yawo.

Tana shiga a parlor ta samesu saida ta rungumi kowa alamar gaesuwa harda Sadiq cos ita bata da riko al-adarta kenan ci gaba sukayi da holewarsu hankali kwance gata a tsakiyarsu.


*Don Allah inka karanta ka turawa wasu, so nike sakon ya isa ko ina*

Emm Iyy luv


*ADDINI NA*


*KAINUWA WRITER'S ASSOCIATION*
*BY MARYAM ISMAIL*

*DON GIRMAN ALLAH INKA KARANTA KA TURA A WASU GROUPS DA FACEBOOK DA SAURAN YANAR GIZO*.
*TRUE LIFE STORY*
3
Sai yamma likis ta fito a gidan, gidan da tasan Abi dinta na zama ta isa a kofar gidan tayi parking ta fito tare da kutsa kai a ciki, har inda yake ta isa zama tayi tare da jawo sigari a aljihunta ta kunna mata wuta, shafa kanta yayi yace"y'ar baba daga ina? "

"Gidansu Aliyu Abi na"ta fada a takaice.
Murmushi yayi tare da mikewa yace "inkin gama ki kirani saimu wuce gida"yana zuwa nan yayi gaba abunsa.

Yayinda aka zagayeta suka sona karta da mutanen dake wurin.
Sai bayan isha suka koma gida, a lokaci Aysha ta dade da ficewa a gidan.
Abinci sukaci mai rai da lafiya sannan kowa ya kama gabansa ya nufi part dinsa.

Yaukam Jabir beyi bacciba har Aysha ta dawo, tana shigowa ta rungumesa tare da masa Sannu da gida.

Fuska sake yake ansawa cike dajin dadin ganinta suka rungume juna suka fada bed tuni labari ya canza bako addu'a ya shigeta, sai wurin Asuba suka farka wanka sukayi tare da shaye shayensy suka kumabin lafiyar gado.

Yau ta tashi batajin y'an fita shiryawa tayi cikin black dogon riga ta daura kyalen tayi masifar kyau ta fito asalin balarabiyarta sai zuba kanshi take, tasa masu aekinsu da suyi mata girki zatayi baki, hakan ba bako bane a wurinsu cos bayau su Abbas suka fara zuwa gidanba don saidai ma su kirasu yan gida.

Tana tsakiyar mahaifan nata sunata FIra cos a duniya babu abunda sukeso sama da Khadija basason takura mata ko bacin ranta.

Kai tsaye suka shigo parlon tare da fadin"hyy guys"

Da ihun murna ta tashi tana tarbarsu suna kashewa da juna, sannan iyayen nata suka tarbesu daga nan kuma ko wannensu ya ficewarsa wurin harkarsa.

Disko suka kure sunacin abinci da shaye shayensu ga rawa sunayi ba jimawa bacci keson daukarsu kai tsaye dakin Khadija suka nufa suka fada a bed su duka biyar din suka soma baccin asara.

Sai dare suka farka daga nan sukayi club don suna tunanin anan zasu kwana.

Sosai Sadiq yake wahala da sha'awar Khadija tare dashi abun duniya dukya damesa ya kudurtawa ransa dole a gobe ya kauda sha'awarsa kota halin yaya, da Wannan tunanin ya ware sukaci gaba da sha'anin rayuwarsu.

*Don Allah duk wanda ya karanta ya turamin zuwa wani groups*

Emm Iyy luv


*ADDINI NA*


*KAINUWA WRITES ASSOCIATION*
*BY MARYAM ISMAIL*

*NA ROKA INKA KARANTA KA TURA ZUWA WASU GROUPS*
*TRUE LIFE STORY*
4
Bayan wasu lokaci abubuwa da dama sun faru kuma babu wanda ya sauya da'b'i'unsa daga yadda yake saima abunda yayi gaba musamman daga bangaran iyayen Khadija.

Da sauri ta fito rike da bag yaukam sanye take da bakar jallabiya ta yane kanta da veil black sai zuba kamshi take ta fito asalin balarabiyarta kallonta iyayen nata sukayi Aysha tace"ya naga kina sauri haka ina zuwa kuma".

"Ae kema kinsan kwanan zancen"JABEER ya fada.

Murmushi Khadija tayi tace"iyakata wurinsu Abbas Ummi".

Sai kin dawo suka mata ta fito suna dagawa juna hannu sannan tayiwa motarta key ta cillata kan titi hankali kwance take tukin harta iso club inda tasan zataga su Aliyu da murmushi ta karasa suka kashe da juna suka fara fira.


