Showing 33001 words to 36000 words out of 153711 words

Chapter 12 - FIL'AZAL COMPLETE

kallon photon khalid dataji mahaifitarta zata shigo dakin seta boye photon.

Abangaren matan JAROOD bawacce tadamu wai dan benan musamman hajiya zulaikha harkar gabanta kawai takeyi, tinda hajiya aisha tace mata yayi tafiya kawai tace Allah tsare ko kiransa batayiba. Kwara ita hajiya aishar takirasa daukane kawai beyi ba, itama tafijin dadih da baya nan, seda tayi 2days ma bata kwana agidan ba, tana gün d’an boy yana gargasa mata duri da Jelah, data dawo ma washe gari takoma ya kuma ci, taciyu a kwanakinnan amma dayake hajira ce Kawai kari take nema kullum setaje d’an boy ya gargasa mata duri, ba abinda ya dameta ita bata cikin tension din shaawah, hajiya zulaikha ce ke ciki.

Abangaren JAROOD baccinsa yakesha yanzu sosai, yaci ya koshi ya kwanta , hankalinsa ya d’an fara kwanciya ganin amour tabar kiransa kawai yasan ta hakura ne da Aurennan na dole daza amasa, kawai kuma de dağa Ubangiji yakejin hankalinsa ya kwanta akasin ada, ya rasa dalilin kwanciyar hankalin nasa. Ranar Tuesday dayaje ganin doctor khamis ya tabbatar masa da jininsa ya fara sauka, saura kadan ya rage, yaji dadih sosai wlhi bayasan hawan jini da sugar Suna bashi tsoro, shida ake nema masa lafiyar jaruma kuma hawan jini da sugar yasamesa aiya banu. Dağa asibitin da yayi sallar azahar kawai ya nufa gidan Amour, tinda ya tinkaro kofar gidan yakejin gabansa na dukan uku-uku, daman a hanya ya tsaya ya mata tsaraba irin shi adole dağa tafiya ya dawo dinnan. Yana isa get din yaji kamar ya dawo baya, se kawai ya sadakar ya Danna hancin motarsa cikin gidan. Dai-dai malam wanzan na zaune a compound din gidan gefen wata flower suna hira da Abdul’aziz me gyaran flower, kawai idanuwansa suka sauka akan motar JAROOD,. Zumbur ya tashi cikin murna ya iso inda JAROOD din yayi packing motar ya fito, yana ganinsa ya sakar mata murmushi hadi dacewa “Nayi missing Dinka ubana…” cikin murnar Ganinsa malam wanzan yace “barka da dawowa uban dakina nima nayi kewarka..” JAROOD yayi wata yar siririyar dariya daya jima beyi irintaba yace “Barkade,,,ina Amour, tagajide ta hakura da mgnr Aurennan aini daman nasan seta gaji ta hakura tinda de ai ba a dole,, ni ba burar gwatso ba inta tara yaran mata suna tsinemin sunajin kmr su kasheni dan takaicina dake rayukansu nawa…” JAROOD ya fadi yana bude Murfin bayan motar yana dakko ledojin daya shigo dasu. Karo na farko da Malam wanzan ya farajin kunyar maganar batsar bakin JAROOD da ada ne shike tayasa maganganunnan, JAROOD besan dadin mace ba amma bakinsa akwai batsa sosai. sede malam wanzan yayi shiru bece da JAROOD komi ba, murmushi yayi kawai. Ya tayasa kwashe ledojin suka nufa hanyar zuwa falon hajiya fatima. Suna shiga falon dai-dai tana fitowa dağa bedroom dinta na dakin kasan, idanuwanta sukayi tozali da JAROOD, ta bude ido na mamaki tayi missing danta sosai yau take cewa zata kirasa idan ta tashi daga bacci toh tashinta a baccin kenan tayi sallah ta fito da waya a hannu tana shirin tazauna a falon ta kirasa. “Maraba da yan hijira..” Cewar hajiya fatima data fadi cikin murmushi ta tarı JAROOD da faraah. Nan da nan farin ciki ya kuma lullube JAROOD domin ganin murmushi mahaifiyarsa. Ta karaso tazauna suka ajiye mata ledojin a kusa da kafafuwanta kana ya tsugunna har kasa ya gaidata, cikin fara’ah da zallar farin ciki ya gaidata, ta amsa fuska sake hadi da masa barka