Showing 39001 words to 42000 words out of 42870 words

Chapter 14 - HALLITAR ALLAH CE COMPLETE

11 Jul 2025

2207

zuciyar mai karatu)*

*ALƘALAMIN: RUƘAYYA IBRAHIM LAWAL (UMMU INTEESAR)*


*MARUBUCIYAR: SOYAYYAR MEERAH*
*Y'AR GANTALI*
*RIKICIN MASOYA*
*A SANADIN KAMA*
*RASHIN GATA*
*WATA ƘAWA*

*AND NOW*
*HALITTAR ALLAH CE*

DEDICATED TO: Yar malam member ta halittar Allah ce fans group ina jin daɗin comment ɗinki sosai Allah bar ƙauna
________________________________


*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com


https://www.youtube.com/channel/UCXPmzqpUDDjUfBUkYwadf4w

_*Ku danna mana subscribe kana da kararrawar sanarwa mu gode.*_


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*

PAGE 55-56

Bayan ya koma sashensa ya tarar da Abdul zaune ya buga tagumi da duka hannayensa guda biyu ga hawaye dake bin kuncinsa.

Tsayawa ya yi ya kafe shi da ido, sai dai da alama Abdul ɗin ya yi zurfi a kogin tunani.

Girgiza kai Mahmud ya yi alamun tausayawa, ƙarasawa ya yi gunshi ya zauna daf dashi amma duk yaron bai ɗago ba, alamun ma bai san da zamansa a gun ba.

Sai da Mahmud ɗin ya dafa kafaɗarsa sannan ya yi firgigit kamar wanda aka tayar daga barci.

"Me ya faru Abdul?" Mahmud ya tambaya da damuwa a fuskarsa.
Don har a zuciyarsa baya son ganin damuwar yaron, jinsa yake tamkar ɗansa ko wani jininsa.

"Yaya missa kowa yat-tsani ganin huskata na? Missa kowa bai son in zauna kusa garai?
Saboda banda lahiyar ƙahwa ko don ina da rabin huska? Abin na damuna....."

Yana kai nan a zancensa ya fashe da kuka kamar an kunna shi.

Duk da bakomai Mahmud yake fahimta a Hausar yaron ba, amma ya fara jin wani abu saboda zama da Abdul ɗin.

Nan fa ya shiga rarrashin yaron yana bashi baki "Ka yi haƙuri Abdul, shi komai da ka gani muƙaddari ne daga Allah shi ke jarabtar bayinsa don ya gwada ƙarfin imaninsu. Insha'allah zaka warke watarana kamar ma baka taɓa yin ciwon ƙafa ba..."

"To ita huskata hwa tana gyaruwa?" Abdul ya jefo masa tambaya yana nuna bangaren dake shafe a fuskarsa da yatsa.

Sosai ya ƙara bawa Mahmud tausayi.

A ransa ya ce "Sai dai ka yi haƙuri Abdul wannan halitta ce ba zata taɓa sauyawa ba, haka Allah ya so ya nufe ka da zama, ba wanda zai iya canza maka halitta sai...."

Yana tsaka da zancen zucin Muryar Abdul ta daki dodon kunnensa in da yake cewa "Yaya huskata hwa? Bata gyaruwa koh?" Ya fada kamar zai yi kuka.

"A'a Abdul zata iya gyaruwa watarana kai dai ka ci gaba da addu'a kawai ka ji."

Girgiza kai Abdu ya yi alamun "Eh"

Har Mahmud ya miƙe zai wuce ciki ya tuna abinda ya shigo da ƙudurin yi.

Nan ya ji damuwa ta lulluɓe shi. Amma bashi da wata mafita da ya wuce ya sanar da yaron tafiyarsa don ta yiwu ko da zai wuce da safe yaron na barci ba kuma zai iya tashinsa ba.

Dawowa ya yi ya zauna.
"Abdul!" Ya kira sunan yaron.

Yaron ya ɗago ya kalle shi.

Sai da ya yi jim, sannan ya ce "Gobe zan yi tafiya, zan je ƙasar Spain Amma ba jimawa zan dawo..."

Ai tun bai gama rufe bakinsa ba, Abdul ya rungume shi ƙam-ƙam yana faɗar "Don Allah yaya kat ka tahi ka banni Mama bata sona kora ta zata yi."

