Showing 144001 words to 147000 words out of 163149 words

Chapter 49 - ABINDA AKE GUDU COMPLETE

13 Jul 2025

3563

ya tura qofar daya daga cikin dakunan da ya gani a bude wanda hakan ya tabbatar masa a ciki maryam din take


''assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatu''ya shiga da sallama wanda hakan ba qaramin rage mata fargaba yayi ba,gefan kujerar dakin take zaune,kanta na duqe lullube da alkhyabbar jikinta,tsayawa yayi cak kana ya kingina da bangon dakin yana qare mata kallo duk da bai ganin fuskarta,ya kashe a qalla mintina biyar a haka zuciyarta na bugawa a hankali kanta na a qasa,ta tabbatar har yanzu yana cikin dakin saboda qamshin turaransa da ya cakude da nata ya lullube dakin,haka nan ya sake haifarwa da dakin wani irin ni'imtaccen yanayi,sannu a hankali ya dinga takowa gareta bayan ya ajjiye kayan hannunshi duka saman dan qaramin table na glass dake a gaban gadon,ya isa gabanta ya zube duka kan gwiwoyinshi,hannayenta ya kama ya sanya cikin nasa yana qarewa qunshinta kallo,tamkar yasa harshensa ya lashe haka yaji,sai da ya more kallonsa sannan ya dora kansa saman cinyanta yana leqen fuskarta,bai ga fuskar sosai ba sakamakon hular alkyabbar ta sanya ta yin duhu,a hankali ya sanya hannunshi ya janye hular take fuskarta ta bayyana saidai idon nata a rufe dai yake


Cikin wata sassanyar murya da bata zaton yana da ita ba taji yace''zan rayu dake zan mutu da ke *ABADAN* dani dake zauna''murmushi ya subuce mata don bata taba jin waqa a bakinsa ba sai a wanan karon,sai taji tafi dadi a bakinsa ma fiye da mawaqin,a hankali ta dago brown oily eyes dinta ta zuba masa,dama abinda yakeson gani kenan,shima murmushin ya sakar mata wanda saura kadan ya narka mata zuciya,ajiyar zuciya ya saki ya lumshe sexy eyes dinshi kadan sannan ya sake budesu''ya Allah ka gafartawa mami na,kayi mata albarka data sauqaqamin hanyar samunki,ta shiga lamarina'' kana ya daga girarsa
''yes....zan rayu da ke har *ABADA* maryam,haka kuma nake fatan koda mutuwa tazo min ta daukemu tare....''


Sake maida kansa yayi yi ya kwanta a cinyarta
''soyayya gaskiya ce baby,haqiqa,babu abinda ya kai so dadi,so shine abu mafi girma dake iya sarrafa zuciya kota wanene,haqiqa so ba ruwanshi da kyau nasaba ko cancanta mulki ko wata dukiya,yakan kama mutum ne kansa tsaye ba tare da qwaqwasa qofa ko neman izini ba,maryam kici gaba da zama tawa ni kadai har *abadan* don Allah''idanunta a runtse suke ya riga da ya gama kashe mata jiki baki daya a hankali ta dora hannunta saman sumarsa
''ni taka ce abdallah,takace ni,ina ji a jikina saboda kai aka halicceni,kaga kuwa har *abada* maryam ta abdallah ce,to ta yaya jiki zai iya rayuwa babu daya barin nasa?,ta yaya zuciya zata iya rayuwa da tsagi guda ba tare da daya tsagin ba?,ka zama ni na zama kai *mutu ka raba*'',qanqameta yayi kamar za'a qwace masa ita yana mata godiya tare da sheqar daddadan qamshinta dake barazanar juya akalar tunaninsa


A hankali ya dinga rage mata kayan jikinta tana zaune don ba musua tsakaninsu,a yadda taga mayen sonta cikin idanun abdallah zatayi matuqar qonashi a wanann lokaci idan tayi masa musu,da undeies kadai ya barta kana ya shige bandaki yayi nashi wankan ya fito bayan ya hada mata ruwan,kafin ta fito har ya zura kayan baccinsa ya saka 'yar hularnan tashi ka fiya naci fara ya nutsu saman abun salla,gefe taga nata kayan bacci,sai da ta qare musu kallo tanayi tana satar kallon abdallah dake salla,babu yadda zatayi haka ta juya ta sanyosu,gaba daya bata da maraba da babu dadinta daya akwai babban hijabi dogo a gun shita zura ta koma gefan gadon ta zauna,yayi sallama kana ya mata izini ta taso suyi sallah,raka'a biyu suka gabatar,addu'a mai tsaho suka yi ta neman alkhairai da samun zaman lafiya da haduwar kai a tsakaninsu sannan ya waiwayo ya kama kanta ya karanto addu'ar da annabin rahama ya koyar da mu
'' *Allahumma inni as'aluka khairaha wa khaira ma jabaltaha alaihi,wa a uzu bika min sharriha wa sharri ma jabaltaha alaihi*'',da salatin annabi ya rufe musu suka shafe tare