da dawowa ya amsa da barkade. malam wanzan ya zauna akan kujera sbda hajiya Fatima tace yazauna amma ada yaso ya fita ne. “ saukar ka kenan yanzu?” Hajiya Fatima ta tambayi JAROOD, yace “Ehe Amour…” “masha Allah, kaje gida kayi sallah ka huta zuwa gobe inka huta ka dawo inada mgna dakai domin Abinda ka guda din be fasuba…” JAROOD yayi shiru yana nazarin maganarta ta karshe, be fahimci me take nufi ba, dan haka cikin kaguwa dasan yaji me takeso ta gaya masa yace “Ai nayi sallah Amour, sannan ban bukatar wani Hutu kawai ki gayamin me kkeso ki gayamin…” hajiya fatima tace “Aah kabari de seka samu nutsuwa kaje gida kaga iyalanka ko zuwa dare ne ka dawo…” Sam ba haka JAROOD yaso ba amma dole ya tafi gidan sbda ta matsa seya tafin. Malam yajasa a car, yaje gida ya kuma wanka yayi la’asar ya nufa part din matansa duka ya duba kafiyarsu. Hajiya aisha ta matukar jin bakin çıkın dawowarsa, amma ta boye sbda makirci ta nuna azahiri tayi murnar dawowarsa, kasan ranta ji takeyi kamar ta mutu dan bakin ciki in yana gida bason adinga Yawan fita yakeyi ba. Ita kam hajiya zulaiha azahiri ta nuna masa tayı bakin cikin dawowarsa babu boye-boye ita Sam bata iya makirci da munafunciba komi nata a free takeyi ba tsoro ba gudun zuciya. Daya shiga part din aisha seda yayi 30mnt tana jansa da hira, daya dawo yashiga part din Zulaikha 10mnt yayi ya fito a daddafe, da kyar ma ta iya gaidasa, ita ko miskhala zarratin bata iya makirciba, in kana neman Wacce tafi shedan kisisina da makirci kasamu Aisha magana ta kare, kuma JAROOD be isa ya gano halintaba sbda tasan hannunta.

Bayan yayi isha’i, dağa masallaci malam wanzan yajashi zuwa gidan hajiya Fatima. A hanya JAROOD se jan malam wanzan yake da hira, amma yayi shiru yanacan yana tunani-tunanin shin ya JAROOD zeji in aka gaya masa yarsa aka aura masa a matsayin matarsa ta aure. Ya zurfafa a tunani har suka iso gidan, JAROOD ya kula da Tuna’nın da Malam wanzan yake ciki dan haka suna isowa gidan ya kallesa yace “me kake tunani babana?” Malam wanzan besan sadda bakinsa ya subuceba yace “Na maka lefi…” ya sadda kansa kasa. Çıkın mamaki JAROOD yace “Lefin meka min da har zesaka a tunani?” Malam wanzan yayi shiru. JAROOD yaci gaba dacewa “Kome kamın na yafe maka in har ba Amour da Me-martaba ka kashemunba, wlhi na yafe maka…” malam wanzan ya sauke nannauyar numfashi ba tare dayace komi ba. Suka nufa falon hajiya fatima. Bata falon kasa dan haka JAROOD ya kirata a waya batare data dagaba ta sakko daga upstairs tana dakinta na sama ne tana waya dame martaba, taji shigowarsu domin taji karar bude get din gidan kuma tasan sune. JAROOD naganinta çıkın nishadi da zolaya yace “Barka da sakkowa Giwa me takun kasaita, Giwar me martaba…” “ai yau Kaima ka Ara ka yafa kenan…” ta fadi tana murmushi hadi karasowa ta zauna malam wanzan ya juya ze fita ta dakatar dashi. ”karka fita ka zauna ai dakai za ayi mgnr…” JAROOD ya zauna kasan carpet dai-dai yana facing hajiya fatima. Malam wanzan ya dawo ya zauna a kasa shima kusa da uban dakinsa. “Yaya kasamu iyalin lafiya kou?” Cewar Amour. “AlhamduLillah amour, ki gayamin wani magana zaki gayamin pls dukna kagu…” JAROOD ya fadi cikin kosawa. Amour ta gyara zama ta sosai azuciyarta se Adduah takeyi Allah yasa d’an nata ya aminta domin tasan in be amince ba ba aure, amma inya Amince lafiya lau aurensu yake, daman tinda aka daura Auren taketa Adduah Allah sa inya dawo ya amince da duk abinda tace. “Abinda