"Ba zata kore ka ba mun yi magana da ita ka kwantar da hankalinka." Da haka ya ci gaba da lalaɓa shi har ya samu ya masa wayo ya yarda.

A haka suka kwanta rungume da juna, sosai Abdul ya ƙanƙame shi don ganin yake kamar guduwar zai yi ya bar shi.

A wannan daren Abdul kasa barci ya yi sai wuraren uku na dare barci ɓarawo ya yi awon gaba da shi.

Wannan dalilin ne ya saka da safe ya kasa tashi da wuri sai ƙarfe 9 na safe ya farka.

A hankali ya buɗe idon shi ya sauke su kan katifar sai dai me? Wayam ba Mahmud ba dalilinsa.

Nan ya shiga ƙwalawa Mahmud ɗin kira "Yaya! Yaya!!" Jin shiru ya yi tunanin ko yana banɗaki ne, can kuma ya tuna da maganar tafiyarsa ta jiya kenan bai haƙura ba?

Hankalin Abdul ya yi ƙololuwar tashi. Dabara ya yi ya sako daga kan gadon yana rarrafe tare da duba ko wane lungu da saƙo a part ɗin ba Mahmud ba dalilinsa sai kayan break fast da ya ajiye masa, hakan ya tabbatar masa da Mahmud ya yi nisa da shi ya tafi ya bar shi.

Don haka ya fashe da kuka tare da zama guri ɗaya yana raira waƙa cikin kuka "Yayana ka tahi ka banni, nii Abdul ya zan yi da raina.... Hajiya bata hwa sona ya zata zauna da ni kuma... Don Allah yaya ka dawo ni Abdul na ga ta kaina, kai kaɗai ke sona a duniyata yanzu."

Haka ya cigaba da rera kukansa tare da waƙa har ya gaji amma ko mai kama da Mahmud bai koma gani ba.

Zuwa lokacin tuni jirginsu Mahmud ya lula cikin gajimare sai dai fatan Allah ya sauke su lafiya.

Tun bayan dawowar Hajiya daga rakiyar yaronta a airport take zaune a falonta tana shaƙatawa tuni ta manta da wata amana da ya bar mata har wajajen azahar sannan ta tashi ta shiga ciki domin ta shirya ta fita.

Sai bayan ta shirya ta fito zata fita ne da ta ga sashen Mahmud ta tuna ajiyarsa.

Ya mutsa fuska ta yi tana faɗar "Na manta da ajiyarka son."

Hanne ta ƙwalawa kira da gudu ta ƙaraso ta ce "Gani rankiya daɗe."

Cikin ya mutsa fuska ta ce "Ki ɗebo abinci ki kaiwa waccan halittar dake rayuwa a can sashen." Ta faɗa tana nuna sashen Mahmud da hannu.

"To ranki ya dade." Hanne ta faɗa tare da juyawa ciki don cika umurnin uwargijiyarta.

Ita kuwa Hajiya ɗauke kai ta yi tare da wuce parking space ba tare da ta kuma kallon sashen ba ma bare ta je duba halin da amanarta ke ciki.

Ko da Hanne ta je kicin sai da ta tsaya ta ciji yatsa sannan ta fara zuba masa abincin, irin ƙanzon nan na ƙasa ta karkaro ta zuba masa sannan ta ɗebo gishiri mai ɗan dama ta ƙara masa ta yanda ba zai iya ci ba, ta ɗauka ta fito. Ko da Baba Ladi ta haɗu da ita a kofar fitowa daga kitchen din ta ce mata "Hanne wa zaki kaiwa wannan ƙanzon? Ba dai bil adama zaki bawa wannan abincin ba?"
Sai ta ya mutsa fuska ta ce "Almajirai zan bawa ai su suna so ya fi a zubar."

Girgiza kai Baba Ladi ta yi ta shige kicin ɗin abunta tana yiwa Hanne fatan shiriya don yanzu ta sani tana ƙara magana zata iya zaginta.