Ma'aekatan wurinne suka kawo masu wine din da sukasan sunasha cup biyar aka zuba kowa ya dauki nasa, sabanin Khadija da tace"no i'm ok", mikewa kawai tayi ta shiga fili ta fara taka rawa da wakar dake tashi, saida su Nura suka bugu sosai sannan ta turasu mota ta wuce gidansu dasu ita ke driving.

A parlor suka zube sunata faman surutai, mikewa tayi ta nufi kitchen.
Da ido Sadeeq ya bita kaman tsohwan maye tana lashe baki yace"wallahi yau sainayi zina da Khadija ".

"Kar kayi kuskuran aekata haka"Abbas ya fada.

"Kusa ido ku kallah, naga yadda wannan wasan zai kasance"cewar Aliyu.

Rike take da fruits a plate sai small knife dake gefe zama tayi ta soma yankar Apple din dake ciki.

Zunbur Sadiq ya mike ya soma kamata da kokowa tana shirin barka mata riga yana fadin"yau saina cinma burina gwarama ki bada kai donko babu mai karbarki".

Sosai suke kokowa candai Allah ya bata sa'ar mikewa rai a matukar bace tana huci bata ko ganin gabanta sai huci takeyi yayinda zuciyarta ke azazzalarta wukar hannunta ta daga ta lumata tsakiyar cikin Sadiq tajata zuwa kasan cibinsa sannan ta zaro ta kuma dab'a masa saida ta barka cikinsa sosai, take jini yayi tsartuwa ya soma malala a wurin dukta baci da jinin a hassale take fadin"waye kuma cikinku zaiyi kuskuren aekata haka gareni"lokaci daya kuka yaci karfinta ta fashe da ihu ta duke a wurin tana kuka wiwi me tsima zuciya jikinta sai kyarma yake.

Kallon juna su Nura suka somayi a matukar tsorace sukayi waje da gudu kowa yayi ta kansa, yan sandar dake unguwar suka nuna rashin yarda suka damkesu, anan suka fadi abunda ya faru, rufesu akayi aka tada mota suka isa gidan da abun ya faru.

Yansanda ne suka zagaye gidan sannan wasu suka shiga, gidan nanan yarda yake ga gawar Sadiq a kwance jini dukya malale parlon haka zalika Khadija tananan inda take ko motsawa batayiba hawaye kawai take.
Mikewa tayi ta mika hannuwanta da suka baci da jini ga wukar a hannunta da tissue suka karbi wukar hannuwanta ta mika aka daura mata onka suka sakata gaba har cikin motarsu sukayi police station yayinda akayi asibiti da gawar Sadiq.

Ganin an kulle su Nura hankalinta ya tashi tambayoyi sukayi mata ta bada statement ta kuma kara da cewa"babu ruwansu basu aekata komai ba, nina kashesa da hannuna babu taimakon kowa"

Gamsuwa sukayi da bayaninta don haka aka saki su Nura yayinda aka kulleta cikin cell.


Allah ka gafartawa iyayenmu kayi mana kyakyawan karshe👏🏻

Emm Iyy luv



*ADDINI NA*


*KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*
*BY MARYAM ISMAIL*

*IDAN KA KARANTA DON ALLAH KA TURA MIN ZUWA WASSU GROUPS*
*TRUE LIFE STORY*
5
Kai tsaye gidansu Khadija suka nufa cike da tsoran abunda zaije ya dawo ko wannensu zuciyarsa cike da tunani iri iri da kuma mumunan tashin hankali a tare dasu sunyi sa'a iyayen nata na gida, cike da fara'a suka tarbesu yayinda su kuma suke dardar da sanar dasu abunda ke faruwa. Candai Abbas ya nisa tare da fad'a masu abunda ya faru da y'ar tasu.

Cikin tashin hankali JABEER ya shake wuyan Abbas yana fadin"karya kuke y'ata ba zata iya kashe mutum ba"ganin be cikin hayyacinsa yasa suka kwaci Abbas da kyar.

Kuka AYSHA ta rushe dashi tana fadin"har lokacin fada gareka bayan kaji ance tana rufe"kukane yaci karfinta ba shiri sukayo waje ikon Allah ne kawai ya kaisu station din, sun dimauce sosai dajin case din kuma wai Khadija ta ansa laifinta, kuma babu belinta da kyar aka basu damar ganinta.

Khadija na ganin iyayen nata ta fada jikinsu tana kuka.

Cikin kuka AYSHA tace"haba Khadija koda kinyi laifi meyasa kika ansa kinsan cewa babu abunda zai hanaki zama gidan kaso tunda kika ansa laifinki".