ka gudane kadawo kaga anyi makashi…” cikin rashin fahimta yace “Amour kinsani a duhu abinda na guda kamar yaya? Wallahi bangane ba…” shi sam ma ya mance da maganar Auren. hajiya fatima taci gaba da magana. “Auren dakayi gudunsa Shi aka maka,,,” a razane JAROOD ya kalli amour domin ya tabbatar da abinda tace Akan fuskarta, nan fuskarta ta bashi tabbacin kalamansa. “Innalillahi wa’inna ilaihirraju’un! Wani irin Aure kuma pls? ” JAROOD ya fadi yana dafe kansa, nan da nan zufa ya wankesa Tass. Gaban malam wanzan ya yanke ya fadi ganin yanayin da uban dakinsa ya shiga, yafi yanayin da BATOOL tashiga, dande kawai shi namiji ne. Cikin sassauta harshe dukda an masa abinda bayaso Amma hakan besa ya daga muryarsa sama data mahaifiyarsa ba yace “Dan Allah Amour meyasa kikayi haka? Da gaske kike pls ko wasa amour?” Hajiya fatima ta hade rai tace “Nataba wasa dakaine?” JAROOD ya kuma dafe kansa wata zufar ta kuma wankesa, ji yakeyi kmr yasaka kuka amma ba dama. yace “Yanzu Amour kuma yar 14yrs din kika auramin saboda kawai kibi maganar malami, haba Amour dan Allah Amour ki duba ki gani 50yrs nike amma a haka akamin Auren dole kamar de bansan ciwon Kaina ba Amour,…” a hasale hajiya fatima tace “Da Anyi magana kashe shekarunka hamsin shin kai ka yankewa kasa cibiya ne wai? Kasani yaro baya girma gaban iyayensa ni yanzu sam bana ganin girmanka, a girman naka in har bakama iyayenka biyayya ba yazama na banza? Da girman naka in kana batawa iyayenka rai baze hana Ubangiji ya saba maka ba wallahi, Ka ganni nan Dani da Mahaifinka me martaba? Duk bamufi karfin iyayenmu su samu abu muyishi adoleba kuma ba tare da Muşuba, ko rayukanmu sun baci bamu isa mu nuna agabansuba sbda tsantsar ladabinmu agaresu, nida me martaba hadamu Aure zakayi amma hakan be hanamu kyautatawa junanmuba kaide kana gani kai shaidane yadda muke nida me martaba, Allah yajikan iyayenmu da kaga yadda Ake ladabi da biyayya, kune yayan gata yaran yanzu da iyaye ke fadi kuke fadi…ka duba ka gani harni fatima nake fadi kake fadi JAROOD?..” tana kai karshen mgnrta kawai setasa kuka, ta Kamo gefen zanin jikinta tana share hawaye. Ganin tana kuka yasa JAROOD rikicewa , ya matso ya tsugunna gabanta. “Amour dan Girman Allah kıyi hakuri, kidena zubar da hawaye akaina, aurene tinda an Riga anyi na amsa Amour na Amince duk abinda zesaki kuka bana sanshi, dan Allah kiyi shiru karkisa fushin ubangiji yasameni Amour, wallahi na Amshi Auren na Amince, duk abinda kikeso shi zanyi Amour…” farin ciki ya lullube hajiya fatima daman tana sane ta fara kukan sbda tasan JAROOD besan yaga hawayenta. Malam wanzan yana zaune yayi shiru shide jira yakeyi kawai yaji amour tasanar dashi wa aka aura masan, yağa ya reaction dinsa ze kasance. JAROOD da kansa ya dagota ya share mata hawayenta, acan kasan zuciyarsa yanajin tana masa suya, wannan shine adakeka a hanaka kuka kuma ba yadda ka iya, iyaye Kenan. Ya fadi a ransa. Bayan ya gama share mata hawayen taci gaba da magana “yarinya me hankali da nutsuwa aka Aura maka ina fatan ka riketa çıkın mutumci iyayenta dattawa ne, mahaifinta dattijone, dukda yasan baka da lafiya amma ya baka yarsa, kawai yar ya bamu komi me martaba ne yayi, karka watsa mana kasa a ido in har kanaso kaga farin cikina, kuma ka gama da duniya lafiya…” JAROOD yace “Toh Amour insha Allah wace yarinya ce kuka samamin din? Allah ya bani ikon muku biyayya.” Haka kawai yaji yanaso yasan ko wacece dukda yasan