idanunsa cikin nata wanda a yanzu fargabarta ke dada yawa,girarsa ya daga yana murmushi
''wai duka tsoron nan na meye ne?''cikin nuna dakiya ta noqe kafada
''wanne tsoro?''
''gashinan ina ganinshi cikin idanunki?,kada kice a'a maryam,ina iya karanta abinda ke zuciyarki kai tsaye ta cikin idanunki,ko kin mance zuciyarmu guda ce?''
murmushi tayi cikin son nuna dakiya da jarumta amma sai ta sake ce masa
''ni tsoron me zanji''
tafa hannunshi yayi sau uku yace
''good girl,naji dadin samunki jaruma,kinsan kuwa irinki,nake so saboda irinkin ne kawai zasu iya jurata,ko da yake....nafa gasgata zancanki,kefa kince yadda kike kallon mace yar uwarki haka kike kallon *abdallah* kinga kenan ya kamata yau mu gane hakan ne ko ba hakan ba,uhmmm....are u ready?''
ta tuna sanda ta gaya mishi hakan cikin jirgi,take sai idanu suka raina fata,qwalla ta tarar mata,tana tsoron kada ya mata mugunta fa,cikin shagwababbiyar murya irinta me sonyin kuka tace
''kaima ba ka tsokane ni bane a lokacin?''dariya ya mata
''wasa nake miki matsoraciya,kwantar da hankalinki,babu abinda abdallah zai miki kinji,bacci zamuyi dukkan mu a gajiye muke,koke baki gaji ba ayi miki?''wata iriyar kunya ta dirar mata sai ta cure guru guda ta cusa kanta tsakanin cinyoyinta tana dariya qasa qasa,waishi abdallah wanne irin dan kai tsaye ne?''na gaji,na fika ma gajiya''kai yake gyadawa yana sake gano yarinta quruciya da rashin wayonta
''to kin gani,so ki saki jikinki kinji,ni yayanki ne ko?''da sauri ta gyada kai kuma taji nutsuwa ta saukar mata,umartarta yayi ta samo musu plate da cups a kitchen


da hijabin jikinta ta miqe har ta soma tafiya ya kirata ta dawo,hannu ya miqa mata kana yace
''ciro min hijabina dama aro na baki ai''
sai ta dan zare ido
''amma fa jikina...''
ya katseta ta hanyar dora yatsanshi kan lips dinshi yace
''shshshsh,i know....haka nakeson ganinki,kin mance ba musu?,idan kika qi kuma to yau....''bata ma barshi ya qarasa ba ta zareshi ta miqa masa ya amsa idonsa akanta a haka ta fice zuwa kitchen din ya mata rakiyar idanu


wayon da ya mata yasa ta dan saki jikinta kadan taci naman da dan drinks,sai da ya tabbatar ta kwanta yaja mata bargo har zuwa kafadunta kana ya sunkuya ya sumbaci goshinta
''kiyi bacci baby,kina tare da ni''a hankali ta gyada kanta kana ta lumshe idanunta,shi ya tattara kayan da sukayi amfani da shi duka ya fidda zuwa kitchen


A qalla mintina talatin yayi kafin dawowarsa dakin,ya shigo ya rufe qofar da bismillah sannan ya isa ga makunnin qwan dakin ya maida hasken zuwa kala mai duhuwa ta bacci,tun dazun idonta biyu tadai rufe idin ne kawai amma fargaba ce fal ranta,tana jinsa ya gama tofa addu'ar bacci ya shafe jikinsa da ita,ya karanta mata itama ya soma shafa mata
zarcewan da ya soma yi shi ya sanyata bude idanunta ta riqe hannayensa duka,cikin rawar murya tace
''kayi alqawari fa....''
''baby bazan iya cikawa ba kimin afuwa''ya bata amsa
''amma....''hade bakinsa yayi da nata wanda hakan ya hana mata damar qarasa abinda take ahirin fada din


