Showing 102001 words to 105000 words out of 397668 words
barar addu'ar ku_
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°
~Oum-Deedat ce~
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹
🌺🌺🌺🌺🌺
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>
*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_
*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_
*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._
*Page ~32~*
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°
Cikin sa'a kuwa lokacin da suka isa har dare ya rufa, duk da haka har yanzu Hajiya Kubra bata bar kuka ba, Bilal ɗinne ke bata baki, domin shi dama Alhaji Mustaphn cewa yayi suje zai taho daga baya sai ya tsaya ya bada cigiyar su Suhan ɗin.
Aiko suna isa asibitin suka hango Abie zaune bisa kujerar silver ya haɗe kanshi cikin ƙafafun shi, duk isar nan ta hajiya Kubra sai gata tana gudu zuwa ga Abie ɗin, koda ta ƙara sa ba tayi wata wata ba ta ɗago yaron nata ta rungume tana mai sakin kuka da tambayar inda mafi soyuwa a cikin yaran nata yake.
Da hannu kawai ya iya nuna mata ɗakin da yake kulle, saidai zaka iya hango komai ta fari tar ɗin glass ɗin da aka zagaye ɗakin dashi.
Da hanzarin ta ta saki Abie ɗin tana mai wucewa kaman zata faɗi zuwa jikin glass ɗin, da dukkanin hannuwan ta ta sanya ta dafe glass ɗin tana mai sakin wani tsumammen kuka, hango yaron nata da tayi samɓal, an jojjona mashi wasu na'urori wuyan shi ɗaure da wani abu kaman dai ya samu matsala a wuyan nashi, jikin shi suna sanye ne da bulan yadi, kwance yake samɓal, hatta da hancin shi toshe yake da abun shaƙar iska.
Bilal ma da yake tsaye ta gefen ta, hawaye ne suke ta zurarowa daga ƙwarin idanun shi, hnakalin shi a matuƙar tashe, saidai ya sanya hanky yana sharar kwallar lokaci guda yana jan majina.
Abie ɗinne ya matso yana mai janye mahaifiyar tashi jin ta fara surutai marasa ma'ana, baya so yaji tana ba yayan nashi guda ɗaya tal mutuwa, yafi so ta bishi da addu'a.
Bilal har yanzu bai bar bakin glass ɗin a, yana tsaye hannayen shi soke cikin Aljihu, Alhaji Mustaphan ya kira wayar shi yana tambayar shi jikin Moh'd ɗin.
Sanar dashi kome ake ciki yayi, sun ɗan tattauna kaɗan Bilal ɗin ya nemi da alhakin yayi haƙuri zai kira shi anjima, hango wasu Police su uku da yayi suna nufo ta inda suke.
Suma bakin glass ɗin suka tsaya suna ɗan nazari haka kaɗan, sai kuma suka juya suka ba Bilal ɗin hannu, ganin haka ne ya sanya Mom ɗin tasowa ita da Abie.
Cewa sukayi idan ba zasu damu ba suna so a basu mutum ɗaya zasu je dashi office domin akwai ƴan binciken da suke so zasuyi.
Ba damuwa Bilal ɗin yace masu yana mai ƙoƙarin bin bayan su ne likitan ya ƙara so, shima hannu suka sha dashi suna mai bashi umurnin ya buɗe masu ɗakin zasu yi wani ɗan bincike.
Bawata gaddama likitan da yake farar fata ya shiga buɗe masu ƙofar, shiga sukayi suna ƴan dube duben su da kuma ɗauke ɗauken hotunan su, sannan suka buƙaci likitan da yayi masu ɗan ƙarin bayani dangane da ciwon na Al'ameen ɗin.
Nan ma ba gaddama ya shiga masu ƴan bayanai, duk abun nan da akeyi billa da su Mom ɗin suna cen waje suna hangen su, bayan kammalawar su ne, suka fito tare da cewa bilal ɗin ya biyo su suje.