sanın baze amfana masa komi ba, ya kudirta aransa dole seya saketa koma wacece sbda baze zauna ya dinga cutar yar mutane ba. “Takwara ta, yarinya ta wajen malam wanzan…” JAROOD yayi saurin cewa “waaaaaaaa? Wani malam wanzan Amour?” Şam shi yama mance da wani malam wanzan sbda Dimauta. “Malam wanzan babban Amininka na yanzu…” amour ta karashe Tana nuna masa malam wanzan. Ya kalli malam wanzan wanda yayi kasa da kansa yace “İn har kaga bakayi maka ba na maka lamani JAROOD ka saketa ko yanzu-yanzu bakomai ni nasan uzurinka..” amour ta amshe da “Ai in har kaga ya rabu da yarinyar nan malam toh tabbas sede in lafiya bata samu ba, gudun karya cutar da y’ar mutane seya saketa ta auri me lafiya, amma ni naga yarinya tamin na yaba da kamalar ta da kimarta, da d’a’arta uwa uba kuma da cikar zatinta…” JAROOD ya dafe kai da 2hands yayi kasa da kansa, gaba daya an dauresa da jijiyoyinsa, ya bude baki zeyi magana amour ta dakatar dashi. “Kar kace komi in har kanason farin cikina, kawai kabı abinda nakeso, zan dakko maka maganinka yau in kaje gida ka fara amfani dashi na 1week ne maganin inka gama sekaje ku hadu da Amarya, tini nasa suka dawo nigeria sbda na isa, suna gidanka dake anguwar dosa inka tashi zuwa malam wanzan yakaika, kafin muga yaza ayi adawo da ita gidanka, matanka duk zanzo in sanar dasu zuwa gobe ko jibi inme duka ya yarda sbda kar suga ana shigowa da kayan Amarya suji ba dadih,,,” JAROOD yayi shiru kawai shi kadai yasan me yake sakawa a zuciyarsa, tinda Amour tace kar yasake yayi magana beyi küskuren yin maganar ba. “So nakeyi 💯 kaji aranka ka aminta da Aurennan in har kanasan ganin nishadina…” Cewar Amour. Jiki ba laka cikin ladabi JAROOD yace “Shikenan Amour na Amince kmr yadda kikeso…” dukda tasan mgnr bata kai cikinsa ba. amma taji farin ciki ya rufeta se sa masa albarka takeyi da Adduah tsari. Wuraren 11:pm JAROOD ya nufi gidan malam wanzan ke driving dinsa kawai ya dafe kai tinda ya shigo motar, se hakuri da ban baki hadi da kwarin guiwa malam wanzan ke bama JAROOD. A hankali ya dago idanuwansa dasuka koma kananu sbda damuwa ya kalli malam wanzan yace “Yanzu Amour ta kyautamin, sbda Allah kmr ni ace Amin Aure da yar ….” Se kuma yayi shiru ya kasa karasawa tinawar da yayi yar malam wanzan din aka aura masa. “Gaskiya ba dadih ranka ya dade amma kayi hakuri komi na duniya me wucewa ne ba abinda yake dawwama,,,” bending kawai yayi Akan kujerar yana sauke numfashi öne bye öne daki-daki, gaba daya kawai zufa ke karyo masa sam yau bejin sanyin AÇ ajikinsa se axabar zafi. Suna isa gıda ya fita yama malam wanzan seda safe a daddafe sbda mugun ciwon kan daya dabaibayesa, da ya rabu da ciwon kai yanzu ciwo ya dawo, yana shiga dakinsa ya dauki magungunansa yasha,na asibiti daman dasu yadawo gidan,. Ya taho da magungunan da Amour ta bashi wanda suka amso agun me maganinnan, cikin haushi JAROOD ya kwashesu ya zubasu a bolar, ya dawo ya kwanta se juya maganar auren yakeyi acikinsa. “Namiji kamana akamin Auren dole…” ya fadi dai-dai yana kallon saman Dakin nasa, ya rasama ta ina yau ze fara da tunanin nasa, sbda tunanikan sunyi yawa sun wuce nazarin me karatu a zuciyarsa.Haka ya kwana shide gashinan kamar bashiba yau maganin da kyarma ya masa aiki sbda da kyar yasamu bacci ya daukesa, yaumade mafarkai yadingayi Gashi acikin haske da wasu fararen flowers guda biyar,duk inya yabi se sun biyosa. Ya rasa wannan wani irin mafarkaine yakeyi a kwanakinnan.

