Showing 15001 words to 18000 words out of 19901 words

Chapter 6 - HOORAIN MAI KUSUMBI

10 Sep 2025

1757

domin exactly munanan mafarkin da yayi ya faru a zahiri.

hakan yasa tun daga wannan ranar idan Allah ya sa yayi mafarkin mutum mara kyau, sai yace ayi sadaka, ko kuma yace a dage da tashi sallan dare, in Sha Allah sai mutum ya ga komai lafiya sakamakon addu'a da sadaka da ya yi, hakan yasa da yayi mafarki ya bayyana suna daukar shi da gaske...




*BACK TO STORY*


**********

Sai daya zo daidai kofar gidan su Hoorain ya ja ya tsaya, kana yace "Hoorain Yusuf a yau Allah ya bani ikon ganin maganin lurar ki a mafarki"



ya maimaita hakan sau uku abinka da yan kauye gaba-daya sun zagaye shi, ana ta kallon sa.



Ta bangaren Hoorain kuwa zaune suke ita da Hamdan da kullum sai yazo ya ganta yake samun nutsuwar zuciya.


Mami tana daki a zaune, yayinda Hamdan ke bare mata cashew nut da Aramani ya kawo mata soyayye tana ci, kawai kallon dan tsut din bakin ta yake with much admiring on his face, komai nata na burge shi, kamar ya hadiye ta ɗan so amma sam ba za ka taba gane hakan ta fuskar shi ba.



A lokacin da suka ji Ashimi dan baiwa ya kira sunan Hoorain gaban Mami da ita Hoorain yayi mummunan fad'uwa, cikin rashin fahimta Hamdan ke kallon hanyar soro ta inda yake hango kafafun mutane, gashi hayaniyar su ta cika wajen...



Mami ce ta fito daga daki, sannan ta mikawa Hoorain hannu domin taimaka mata wurin tashi, cikin mugun sanyi da jikin ta yayi ta kama hannu Mami ta mike...

cikin tafiyarta ta masu kusumbi ta bi bayan Mami, Hamdan ma mikewa yayi ya rufa musu baya, nan fa idanun yan k'auyen ya bisu Mami da suka fito zuuuuuuuuu



Cak Ashimi ya sayar da idanun sa masu kwarjini sosai ga fuskar Hoorain, kasa tayi da kanta domin idanun sa tsoro suke bata sakamakon tarin baiwa daya cika cikin su.



"A yau Allah ya nuna min ke Hoorain a mafarki"

Sai ya kalli Mami da idanun ta ke dauke da hawaye yace

"wannan kusumbi ba da shi kika haife ta ba, tana da Shekara daya a duniya aljanin daya yi sha'awar surar ta ya sanya mata sakamakon wata rana kin kwantar da ita tana bacci babu wando a jikin ta, kina band'aki, shi kuma ya bayyana gareta, surar Hoorain ya burge shi kana ya bashi sha'awa duk da karama ce, hakan yasa ya mika hannunsa daidai bayanta wani koren haske ya bayyana ya shiga ratsa bayanta, bayan wasu Mintuna ya bace bat.

Manufar sa ta yin hakan shine saboda kada wani da namiji ya aure ta ko ya so ta, shi kadai ne zai mallake ta. Kamar wasa a hankali kusumbi ya fara tsiro wa har yayi wanna girman, a ko wacce rana wannan Aljani mai suna mushkaf sai ya zo ya kara mata girman sa, shiyasa kullum kusumbin ke cigaba da mamaye bayan ta, idan kuma aka cigaba a haka watarana zai rinjaye ta ta yanda ko tashi zai gagare ta..."




Salati, ihu, hadi da surutai kala-kala ke tashi a wajen, Mami hawaye take abin tausayi, tabbas Ashimi dan baiwa bai yi karya ba, ba haka ta haife yar ta ba, nadama sosai ya rufe ta, domin bata manta lokacin da mahaifin Hoorain ke yawan cewa ta daina barin Hoorain ba kaya, ashe ita ta ja wa yarta wanna lalurar sai ta rushe da kuka hadi da saka matacciyar hijab dinta da shi kadai ta mallaka ta toshe bakin ta dashi ....


Muryar ASHIMI dan baiwa daya cigaba da tashi ya sa wurin ya dawo so slient kamar ba hallitu a wajen duk suka kasa kunne suna sauraron sa


"Alhamdulillah! Allah ya nuna min maganin, wanda maganin warakar kusumbi Hoorain yana world of dead (duniyar mutuwa)"



Salati aka kara saki, wasu har da dora hannu a kai.