Ya kusa minti goma bakinsa kan kunnenta yana gaya mata wasu kalamai da suja kashe mata jiki gaba daya shi kuma ya samu daman aika mata da saqonni kala daban daban masu dauke duk wani tsoro da fargaba,cikin shu'umancinsa ya mantar da ita duk wani tsoro da wata fargaba,sai da ya mata jagoraxa duniya ta daban wadda ko cikin mafarki bata taba shiga makamanciyarta ba sannan ya fito mata da muradinsa muraran,sai a lokacin ta gane lallai wayo abdallah kawai ya mata,kuma a lokacin ta raina duk wani wayo nata,koma mata yayi tamkar mahaukacin zaki da yunwa ta koroshi ya fito farautar abinci,ba qaramin tsorata tayi ba,ya koma mata gaba daya kurma bebe kuma makaho,bai sauraran komai sai abinda yasa a gaba,cikin zafin nama yake fidda zazzafar soyayyarta data jima danqare cikin zuciya da gangar jikinsa


Bai ankara da barnar da ya tafka ba sai bayan shudewar awanni kusan shida,kuka take sosai idanun nata sun gama zama gauta saboda ja,sosai suka kumbura kamar an hura su,duk yadda yaso ta tsaya tsaiwar ta gagareta,dole ya maidata ya kwantar,tausayinta ya ratsashi,ta ya akayi ya yiwa maryamunsa irin wannan barnar?,shi kansa bai sani ba baisan lokacin da ya aikata ba,kawai sai ya koma saman gadon ya fara qoqarin janta jikinsa,a tsorace take da shi sosai saboda haka runtse idonta tayi sosai ta qanqame jikinta guri guda duk da ciwon da jikinta yake mata,bata so ya ko taba ta,gani take tsabar mugunta ce yana sane ya mata hakan bayan ya mata alqawarin babu abinda zai mata,wanne irin roqo da magiya ne bata masa ba amma yayi banza da ita,shi kurma ne ko makaho ne?
sarai ua fuskanci batason ya taba ta ne shi kuma kukan nata ne bayaso,cikin matuqar sanyin jiki da na murya tamkar ba abdallahn mami ba yace
''ba wani abu zan kuma miki ba maryam,kiyi haquri ki kwanta jikina,baki ganin yadda jikinki ke rawa kina buqatar taimako na''


cikin muryar kuka tace
''ko mutuwa ma nayi ba kai ka jawo min ba,ina zaman zama ne ashe baka da imani,so kake na mutu''duk da hankalinsa,a tashe yake sai da taso bashi dariya,ta yaya wannan abun zai kasheta,idan da yana kisa ai da mata da yawa sun mutu kenan,ganin ta kafe kai da fata bazai taimaka mata ba ya sanyashi shareta,ya sanyata cikin jikinsa ta dolenta,babau qarfin qwatar kai hakan ya sanyata taci gabq dq kukanta tana cewa baya sonta dama,bashi da bakin magana illa
''am sorry,am verry sorry,kiyi bacci idan yaso gobe saikimin duk hukuncin da ya dace da ni abdallah zai karba saboda laifi yayi miki,shi kansa yasan ya cancanci hukunci''
tun yana jin surutanta har yaji dif,ya keqa fuskarta data hada ja yaga bacci ne yayi awan gaba da ita,ajiyar zuciya ya kuma sake ya sake maidata jikinsa,sam bacci qauracewa idonsa yayi,tausayi qauna da soyyarta ke addabarsa,a hankali yaji jikinta ya fara daukar zafi da alamun zazzabi ne yake kamata,addu'a ya dinga yi,cikin zuciyarsa Allah ya kawar da zazzabin nan kada abun ya yiwa diya nan yawa,kafin asuba kuwa jikinta yayi rigif da zafi,har wani huci yake fitarwa



Cikin baccinta ta jita aruwan zafi yana ratsata,da azama ta bude kumburarrun idanunta ta saki qara data bashi tausayi,duk yadda yaso sata ciki ruwan dumin taqi shima kuma ya kasa saboda baison kukan da take,ahi ya gama shiryata tsaf kana ya bata guri don ta tubure masa sai wani dakin ya canza ya bar mata wannan


Qarfe bakwai ya sake leqota sai ua sameta kwance kan abun sallah bacci ya dauketa,a hankali ya lallaba ya dauketa ya maidata kan gadon ya fara qoqarin rabata da hijabin jikinta saboda zafin zazzabin dake tashi a jikinta,garin haka ta bude idonta sai ta tabe fuska zata saki wani kukan,da sauri ya kwantar da ita yana daga hannayenshi sama
''ni fa babu abinda zan miki,hijabin da kika bari a jikinki qara miki zafin zazzabin yake''
kanta ta cusa cikin filo tana fadin
''nidai ka fita wallahi''
tsam ya miqe ya fice daga dakin yana waiwayenta,ta sa gefan hijabinta tana share hawayen da yaqi tsaiwa,itakam da tasan haka ake shan wuya da ta gudu wlh,ashe duk wayo abdallahn yake mata don yaga ya girmeta


