Showing 12001 words to 15000 words out of 32024 words
taƙi kallonsa.
“Negar! bana son kukan banza fa. Ko kina son bugu ne?”.
Kafaɗa ta maƙe masa tana ƙara matso hawayen.
“Wani guri na miki ciwo ne?”.
Nan ma kafaɗar ta noƙe. Jimm yay yana kallonta, sai kuma ya sake faɗin,
“Mi kike so?”.
Yay maganar yana matso da ita sosai jikinsa ta sake duƙawa cike da lallashi, har tana ɗora hannunta saman cinyarsa bata farga ba.
Cikin rawar murya tace, “Ina jin tsoro”.
Wani irin motsawa zuciyarsa tayi, ya dai dake ya furta,
“Tsoro dai? Na miye?”.
Kuka ta sake fashe masa da shi taƙi magana. Sai kawai ya miƙe itama ya miƙar da ita ya sakata a jikinsa ya rungume. Daburcewa tai gaba ɗaya, dan abin yazo mata a bazata. Kodan jiya ba cikin hankalinta take ba duk bata san mita dinga masa ba da yanda shima yayta rungumeta.
“Kar kiji tsoro Kiddo. Matsoraci baya zama gwani. Kiyi addu'a, amma miyasa kike jin tsoro? Sun miki wani abu ne?”.
Kanta dake kwance a jikinsa ta girgiza.
Ɗagota yay ya zaunar a bakin gadon, ya matso kujerar sa kusa da ita sosai har jikinta na gogar nashi, dan ƙafafunta ma tsakiyar nashi ƙafafun daya ɗan wara suke. Idanunsa a kanta, hannayensa cikin nata ya ce, “Faɗa min tsoron mi kike ji?”.
Ta kasa danne abin, dan ya tsaya mata a rai matuƙa har zuciyarta da ƙwaƙwalwa sun kasa ɗauka kamar sauran abubuwan. Tana kuka sosai ta ce, “Dada sun ce an min aure. Da wani mutumi”.
Wani irin Bimmmb!! Yaji zuciyarsa ta bada sauti. Ya danne da ƙyar yace, “To shine abin kuka Kiddo. Dama duk mace dole tai aure ai ko?. Kuma kema ai kin girma.”
“Dada ni dai zan zauna wajen Mammah ta. Ban girma ba. Ba'aina Small Mom aure ba da su Uncle Billa sai ni”.
Murmushi yayi kaɗan a ransa yace (Kiddo ki illatani har duniya tasan halin da nake ciki kawai ki huta). A zahiri kam ɗan gyaran murya yay da faɗin, “A'a Kiddo, zama wajen Mammah kam na lokaci ne. Sai dai randa na aurar daku halan da Mammah zaki tafi?”.
Jin abinda ya faɗa ya sata kallonsa, ganin ita yake kallo tai saurin janye wa tana shagwaɓe fuska da faɗin, “Ni bazan yi auren ba fa kwata-kwata bana so Dada?”.
Idanunsa ya ɗan waro waje shima kamar yanda ta waro masa nata a furucin ƙarshe.
“Kice malam gari su fara addu'a, Kiddo bata san aure ai asirin Dada ya gama tonuwa”.
Kunya ce taji ta kamata a karo na farko, duk da dai dama dakewa kawai take tun ɗazun, dan maganar ta mata nauyi, amma tana son ta amayar ko zataji sauƙin nauyin da ƙirjinta yayi saboda girman ta a ranta. Tasa ɗayan hannuta ta rufe idannunta tana haɗiye ƙwallar da suka sake cika mata ido. Shima da yanayin ya fara masa tasiri sai ya gyara zama yana ɗan matsa hannunta da har yanzu ke riƙe a cikin nashi.
“Uhmmm faɗa min miyyasa. Kinga idan naji dalilin ki mai ƙarfi ne sai nima na yarda bazan miki auren ba. Kawai muyi zaman mu muna cin tuwon Mammah kullum”.
“Ai banda kai. Tunda kana da mata”.