Ashimi dan baiwa ya cigaba da cewa "world of dead na da matuƙar hatsari fiye da tunanin ku, mugayen Aljanu, mayu masu shawagi da rana hadi da wasu hallitu marasa kyauwu ne suka cika duniyar mutuwa, duk mun san cewa babu wanda ya taɓa zuwa ko yin hanyar duniyar mutuwa. Toh anan maganin warkar da kusumbin Hoorain yake cikin wata kwarya a karkashin bishiyar kuka..."


Shiru ya dan yi yana bin mutane da kallo kana ya cigaba da cewa "zaratan samari bakwai ne zasu yi wanna tafiyar zuwa duniyar mutuwa domin dauko kwaryan nan, ba karya zaku hadu da miyagun hallitu da zasu yaudare ku, domin da siffa mai kyau zasu zo muku amma kada ku yarda da su daidai da ƙwayar zarrah, ku karfafa zuciyar ku, ku rike addu'a, ga wadanda suka shirya wannan tafiya zan baku wasu addu'o'i domin kare kanku, Hoorain na da kyakkyawar zuciya, ga duk wanda ya ga zai taimaka mata Allah ya biya shi, jibi ne tafiyar, na barku cikin aminci" yana kaiwa nan ya juya cikin tafiyar sa ta sauri_sauri ya bar wajen...



*HOORAIN*
Kamar wacce aka datsa haka ta cigaba da tsayawa idanunta kurrr kan dan baiwa Ashimi har ya tafi ta kasa kyafta idanun ta a wajen da ya tsaya, tsananin shock yasa ta kasa motsi, sai ruwan hawaye dake bulbulowa daga idanunta kamar an kunna famfo...



*HAMDAN*
Kallo daya zaka masa ka hango tsantsar damuwa daga cikin blue eyes dinsa daya Sanja launi, gaba-daya ransa a bace yake, duk da kasancewa mushkaf ba a jinsin bil'adama yake amma wani mugun kishi ke caccak'ar zuciyar sa game da shi, tausayin babe din sa ya kara yawaita a zuciyar sa.



Mutane ne suka fara watsewa kowa da abinda yake cewa, cikin sauri Hoorain ta fada cikin gidan tana kara sakin kuka mai tsuma zuciya, Mami ta biyo bayanta, kana Hamdan ya mara musu baya... hannunsu zube cikin aljihun wandon sa ya kafe ta da idanun sa masu ɗauke da tausayi, tsananin so, zallan kishi, hadi da bacin rai amma bai ce komai ba.



Abin tausayi haka Mami ta zube gaban Hoorain hadi da dafa ta, cikin sauri ta dago, ganin Mami ce yasa ta fada jikin ta hadi da kiran "Mami mie" cikin kwarewar zuciya.



Hugging dinta back Mami tayi tana rarrashin ta, kana tace "Hoorain haka Allah ya ƙaddara Maki, amma har da laifina ciki domin tabbas kina yar karama ban fiye son saka Miki kaya ba, ki yafe....."



"A'a A'a Mami, wallahi bazaki taba Zama mai laifi a gareni ba, ke ce duniya ta, ke kika kila da Ni har na kai iyanzu, Mami kada ki ci komai dan Allah, ina son ki Mami mie"



Kuka Mami ta sa, kauna da tausayin tilon yarta na kara mamaye zuciyar ta.

Hamdan kuwa bai taba ganin abinda ya ta6a zuciyar sa hadi da bashi tausayi kamar Hoorain ba, karamar innocent girl da take cikin K'addarar rayuwa.



Kasa jurar kallonsu yayi ya fita waje ya samu wani benchi na karfe a dan nesa da gidan su Hoorain ya zauna hadi da nausa hannunsa cikin sumar kansa yana mai rufe idanun sa.



****************


Da misalin K'arfe biyar din yamma, sai ga Aramani tare da wasu samari biyar sun zo gidan su Hoorain.

Abin mamaki suka sanar cewa zasu je duniyar mutuwa domin dauko maganin nan da zai warkar da kusumbin ta, sun kuma sanar da su cewa zasu Yi wannan sadaukarwan domin son fisabilillah da suke wa Hoorain, hakika ta sha gwagwarmayar rayuwa da tarin kalubale, ya kamata zuwa yanzu ta ji dadi ko yaya ne. Suka kara da cewa suna saka ran in Sha Allah su samu cikon na Bakwai din zuwa gobe tunda jibi ne tafiyar.



