Showing 1 words to 3000 words out of 25334 words

Chapter 1 - GUDUNA AKE

10 Sep 2025

1968



𝐆𝐔𝐃𝐔 𝐍𝐀
𝒜𝒦ℯ 𝔂𝓲.





𝓐𝓼𝓱𝓪𝓷𝓽𝔂 𝓵♡︎𝓿𝓮






/Wannan labarin k'irk'irarren labari ne. Ba'a yishi don wani ko wata ba. Duk wanda yaga ya yi daidai da rayuwar sa arashi ne.






بِسْمِ اللهِ الرَّحْمٰنِ الرَّحِيْمِ






1/5.





Ruwa ne ake yi sosai kaman da bakin ƙwarya. Yau ranan ce ta litinin ,watan na August. Wata ne na ruwa abun sai godiyar ubangiji. Ƙaramar motace ƙirar pecanto mai ƙofa ɗaya fake gefen titi daidai gada ta kabuga. Tsananin ruwan da ake yasa mutane da yawa suka faka motocin su gefen titi ,saboda rashin gani da gudun faruwar wani mummunan hatsari. Cikin su harda Jaleela dake zaune cikin motar ta Pecanto jaa, wajen zaman direba. Bayan motar yarinya ce ƙarama da bata haura shakera bakwai ba. Tsakanin yarinya da Jaleela babu banbanci ,tamkar tayi ka ki ne ta tufar saboda tsananin kamar da suke da yarinya. Anees dake zaune tana ta zuba da ƴar muryar ta mai daɗi da zaiyi maka nuni da tabbas tana cikin nishaɗi, na wannan yanayi da ake ciki. Harshe Jaleela ta taune tana tura labbanta cikin baki daya zame mata kaman al'ada, musamman idan tana cikin stress. Numfashi ta sauke mai zafi takai hannu tana goge glass ɗin motar da ya yi naso sosai. Ranta gaba ɗaya a dagule yake. Hankalin ta gaba ɗaya ya karkata ne wajen aikinta data makara sosai ,ga makaranta da zata kai Anees. Yau gaba ɗaya bata fito daga gidan ba sai ƙarfe takwas saura, tana fitowa kuma hadari ya haɗu lokaci guda aka tsuge da ruwa mai ƙarfi gaske daya sata dole fakin gefen titi.

"Kinji Mummy"

Numfashi ta ƙara saukewa tare da lumshe ido ta buɗe ta juyo tana kallon Anees. Manyan Blue eye's nata ta watsawa y'ar tata dake da sak irin su. Muryar a hankali da tsananin taushi tayi magana tana ƙoƙarin ɓoye ɓacin ranta tace

"Sorry, me ki ka ce?"

K'aramin bakin ta Anees ta ƙara turowa da ƴar shagwaɓa tace

"Mummy kullum nace miki ina Daddy sai kice ya yi tafiya. Ban taɓa ganin Daddy ba. Makaranta, Aunty mu kullum sai ta tambaye ni sunan Daddy ,amma kin ki gayamin Mummy "

Wani irin dum ƙirjin Jaleela ya matsanancin bugawa. Lumshe ido tayi tana kiran sunan Allah cikin ranta. Saboda yanda ta tsani mutumin da duniya bata da maƙiyi kaman sa, Anees ke amfani da Baby Anees a makaranta babu sunan uba. Haƙiƙa tana tsananin tsoron ranan da sirrin data jima tana ɓoyewa zai tuno. Sirrin daya sa take ta guje-guje ta kasa samun mafaka. Tabbas yanzu ma lokacin barin ta Kano ya yi. A shirye take ta tsare ƴar ta daga dukkanin wani ƙalubale da hantara na rayuwa.

"Kiyi haƙuri Anees. Nayi miki alƙwari mahaifin ki na nan zaki sanshi very soon inshaAllahu. "

Cutely Anees ta harde hannu a ƙirji tana ɗan zumburo baki kaman mai shirin yin kuka. Furzar da numfashi Jaleela tayi mai zafi ta juya tana kallon waje. Babu laifi yanzu ruwan ya fara tsagaitawa don mutane har sun fara tafiya. Motarta itama ta tayar a hankali ta haura kan titi tana kallon agogon dake ɗaure tsintsiyar hannun ta.
Ƙarfe tara da minti biyu ya nuna. Tasan da ace ba ruwa ake ba da tuni an nemeta daga gurin aiki. Maganan Anees ce ta katse mata tunanin da take taci wani mugun burki kan titi ,saboda mota data kusa bugewa. Kalman da Anees ta furta tayi masifar jefata cikin tashin hankali daya sai da idanuwan ta suka cika tab da hawaye.