Ɗan tsai yay yana kallonta cike da nazari. Sai kuma ya basar da faɗin, “Waya gaya miki?”.
“Na sani ai. Ba itace ta taɓa yankamu ba, ga tabon a cinya na ma. Ranar ma kuma ta dawo sunyi jere a part ɗinka itada masu kama da karuwan nan.” takai ƙarshen maganar tana yaye rigar jikinta cinyarta ta bayyana. Da sauri ya haɗiye yawun dake neman sarƙe shi, ya ɗan zubama tabon da ya zama dogo sosai idanunsa da suke rinewa, ga yanda fatar jikinta ke wani sheƙi da kwanciyar ɗaukar idanun mai kallo ya saka tsigar jikinsa tashi. Yanda yanayinsa ke canjawa yasa shi kai hannu da kansa yaja rigar ya maida mata.
Received at 10:47 AM
[14/02, 9:15 am] Abue Saleh: Cikin rashin damuwa ta gyara zama da faɗin, “Dada kaga nasan kana da mata ko?”.
A ransa yace (Wata sabuwa, wannan ficikar fa da wayonta) a zahiri kam sai ya basar ta hanyar faɗin, “Shike nan ke faɗa min miyyasa baƙya son kiyi?”.
“Saboda bana son na bar Mammah da su Uncle's, da Ruky. Da Daddy, da su Ammie. Nafi son muyita zaman mu a haka lullum-kullum muna jin daɗin mu, muna hira. Dada ƙarya suke ai ba'a min aure ba ko?”.
Ji yay kamar ya kwashe da dariya saboda yanda tai tambayar cikin marairaicewa, amma ya gimtse abarsa “Uhmm ƙila da gaske suke yi dai, amma miyasa baki tambaye su waye mijin ba to tun acan?”.
Baki ta sake turawa. “Wai sunce assignment ne naje na bincika kai ko Mammah zaku faɗa min”.
Maimakon ya bata amsar sai ya waske da faɗin, “To amma ai naga kina son yara sosai. Kuma sai anyi aure ake haifar yara ai ko, yaya zakiyi kenan?”.
Yanzu kam har cikin ranta ta ce, “Dada baga su Afrah ba. Kuma su Ammy suna ƙara haifo mana wasu, ai sun ishe mu mu duka.”
“Duk da haka kema zamu so ni da Mammah da Uncles ɗinki muga naki ai”.
“To kawai basai na haife su a haka ba?”.
“Babu auren?”.
Ya faɗa cikin ɗan waro idanu. Kawai sai abin ya bama Nimrah dariya, ta shiga ƙyalƙyalawa. Shi kuma ya shagala kawai yana kallonta. A ranta ko rayawa take (Dada fa kallon ƴar yaye yake min ko? Bari muje a hakan to). Sai da tai dariyarta sosai sannan ta jinjina masa kai. Kai tsaye ta ce, “Eh, ai ko bakai aure ba idan malamai suka maka addu'a sai kawai kaga ka samu Baby”.
Samun kansa yay da tsareta da idanu kawai. A ransa yace (Zakiga malamai kuwa yarinya, harda ma masu addu'ar saukar aljanu nan kusa kaɗan).........✍️
🤣🤣Zamu so ganin malam saukar aljanun nan kuwa Dada🥱🤭.
Received at 10:47
[14/02, 9:17 am] Abue Saleh: “Yaya jikin naki?”.
Sharrr hawayen da ita kanta bata san na miye ba suka zubo mata. A haka ta furta, “Na warke”.
Kallonta yay da mamaki. Ganin kuka fa take bil-haƙƙi abinta. Sai kawai yakai hannu ya shafa kwantaccen gashin fuskarsa. Itama dai-dai tana miƙewa zata bar wajen. Hannunta ya riƙo kawai ya dawo da ita, sai dai yanzu tana daga tsaye ne tana sharɓar hawaye taƙi kallonsa.
“Negar! bana son kukan banza fa. Ko kina son bugu ne?”.
Kafaɗa ta maƙe masa tana ƙara matso hawayen.
“Wani guri na miki ciwo ne?”.
