Showing 108001 words to 111000 words out of 136985 words

Chapter 37 - DIJE ƘARANGIYA

09 Apr 2026

1141

sabuwa na yi nan WALLAh🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️ tun kafin Zee ta gano ina masu leƙe ta shaƙo wuyana😅




Ina baran adduarku akan ALLAH ya baiwa Mahaifiyata lafiya mai ɗorewa😢saboda kwana biyun nan jikin sai a hankali😭





Akafta😝





D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Alhmdllh jikin Mummy ya yi sauƙi masha ALLAH, naji daɗin addu'o'inku sosai da sosai, hakan ya tabbatar man da cewa ni ma ɗin ashe kuna yi na😉, don da har na fara kishi da Dijen Baffah saboda yanda naga kuke sonta da yawa, shine na yi zaton kamar ta fini matsayi😅 ashe dai Ni ma ɗin ta ku ce ba algus tom Alhmdllh na gode sosai🙏🏻*


*Lamba ta 62*



Safwan ya bi ta da kallo baki a sake ya ce "wai ke me yasa ko kaɗan ba ki da hankali ne?, Yanzu ke ashe zaki iya kashe mutum da hannunki saboda kishi?"

Ta murguɗa masa baki tare da riƙe ƙugu tace, "kai da bakinka ka sanar da ni cewa ƴar aikinku ce, kuma daga kai har munafukar ƙanwar ta ka kun nuna man cewa ita ce ke sonka kai baka sonta, to yanzu kuma akan mi take bibiyarka? kuma sannan har ka bata damar da Ni ma da kake aure baka bani irinta ba? Ga shi ka janyo ta yi nasarar shiga tsakanina da kai, don na tabbata akanta ne kake raba daren da kake yi a waje, to WALLAHI ka ji da kyau ka ƙara ji matuƙar baka sanar da ita ta fita sha'aninka ba WALLAhi ka ji na rantse sai na watsa mata fetur na ƙoneta ƙurmus kowa ma ya huta da mugun halinta na bin Mazajen mutane, yar iskar banza baƙar karuwa ALLAH ya tsinewa iyayen da suka kawota duniya ma balle it.......... "

Saukar marin da ta ji ne a kumatunta yasa ta yi saurin haɗiye sauran maganar, cike da mamaki ta ke kallonshii hawaye suna sauka akan idonta ta ce

"My man ni ce na zama jaka a hannunka saboda matarka?, Yanzun ma kuma saboda da tsananin lalacewar akan wata ƙaramar karuwa ka ɗaga hannu ka mareni?"

Safwan ya yi saurin ɗaga hannun da nufin ya ƙara kai mata wani marin, me ya tuna kuma ya dunƙule hannun ya naushi iska sannan ya nunata da yatsa kamar zai tsole mata ido, jikinshi sai tsuma ya ke yi saboda tsabar ɓacin ran da ta cusa masa, ya ce

"Duk ranar da kika sake kiran Matata da sunan karuwa to WALLAHIL'AZIM kin ji na rantse a ranar zaki gano ainahin wanene Safwan, don kuwa sai na yi maki dukan da a RAYUWARKI kaf ba'a taɓa yi maki irinshi ba"

Sannan ya cisgo gashinta da ƙarfin gaske ta yi ƙara fuskarshi daf da tata suna kallon juna ido cikin ido ya ce

"Wannan da kike gani ita ce Matata Khadija kuma Uwargidana wadda kike da labarin na aureta tun kafin ke, zancen Ƴar aiki ya riga da ya wuce tuni don daman cen kawaici ne na yi maki na ƙi sanar da ke gaskiyar wacece, saboda kawai bana son ranki ya ɓaci idan kin ji ina da aure, to amman yanzu tunda har kin gano komi to kenan ɓoyon da nake maki ma ba shi amfani, saboda haka ki kwantar da hankalinki zan baki wata dama"