"Ummi na bansan ya zanyi ba zuciyata ce tasa na kashe Sadiq kuma ita tasa na ansa laifina nidai kawai bansan karyaba Ummi na".

Kallonta JABEER yayi yace"aeko kinyi kuskure Khadija na ansa laifinki".

Yar sanda macace tazo tace"lokacinku ya kare"bata jira cewarsu ba ta janye Khadija daga jikin Aysha kuka kawai suke sunaji suna gani aka kuma kulleta kuma sunce gobe za'a kaita kotu.

A ranar basuyi bacciba banda barin dukiya babu abunda sukeyi na ganin an kashe case din amma abun yaci tura dole sukayi hakuri.

Washe gari tunda safe suka nufi babbar kotun da za'akai Khadija kan kiceme kotun ta cika da D'an Adam kasancewar tuni yan jarida da gidajen TV sun yada al-amarin kotun ta cika makil, motar yan sandace ta kutso kai wurin saida aka tare mutane dayan jarida sannan aka samu damar fiddo Khadija, fuskarta tayi jajir idanuwanta sun kunbura dukta fada ta fita a hayyacinta kuma har lokacin yanzu hawaye basu kafeba da zubowa a kyakyawar fuskartaba, tana dago ido ta hada ido da mahaifan nata ga abokanayenta a gefe suma a rude musamman Aliyu da yafi kowa shakuwa da ita, tusata gaba sukayi har cikin kotun ta tsaya cikin akwatin da ake tuhumar mai laifi.

Alkali ya shigo take kowa ya mike don girmamasa, anan ya bada izinin zama sannan aka karanto shari'ar su Khadija, sannan aka mika masa.
Karba yayi tare da dubawa ya dago fuskarsa sanye da farin gilashi yace"Khadija Jabir kina da lawyer? "

"A'a bani da lawyer".
"To kinji laifin da ake tuhumarki dashi na kashe abokinki me zakice akan haka".

Dukar da kanta tayi ta share hawayen dake zuba tace"na aekata da wannan hannun na kashesa, ina rokon kotu data yankeman hukunci".

Y'an rubuce rubuce yayi sannan ya dago yace "kotu ta yankewa Khadija shekara 5 gidan yari zata iya daukaka kara bayan shekara 1"yana zuwa nan ya buga tebur alamun ya tashi, take kowa ya mike, kamo Khadija akayi yayinda yanzu take murmushi wanda yafi kuka ciwo, Aysha ko kuka take iya karfinta Jabir na rike da ita, sunaji suna gani aka tafi da ita, suma a dole suka tafi gida.

Uniform aka bata aka shiga da ita cikin gidan na mata daki aka sakata aka rufe, su biyune a dakin.
(Kunsan su sunada wuri me kyau ba kamar Nigeria ba, kuma suna hukunci kodan waye yayi laifi).

Kuka ta saki ta rakube gefe kanta na mugun sara mata.


A page na gaba zamu tashi a rayuwarta na gidan yari.


Allah ka gafartawa iyayenmu kayi mana kyakyawan karshe👏🏻

Emm Iyy luv



*ADDINI NA*


*KAINUWA WRITES ASSOCIATION*
*BY MARYAM ISMAIL*

*DON ALLAH INKA KARANTA KA TURA WASU GROUPS*
*TRUE LIFE STORY*
6
*RAYUWAR KHADIJA A GIDAN YARI* 😭😭😭

*Abun lura da takaici na rayuwarta*.


Yanzu kam ta ware ta rage kuka da damuwa iyayenta na ziyartarta da abokanayenta ta rungumi kaddararta da hannu bibiyu, abunda ke daure mata kai kullun zataga su Asiya suna wani abu da bata sansaba (dakinsu daya da asiya).

Yau kusan watanta ukku Amma kullun sai sunyi abun ba laifi suna shiri da Asiya don haka yau ta yanke shawarar tambayarta, kallonsu take daga daki ta sako kanta ta karafa tana lekensu har suka isa inda sukeyin sallah.


Bayan sun gama cin abinci ne tace "nikam Asiya inaso na tambayeki".

Duka ta tattaro hankalinta ga Khadija tace"ina jinki".

Numfasawa tayi tace"Asiya meye sunan abunda kukeyi kullun so biyar kuma kuje can kuita dukawa".

Sake da baki Asiya ke kallon Khadija da matukar mamaki tace"kai Khadija banason wasa, wannan wacce irin tambayace kina cikakkiyar musulma".

Sosai Khadija ta natsu tace"nasan abu daya Asiya ana kirana musulma kuma ina ansawa amma bansan me yake nufiba balle

1
2

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login