Nan ma kafaɗar ta noƙe. Jimm yay yana kallonta, sai kuma ya sake faɗin,
“Mi kike so?”.
Yay maganar yana matso da ita sosai jikinsa ta sake duƙawa cike da lallashi, har tana ɗora hannunta saman cinyarsa bata farga ba.
Cikin rawar murya tace, “Ina jin tsoro”.
Wani irin motsawa zuciyarsa tayi, ya dai dake ya furta,
“Tsoro dai? Na miye?”.
Kuka ta sake fashe masa da shi taƙi magana. Sai kawai ya miƙe itama ya miƙar da ita ya sakata a jikinsa ya rungume. Daburcewa tai gaba ɗaya, dan abin yazo mata a bazata. Kodan jiya ba cikin hankalinta take ba duk bata san mita dinga masa ba da yanda shima yayta rungumeta.
“Kar kiji tsoro Kiddo. Matsoraci baya zama gwani. Kiyi addu'a, amma miyasa kike jin tsoro? Sun miki wani abu ne?”.
Kanta dake kwance a jikinsa ta girgiza.
Ɗagota yay ya zaunar a bakin gadon, ya matso kujerar sa kusa da ita sosai har jikinta na gogar nashi, dan ƙafafunta ma tsakiyar nashi ƙafafun daya ɗan wara suke. Idanunsa a kanta, hannayensa cikin nata ya ce, “Faɗa min tsoron mi kike ji?”.
Ta kasa danne abin, dan ya tsaya mata a rai matuƙa har zuciyarta da ƙwaƙwalwa sun kasa ɗauka kamar sauran abubuwan. Tana kuka sosai ta ce, “Dada sun ce an min aure. Da wani mutumi”.
Wani irin Bimmmb!! Yaji zuciyarsa ta bada sauti. Ya danne da ƙyar yace, “To shine abin kuka Kiddo. Dama duk mace dole tai aure ai ko?. Kuma kema ai kin girma.”
“Dada ni dai zan zauna wajen Mammah ta. Ban girma ba. Ba'aina Small Mom aure ba da su Uncle Billa sai ni”.
Murmushi yayi kaɗan a ransa yace (Kiddo ki illatani har duniya tasan halin da nake ciki kawai ki huta). A zahiri kam ɗan gyaran murya yay da faɗin, “A'a Kiddo, zama wajen Mammah kam na lokaci ne. Sai dai randa na aurar daku halan da Mammah zaki tafi?”.
Jin abinda ya faɗa ya sata kallonsa, ganin ita yake kallo tai saurin janye wa tana shagwaɓe fuska da faɗin, “Ni bazan yi auren ba fa kwata-kwata bana so Dada?”.
Idanunsa ya ɗan waro waje shima kamar yanda ta waro masa nata a furucin ƙarshe.
“Kice malam gari su fara addu'a, Kiddo bata san aure ai asirin Dada ya gama tonuwa”.
Kunya ce taji ta kamata a karo na farko, duk da dai dama dakewa kawai take tun ɗazun, dan maganar ta mata nauyi, amma tana son ta amayar ko zataji sauƙin nauyin da ƙirjinta yayi saboda girman ta a ranta. Tasa ɗayan hannuta ta rufe idannunta tana haɗiye ƙwallar da suka sake cika mata ido. Shima da yanayin ya fara masa tasiri sai ya gyara zama yana ɗan matsa hannunta da har yanzu ke riƙe a cikin nashi.
“Uhmmm faɗa min miyyasa. Kinga idan naji dalilin ki mai ƙarfi ne sai nima na yarda bazan miki auren ba. Kawai muyi zaman mu muna cin tuwon Mammah kullum”.
“Ai banda kai. Tunda kana da mata”.
Ɗan tsai yay yana kallonta cike da nazari. Sai kuma ya basar da faɗin, “Waya gaya miki?”.