Bayan sun isa ne suka shiga yi mashi bayanin accident ɗin da yanda ya faru da kuma kyautata zaton da sukayi cewa lallai da sa hannun wasu akaso aga bayan Al'ameen ɗin, domin dukkan abubuwan da akeyi camera ta sirri cctv tana naɗar komai, tin daga zuwan motar zata gitta har zuwa lokacin da suka ga motar ta tsaya dreban ya fito yana dudduba motar alamar matsala ta samu, da lokacin da Al'ameen ɗin ya fito daga motar yaja gefe ya tsaya, sai suka ga dreban ya matsa kusa da Al'ameen ɗin ya mashi magana, sai kuma suka ga Al'ameen ɗin na gyaɗa mashi kai yana mai duba agogon da take ɗaure wutsiyar hannun shi ƴar traveling bag ɗinshi na a hannu.
Ba suyi aune ba sai suka ga mai motar na tsaida wata taxi dreban ya fito suna magana, shi dai Al'ameen na tsaye gefe yana ta famn duba agogo, sai suka ga wannan mai taxi ya ɗaura igiya yaja taxi ɗin da Al'ameen ɗin ke ciki, sai kuma camera ta ɗauke ɗif, lokaci guda kuma ta kawo biji biji haka sai kuma ta koma normal, to fa a lokacin ne suka hango wata mota tayi sama sama da Al'ameen ɗin ta tsere, ko numb ta ba'a gani yayin da shi kuma Al'ameen ɗin ya faɗi ƙasa yana murmula sosai, jini duk ya wanke mashi jiki.
Salati bilal ɗin ya saki, yana mai miƙewa tsaye hannayen shi goye a bayan shi. Bai a san yana kaiwa da komowa ba, har saida ƴan sandan suka buƙaci da ya zauna.
Zama yayi yana mai sauraren su, lips ɗinshi cikin bakin shi, domin kanshi ya riga ya kulle, bai ma san wane kalar tunani zai yi ba kuma.
Nna suka buƙaci da ya sanya hannu akan binciken da suke yi, sannan ya basu haɗin kai duk lokacin da zasu buƙata gami da ƙoƙarin lalubo su victims ɗin, sannan ba zasu iya kammala bincike ba har sai Al'ameen ya farfaɗo sun ji daga bakin shi.
Haka ya koma asibitin wurin da su Mom ɗin suke, nan dai ya sake iske su, duk da dare yayi Amman likitocin sun hana su shiga, saida suka ga lallai lallai anan zasu kwana ne ya sanya suka basu ɗakin kusa da na Al'ameen ɗin da yake empty saidai zasu iya hango dukkan Abunda ke wakana a cikin ɗakin.
To koda dai suka shiga ma kasa taɓukabkomai sukayi, yayin da bilal ɗin har yanzu hankalin shi a tashe, to wanene ke son ganin bayan aminin nashi a ƙasar ta amurka da take ba baƙuwar su ba?
Mom ma saida ta tambaye shi, bai ɓoye mata komai ba, ya zayyana mata dukkan Abunda ke faruwa, wani kukan ta saki, tana mai tsine ma dukkanin mai hannu acikin son salwanta mata Rayuwar yaro
(Hmmmmmmm)
*****************************
Atare da umman tawa suka rankayo har ƙofar gidan da nake tsaye, da yake tin lokacin da naji suna shirin fitowa na ruga da gudu cikin sanɗa na fice a gidan.
A tsayn suka tadda ni, har yanzun ba wai malam ɗin ya gama yadda bane, haske ni yayi da acibalbal ɗin da take saura ƙiris ta mutu saboda iska da hunturun sanyi.
Ƙure ni yayi da ido, shi dai a gaskiya ba zai iya sheda ni ba, Maryamar kawai zai iya ganewa shima kuma ƴar kamar ce da kuma muryar, sai kuma hasken da take ɗauke dashi har yanzu, Amman gashi girma ya kama ta, ba kaman da da take ƴar matashiya ba.