Har qarfe goma na safe yana fama da ita,taqi yarda ko dakin ya shigo bare ta sha tea din da ya dafa mata,don ba girki ya iya ba,da zarar ya shigo dakin zata fashe masa da kuka,duk yabi ya susuce,ga ciwo da alama tana jinsa sossi,ya kira raaliya bai sameta ba tilas ya kira baaba uwani,a falo ta taddashi kwance kan doguwar kujera rigingine,da sauri ya miqe yana tambayar baaba uwanin
''gaskiya ranka ya dade kuje asibiti,ta gayamin tana jin ciwo,sosai hakanan ba zata iya shiga ruwan zafin ba''shiru yayi donshi ba wani asibiti da ya sani idan ba mallakin maminshi ba,don tun yana yaro acan ake bashi duk wata kulawa saidai idan abbanshi ne yace a fiddashi waje,yana kunya kuma yajewa mami da maryam a hakan,dabara ta fado masa don haka da sauri ya yiwa baaba uwani godiya yasa driver din gidansu ya maidata


Sai da ya hada girar sama da ta qasa sannan ya shiga dakin,tana kwance don bata isa ta zauna ba,ganin fuskarsa a haka yasa bata yi masa boren ba,don ta manta rabin da ta ga fuskarsa a hakan,gaban ma'ajiyar kayanta ya isa ya ciro mata atamfa da hijabi,ganin yana niyyae sa mata su ns yasa ta saki shagwababben kukan nata sai ya kauda kai yana jin ciwon kukan har cikin ranshi ya zube hannayensa cikin aljihun wandonsa
''ya isa,idan zaki iya ki sauya da kanki yanzu na baku minti goma''ya fada yana ficewa a dakin


Cikar mintina goma ya dawo dakin har ta sauya din kuwa saidai zanin da bai dauru ba,ya dagata ya gayara mata daurin zanin kana ya dauketa cak ya fice da ita,Allah yasa babu kowa a gidan don har security dinshi ya basu hutun sati guda,a motar ya sakata ya dan kwantar mata da kujerar sanann ya dawo ya rufe ko ina


Sunan asibitin kawai data gani yasa ta tuna cewa asibitinsu ne,idonta cike da qwalla ta dubeshi yana gyara parking na motarsa a inda taga manyan likitoci ke parking kawai a gun
''amma ya za'ayi ka kawoni gun mami abdallah baka jin kunyarta ne?''sai da ya daidaitata ya kashe kana ya jingina jikinsa da makarin kujerar ya dubeta
''ba gun mami zan kaiki ba nima ina jin kunya ai dear,akwai doctor farida ita zara ganki kin gane?''limshe idonta kawai tayi ta kwantar da shi ba tare da ta amsa masa ba,sai taji hannunsa kan fuskarsa yana share mata hawayen
''bansan ganin hawayen nan mana maryam,ki zama jaruma kinji matata,ni da nakeson shekara iwar haka na kawoki kina naquda''ai batasan sanda ta bude idonta ta watsa masa harara ba,ana fama a yanzu ma ba'a warke ba yana mata zancan naquda,shi don ba jikinsa bane wato,dariya ua qyalqyale da ita kamar yasan me take rayawa cikin zuciyarta,bai sake cewa komai ba ya ciro wayarsa ya kira reception na asibitin yace a turo masa nurse din da take on duty


Cikin minti uku kacal ta iso sanye da fararen uniforam,matashiya ce yar kimanin shekaru talatin mai yawan fara'a,ta gaida maryam ta amsa mata cikin fara'ar yaqe tana satar kallin abdallah,ranshi a hade kamar bashi ya gama qyaqyata mata dariya ba yanxun,tambayarta yake doctor farida tazo?
''eh naga office dinta a bude duk da banga wucewarta ba amma nurse halima naga ta fara shigar da files''
''mami na fa''
''office dinta gaskiya a rufe yake''ya gyada kai kana yace
''ok,inason ki bawa nurse halima din wannan ta kaiwa doctor faridan yanzu zan shigo na gantq ni da madam''a ladabce ta amsa kana ta juya ta shige,ratar minti biyar ya bada ya fito daga mazauninsa ya rufe motar kana ya zagaya bangarenta,daukarta yayi da gaske tana masa mitar ya ajjiyeta kada ya jawo musu yan kallo
''idan daukar da na miki bata jawo mana yan kallo ba sauke kin da zanyi ya jawo mana tunda kona ajjiyekin ba iya tafiya yadda ya kamata zakiyi ba''ta yarda haka dinne don haka tayi luf ajikinsa idonta aruntse duk kunya ta gama kamata