"Mummy ina naki Daddy da Mummy ɗin. Ko ƴan uwanki?. Ban taɓa ganin kowa yazo gurin mu ba sai kawayan ki kawai. Ko bamu da kowa ne?"

Anees yarinya ce ƙarama amma tana da tsananin fahimta . Idan tayi wani abu wani lokacin sai kayi zaton ta haura shekarun ta. Akwaita da manyan ce gata da ɗaukan abu. Shi yasa Jaleela ke iya bakin ƙoƙari wajen ganin ta ɓoye dukkanin wani sirri nata, musamman ɗaya sana'ar ta da take. Rai a ɗan ɓace ta juyo ta kalli Anees tace

"Tambayoyin menene haka? Bana hanaki idan ina tuki ki dameni da magana ba?. Kina kallo yanzu na kusa buge motar wasu. Ko kina so ranki ya ɓaci?"

Shar hawaye suka biyo kuncin Anees a hankali tace

"Kiyi haƙuri Mummy "

Bata bata amsa ba sai kai data jinjina ta tada motar suka cigaba da tafiya. Harta sauke Anees a k'ofar makaranta tana sharar hawaye. Da ido ta bita harta shige kamartar mai suna Kamfa dake wajen BUk old side. Tanayin dukkanin wani bakin ƙoƙarin ta wajen ganin ta bawa Anees rayuwa da ilimi mai kyau a matsayin ta na Single Mom. Hawaye mau zafi suka biyo kuncinta. Haɗa kanta tayi da sitiyarin motar tana zubda hawaye. Sosai rayuwarta da dukkanin wasu abubuwa da suka gushe suke dawo mata kaman lokacin komai ke faruwa.

"Abhie, Ammi. Ya Almu . Ku yafeni"

Ta furta a hankali tana wani irin kuka mai taɓa zuciya. Haƙiƙa ta gogawa kanta bakin fenti da bazai zai taɓa gogewa ba a rayuwar ta ba. Ina ma dai ace ana dawo da hannun agogo baya data goge dukkanin wani fenti da tayi wa kanta. Ta nesanta kanta da wanda ya yi sanadin faɗawarta ciki wannan musiba da tashin hankali. Shine ya yi sanadin rabuwarta da gida. Ta baro gatanta, ta baro soyayyar ƴan uwa da kuma Iyaye. Ya gama cutar ta a rayuwa. Da ƙyar ta iya lallashin kanta ta, ta tada motar ta bar ƙofar makaranta. Tara da rabi daidai tayi fakin motar ta ƙofar office nasu na WOMAN RIGHTS HISBA .A hanzarce ta fito riƙe da yar jaka ta ratayawa dake lauke da waya da keys nata na gida dana mota. Sai abaya dake hannun tana ƙoƙarin ɗurawa kan damammiyar doguwar rigar dake jikinta. Tana ƙarasawa bakin ƙofar security ya buɗe mata yana mata sannu da zuwa. Kaman ko da yaushe murmushi tayi masa kafin ta shiga.

Numfashi ta sauke bayan ta shiga. Kaman jira ake ta shiga kuwa dukkanin wani ma'aikaci dake gurin ya juyo yana kallonta. Idan da sabo ta saba da irin wannan kallo ,amma abun na yau sai taga kaman yafi yawa ,musamman yanda taga matan na jefan ta da wani irin kallo na izgilanci da ƙyama. Kai ta jinjina ta fara takawa a hankali don zama wajen tebir nata na chasier.

"Dubeta da Allah. Kyau babu kyan hali sai shegen girman kan tsiya kaman yar sarki. Ai ni Jamila na gayamiki irin wannan masu Shiru-shirun munafukai ne. Ki duba kiga duk wannan shegen kyan, ashe ciki Fir'auna ne waje Musa. Kina ji ashe y'ar tata Shegi..."

