Showing 123001 words to 126000 words out of 397668 words

Chapter 42 - BAN FI KARFIN TA BA

Oum Deed   

10 Sep 2025

21748

sai gobe in wuce"


Ta faɗi hakan ne tana mai miƙewa ta ɗauki jikkar ta, hankalin ta kwance, ga fara'a har yanzu saman fuskar ta, tabbas yanzu ne Salim ya samu mata ɗaya da ɗaya, yanzu ne take tunanin zai samu kwanciyar hankali da walwala a tattare dashi, tabbas ta shaida cewa kuɗi ko mulki basa sanya kwanciyar hankali muddin baka tare da iyali mai natsuwa da sanin ya kamata.

Har wajen mota na raka ta, wannan karon Sir Salim ɗin yana gefe shida wasu ɗalibai suna magana, dreban kuma ya buɗe gaban motar ya shiga sai faman gyangyaɗi yake.


Hangomu da yayi ne tafe hannuwa na riƙe cikin na umman tashi ya sanya shi sakin murmushi, sannan ya sallama ɗaliban da suka same shi akan yayi masu afuwa basu samu rubuta accessment nashi da yayi jiya ba.

Ƙarasowa yayi yana mai faɗin


"Lallai Ammi naga alama yarinyar nan rana neman ƙwace man fada, gaskiya ba zan yarda ba, da sakyal gaskiya"


Ya faɗa cike da shagwaba, ni sai a ya bani kunya, ɗan murmushi nayi na gefen baki, ina mai yima Ammin sallama da ya buɗe mata bayan motar ta zauna, tana mai miƙe mani fara ƙar ɗin emvelop, ban amsa ba, sai shine ya amsa yana mai godiya cikin zaulaya, ga dukkan alamu ya saba zaulayr Ammin tashi kuma tana ji dashi matuƙa gaya.


"Ka kiyayeni fa Son, na faɗa maka kada kayi ƙoƙarin shiga tsakani. Suhan jeki kiyi Lecture ɗinki mun sanya ki makara, sai munyi waya"

Ta faɗa tana mai jan murfin ƙofar ta rufe


Juyawa nayi ina mai mata sallama gami da ɗaga mata hannu, ban bi ta kan emvelop ɗin da ta bani ba, wadda Sir Salim ɗin ya zura ta cikin Aljihu gami da zagayawa ya shiga kujerar mai zaman banza dreban yaja motar suka ɗaga.


A haka na isa hall ɗin, raina fari tas, ko ba komai matar ta nuna mani ƙauna, ta nuna mani zallar soyayya kuma ta soni da yaron nata, ba kaman hajiya Kubra ba, mai ƙyamatar mu, mai zallan son zuciya, mai ɗaukar talaka ba a bakin komai ba, zullumi na ɗaya da tace wai gidan mu wurin ummata zata kwana, gashi ba waya balle inyi maza in kira umman tawa asamu a shirya mata wani abu ko kuma a san inda za'a ajiye ta ta kwana.

Da haka har aka tashi lecture ɗin na koma ɗaki su Raihana ɗinne masu ceman gaskiya sun yaba da kirkin matar ganin yanda ta amsa masu fuska sake duk da ita ɗin wata ce ga dukkan alamu.


Wannan ne ya sanya ranar nayi kwanan farin ciki da na rabu dayin irin shi a rayuwa da tin bayan shuɗaɗɗen lokaci a gidan su Ya Ameen ɗin. Ban kuma jin ɗuriyar Sir Salim ba har nayi bacci ina ta faman tinane tinane, yanzu fa suna nufin Sir Salim shine mijin da zan aura nan da wani lokaci ƙanƙani kenan? Ya zama saurayi na kenan a karon farko a rayuwa ta, wata irin kunyar shi ce ke kwarara a sassn jikin nawa duk kuwa da cewa baya a tare dani.


Su ma su Raihanan da murmushi suka dinga bina, ganin da sukayi ina cikin farin ciki, duk sai suka ji daɗi, kasancewar kanmu a haɗe yake babu wanda ke shiga hidimr wani gudun samun saɓani.