Ya fidda wayar da key ɗin da take ya damƙa mata wayat a hannu cikin fusata ya ce "karɓi ki shiga chat ɗina da ita da kike son ganin abunda ake yi maki ɓoyo kullum, to yanzu ki shiga duk inda kike so na baki wannan damar ki karanta komi kuma ki ga komi da idonki, kin ga kin hutar da ni akan duk wani labari da zan sake ba ki a yanzu kuma da gaba ma idan ta kama, na ba ki awa biyu ki yi duk abunda kike so saboda kawai idan kin ta shi kashetan sai ki haɗa da Ni, ke in ma da hali ki fara ta kaina kafin zuwan lokacin da za ki haɗu da ita itama ki kashetan"

Yana ƙare maganar ya fice ya barta da waya a hannu baki a sake kamar wata sakarya, idonta akanshi suna zubar da hawaye wasu bayan wasu, saboda tsabar baƙin ciki da takaicin da ya cika mata ciki, cikin sauri ta jefar da wayar kan kujera itama ta durƙushe ƙasa tana wani irin kuka gwanin ban tausayi.

Saboda izuwa lokacin ta fara yin nadamar biyewa son zuciyarta da ta yi ta aureshi, yanzu ga shi ba'a je ko'ina ba ta fara cin karo da takaicin auren mijin wata da ta yi, don ta tabbata inda Aminu ta aura to da babu yanda za'a ya yi mata irin wannan wulaƙancin akan wata mace, tuno irin renin hankalin da ta yi wa Aminun yasa ta ƙara sautin kukanta, don har awa biyun suka cika ya dawo bata daina kukan ba.

Ganin hakan ya ji jikinshi ya yi sanyi ya zo inda take ya ɗagota daga durƙushen ya zauna kan kujerar da ita a jikinshi yana bubbuga bayanta alamun ta yi shiru, saboda shi kanshi zuciyarshi cike take da ƙuncin da ya fi nata, saboda har ga ALLAH ba da son ranshi ya ke yi mata abunda ya ke yi ba, kawai dai don ya kasa controlling ɗin kanshi ne akan Dijen Baffah, shiyasa ya ke jin komi ma zai iya aikatawa in dai hakan zai farantawa Dijenshi, don izuwa lokacin ya fara fahimtar irin yanda take sonshi itama, kawai dai tana ɓoyewa ne don bata son ya fahimci itama ta yi kewarshi don wata manufa ta ta da shi bai gano nufinta ba, haka ya danne ta shi damuwar ya koma lallashinta har ya samu ta yi shiru sai dai ta ƙi cewa da shi ƙanzil har suka shiga bacci.

****

Haka rayuwar auren nasu ya ci gaba da zama yau fari gobe baƙi, duk da ya rage wasu abubuwa da yawa don kawai su sami zaman lafiya, amman kishinshi da Zee ta ke yi abu kaɗan ne zai janyo masu matsala sai an hau sama a dawo a shirya, don izuwa lokacin ita kanta ta matsu da su gama karatun su dawo gida, saboda tunanin da take yi yawan yi akan ita fa muddin bai canza hali ba idan suka dawo gidansu zata koma, ta sa Mahaifinta ya karɓar mata takardarta, don ba zata zauna ciyon zuciya ya kasheta da ƙurciyarta ba akan wata ɗiya macen da bata fita da komi ba.

Haka rayuwa ta yi ta shurawa sati ya zo ya wuce wata ya zo ya wuce shekara ta gangaro itama har ma ta nemi wucewa, sannu a hankali sai ga su Safwan sun kammala karatunsu, sun ƙara wasu watanni ne saboda su harhaɗa komi sannan su dawo, duk da turawa sun so su riƙesu su yi aiki da su ko na shekara ne, amman fafur Safwan ya buga kanshi akan cewa ƙasarsu za su koma itama ta moresu.

***

Dije kam a lokacin tana Ss 3 har ana cukucukun fara jarabawar candy, ga shi Hajiya Mama ta yi wa Safwan alƙawarin duk lokacin da zai dawo zai taradda ita cikin gidanshi, sai dai karatun da take yi yana so ya wargaza alƙawarin, don bata son ta dawo ba tare da ta kammala karatunta ba, amman duk da hakan da lokacin dawowarshi ya ƙaraso dole ba don dukansu sun so ba Aunty Ummin ta tattaro khadija ta dawo da ita Yola.