“Na sani ai. Ba itace ta taɓa yankamu ba, ga tabon a cinya na ma. Ranar ma kuma ta dawo sunyi jere a part ɗinka itada masu kama da karuwan nan.” takai ƙarshen maganar tana yaye rigar jikinta cinyarta ta bayyana. Da sauri ya haɗiye yawun dake neman sarƙe shi, ya ɗan zubama tabon da ya zama dogo sosai idanunsa da suke rinewa, ga yanda fatar jikinta ke wani sheƙi da kwanciyar ɗaukar idanun mai kallo ya saka tsigar jikinsa tashi. Yanda yanayinsa ke canjawa yasa shi kai hannu da kansa yaja rigar ya maida mata.
Received at 10:47 AM
[14/02, 9:17 am] Abue Saleh: Cikin rashin damuwa ta gyara zama da faɗin, “Dada kaga nasan kana da mata ko?”.
A ransa yace (Wata sabuwa, wannan ficikar fa da wayonta) a zahiri kam sai ya basar ta hanyar faɗin, “Shike nan ke faɗa min miyyasa baƙya son kiyi?”.
“Saboda bana son na bar Mammah da su Uncle's, da Ruky. Da Daddy, da su Ammie. Nafi son muyita zaman mu a haka lullum-kullum muna jin daɗin mu, muna hira. Dada ƙarya suke ai ba'a min aure ba ko?”.
Ji yay kamar ya kwashe da dariya saboda yanda tai tambayar cikin marairaicewa, amma ya gimtse abarsa “Uhmm ƙila da gaske suke yi dai, amma miyasa baki tambaye su waye mijin ba to tun acan?”.
Baki ta sake turawa. “Wai sunce assignment ne naje na bincika kai ko Mammah zaku faɗa min”.
Maimakon ya bata amsar sai ya waske da faɗin, “To amma ai naga kina son yara sosai. Kuma sai anyi aure ake haifar yara ai ko, yaya zakiyi kenan?”.
Yanzu kam har cikin ranta ta ce, “Dada baga su Afrah ba. Kuma su Ammy suna ƙara haifo mana wasu, ai sun ishe mu mu duka.”
“Duk da haka kema zamu so ni da Mammah da Uncles ɗinki muga naki ai”.
“To kawai basai na haife su a haka ba?”.
“Babu auren?”.
Ya faɗa cikin ɗan waro idanu. Kawai sai abin ya bama Nimrah dariya, ta shiga ƙyalƙyalawa. Shi kuma ya shagala kawai yana kallonta. A ranta ko rayawa take (Dada fa kallon ƴar yaye yake min ko? Bari muje a hakan to). Sai da tai dariyarta sosai sannan ta jinjina masa kai. Kai tsaye ta ce, “Eh, ai ko bakai aure ba idan malamai suka maka addu'a sai kawai kaga ka samu Baby”.
Samun kansa yay da tsareta da idanu kawai. A ransa yace (Zakiga malamai kuwa yarinya, harda ma masu addu'ar saukar aljanu nan kusa kaɗan).........✍️
🤣🤣Zamu so ganin malam saukar aljanun nan kuwa Dada🥱🤭.
[16/02, 10:58 pm] null: KIƊA A RUWA 3
11
.........“Amma mutanen nan ƴan iska ne Haysam. To taya ma suka san ka auri Nimrah? Nifa abin nan na bani mamaki”.
Dada dake zaune a kujerar kusa da gadon jiyyar Daddy Imran ɗin yaɗan furzar da iska yana jan ƙaramin tsoki.
“Imran ba abin mamaki bane dan nasan mutanen nan dama dole suna zagaye damu. Kawai yanda suka gaya mata wannan zancen ne sai na fahimci akwai manufa, akwai kuma abinda suke son isarwa ga yarinyar musamman da suka ce taje ta bincika mijin da kanta...”
“Tabbas nima na fahimci hakan, tunda kaga harta kasa riƙewa ta faɗa maka. Indai haka ne to ya kamata mu zauna da ita a mata bayani. Dan a yanzu ni kaina banga amfanin cigaba da ɓoye mata kai mijinta bane. Sannan dolene fa ta koma kusa da kai gaskiya.....”
“Imraaan!”.