****************



Kai tsaye gidan hafsat ya nufa, ko gida ma baya jin zai iya zuwa har sai yaje gidan ta ta bashi cikakken bayani.

Tana zaune shirim da uban ciki a jikin ta taji ana latsa door Bell, da ƙyar ta ɓaɓɓaka ta nufi ƙofar gami da leƙa wa ta ƴar ƙofar da zata sada ka da mai latsa doorbell ɗin, to saidai bata ga kowa ba, hakan ce ta sanya ta buɗewa domin ta san ba abun cutar wa bane tinda akwai mai gadi.


Baya tayi mana zata faɗi ganin ko wanene, sanye yake cikin ƙananan kaya, baƙin wando ne, sai rigar polo kalar sararn samaniya, idanun shi daɗe cikin baƙin glass sosai, fuskar nan babu alamun walwala ko annashuwa tattare da ita, yayi fari tas ya ƙara kyau, fatar nan tashi har salƙi takeyi ga baƙa suɗik ɗin gargaza da ta samu wuri ta lafe abunta, kan nan kuwa nashi yasha gyara yayi luf dashi har ya kusan sauka ƙyeyar shi, da gani dai sumar nan tana shan gyara yanda kasan ta shahrokhan ko Omair na cikin tarkon ƙauna.


Hannu ya sanya ya taro ta, ganin yanda ta firgita har tana neman faɗuwa ga uban ciki a jikin ta.

Saida ya tabbatar da ta daidaita tsayuwar ta, sannan ya sake ta tyaa mai raɓeta ya shiga ciki zuwa falon kai tsaye.

A hankali ta maida ƙofar ta kulle, ta shiga bin bayan shi, saidai kafin ta zauna ta wuce kitchen ta haɗo mashi abun Sanyawa a baki da lemo da ruwa ta kawo mashi ta janyo stool ta ɗora bisa, haɗi da zama tana mai gaishe shi cikin rawar murya.


Bai ko bi ta kan abunda ta ajiye mashi ba, ya sanya hannu ya matsar da stool ɗin gefe, yana mai ɗan zamowa daga bisa kujerar alamar magana zasuyi mai muhimmanci, haɗi da amsa mata gaisuwar a gaggauce.


"Magana zamuyi Hafsat, tinda Naji kina kuka na san da akwai wani abu dake faruwa, ki natsu Hafsat ki gaya man dukkanin abunda ya faru bayan tafiya ta, muddin kinsan wani abu ban yarda ki ɓoye man shi ba komin ƙanƙantar shi"

Ta ruɗe ita ruɗewa, yaron dake cikin cikin ta ne ya shiga dunƙukewa yana curewa wuri guda saboda tsabar kaɗuwa da tayi, gashi kuma Dad ya hana a sanar dashi komai, idan aka ji a bakin ta yaji, ita yanzu ina zata sanya kanta

Lura da hakan da yayi ne ya shiga kwantar mata da hankali yana mata alƙawarin babu wanda zaiji cewa a bakin ta yaji, kai babu ma wanda zai san ya shigo ƙasar in ka ɗauke ta da Bilal shima idan ya kama ya sani kenan.

Saukowa tayi ƙasa haɗi da zama bisa tiles inda zata fi jin daɗi daɗi, sannan ta miƙe ƙafar ta, ko ba komai tana so ya nemo mata Suhan ɗin, tayi kewar ta sosai, tana tausaya ma rayuwar ta, bata so ta shiga wani mugun halin ko kuma yana yin da zai iya Sanyawa ta faɗa cikin wata Rayuwar, duk da kasancewar umman tata mace tsayayya.


A hankali ta shiga warware mashi dukkanin Abunda ta san ya faru bayan tafiyar shi, har kawo inda ake yanzu, kuka take wiwi tinowa da Ƙawar tata da tayi.