Mami tsabagen al'ajabi yasa ta kasa magana. Hoorain kuwa kuka ta samu musu tana cewa "Aramani, Danjuma, salihu, yakubu, oshimana, Abu, dan Allah karku je, bana so ku mutu, karku jefa rayuwar ku cikin hadari saboda Ni, ina farinciki da godewa Allah a yanda nake, dan Allah bazan iya jurar rasa ku baaaaaa" ta ja karshen maganar sakamakon mugun kukan daya kufce mata.



"Tafiya babu fashi Hoorain yar'uwar mu, matukar kana son mutum zaka iya sadaukarwa mai girma domin shi, ki mana addu'a kin ji ko? In Sha Allah zaki mike kina tafiya kan kafafunki kamar kowa"


samarin suka hada baki wurin fadin haka, daga nan suka fice a gidan.



****


A ranar kam har dare Hoorain idanun ta jike suke da ruwan hawaye, ta kasa daina kukan, Mami kallon ta kawai take cikin tausayawa domin babu wani karfin guiwa a tare da ita, jikin ta gaba-daya ya mutu, a ranar sun manta sunan abinda ake cewa *YUNWA* saboda tsananin damuwa daya cika zuciyar su, ko lokacin da Hamdan ya tafi ma basu sani ba.





Ta bangaren yan kauyen Oguma kuwa, ko wani gida da ko wani majalisa hirar Hoorain ke tashi kowa na fadin albarkacin bakin sa.


*WASHEGARI*


*HAMDAN*

Tun ranar da suka gama chat da Imran bai kara kunna wayar ba sai yanzu, kallon percentage din wayar yayi ga sauran masa 10% a hakan ma ya ga kokarin ta, domin iPhone baya mugun rikon chargi, gashi tunda yazo kogi bai yi mata chargi ba.



Contact list ya shiga, inda ya tsayar da idanun sa kan number'n Ammi, wata karfafar ajiyar zuciya ya sauke, kana ya danna number'n ta hadi da kara wayar a kunnen sa yan sauraron ringing din da yake...







*Mun fara shigowa cikin labarin, i swear basan yadda zan kwakwanta zafin book din nan ba. Abubuwan ciki na daban ne, just continuing following my pen, sahihiyyar kauna Noor ke wa masoyan ta na fili dana boye*


*Naso kara yawan typing amma banda a enough charge*


*_guys Meye ra'ayinku kan page din yau_?*





*Two free page left karku ji dif*🤸💃



NoorEemaan
07082281566



Thank you for reading my story
🍇#Hoorain the hunch back girl🍓



Share
Share
share

Please🙏



9:07
26/5 2022
[14/12, 12:54 pm] 𝙽𝚘𝚘𝚛𝙸𝚖𝚊𝚗✨: 🍇🍓🍇🍓🍇🍓🍇🍓🍇🍓🍇
HOORAIN MAI KUSUMBI
(The hunch back girl)
🍇🍓🍇🍓🍇🍓🍇🍓🍇🍓🍇




_written by NoorEemaan_ 📚✍️




Chapter 1️⃣9️⃣⏩2️⃣0️⃣


Hannun Mami ta rungume gam tana cigaba da kukan, ga muryar ta ya fara dashewa... haka ta cigaba da kallon su har ta daina ganin su.



Mami ta kamata da k'yar domin ita ma babu karfi a jikin ta suka nufi dan gidan su.


Mami ta shigar da ita daki, Hoorain ta sulale kan yoluluwar kafitar su ta kwanta, babu jimawa wani zafaffan zazzab'i ya rufe ta, jikinta ya dau zafi, hak'oranta na had'ewa dana juna yayinda jikinta ke rawa kamar mazari...

Hankali tashe Mami ta dauko yan jike-jike irin na su na kauyen ta bata ta sha, sannan ta dauki zanin ta ta rufa mata, bayan Mintuna talatin wani bacci mara dadi ya dauke ta cike da mafarkin su Hamdan.



*********



*NASARAWA GRA SULTAN ROAD*
_10:00am_

A dai-dai lokacin Ammi ta tashi daga bacci, domin raba dare tayi tana ibada, bayan tayi sallar asuba kuma bacci ya dauke ta, sai yanzu ta tashi.