Bai damu da jama'ar dake reception din ba kansa tsaye ya wuce office na doctor farida da ita,bayan ya sauketa a bakin qofar office din ya kama hannunta,ya tura qofar kana yayi sallama,ya juya yana maida rufin qofar ta dago kanta daga laluben takardun da takeyi,mami ce zaune kan kujerar zaman likitan,zame hannunta maryam tayi tana fatan ina ma zata iya gudu babu shakka da fellawa zatayi
fes ta gane kunya ke damunsu tunda taga highlight na problem dinsu a short note din da ya bada a kawowa doctor farida, don haka sai tayi mirsisi kamar bata sansu ba ta musu nuni da gurin zama
''bismillah''abdallah yayo gaba yayin da maryam cikin lallaba takunta ta biyo bayansa,mami ta dan bita da kallo cikin tausayawa amma afuskarta ba zaka gani ba idan baka lura ba sosai,sai da tayi yan rubuce rubucenta kana ta dago da kanta ta gyara zaman glass dinta
''uhmmm,meke damun patiente din?''sai aka rasa mai magana tsawon mintina,dariya ta dinga cin mami kamar ta fito ta dara ganin yadda sukayi tsilli tsilli maryam harta fara sharan hawaye


Abdallah ya miqe yana fadin''ummm...ina zuwa,bari naje na dawo doctor ta miki bayani''sai ta kuma hade rai
''c'mon dawo mara haquri kawai ina zaka,dora min ita saman can''ta nuna mishi wani dan gado da take duba marasa lafiya kana ta dake kamar ba ita tayi maganar ba taci gaba da rubuce rubucenta gami da dauke kanta cikin zuciyarta tana tausayin maryam tare da dariyar abdallah,tunda suke bata taba ganin bala 'yar iyar kunyarta cikin idanunshi ba irin wannan karon,sai da ya dorata kana ya taho gefanta ya tsaya
''mami,na dorata''
''doctor ce ba mami ba''ta fada cikin shan kunu,sai ya dan shafi gefan fuskarsa kana yace
''sorry......doctor''
allurai ta hada pain killer harda wadda zata sata bacci na yan lokuta kafin ta gama dubata ,don ta san da kunya musamman maryam dake da bala'in kunya,bai yiwuwa ta dubata a sake kuwa alhalin idonta biyu




*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[5:58pm, 10/14/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

▶6⃣5⃣

*Daga abdullahi dan umar R.A.H.M yace:Manzan Allah S A W yace:((haqiqa mafi soyuwar sunaye acikin sunayenku a wajen Allah mai girma da daukaka sune ABDULLAHI DA ABDUR RAHMAN))*


✊🏽✊🏽✊🏽✊🏽✊🏽✊🏽✊🏽🙇🏽‍♀🙇🏽‍♀🙇🏽‍♀🙇🏽‍♀🙇🏽‍♀🙇🏽‍♀
💞💞💞💞💞💞💞

*cike da girmamawa mutuntawa da qauna tare da qasqantar da kai nake miqa wanna shafi a gareku*

*IBAADALLAH wato duk wani mai suna ABDALLAH*

_*musamman mahaifina,abin qaunata abin alfahari na,jigo na*_

*ALHJ ABDULLAHI MUSA HUGUMA*

*_haqiqa kai mahaifi ne daya tamkar da miliyan,mahaifine da samun kamarsa sai an tona,mahaifine daya da daya,mahaifi ne da babu kamarsa,Allah ya shige maka gaba,ya maka jagora cikin lamuranka,ya zama jinka ganinka,ya rabaka da sharrin mahassada magauta da maqiyanka,Allah ya cika maka burinka duniya da lahira,Allah qara maka lafiya da tsawon kwana mai amfani,ya cika rayuwarka da farinciki nutsuwa da kwanciyar hankali,yasa kayi kyakkyawan qarshe,babu shakka ka gama mana komai a rayuwa,addu'arka garemu na bin mu har kullum muna ganinta,Allah ya jiqan magabatanka ya maka jagoranci tare da dukkan nagartattun iyaye kamar KAI_*🙏🏽🙏🏽💖💘😍😘💝❣










Komawa tayi taci gaba da rubuce rubucenta kafin allurar tabi jikinta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login