Tini kalar idanun shi suka cenza, wata jijiya ta taso mashi raɗau bisa kai, yayin da kanshi yake ta sa rawa, idanun nan kuwa sunyi jawur, hannun shi ya dunƙule yana bugawa a cikin gudan cikin tsananin tashin hankali, lallai aiki ja ya ganshi, duk inda suka shiga a faɗin ƙasar nan dole ne ya binciko su, ashe burin da Mom ɗinshi ta ɗauka na ganin sai sunbar gidan, bata barshi ba, Meyasa Bilal ya ɓoye mashi? Shi a tunanin shi zai nemo su ne, ya maido su ba tare da shi ɗin ya sani ba? Wannan itace amanar daya bashi? Lallai kuwa Mama Talatu zata gane kuren ta, tabbas dole ne dukkan mai hannu acikin wannan al'amari ya gane kuren shi, koda kuwa Mom ɗin tashi ce ba zai lamunci wannan zaluncin ba, yarinyar marainiya da ita ace ba za'a tausaya mata ba, har sai an koresu an raba su daga inda suke samu suci abinci.


Miƙewa yayi a matuƙar fusace da niyyar ficewa, bata san lokacin da ta miƙe ba tana mai taro shi gami da shiga yi mashi magiya akan ya rufa mata asiri.

Da dukkan hannuwan shi ya sanya ya tallabo fuskar ta, sannan ya shiga cewa


"Hafsat kar ki damu, ba zanyi Abunda zai sanya ki shiga matsala ba, hasali a yanzu ba guda na nufa ba, zan bar garin ne baki ɗaya in shiga neman su da kaina, ko Bilal bana so ki faɗa mashi nazo kai koda kuwa ace Sadeeq ne tinda kinga shi ɗin abokin shi ne"

Da alamar gamsuwa ta shiga jinjina mashi kai, tana mai zame fuskar tata ta shiga buɗe mashi ƙofar gami da cewa "Allah ya tsare hanya Yaya sai munyi waya"

Har bakin gare ta raka shi, da yake ba da mota yazo ba, har ya fice tana mai kallon shi zuciyar ta a matuƙar cunkushe, saidai ma ko menene ta san lokacin gano su Suhan ɗinne yazo, kuma tayi matuƙar farin ciki da hakan.

Saida taja ma mai gadi kunne akan kada ya faɗa ma Sadeeq ɗin Ya Ameen ɗin yazo, sannan ta juya cikin gidan tunani fal a ranta...



*******************



Ya matuƙar daɗewa a cikin makarantar, duk inda yake sa ran zai nemo wani bayani daya Ƙunshe ta ya kasa samun cikakken bayani saboda tsaro, kusan yini yayi yana zarya ofisoshin makarantar, babu wani cikakken bayani dai, rashin sani, kuma ta gaban shi Suhan ɗin ta wuce zuwa masallaci da niƙab a fuskar ta, Sam bai gane ta ba, bai fahimci komai ba, tinda bai kawo ma ranshi komai ba, itama ɗin bata lura dashi ba, tinda yana ta cikin mota ne zaune, har ya gaji yabar makarantar zuciyar shi na raya mashi cewa Suhan ɗin na kusa, kuma tana cikin makarantar idan dai har Umman tata ta barta akan ta cigaba da zuwa makarantar.

A haka yaja motar shi ya fice, zuciyar shi cunkushe, ya kusan kai kwana nawa yanzu yana shigowa makarantar ko zai dace da ganin ta, Amman babu wani labari.

Ya yanke hukuncin komawa abujan ko kuma yaje ya roƙo Hajiya Kubran akan cewa idan tanada masaniyar inda suke ta taimaka mashi ta bayyana masu, ko zasu samu su fita daga cikin halin da suke ciki tin kafin aminin nashi ya Samu labari.

Ya yanke shawarar nan da zuwa wani lokaci kaɗan, idan har bai ganta ba, to fa zai shaida ma Ameen ɗinne asan wacce za'ayi, domin barin kashi a ciki baya maganin yunwa, ya gaza, ya gaza cika ma aminin nashi alƙawarin daya ɗauka, kunyar abokin nashi tana cike a cikin zuciyar shi tin kafin ma su haɗu.