Mikewa tayi tana dan yamutsa fuska abinka da jikin tsufa, toilet ta nufa tayi wanka sannan ta fito ta shirya cikin had'add'e kuma tsad'add'en atamfar *English gold* ta shafa humra da wasu turaren ta masu dadin k'amshi.
Ammi macece mai son gayu, tsafta, hadi da k'amshi, a takaice dai a wurin ta y'ay'an ta suka gado hakan.


Bakin gado ta zauna, ta latsa wayar ta, inbox dinta ta gani ya nuna an turo message, hakan yasa ta shiga, ganin number'n Hamdan ne yasa ta danna da sauri...



Sau uku ta maimaita abinda ya rubuto mata, jikin ta yayi sanyi sosai kalaman sa sun ratsa zuciyar ta, tausayin sa da son sa sosai taji ya kara shigar ta har hakan yasa wasu hawaye Masu dumi suka biyo kuncin ta, hannun ta daga sama a fili tace "ya Allah ka fini sanin abinda yarona ke yi, ya Allah ka bashi Sa'a, ka zaba masa abinda yake mafi alkhairi, ka tsare shi da tsarewar ka ya Allah, ka kiyaye shi da kiyayewar ka, mugun ji, mugun gani ya Allah ka raba shi da su, sharrin mutum sharrin Aljani ya Allah ya kiyaye shi, Allah ka dawo min dashi cikin koshin lafiya" ta shafa addu'ar wasu hawayen na kara zubo mata.



"Falmata! Falmata!! Wai baccin ne yar yanzu? inci dai Lafiya ko?" Ayiyah data zo bakin kofar yanzu ta fada.



Cikin gaggawa Ammi ta share hawayenta, sannan ta dai-dai ta Muryar ta ce
"gani nan Ayiyah" ta fada tana nufar bakin kofar, ta bude, ta wani dogon corridor ta bi sai ga ta a babban falon ta wanda ya kasance kamar general falo domin duk a nan suke jin abincin.


Ayiyah ta gani zaune ta kurawa tv ido, kamar idanun ta zasu fado ciki, jin takun tafiyar Ammi yasa ta waiwayo, ta zubawa Ammi idanunta da ta rambada musu kwalli har yaso yayi yawa, tace "Falmata! wanna wani irin Bacci mai nauyi kika yi haka? Hankalina ya tashi ba shiri na kwashi kafafuna nace bari na dubo ko lafiya, yo Allah na tuba kana zaune da mutum yanzu, daya shiga daki babu jimawa sai dai ka ji ya zarce lahira, su Anas ma sun tambaya nace baki tashi ba, har sun wuce aiki domin sun ce basa son tashin ki"



Murmushin k'arfin hali Ammi tayi a ranta tana jinjina surutun Ayiyah ko full stop babu, rissinawa tayi kamar yadda ta saba ta gaishe da Ayiyah, cikin kulawa Ayiyah ta amsa tana sa mata albarka, domin ta kasance mace mai son a girmama ta, sannan tana yawan yabon Ammi a ranta domin duk da danta Wanda shine mijin Ammi ya rasu, amma hakan bai sa ta fasa girmama ta ba.



"Kiyi karin kumallo ko? yau kin makara... Nace wai ya wanna dan fadin rai da miskilancin tsiya, ince kun yi waya mara kirki ko neman kakar sa baya yi"



Danne damuwarta Ammi tayi sannan tace "eh Ayiyah yana lafiya, yace ma ce na gaishe ki" ta karasa domin faranta ran Ayiyah.



Ta kuwa washe hakoran ta tace "Masha Allah, dan k'wal uba yau ya ga daman tambayata kenan" ta karasa tana sakin dariya irin nasu na tsofaffi.


Ammi bata kuma cewa komai ba ta nufi kan dining table, tea da Irish kaɗai ta ji domin sam bata jin yunwa, haka ta wuni curr jikin ta ba dadi, Mintuna kadan sai tayi wa Hamdan addu'a a ranta.



***********




*KOGI STATE*

Sunyi tafiya mai nisan awannin goma kana suka shigo *land of death (duniyar mutuwa)*.
Ko gida daya babu bare ka saka ran ganin wata hallita, sai ciyaye hadi da bishiyoyi, kasan wajen tsaf kamar akwai masu sharewa kullum, da shigar su duniyar mutuwa komai ya sauya, ita kanta duniyar abar tsora ce ga duk wanda ya kalle ta, sai kukan wasu abubuwa kamar na tsuntsaye marasa dadin amo ke tashi.