Hajiya ta zaunar da ita ta fayyace mata komi dalla dalla akan auren da Safwan ya yi ba tare da saninta ba, sannan ta sanar da ita alfanun kaita Abujar da ta sa aka yi don kawai itama ta san minene rayuwa, Dije tasha kuka saboda kishin auren da ta ji ya yi, amman sannu a hankali Hajiya tana ta tausarta tare da nuna mata cewa ita ɗin tana da damar dawo da Mijinta hannunta don ba'a fita da komi ba, sannan ne hankalinta ya ɗan kwanta ta ji sanyi a ranta ta saki jikinta, sai dai duk lokacin da ta tuna da wata mace a tare da shi sai ta yi kuka a ɓoye.

Hajiya Mama ta saki jiki ta gyarewa Dijen Baffah ɗakinta tamkar kowace yarinya mai gata a wurin iyayenta, itama kanta ta fara gyarata ciki da bayanta lungu da saƙonta, don takanas ta nemo wata Mata ta dinka tsima Dijen tun tana jin daɗin karamcin har ta kai ta fara nuna gajiyawarta, dole Hajiya ta ce a dakatar da komi sannan aka koma gyara mata jiki Dilka halawa duka ba wanda ba'a yi mata ba, jikinta ya dawo smuth har wani sheƙi yake yi, ga fatarta hutu yasa ta murje ta cire baƙin ta zama chocolate color, ga gashinta Kuma da kullum yake ƙara cika masha ALLAH, shi ma ba ƙaramin gyara ya ke sha ba a hannun Matar, Fiddo kanta ba Dijen ta burgeta saboda ganin yanda gaba ɗaya ta sauya tamkar ba ƴar ƙauyen da ta sani ba, saboda ta zanzare ta zama wayayyi ƴar boko musamman yanzu da Safwan ya ƙara buɗe mata idanuwa da salon Soyayyarshi, amman duk da hakan ba wata magana mai tsawo da ke haɗasu, saboda ita kanta a yanzu jinta take yi dai dai da kowa, musamman idan ta tuno da ita ɓangaren Amarya take shiyasa ma ko kaɗan bata shiga shirgin Fiddon matuƙar ba dolen dole ce ta janyo ba.

Ana gobe su Safwan za su da wo ne Hajiya ta saka Aunty Ummi da su Surayya da sauran wasu ƴan uwa suka yi wa Dijen rakiya gidan angonta Safwan, zuciyarta cike da farin cikin ganin wannan rana mai cike da ɗinbin tarihi a rayuwarta, saboda tsabar murnar ganin muhallinta har da kukan farin ciki Dijen ta yi, musamman da ta kalli ko'ina sama da ƙasa gabas da yamma Kudu da Arewa taga uwar dukiyar da aka narka mata, ta yi sha'awar ina ma ace Inna da Baffah'nta da ƙawayenta su ma su zo su ga muhallinta, ta ruƙunkume Aunty Ummi sai kuka take cisga, Fiddo kam sai wani yatsine yatsine take yi zuciyarta cike da jin haushin kwashe masu dukiya da Hajiyar ta yi ta zube a ɗakin Dijen, a ranta ta ƙara tabbatar da cewa lalle ba ƙaramin asiri su Baffah su ka yi masu ba musamman ita da SAFWAN ɗin.

Surayya tana dariya zuciyarta cike da jin daɗi ta yi mata raɗa a kunne sai ga Dije ta sunne kai cike da kunya tana dariya, saboda cewar da ta yi

"Ba wani kuka yarinya gobe iwar haka har kin mance da mu kina ta Mijinki"

Haka suka tasata da wasa har ta ware tana mayarwa Surayya suna gidan har dare sannan aka barta da Husnah da wata dattijuwar da zata riƙa yi mata hidima, haka ta kwana cikin farin cikin dawowar Angonta masoyinta kuma Malaminta Muhammad Safwanu JABB'I YOLA.