********************


A tare suka isa ƙauyen da Sir Salim ɗin, da taimakon shi ma ne suka samu suka gane gidan, da kallo ita kanta Hajiya Khaltum ɗin tabi gidan, to saidai koma menene su dai sun ji sun gani kuma a haka suke so, ba kuɗi ne matsalar su indai za'a amince a basu auren yarinyar da ta kwanta mata arai fiye da duk wata ɗiya mace da ta gani tana son yaron nata.


Da sallama ta shiga gidan, yayin da tabar su Sir Salim ɗin nan jingine jikin mota.


Umma ta ce zaune tana tanƙaɗen dawa, ita kuma Hajjo tana iza wutar miya bisa murhun duwatsu da yake cen madafa.


Da ɗan sakin fuska umman tawa take amsa mata sallamar da tayi mata, ko ba'a faɗa ba ta shaida umman tawa, hango tsantsar kama dake saman fuskar tamu, da kuma sanyin dake tattare damu daya kasance iri ɗaya.

Ajiye tiren tayi ƙasa gami da yima matar maraba, duk da bata shaida ta ba, tabarmar kaba ta janyo gami da shinfuɗa mata daga gefen ɗakin namu.

Cikin mutunci suka gaisa harda Hajjo data fito, itama ganin bata shaida ta ba, ya sanya ta janyo kujera ƴar tsugunno ta zauna kaman yanda taga umman tawa tayi.


Sake sabuwar gaisuwa sukayi, yayin da Hajjon ta miƙe ta ɗebo mata ruwa cikin kofin silver sai ɗaukar ido yake.

Ga mamakin su Umman tawa, matar kafa kai tayi tasha ruwan nan a haka da yake fari fat duk laka a cikin shi, wai nan haka ma don sai sun dafa suke zubawa a randar ya kwanta.

Hajjo da umma ce suka kalli juna, saidai basu ce komai ba, har ta gama sha ruwan tayi hamdala tana mai cewa "Aikuwa Ruwan fa da daɗi gwanin garɗi"


Su dai da kallon mamaki suka bita, gata dai ƴar gayu Amman bata da jin kan masu kuɗi.

Hajjo ce tayi ƙarfin halin tambayar ta daga ina take?

Ɗan murmushi ta sake saki tana mai cewa "Eh gaskiya ba zaku shaida ni ba, kaman yanda nima yau ne karon farko ɗana sanya ku a idona har ita ɗiyar tawa, Sunana Hajiya Khaltum, kuma nice Mahaifiyar Salim Bawa, malamin su Suhan yarinyar wajen ku"

Toh fa!


"Ikon Allah, yaron kirki kuwa ɗan albarka, Allah dai ya biya shi abun alkhairin da yake yi mana, yana ta ɗawainiya da yarinyar tamu". Cewar Hajjo da yanzu ta shaida ko wacece matar kuma sai yanzu ne ta hango ƴar kamar da suke yi.


Umma ta ma saida tayi mata godiya sosai, tana mai cewa Salim ɗin ya shigo mana, ai yanzu ya zama ɗan gida, bayan Ammin tashi ta shaida masu tare suke ma.

Harda dreban Hajjo ta leƙa tace su shigo, suma tabarmar kabar suka shimfiɗa masu suka sake gaggaisawa, shi dai Salim kanshi a duƙe yake duk kunyar ummata ta cika shi, duk da har yanzu bata san me ke tafe da su ba.


Shaida ma Ammin sukayi akan cewa zasu fita cen hanya ko zasu samu Hotel ɗinda zasu kwana, kafin zuwa goben su wuce.

Da to tabisu yayin da sukayi sallama dasu umman tawa suka fice, har Hajjo ke ce masu ba zasu tsaya suci tuwon dawa ba?


A kunyace suka ce sun ƙoshi, gami da shiga motar su suka bar ƙauyen, hakan ce ta sanya Ummata da Hajjo gane cewa anan gidan matar da ta kira kanta da Hajiya Khaltum zata kwana kenan, Hajjo ce ta karɓi girkin daren, yayin da Ummata ta shiga ɗakin nata domin gyara mata inda zata kwanta daidai ƙarfin ta.