Abangaren BATOOL tashiga damuwa sosai, kullum bata da Aiki Sena zaman daki, tafiso ta zauna ita kadai adaki, saboda tasamu damar tunanin Khalid dinta, kuka yazama Aikinta, mahaifiyartace ke kusantota sosai, saboda tadinga kwantar mata da hankali, mahaifinta ma da kansa inya dawo yana samunta yayita mata natsiha da lallami hadi da kwantar da hankali.

Abangaren JAROOD bayan dawowarsa gidansa, da 1week hajiya Fatima tazo ta sanar dasu ta karawa JAROOD aure, amma bata gaya musu waya aura ba, dukda Mijin beda mamora amma sun shiga damuwar Karin Auren nasa, bakamar hajiya zulaikha ita datakeda mugun kishin tsiya, ta mugun ji haushin JAROOD ganin su be gama da bukatarsuba kuma yaje ya karo wani auren dan mugunta aganinta, haka de sukayi shiru basuce komi, sun san ba ama giwar sarki gaddama in tana magana. Tana gamawa dasu ta nufa part din JAROOD ta tadda baya nan yaje office dinsa, sbda ya gaji da zaman gidan kawai yaje office dinsa, shi har yanzu bega Amaryarba kuma beson yaganta, sbda bata gabansa. Hajiya fatima takirasa tace yazo yasameta agidanta yanzu. Ta hau motarta dreva ya maidata gida.
Ba jimawa, Cikin hanzari JAROOD ya bar office ya nufo gidan Amour, sam shi inda abinda ke daga masa hankali toh damuwar Amour ne ko bacin ranta. Har falonta yasameta ya gaidata kusan 1week yau basu hadu ba. “Ka gama amfani da maganinnan? Hajiya fatima ta tambayesa cikin hanzari yace “Ehe Amour…” alhalin karya ne beyi amfani dako daya ba illa ma yasashi abola. “Okay,,toh kaje kaga Amaryar taka ne baka gayamin ba,?” Ta kuma jefo masa tambayar. Dagowa yayi ya kalleta yace “Banje ba Amour,…” se kuma ya sadda kansa kasa yaci gaba da magana. “Amour ai naga ban warke din ba kmr yadda akace dana Aureta zan warke, kinga alamun duk karyane, dan Allah Amour ina gaskiya anan? Kawai wani can yaja an kashema yarinyar mutane rayuwa fisabilillahi fa Amour? Innaje naganta mezan mata pls Amour? Tinda ba warkewar nayi ba ai kinga amour zuwan ba amfani, ki duba ki…” ta dakatar dashi dacewa “in bakajeba wallahi zan saba maka kaji nagaya maka karka bari nida kai musamu matsala, kawai tinda nace kaje, kajedin kawai kamar yadda nace…” JAROOD ya rissina yace “Yadda kikace haka za ayi amour,,,” hajiya fatima najin dadin yadda JAROOD ke mata biyayya.

A ranar sam JAROOD beje ganin wata Amaryaba, yana barın gidanma ya mance da abinda Amour tace masa kasancewar se dare yabar gidan. Sam amour batasan beje ba, har akayi 2weeks bata sani ba, aka kara 1week duk bata san yaje ko beje ba, sbda a yadda ta masa magana ya amsa batayi tsammanin beje ba. Se yau ta samu malam wanzan ta tambayesa zuwan JAROOD nawa gün BATOOL. Sam besan me ake ciki ba kuma be saba karya ba balle ya mata, dan haka ya gaya mata be taba zuwa ba. Nan take Amour ta fara matsifa “Ashe yau 1month da dawowarsa, amma har yanzu beje yağa yarinyar mutane ba,? Dole seya zubarmin da mutumci hankalinsa ze kwanta kou? Shikenan ai…” malam wanzan se bata hakuri yakeyi. Ta nufa falonta ta jawo wayarta ta kirasa, harta kusa katsewa kana gogan ya dağa. “Assalamu Alayki Amour…” ba tare data amsa sallamarsa ba ta rufesa da fada. “Yanzu JAROOD bakaje kaga yarinyar nan ba? So kakeyi kawai kaga bacin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login