Jaleela tayi wani irin kukan kura ta d'auke ta da mari da gaba d'aya floor d'in saida ya amsa. Ihu da kururuwa Zainab ta sa ta riƙe kuncinta tana kallon Jalila da hargagi tace

"Ni ki ka mara?"

"An mare ki. Ki k'ara furta wata kalma kan y'ata yanzu kiga in ban chanza miki kamanni ba. Shiru ai ba tsoro bane. Nasan mutuncin kai na ne shi yas..."

Wata irin dariya Zainab ta saki tana tana hannu. Dole Jaleela tayi shiru tana kallon ta ranta na suya.

"Yoo wane mutunci kuma da an riga da an zubar dashi tuntuni a titi. Ko kin d'auka bamu san me ki ke aikatawa ba bane. Y'ar taki ai ba k'arya a kayi ba shegiya ce da bata da uba. Korarriya daga gidansu saboda tayi cikin shege. Kinzo nan kin fake mana da sunan salihar mace mai tsoron Allah. Ashe simimi kasau ce. Waje Musa, ciki Fir'auna. Babu fuss ,babu asss"

Duk yanda Jaleela ke k'ok'arin wajen ganin ta danne hawayen da suka cika mata ido zuba, saida suka biyo kuncinta. Taune lebe tayi don bata da wani kalma da zata furta , dukkanin abun da Zainab ta fad'a gaskiya ne. Bata da wani abu da zatace ta kare kanta.

"Mtswwwwww."

Zainab ta k'ara jan wani irin dogon tsaki jikinta na tsuma kaman mai shirin yin dambe. Numfashi Jaleela ta sauke mai zafi ta d'an ja baya tana kallon mutanen gurin da sukayi shiru kaman ruwa ya cinye su. Yawancin su suna cikin nishaɗi n abunda ke faruwa. Tasan kuma yanda da yawa suke jin haushin ta sai sunfi kowa san ganin sunyi damben da Zainab.

"Jaleela Mukhtar Bature"

Babbar shugabar su ta Woman rights ta kira ta tsaye daga bakin k'ofar office nata. Hakan kawai sai taji gabanta ya tsananta fad'uwa. Da kyar ta iya taka k'afarta ta bita office d'inta. Bata yarda ta juya ta kalli su Zainab da take jin tashin dariyar su. A hankali ta tura k'ofar ta shiga bakin ta d'auke da yar siririyar sallama. Zaune ta sami shugabar tasu kan makeken kujerar ta dake d'auke da tebir. Da hannu ta nunawa Jaleela kujerar dake fuskantar ta. Jiki a sanyaye ta ja kujerar ta zauna tana kallonta. Bata ce mata uffan ba saida ta gama dube-dube cikin drawer ta fito da wasu takardu. D'agowa tayi ta kalli Jaleela take faman had'a zufa duk matsanancin sanyi da office d'in ke dauke dashi. Da murya mai kaushe tace

"Jaleela. Nasan kina cikin fargaba na wannan kira da nayi miki. Tambaya d'aya ce nake sonyi miki."

Shiru tayi tana kallon Jaleela dake sauke numfashi da a hankali. Kai ta d'an jinjina ta cigaba da cewa

"Tambayar da nake sonyi miki shine. Kin tab'a aure ne?"

Dum k'irjin Jaleela ya buga har H lami dake fuskantar saida taji yanda zuciyar ta ta ke bugawa.

"Ki kwantar da hankalin ki. Ina so ne mu kawar da zargi da ake miki. Kwana biyu da suka wuce an kawo mana wasu korafi a kan ki. Saboda girman abunda aka kawo mana yasa muka k'ara yin bincike a kan background naki. A iya sanin mu kin sanar damu cewa baki da aure. To shin kin tab'a aure ne wata kaddarar ta sameki har ki ka rabu da mijin ki?"