"Yarinya zo mu shiga gida kinji? Nan akwai sanyi sosai" cewar malam ɗin da yake ta ƙoƙarin sai yaga fuska ta cikin ɗan hasken farin watan daya hudo, da yake tini ƴar acibalbal ɗin ta idasa mutuwa.
"Kayanmu fa baba?" na faɗa ina mai zuƙunnawa na kinkimi ƴar gana mustgo ɗin da kayan sawar mu yake ciki.
"Eh fa hakane, tau ku kwaso mu shiga daga ciki, akwai sanyi nan ba mun tsaya nan ba, banda haka ma yanzu masu farauta zasu fito, kuma akwai matsala idan suka gammu nan"
Ya faɗa yana mai zuƙunnawa shima ya ɗauki wani ƙaton ƙwali da kayan provision ɗina na makaranta suke ciki.
Jin hakan ne ya sanya jikin mu fara ɓari, tsoro ya kama zuciyar mu, da sauri muka shiga jifar kayan har zuwa cikin gidan, saida muka kwashe tas ne sannan ya maida ƴar ƙofar wacce aka yi da zallan kara da itatuwa ya saya gidan.
Tsakar gida muke tsaye, hakan ya bani damar ƙare ma gidan kallo, ƴan ɗakuna ne guda uku kaman rumbu, sai madafa da take gefe guda da bayan gidan da idan kana wanka ka miƙe tsaf za'a hango rabin jikinka.
Shi kau Malam wucewa yayi zuwa ɗakin yana faɗin "Hajjo fito ki buɗe masu wanga ɗakin da yake haka su sanya kayansu, duk da yayi ƙura a kakkaɓe shi a haka zuwa wayewar gari, bari in kaɗa masu lagwani suga haske"
Fitowa tayi tana faɗin. "To malam" Amman fa har yanzu ɗari ɗari take yi damu, ƴar dattijuwa ce itama don zata fi ummata da kaɗan amman, wucewa tayi kai tsaye zuwa ɗakin da yake gefen nasu ta fara kiciniyar buɗe shi, ga dukkan alama ma ana jimawa ba tare da buɗe ɗakin ba.
Ƴar fitilar acibalbal ɗin da ta sake kunna wa da ita tayi amfani wajen buɗe ɗakin da haska shi, duk da ba wani haske ne ya wadata ba, ga dukkan amu ma dai basa da wata fitila da tafi wannan Aci balbal ɗin.
Kayanmu muka fara kwasa muna kaiwa zuwa cikin ɗakin da sai mun duƙa zamu iya shiga, masalan ma ni da nake da ɗan tsawo.
Har yanzu dai bata tanka mana ba, da gani dai a tsorace take damu.
Ɗakin kam yayi ƙura, a haka ta koma ta ɗauko mana tsintsiya ta kakkaɓe mana muna tsaye gefe ni da ummata da har yanzu bata wani kula ni.
Ƴar yalolon tabarmar kaba ce shimfiɗe a ɗakin dagani dai ana nufin a bisa ita zamu kwana, gashi ba wani girman kirki ne da ita ba, sai ɗan yalolon filon da ta shigo mana dashi guda ɗaya a hannun ta riƙe da ƙwarya mai kyau da fura ciki wadda tasha nono kindirmo.
Zama mukayi muna bismilla, cikin mu ma babu wanda yabi ta kan furar, daf da zata fita ne ummata tace mata "Hajjo muna so muyi salla ne"
Da to tabi umman tawa tana fita, bata daɗe ba ta miƙo mana ƙatuwar buta ta tasa cike da ruwa, amsa umman tawa tayi tana mai ficewa daga ɗakin.
Zurut na tashi ina mai biye bayan ta, domin Nidai harga Allah tsoro nake ji, bata ko kalle ni ba, da yake ta san kan yanda gidan yake bayan ɗakin kawai ta nufa ta kamo ruwa gami da fitowa ta ɗaura Alwala, bayan ta gama ne ta miƙa man da niyyar nima inyi.
