Showing 18001 words to 19901 words out of 19901 words

Chapter 7 - HOORAIN MAI KUSUMBI

10 Sep 2025

1761

ya dinga karantowa da karfi cikin fitar hayyaci, abin so Funny da a ce suna cikin yanayin mai kyau babu abinda zai hana su Aramani dariya.


Bayan kamar mintuna arba'in dif suka ji dariyar ya daina kana wadannan addu'an suka bace. Still hakan bai hana su shiru ba, addu'a suka cigaba da yi...

Babu wanda ya ƙara gingin komawa Bacci cikin su, har asuba ta gabato suka yi taimama, Hamdan ya ja su sallah, bayan sun iddar suka cigaba da tafiya domin haske ya ɗan fara bayyana kadan-kadan.




HOORAIN!
Zaune take ta kurawa waje daya ido bata ko kiftawa yayinda hawaye ke sauka a k'yak'yawar fuskar ta, da alama ta zurfafa a kogin tunani.

Ammi data fito a sanyayye ta zauna kusa da ita, sannan ta ɗora hannun ta kan kafad'ar Hoorain trying to comfort her, Wani sabon kuka Hoorain ta fashe da shi tana shigewa jikin Mami gaba-daya...



"Ya isa Hoorain! kuka baya magani, addu'a zamu dinga musu kinji"



Cikin Muryar kuka tace "Mami ina tsoro ne, banason wani abu ya same su, a wani hali suke ciki oho? Na san ko abinci basu ci ba mami, ga ya Hamdan bai saba da wuya ba amma saboda ni yasa kan sa a hadari, ina tausaya musu Mami, fatana su dawo cikin koshin lafiya bana son rasa masoyan asali masu nagarta kamar su mamiiiiiiiii" ta ja sunan cikin kuka.


Bubbuga bayanta Mami ta dinga yi tana rarrashen ta kan tayi shiru. Ta b'angaren Mami ma tana cikin damuwa kawai dannewa take a zuciyar ta.




*BUKAVU BARRACKS KANO*


Cikin yanayin mai nuni da fushi FIELD MARSHAL ke wa commander magana kan rashin dawowar Hamdan wanda ya saba ka'ida da doka.


A tausashe commander'n Wanda ya kasance dan kabilar Nupe ya dinga bashi hakuri hadi da tausar sa cewa jiya ya ce gidan su dake Nasarawa GRA ya kuma tattauna da Ammi inda tace a kara masa hakuri soon zai dawo, domin yanayin ta ya nuna cewa akwai wani Abu a kasa kan rashin dawowar Hamdan din.



"Zan kara masa wasu kwanaki matukar bai dawo ba, he will be punished, domin ya saɓa dokar aiki" Marshal ya fada yana katse wayar sa, duk da kasancewar yana son Hamdan domin Allah ya had'a jininsu, amma baya so sam a dinga wasa da aiki...



Commander numfashi ya sauke yana son gano menene ya hana Hamdan dawowa, amma ya kasa, domin abu ne wanda kowa ya riga ya sani cewa baya wasa da aikin sa, kara kiran Ammi yayi ya sanar mata abinda Field Marshal yace, kana ya dora da cewa idan ta same shi a waya ta sanar masa, shima zai dinga gwad'a kiran nasa, idan hakan ma bai yu ba sai a aika wasu soldiers din chan kogi a dubo shi.


Da haka suka sallama Ammi tayi masa godiya, jikin ta ya kara sanyi sosai, sam bata so damuwar ta yayi tasiri a kan Hamdan balle har ya kasa samun sukunin zuciya a duk inda yake, hakan yasa take kai zuciyar ta nesa tana masa addu'a.



*DUNIYAR MUTUWA*
(Land of death)


Tun suna tafiyar marmari har gangan jikinsu ya fara gajiya, kafafuna su ya yi tsami, ga yunwa ga ƙishirwa.

Hamdan shine karfin guiwan su, domin ganin babu gazawa a tare da shi yasa suma suke bada himman wurin bin sa, tafiya suke amma ko alama basu zo inda kwaryan maganin kusumbin Hoorain yake ba...


Sai da suka daidaici lokacin magriba yayi sannan suka tsaya domin yin Sallah.



Taimama duk suka yi, amma banda Danjuma dake zaune yana sauke numfashi daidai alamun yunwa na k'walk'walan sa gwanin tausayi.



Bayan sun daidaita tsaho Hamdan ya juyo ya kalleshi, tsaf Danjuma ya gane Meye ma'anar Kallon, marairaicewa yayi yace "zan yi sallah amma bari na huta kaɗan wallahi na gaji" ya karasa kamar numfashin sa zai dauke saboda tsabar yunwa da gajiya.


Hamdan bai ce komai ba ya shiga jansu sallah, Danjuma ya kafe su da ido yana kallon su....Can yaji alamun mutum a gefen sa, a dan firgice ya juyo, wata k'yakk'yawar budurwa ya gani zaune gaf dashi tana sakar masa Murmushi mai sumar da mutum, dan zabura yayi zai mike tayi saurin riko hannunsa, lumshe idanunsa yayi saboda tsananin taushin hannun ta, so yake yayi addu'a amma kamar an sa kwado an rufe mai baki.