Gumi ne mai zafi ya karyowa Jaleela bakinta na rawa a mugun hankali tace

"A'a "

"Ikon Allah. To ya aka yi kuma ki ke da y'a dake da shekaru 7 a duniya. Kina so kice min yarinya taki bata hanyar Sunna aka same ta ba?. "

Wani irin kuka ne ya kwacewa Jaleela ta danne shi, hawaye masu zafi suka biyo kuncinta ta. Kai H Lami ta girgiza rai a dagule tace

"To maganan gaskiya Jaleela baza mu cigaba da d'aukan ki aiki a nan ba. Mu hisba ne da muke yak'i da mutane masu miyagun hali ,wajen ganin mun d'ora su kan turba mai kyau. Bayan haka mun samu labarin wani mummunan sana'a da ki ke aikatawa bayan wannan. Saboda haka mun yanke hukunci sallaman ki. Bazamu iya cigaba da zama dake ba. Ina so ki saka hannun a wannan takardar don mun kore ki "

Hannun Jaleela na rawa ta karb'i takardar data mik'o mata ta saka hannu hawaye na diga kan takardar. Da wani irin sanyin jiki ta miƙe tayi bakin k'ofa zata fice. Lami tace

"Amma naji mamakin wannan mummunan dabi'u da ki ke a b'oye Jaleela. Yanayin ki baiyi kama da mace mara daraja ba, mace mara sanin ciwon kanta na y'a mace. Mace data fifita duniya a kan lahirar ta. Yanzu me zaki ce da y'ar taki da ki ka haifa a titi a duk lokacin data buk'aci sanin waye uban ta?"

A guje ta buɗe k'ofar ta fice tana wani irin kuka kaman mai shirin tada asmah. Zainab da sauran ma'aikatan dake jiran fitowar ta suna ganin yanda ta fito suka kwashe da mahaukaciyar dariya harda masu tafawa. A guje ta fice tayi wajen motar ta. Jiki na rawa ta buɗe ta shiga. Had'a kai tayi da sitiyarin motar tana kuka sosai kaman babu gobe. A karo na babu adadi nan ma sun Guje ta saboda kaddarar data same ta.


𝐆𝐔𝐃𝐔 𝐍𝐀
𝒜𝓀ℯ 𝔂𝓲.







𝓐𝓼𝓱𝓪𝓷𝓽𝔂 𝓵♡︎𝓿𝓮






6/10.






Ta jima zaune cikin motar kafin tayi jarumta ta bar k'ofar office d'in. Maimakon tayi gida sai tayi inda take tunanin nan ne kad'ai zatafi samun nutsuwar zuciya. Kai tsaye tayi club dake can wajejen Suleiman crescent. Harabar gurin cike yake da motoci kace dare ne. Kowa yasan club yafi ci da daddare. Guri ta samu ta faka motar ta, bata fito ba saida ta cire abayar dake jikinta da d'ankwalin ta. Dogon gashinta dake nan har wanen hips nata ta sake shi wanda ta d'aure da ribbon . A hankali ta fito riƙe da waya da muk'ullin motarta a hannu. Rigar dake jikinta ba k'aramin kamata tayi ba wanda hakan ya bawa shape nata da k'irar ta fitowa muraran. Abun sai wanda ya gani tabarakalla Jaleela ba dai kyau. Akwai kyawu na fuska dana jiki amma babu na zuci. Daidaikun manyan Boy's dake gurin suna ganin fitowar ta suka bito da ido chaa kaman kura taga nama. Yanda take jinta a yanzu bata tunanin zata saurari wani namiji. Rai a dagule ta shige club d'in. Saida ta fara yiwa kanta order na drinks masu sanyi da y'an snack sannan ta wuce ta samu guri daga can b'angaren Vip ta lafe a bunta. Sosai tayi zurfi cikin tunanin rayuwar ta da irin kalubale da take fuskanta tun daga ranan data baro gida da gatanta, har zuwa yanzu da take iya bakin k'ok'ari wajen ganin ta bawa Anees rayuwa mai kyau. Duk wani namiji daya yunƙuro inda take zata watsa mata mugun kallo dole ya juya yana cije lebe. Yau sam bata marmarin kasancewa da wani namiji. Numfashi ta fesar ta d'aga lemonta na orange juices mai sanyi ta kora tana tunanin ,wai shin duk ina mutumin daya jefata ne cikin kangin rayuwa?. Mutumin da ya yi sanadin ta zama abun gudu da kyama?. Idan yasan cewa tana tare da y'ar sa zai k'arbe ta hannu biyu?. To wai shi d'in waye ne ma?. Menene asalin sa?. Haka tayi ta jerawa kanta tambayoyi har na tsawon wasu lokata. Hak'ika idan ta k'ara had'uwa da Mutumin nan bazata tab'a yafe masa uk'ubar daya jefata a ciki ba. Baza ta daina yi masa Allah ya isa ba da yi masa Addu'a, Allah ya gaggauta k'arban mata hakkin ta a duk inda yake a fad'in duniya. Ya hukuntashi kwatankwacin uk'ubar daya jefata a ciki.