Amsa nayi ina mai cewa "Umma Don Allah ki jiran in gama, wallahi tsoro nakeji" bata ceman ƙala ba sai ma ja da tayi gefe ta tsaya tana mai bin ko ina na gidan da kallo da dukkan alamu dai tana fahimtar ba'a samu kowanne sauyi ba acikin gidan illa ma ƙara ruɓewa da gidan yayi.
Koda na shiga bayin, rasa inda zan zuƙunna inyi fitsarin nayi, domin ko ina ƙasa ce kwance, a haka dai na samu na raɓa nahau wani shimfiɗaɗɗen dutsi mai ɗan tudu da aga alamar wanda ake zama ne bisa in za'ayi wanka.
A kanshi na hau na tsula fitsari na, na gama na fito tare da ɗaura Alwalar sannan muka ranka ya zuwa cikin ɗakin.
Har muka gama salla babu wanda ya kuma shigowa, ganin hakan da mukayi ne ya sanya muka gane ba zasu dawo ba, sakaya ɗakin mukayi saboda sauro gashi babu maganin sauro, mu kuma namu dake cikin kaya yana cen ƙasa bama mu san ta inda zamu fara neman shi ba.
Hakanan dai muke zaune, cikin mu babu wanda yake da niyyar kwanciya, ganin hakane umman tawa ta miƙe gami da zaro wani zaninta cikin Ghana must Go ɗin tamu ta shinfiɗa mani gami da cewa idan ba zan sha furar ba in kwanta in huta.
Allah sarki mahaifiya, duk duniya babu yake, haka nan kasa kwanciya, itama ta kasa kwanciya, tana ta ƙare ma ɗakin kallo.
Cen kaman an buɗe mata baki an zaro maganar Naji tace
" *Anan fa aka Haifeki* "
Ai bansan na zabura ba na tashi tsaye, har saida Naji tace "to miye na tashi tsaye? Ni kar ku faɗo mani"
Sannan ne fa na koma na zauna, tinani fal cikin raina da tarin tambayoyi.
Ban ce mata ƙala ba, sanin halin ta da nayi, yanzu ina iya tambayar ta cibi ya zama ƙari, koma ta fasa faɗa man Abunda tayi niyya.
An kusa awa bata ƙara ceman komai ba, sai nice nayi shahadar fitowa in mata maganar karatuna ganin mun samu lokaci mu da ita.
"Umma ya maganar makaranta ta? Ki taimaka mani umma kada wannan damar ta kucce mani, bani da kowa sai Allah sai kuma ke, wannan karatun da zanyi zai taimaki Rayuwar mu ya tallamu ta ni dake baki ɗaya"
Shiru tayi tana mai nazarn kalaman nawa, cikin tausaya wa irin na uwa ta buɗe bakin ta ta shiga cewa
"Mamana, nice nan na yarda kiyi karatu, saidai kuma yanzu bana buƙatar karatun ki a waccen makarantar da suka sanya ki, dukkan Abunda ya shafe su ma bana buƙatar shi atare damu, kuma inaso kiyi mani Alfarma da alƙawalin cewa zaki manta dasu duk kansu, kuma ki binne labarin su da babinsu a Rayuwar ki"
Gabana ne ya tsananta bugu, me umma ke nufi, Amman dai koma minene tinda Naji tace zata barni inyi, ai ina tinanin zai zo mani da sauƙi
"To umma hidimar karatun fa waye zai yi mani? Kada ki manta fa, nan ba aiki mukeyi ba, ba kuma albashi ake bamu ba, umma Meyasa kika zaɓi mu baro cen gidan dukkan irin muzguna mana da akeyi, kika zaɓi muzo nan muyi Rayuwar mu?"
Na faɗa ina mai saddar da kaina ƙasa domin bansan da irin ɗauka da fassarar da zata yi ma maganar ba.