Yamma sosai yayi domin duhun almuru ya fara, sam babu gazawa a tare da su duk da dare ya fara amma basu fasa tafiya ba, bare Hamdan sam babu alamar gazawa a fuskar sa bare gangan jikinsa su gaji.

Da sun daidaita lokacin sallah sai suyi taimama su gabatar da sallar su.
Ga yunwa ga k'ishirwa daya fara sanyayyar wa su Aramani jiki, amma haka suka daure, domin babu ruwa balle ka saka rai da samun abincin.

Har taran dare suna tafiya, wanda zuwa wannan lokacin Danjuma da Ya fi kowa gajiya cikin su ya tsaya, hakan yasa sauran dakatawa fuskar su cike da karin bayani.



Cikin Muryar galabaita yace "wallahi na gaji, har jiri ya fara diba na, dan Allah ku bari da asuba mu cigaba da tafiya, bazan iya ba, yunwa sosai nake ji"


Cikin tausaya wa duk suka kalle shi, ko wa yasan Danjuma baya wasa da cikin sa, Hamdan dake jikin su ya ɗan kalli Danjuma sannan ya motsa bakin sa a hankali yace
"mu huta zuwa asuba sai mu cigaba" yana fadi hakan ne domin saukaka musu, dan ta shine bai gaji ba, kuma baya jin yunwa ko dan bai damu da abinci bane...
Tabbas yasan akwai sauran lafiya sosai a gaban su, tunda ko alamar bishiyar kuka basu gani ba.

Gwara su huta domin kada karfin su ya ƙare, ya aiyana hakan a ranshi, sannan ya cire takalmin kafar sa ya zauna a kai yana mai lumshe idanun sa.



Su Aramani ma zama suka yi, bayan sun ajiye addinan su a gefen su, aramani Sarkin barkwanci kuwa ya dasa hira, nan suka saka bak'i aka cigaba da hira.



Hamdan kuwa sam bai san abinda suke cewa ba, domin ya zurfafa kogin tunanin Hoorain din sa, a ransa yana addu'ar Allah basu nasara....Tuno yanayin daya barta dazu ya sa zuciyar sa sosuwa, kukan da take yi hadi da kiran sunan su a lokacin da suka fara tafiya sai amsa kuwwa take a kunnen sa tamkar yanzu ne take yi, iska mai zafi ya furzar daga bakin sa, yana fatan ace ta daina kukan yanzu.



Sai sha biyun dare su aramani suka hakura da hiran da suke, Sakamakon baccin daya fara cika idanunsu, nan duk suka kwanta a kasa babu jimawa bacci ya dauke su...


Hamdan karewa wajen kallo yayi baya iya ganin ko tafin hannunsa ne, sakamakon tsananin duhu daya kara mamaye wajen, ga wasu Kuka iri daban-daban marasa daɗin amo daya cika kunne sa...


Da misalin ƙarfe dayan dare wani irin dariya mai matuƙar tsorata rai hadi da sanya Mutum cikin rudu da tashin hankali ne ya cika kunnen su tamkar zai fasa musu dodon kunne...


A firgice su Aramani suka farka daga nannauyyan baccin daya d'auke su, a tsorace suka fara kalle-kalle amma basu ga komai ba, sai can suka kalli sama inda suka ga wasu hallita masu tsorata ruhi suna shawagi a sararin samaniya tamkar suna tseren jirage yayinda kawunan su ke kallon kasa...


Hamdan ya bude idanun sa ya kalli saman sannan ya dawo da kansa kasa, sam babu wani tsoro a tare dashi, domin a cewarsa bai ga amfanin tsoro ba, addu'a kadai ce babban muk'amin mumuni.


Addu'a ya fara a ransa, cike da nutsuwa, a tsorace Danjuma da yafi kowa tsorata ya dawo gefen sa ya rakube, kallon sa hamdan yayi ya dauke kansa, gaba-daya Danjuma ya jike da gumi barin ma fuskar sa.



"Kuyi addu'a kada ku bari tsoro yayi tasiri a zuciyar ku"

ya fada hankali a kwance cikin k'asaitacciyar Muryar sa.


Nan suka samu sukunin fara addu'a, Danjuma saboda sabar tsoratan da yayi har addu'an shiga banɗaki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login