Ba ita ta baro Club d'innan ba saida ta daidaici lokacin tashin Anees ya yi daga makaranta. Tana fakin motar k'ofar makarantar su ana tashin su. Bata jima ba Anees ta fito a guje hango Mummyn nata datayi. Suna tafe a hanya tana bata labarin abunda yau sukayi a makaranta. Duk irin damuwar da take ciki haka ta daure tayi ta biye bata ko itama zata samu salama a zuci. Ta gama yankewa gobe inshaAllahu zasu bar Kano sai kuma wani lokacin bi'iznillahi. Saida suka tsaya nan Rufaida. Suka siyi yan snacks da fura sannan suka wuce gida. K'arfe biyu ta miƙa Anees makarantar Islamiya dake can gabn layinsu nan first gate. Kafin Anees ta dawo daga makaranta tuni Jaleela ta gama had'a musu kayansu da dukkanin wani abu da zasu buk'ata. Masu gidan ta kirasu ta sanar dasu zata tashi gobe inshaAllahu. Bayan dawowar Anees daga islamiya ta iske kayansu a fake guri d'aya. Ran Anees sosai ya soso dan ta gaji da wannan yawace yawacen da suke gari-gari. Yarinya ce ita k'arama amma tana da hankali. Yanzu idan suka koma wani garin shima haka zata fara komai sabo. Makaranta, kawaye. A guje ta shige ɗakin dake kallon na Jaleela tana kuka. Da yake gidan flat ne k'arami mai d'auke da d'aki biyu sai toilet daga tsakiyar sa inda ya raba dak'unnan. Sai falo da kitchen. Daga waje gidan nada y'ar relar da aka kawata da y'an bishiyu na furanni masu kyau. Babu yanda Jaleela batayi ba don ta rarrashe ta amma fafur tak'i ko abincin dare tak'ici ,k'arshe haka ta zuba mata ido har barci ya d'auke ta. Numfashi mai k'arfi Jaleela taja ta gyara mata kwanciya ta rufe ta. Tasan akwai gajiya, amma duk abunda takeyi tana yine saboda ita. Bayan tayi sallan isha zama tayi sosai tana rera kira'a mai tsananin dad'i kace Sudais ne a mace. Ni kaina mamaki ya kamani na zuba mata ido baki a sake ina kallon yanda take karatu a nutse babu gargada. Komai tana bashi hakkin sa yanda ya dace . Ikon Allah idan kaga Jaleela a yanzu koda wasa aka ce maka itace d'azu a club baza ka tab'a yarda ba. Kai k'arshe ma sai kayi fad'a da mutum don babu abunda zai hana kayi zaton sharri ne ko kage ake mata. Yanda take rera karatun zai tabbatar maka tayi sauka ba d'aya ba, bare biyu. Wai shin wacece ne Jaleela?. Awa guda cur ta d'auka tana rera karatun Qur'anin nan mai saka zuciya da kwanji cikin nutsuwa da annashuwa. A hankali ta rufe Qur'anin ta ajiye gefenta. Hannu ta d'aga tana rera Addu'o'i masu tab'a zuciya da bargon jiki. Sosai hawaye suke bin fuskarta tana rerawa Annabi salati da kiran sunanyen Allah, kyawawa ya kawo mata sauk'i cikin wannan rayuwa data tsinci kanta a ciki.

Washegari misalin k'arfe bakwai na safe suka d'auki hanyar Abuja. Saida Jaleela tayi Addu'a sosai kafin ta shiga mota suka d'auki hanyar. Sosai Jaleela ta kware wajen tukin mota tana bin dukkanin wasu k'aidoji daya dace. Ga motar ta saki karatun Qur'ani na sheikh Sudais da Ali jabir. Bata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login