Cikin wata murya mai dadin gaske budurwan nan tace "kar ka ji tsorona, naxo taimaka maka ne, kaji" ta karasa da mayaudariyar muryar ta.



Zuciyar Danjuma ta kasu kashi goma, yakasa tsayar da ita wace daya, before he could think of any other thing yaji ta kama hannunsa cikin wani salo ta fara cewa "ka yarda dani, bazan cutar da kai ba, abinci na kawo maka, kasan yunwa kake ji" ta karasa tana mika hannun ta bayan ta take wani bowl mai sheke da lafiyayyen abinci ya bayyana, ta dawo da shi gaban ta hadi da jefan sa da wani kallo mai kona ruwan ƙwaƙwalwar mutum sannan tace

"kaci, idan baka koshi ba zan kara maka kaji" ta fada calmly.


Wani dunk'ulallen yawu Danjuma ya hadiye, yayinda cikinsa yayi kiran ciroma, yunwar da yake ji ta karu sosai, lashe baki yayi, duk da yanda ran sa ya biya da abincin, amma kasan zuciyar sa yana tuno maganar dan baiwa inda yake cewa


_Kamar Yadda na fada zaku gamu da mugayen Aljanu, mayu, Hadi da Wasu hallitu marasa kyau a tafiyar ku da dawowar ku, ina so ku karfafa zuciyar ku, kada ku bari yayi rauni, duk wata yaudara da zasu muku kada ku amince_



Numfashi ya sauke ya kalli su Hamdan dake sallah cike da nutsuwa, da alama basa jin Muryar budurwan, wanda hakan ya bashi mamaki.



"Ka ci ka ji kada yayi sanyi, har ruwa mai sanyaya makoshi zan samo maka" ta fada tana mika masa abincin.
Hannu yasa ya karba Kamar wanda aka umarta, cikin gaggawa ya sa hannun sa cikin bowl din ya dibi abincin fuskar sa kuri kan na budurwan dake ta faman jan hankalin sa cikin salon k'issa da kisisina.



Bakinsa na rawa tsabar yunwa ya kai loma daya bakin sa, ya ma manta bai yi bismillah ba, wani lumshe ido yayi domin tunda yake bai taba cin abinci mai dadi dandano irin wanna ba...



Cikin sauri-sauri ya dinga ci... ya kusan gama cin abincin ya ga budurwan ta dawo wata mummunan hallita mai tsoratarwa, ta jefa masa wani kallo da jajayen idanunta kana ta bace bat.



Wani tashin hankali yaji ya shiga, abincin bakin sa kuwa ya kasa hadiye wa, bowl din hannunsa ma ya bace kamar a mafarki, wani sabon tashin hankali ya shiga, tamkar an yaye masa komai sai yanzu ya dawo cikin hankalinsa...

wata mahaukaciyar murdawa Cikin sa yayi, ya dinga ji kamar ana saka mashi ana huda masa cikinsa, zubewa kasa yayi ya rike wuyan sa da yake jin wata azaba a cikin ta, yayinda kumfa ya dinga bulbulowa daga bakin sa, tsananin azaba ya sa ya dinga shure-shure da kafafun sa.... Daidai lokacin ne su Hamdan suka sallame sallah idanun su ya kai wajen Danjuma da har ya daina shure-shuren, jikinsa ya saki alamun rai yayi halin sa, da wani mugun sauri suka yi kansa hankalin su a matuƙar tashe......




*Alhamdulillah!*
_*A nan na kawo karshen free pages na Hoorain mai kusumbi, ga mai son cigaba da karanta wa ya biya #300 ta wannan asusun 2261488155 Rukayya haruna zenith bank. Marasa bakin kuma zaku iya zuwa pos ku biyani #250 sai ku bawa mai pos #50 kuɗin charges din sa, na yi wanna ragin ne saboda mutanen da suka min maganar cewa basu da banki, idan kun biya sai ku nuna min shaidar biya ta wannan number'n 07082281566*_

_*Yan nijer kuma su min magana domin na gayamasu yanda zasu biya*_.



_*fadin zafin littafin nan bata lokaci ne, ya kunshi abubuwa da dama wanda baku saba gani a novels ba, wandanda suka sanni sun san salon rubutu na, sai dai wannan ya sha bambam, ina kaunar baku dukkanin littafina a kyauta, sai dai tanadin daya yi Hoorain yasa bazan iya sakin sa a free ba, dan haka ku hanzarta biya. Mu hade a original group Habibte's wanda a nan ne zan cigaba da posting ga wandanda suka biya*_



*Shin zaratan samarin nan zasu dawo da ransu*?


*Shin kusumbin Hoorain zai warke ta dawo cikakkiyar mace kamar kowa*?


*Shin akwai sauran kalubale da ƙaddarar rayuwa da zai sake shigowa rayuwar Hoorain*?


*Da sauran wasu tambayoyi dake zuciyar ku, inda duka amsoshin ku na tafe a paid book*.




_Sai na jiku, soyayyar da zasu nuna min kadai shine ku siyi littafin HOORAIN THE HUNCH BACK GIRL_.

_i love all my fans, known and unknown_💖🔐



Thank you for your patronage🙏🥰



NoorEemaan
07082281566





I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500

Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.

*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

5
6
7

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login