Har aka gama tuwon aka kwashe babu abinda ya tada Hajiya Khaltum sai Sallah, bayan ta gama ne ta jawo wani mai, wanda ke hana sauro cizon mutum duk ta shasshafa jikin ta, dama ummata ta shigar mata da ƴar ƙaramar jikkar ta ɗaki. A haka aka gama tuwon aka zuba mata, nan ma babu wani ƙyanƙyami taci abunta hankali kwance, harma tana zuba santin cewa ta daɗe bata ci tuwon dawa da miyar kuka da manshano haka ba.

Duk kansu sun ji daɗin sakin jikin nata dasu, gashi bata nuna masu komai ba ko ƙyama, balle har ta kasa cin abincin su.

Bayan ta gama cin abincin ne take shaida masu da akwai maganar da ta kawo ta mai matuƙar muhimmanci, wanda take so tayi da su da kuma mahaifin Yarinya Suhan.


Nan fa gaban Ummata ya shiga faɗuwa, Hajjo ce tayi ƙarfin hin cewa to su jira shi ya dawo daga kasuwa domin ko ina yake yanzu fa yana hanya ne....


Da haka suka shiga firar su ta manya da kuma halin da duniya da ƙasa take ciki, masalan na rashin abinci da kuma kidnapping ɗinnan da ake fama dashi a arewacin nigeria ɗin.


Sallamar Malam na daga cikin Abunda ya ƙara tsananta faɗuwr gaba ga Umman tawa, domin batasan ko da wacce wannan matar take tafe ba, duk da kuwa ta yaba da hankali da natsuwar matar, kuma tayi imanin bata tare da abun cutuwa ko da zai iya zama barazana ga lafiyar tata data yarinyar tata.....






~Oum-Deedat ce~
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._


*Page ~37~*



*YAN UWA MUNA KARA KIRA DA MABIYA LITTAFAN GOLDEN PEN WRITTERS ASSOCIATION DA SU KIYAYE DA WANNAN MAI CUTAR TASU DA SUNAN YANA SAIDA LITTAFAN KUNGIYARMU,TO KARYA YAKE MACUCI NE KAWAI LITTAFANMU IS FREE 1 NE KAWAI NA KUDI,KUMA DA YACE YANA BA KUNGIYARMU KUDIN REGISTER DIN DA KUKE BIYA DOMIN MU TURA MASHI SABBIN LITTAFAN MU,TO WALLAHI DUK KARYA YAKE MANA MU BAMU DA MASANIYA AKAN WANNAN B'ARNAR DA YAKE MANA SAI DAGA BAYA MUKA JI,SANNAN KUMA INA SON KUSAN NUMBER DIN SHI SABODA YANA NAN YANA SHIGA GROUPS NA MATA DA SUNAN MACE SABODA HAKA KU KIYAYE GA NUMBER DIN SHI NAN (08107707692)*


*Ammin Islam Pls ki sassauta ma Hajiya Kubra, 🤣🤣ai indai kina yin Ya Ameen dole ne ki so Mom ɗinshi, kiyi mata addu'a Allah ya shirya ta. Team Sir, Salim ina gaishe ku muna mugun tare🤝🏻🤝🏻👌🏻*


°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°




Kai tsaye ɗaki malam ya shige, bayan sun gaisa da Ammi wadda bai wani waye ta ba sosai.

Sai bayan da ya kammala cin tuwon daren ne, sannan Hajjo take shaida mashi ko wacece Ammin da abunda yake tafe da ita kuma. Cewa yayi ta shimfiɗa mashi darduma zai fito suyi magana, saboda ɗakin akwai zafi.

Daga cen gefe ta shimfiɗa mashi dardumar, sannan ta shaida masu ga malam ɗinnan fitowa.

Bai wani ɗauki lokaci ba, ya fito haɗi da zuwa ya ɗauraye hannuwan shi, sannan ya koma ya zauna suka sake sabuwar gaisuwa.

Cikin salon magana irin ta manyan ƴan boko da suka iya tsara kalamai Hajiya Khaltum ɗin ke bayyana ma malam ita ɗin wacece, da kuma dalilin zuwan nata gidan.

Tsaf ya tsaya ya saurare ta da kunnen basira da kuma fahimta, ummata da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login