" Hauwa'u ke yarinya ce har yanzu, ba zaki gane ba, ba zaki fahimta ba, Hajiya Kubra bata da zuciyar imani, ta sanya su Hajiya Sa'a suyi dukkan yanda zasuyi mubar gidan nan, har Rayuwar mu ma zata iya Sanyawa a hallaka saboda tana tunanin ke ɗinnan zaki mallake mata yaro ne, a yayin da take kallon shi ɗin yafi ƙarfin ki ba sa'an yinki bane, ni kuma na kwammace mu bar gidan tin kafin mu nemi rasa Rayuwar mu a karo na barkatai, ki bar maganar su, dasu da Abunda ya shafe su gabaki ɗaya yanzu bana son maganar su, Alkhairin da Alhaji da Shi Ameenullahin yayi mana Mungode Allah ya saka, Amman bana kyautata zaton akwai Abunda zai ƙara haɗa mu dasu"
Tinda ta fara magana bata tsaya ba, haka kuma bani take kallo ba, hasali ma idanun ta a kulle suke gam, nikau da kwalla take shatata da zuraro mani sai faman ajiyar zuciya nake sauke wa,
Ban aune ba naji ta sake cewa
"Karatun ki Allah ne zai yi mana, Allah ne zai bamu iko da Abunda zakiyi karatun dashi, Mamana inaso ƙibar sanya ma ranki cewa dole sai dasu ne zamu iya, inaso ki sani su ɗin da Allah ya basu kuma ba zai manta damu ba, kiyi ta addu'a komai zai zo da sauƙi insha Allah, wannan halin da muke ciki zai zama tarihi da izinin wanda ya halicce mu"
"Ameen Umma"
Shi kaɗai ne Abunda bakina ya samu ya iya furta wa, duk kuwa da tarin kaman da suke cikin shi.
Kusan a haka muka kwana zaune, kowa da Abunda yake saƙawa, saidai daf da asuba ne wani nannauyan barci ya kwashe ni, cike da mafarkai masu ban tsoro kuma duk Al'ameen ne nake hangowa a ciki, koda na tashi na tadda har gari ya fara wayewa, sanin da ummata tayi cewa baccin na gajiya ne ya sanya bata tadani ba, ta bari idan na tashi nayi sallar.
****************** To kusan muce yanda su Suhan ɗin suka kwana zaune cikin ƙututun ɗaki, haka suma su Umman suka kwana, duk da ga gado ga Ac Amman hakan bisa ɗaya daga cikin su ya runtsa ba, gashi kuma Al'ameen ɗin fa har yanzu bai motsa ba, haka umma ta kwana a tsaye jikin glass, Allah ya isa dai Suhan tasha ta, domin ita a gani ta duk itace sila ko ince sanadin da ya sanya Al'ameen ɗin yabar ƙasar tashi, gashi yazo ya haɗu da mahassada masu neman ganin bayan shi, ai gara ma da ta tafi cen daga cen ayi cen insha Allahu ba dai yaron nata da wannan matsiyaciyar yarinyar ba ƴar matsiyata.
Saidai likitocibsu shiga su dudduba shi, gami da gyara mashi kwanciya su fita, Abunda ya ƙara ɗaga hankalin su shine ganin da sukayi wasu gungun likitocin kusan su biyar sun rugu a kanshi, dagani ma manyan likitocin ne da ba'a asibitin suke aiki ba kiran su aka yi.
Bayan sun gama ne suka fito su duka, fuskar su babu walwala suka ce su Mom ɗin su biyo bayan su zuwa office ɗin.
Hajiya Kubra ce da bilal ɗin suka bisu, yayin da aka bar abie nan zaune yana hango Al'ameen ɗin.
Bayanin komai sukayi masu, ai tini Hajiya Kubra ta rushe da kuka, tana cewa "wai ina Alhaji ne? Yazo yaji, yazo yaga yaron nan kada ya mutu, me ke damun Al'ameen haka da har ciwon zuciya ya kama shi har ta kumbura? Tunanin me yake yi haka? Me ya nema ya rasa? Bilal kira man alhajin kace don Allah yazo yaji Abunda likitocin nan ke faɗi.
Ai