“Haysamm!”.
Shima ya tari numfashinsa. Sai kawai suka zubama juna idanu. Babu wasa sam a idanun Daddy Imran ya cigaba da faɗin, “Wai mi kake shakku ne? A tunaninka Nimrah bata san komai bane? Kana ganin lafiya-lafiya idan tana hannun iyayenta ne zuwa yanzu basu jima da mata aure ba, maybe ma ta haihu to wlhy. Balle yanzu da a cikin birni take tana samun abinci mai ƙyau. Ni bance dole sai ka kasance da ita ba, amma ta zama kana sanin duk motsinta tunda har mutanen nan suka fara da wannan salon. Sannan karka manta Nabeeha ma ta dawo gidan a yanzu. Ita kanta idan taga kana cigaba da ɗaukar Nimrah yarinya har yanzu zata tsiro maka da wasu fitinu ne. Amma idan ta tabbatar da fa da gaske kake shike nan sai kowa tai yaƙin kanta. Kaifa kake gaya min yanzu Nimrah ta gama faɗa maka tasan kana da mata, harma bata manta ta yanke ta ba. To kasan waye Nimrah kuwa a rashin ji? Har yanzu ƙananun ayyukansu kake gani wlhy, amma tunda har bata manta wannan batun yankan ba ni nake faɗa maka sai tayi wani abu.....”
Yanda Dada ke masa kallon mamaki yasa shi yin ƴar dariya.
“Hummm sa wasa, kai dai ka saka ido kawai a kanta. Amma kasan ALLAH Nimrah Zakanya ce ta gaske. Kawai sauƙin abun tana shakkarka ne tunda baƙo kake a idanunta har yanzu. Amma ka ma shirya, dan in dai tsoro ne Nimrah bata san wani abu wai shi tsoro ba”.
Hararasa Dada yayi da faɗin, “Duk baku kuka ɗaure mata take yi ba. Yanzu haka idan ta sakani gaba da fitina rasa ma abin yi nake yi. Ina ga ta dawo kusa dani, ai wannan aikin ma bazai yiwu ba, dan bazan iya haɗa rikicinta da aikina ba gaskiya. Kana maganar ta girma, to yanzu take cemin ai idan malamai sukai addu'a ko ba'ai aure ba ana samun Baby, ina hankali anan Imran?”.
Duk yanda Daddy Imran yaso gimtse dariyarsa ya kasa, sai da yayi mai isarsa.
Sai kawai Dadan ya kuma zuba masa harara. “To miye abin dariya anan kuma?”.
“To kai miye na tsarguwar? Ko kaji nace wani abu?. Tunda dai in malamai sukai addu'a ana samun Babyn kai ba sai ka zama Malamin nata ba. Miye abin wahala a ciki ba koyar da karatu bane kawai ta fahimci baƙaƙe da wasilla”.
“Wlhy kaji kunya uban banza”. Dada ya faɗa yana miƙewa ya nufi hanyar fita. Shima Imran miƙewar yayi yana ƙyalƙyala dariya dan an sallamesu har Nimrah ɗin ma. Duk da bakwai sun zama normal bane gaba ɗaya musamman ma shi mai rauni akai. Kawai dai zaman asibitin ne bashi yiwuwa a wannan gaɓar.....
©©©©©©©©©
A ɓangaren shugaban ƙasa Yusuf Shu'aibu Tafida ƴan jam'iyya sun bala'in saka rayuwarsa gaba ta ƙarƙashin ƙasa akan naɗin muƙamai. Dan tun suna ƴar percentage har sun fito masa ƙuru-ƙuru da sunayen waɗan da suke buƙatar a bana manyan muƙamai. Hankalinsa ya tashi, duk da kuwa wanda suka kawo ɗin shi bazai ce suna da wani baƙin hali na zahiri bane. Amma a muƙaman da suka riƙe a baya a bayyane take su masu rauni ne ga sauke haƙƙokin talakawa. Babu abinda suke yi sai raya kansu da iyalansu da dukiyar ƙasar. Shiyyasa babu wani ayyukan cigaba