Ayyururui Amarya ta ango🥳






Akafta😝







D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Ruwan sharhin da kuke ta bugawa akan book ɗin nan ba ƙaramin daɗi yake sakani ba, saboda haka ku ci gaba da fafatawa ni ma in ci gaba da sambaɗo maku labarai😉😂*



*Lamba ta 63*



Tunda sassafe Surayya ta zo suka shiga kitchen sunata hidimar ɗora abincin tarbon baƙi kala kala, ko da sha biyu na rana ta yi duk sun kammala abunda ake buƙata, Dije ta je ta sullo wankan da sai da ta ɓata lokaci sosai wajen wanke ko'ina lungu da saƙo na jikinta, tare da ɗimama kanta da turarukan wanka masu daɗin ƙamshi, waɗanda a hankali har sun fara bin jikinta saboda yanda take yawan amfani da su akai akai tun dawowarta Abuja.

Bayan ta yi SALLAHr azahar ne Surayya ta zauna ta tsara mata kwalliya cikin tsari irin na wayayyun yan birni, kafin ka ce me sai ga Dijen Baffah ta fito sharr! Abunta cikin wata rantsattsiyar shadda golden color har sheƙin maiƙo take yi, ga ɗinkin da aka watsawa shaddar na stone work shuwari stone sai walwalniya suke yi ta ko'ina idan ta motsa, sannan ga danƙareriyar sarƙarta ta gold da ta ƙara ƙawata kwalliyar, wadda Hajiya ta bata a matsayin kyautar suruka lokacin da za ta zuwa gidan mijinta, ta sha manyan awarwaro da agogo tare da Zoben azurfan da ke maƙale a yatsanta na biyu, wanda ya ƙara fito mata da zarazaran dogayen yatsunta da suka sha ƙunshin jan lalle masha ALLAH.

Dijen Baffah ta yi kyau iya kyau kamar ka saceta ka tsere saboda wankan ya hau jikinta sosai ya zauna, suka fito harabar gidan sai ɗaukar photuna suke yi ita da su Surayya da Husnah, Fiddo kam latsar wayarta kawai take yi saboda fushin da take yi na tilastata da Hajiya Mama ta yi akan sai ta zo gidan, don ta so ta yi zamanta acen gida tunda dole a cen ne zasu fara zuwa su ga Hajiyar sannan su yo nan gidan.

Shiyasa tunda ta zo ba wanda ta shiga sha'aninshi sai sabgoginta ta ke ita kaɗai, yanda ta share kowa haka duk cikinsu kowa ya shareta suna ta harkokinsu.

****

Malam Safwanu kam suna fitowa jirgi ya ja numfashi ya shaƙi iskan ƙasarshi ta Nageria da ƙarfi tare da lumshe ido ya kallo Amaryarshi da ke gefenshi cike da wani salon da shi kaɗai yasan ma'anar kallon, ganin haka ta ƙara maƙale hannunshi da take riƙe da shi tare da ɗora kanta a kafaɗarshi tana murmushin itama, don on ready ko da suka sauko direba yana airport ɗin yana jiran saukarsu, shiyasa ba tare da ɓata lokaci ba ya kwasosu suka nufo unguwarsu Hajiya Mama domin su fara gaisawa kafin su je cen gidan nasu, Zee haka kawai ta tsinci kanta da faɗuwar gaba tare da jin kwatakwata bata son zuwa gidansu Hajiya Mamar, saboda tunaninta ya tafi ne akan cewa Dijen tana gidan, sai dai har aka gama gaisawa da juna cikin farin ciki da ɗoki tare da murnar ganin juna bata hango ko mai kama da Dijen Baffahn ba, taji daɗi sosai a ranta saboda tunaninta har lokacin tana cen Makarantar da aka ce tana yi, shiyasa ta saki jiki sai wasar baki take yi anata gaggaisawa kafin su yi sallama da juna su fito gidan, tare da rakiyarsu Hajiyar da Aunty Ummi da yaranta da wasu ma'aikata mata da suka biyosu suna yi masu addu'ar sauka lafiya, Safwan ya kalli Hajiyar bakinshi yana rawa saboda son tambayarta da ya ke yi akan alƙawarin da ta yi masa, cikin dariya Aunty Ummi da ta fahimceshi ta yi saurin faɗin

"Mun kai maka tana cen kai take jira"

Zee da ke mota tana wasar baki ba shiri ta ji ƙirjinta ya buga, duk da ce wa bata gano ma'anar inda maganar ta dosa ba amman ta yi wasiwasin cewa

_"Anya ba wannan mayyar yarinyar ba ce ake magana a kanta ba kuwa?"_

Sai gata da haɗe fuska tana dariyar yaƙe har suka bar gidan, cike da tsananin farin da jin daɗi Safwan ya riƙo hannunta ya ce

"Hajjaju ayi murna mun dawo ƙasarmu ta gado, sai hankali ya kwanta ga ki kusa da Daddynki da kullum kike ta faɗin kin matsu ki ganshi, tsorona ɗaya shine kada ace gulmata ce ake zumuɗin kai wa?"

ZEE ta yi dariyar yaƙe ba tare da ta ce komi ba, saboda faɗuwar gabanta da ya tsananta bugawa cikin sauri da sauri, har suka je bakin kantamin Gate ɗin gidan nasu bata ji natsuwa ta zo mata ba, hankalinta ya fara ta shi ne lokacin da Direban da ya ɗaukosu ya ke ta buga horn wani bayan wani alamun sanarwar zuwansu.

Ai kuwa kafin ma su je parking space ya ajiye motar sai ga su Surayya da su Husnah tare da Ruma ƙawar zee da wasu ƴan'uwanta biyu aguje sun fito, su Surayya daga sashen Khadijar suna ihun murnar dawowarsu, yayin da su Ruma suka fito daga nata sashen cike farin ciki, gaban Zee ya ƙire ya faɗi ba shiri ta yi saurin fitowa tana ƙarewa gidan kallon yanda aka ƙawatashi da sabon fenti, sannan ta dawo da kallonta ga su Surayya da suka maƙalkale Safwan suna murnar ganinshi, su Ruma suka ƙaraso wurinta cike da murna suna yi masu sannu da zuwa, Fiddo ta saki Safwan ta nufo Zee inda ta wani haɗe rai tana yi mata wani mugun kallo, ba shiri Fiddo ta sha jinin jikinta tare da wayancewa da dannar wayar da ke hannunta.

Cen sai ga wani taku da ya ja hankalinsu duka tare da shaƙo wani daddaɗan ƙamshin da iska ya kwaso ya shaƙawa Zee cikin hanci tamkar da gayya cikin lamarin, ta yi saurin kallon inda take jin sautin takun takalmin sai gata da dafe ƙirji ba shiri, cikin matsanancin faɗuwar gaba tare da dakan luguden da zuciyarta ta ke yi ne ta yi mutuwar tsaye, Dukansu suka ƙurawa Dijen kallo musamman ita da ta kafeta da ido ƙur har ta ƙaraso wurinta, cikin sigar duniyanci Dijen ta rungume Zee fuskarta ɗauke da fara'a ta ce

"Oyoyo Ƙanwata sannunku da zuwa da fatar kun iso lafiya"
Ta ƙare maganar tare da fesheta da wani sabon murmushin da Zee ta kasa gano ko na minene, sannan Dijen ta saketa ta nufi Safwan ɗin da tunda ya ƙyalla idonshi akanta gaba ɗaya ya susuce, yanda ya ke kallonta cikin shauƙin sonta da ke fisgarshi haka ita ma Zee ta bi ta da kallon mamaki, tare da su Ruma da suma ta zamo masu tv saboda kallo.

Dije kam tana zuwa ta yi saurin maƙaloshi tare da yin tsalle ta kai masa kiss a kumatu sannan ta faɗa jikinshi ta ruƙunƙumeshi sosai cikin wani tsantsar farin cikin ganinshi tana faɗin

"Am happy to see you my Husby, your welcome key to my life"

Daga Safwan ɗin har su Zee kasa ɗauke idonsu suka yi gareta saboda tsabar mamakin da ta ba su, duk da wani sashe na zuciyarshi yasan fiye da hakan ma zata iya aikatawa tunda har yasan kalar koyarwar da ya yi mata, sai dai ita Zee mamakinta ya Sha bambam da na shi don kuwa ita ƙarfin halin yarinyar take mamaki musamman da ta kirata ƙanwarta, amman kasancewar itama ɗin ba baya ba wajen kishi shiyasa ta yi saurin ɓoye kukan da ya zo mata ta nufi sashenta su Ruma suka dafe mata baya suka barsu anan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login