Ita kuwa Hanne tsaki ta ja tana faɗar "Gulmammiyar tsohuwa kawai 'yar sa'ido. Wallahi kowa ya shiga gonata a gidan nan sai na aske shi tas, bari dai na gama da wannan mummunar halittar na dawo kanki daga baya." Ta faɗa ƙasa-kasa tare da wucewa zuwa sashen Mahmud don kaiwa Abdul abunda take kira da abincinsa.


To fah readers? Me Hanne ke shirin aikatawa..
Wannan fa shi ake kira da rijiya ta bada ruwa guga ta hana.


Mu je zuwa dai don ganin ya za'a garƙe.

More comment more typing












Follow me on Wattpad @Ruky_i_lawal

Instagram: Rukayyarh_ibraheem












UMMU INTEESAR CE


*HALITTAR ALLAH CE*

🧑🏻‍🦼🧑🏻‍🦼🧑🏻‍🦼🧑🏻‍🦼🧑🏻‍🦼

*(Labari mai taɓa zuciya, da sanya imani da tsoron Allah a zuciyar mai karatu)*

*ALƘALAMIN: RUƘAYYA IBRAHIM LAWAL (UMMU INTEESAR)*


*MARUBUCIYAR: SOYAYYAR MEERAH*
*Y'AR GANTALI*
*RIKICIN MASOYA*
*A SANADIN KAMA*
*RASHIN GATA*
*WATA ƘAWA*

*AND NOW*
*HALITTAR ALLAH CE*

DEDICATED TO ALL MEMBERS OF HALITTAR ALLAH CE FANS GROUP.

________________________________


*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com


https://www.youtube.com/channel/UCXPmzqpUDDjUfBUkYwadf4w

_*Ku danna mana subscribe kana da kararrawar sanarwa mu gode.*_


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
PAGE 57-58


Ƙofar Sashen a buɗe take don haka ta shige kai tsaye.

Lokacin Abdul na kwance kan doguwar kujera fuskarsa har ta kumbura ɗayan idonsa ya yi ja, da alamu ya ci kuka har ya ƙoshi.

Jin an banko kofar da ƙarfi ya saka shi zabura, ya tsorata sosai.

Hanne ta ƙaraso gabansa tana tamke fuska, sannan ta miƙa masa abincin.

"Kai Dabba tashi ga abincinka." Ta faɗa.

Baki na rawa ya ce "to." Tare da amsar kwanon don tun ranar farkon zuwansa gidan yake tsoronta.

Fara ci ya yi hannu baka hannu ƙwarya saboda matsananciyar yunwa da ya jima bai ji irinta ba.

Lomar farko da ya yi ya fito da idonsa waje, kamar zai dawo da abincin waje. Sai kuma ya tuna ai ya saba da irin wannan, tunda ya ci wanda bai ma kai wannan tsafta da daɗi ba.

Tsawa ta daga mishi "Ubanwa kake fiddowa ido? Nakasasshen banza maza ka cinye shi tas. Kuma wallahi idan ka sake ka gayawa wani a cikin gidan nan kalar abincin dana baka sai na ƙwaƙule ma ɗayan idon da kake da kowa ya huta. Dama miye amfanin ka?"

Ɗaga mata kai ya yi alamar to. Ya ci gaba da tura abincin yayin da ta yi ƙwafa ta juya ta fice daga ɗakin.

Hawaye ne suka ci gaba da bin kuncin yaro Abdul. Kukan zuciya yake tare da kuka na sarari. Maganganu Hanne sun tsaya masa a rai, haka sun zauna a kwanyarsa daram.

"Dama ashe bani da amfani shiyasa mutane basa sona?" Ya faɗa a ransa.

Nan fa zuciyarsa ta yi ta masa saƙe-saƙe akan rayuwarsa.

"Tabbas banda amhwani ga kowa, don ga shi sauran yara dut suna makaranta wanga lokaci amma ni gani nan kulle cikin ɗaki saboda kowa tsoro na ya kai."

Ya faɗa yana daɗa fashewa da kuka.

Bayan kwana biyu gidan ya gama yiwa Abdul zafi don nan ɗin ma dai kamar gidan Kande, ya zame masa inuwar bagaruwa ga sanyi ga ƙaya.

Don haka ya fara tunanin guduwa sai dai ba hali tunda ƙafafunsa basa tare dashi (sanduna). Dole ta saka ya haƙura don ba zai iya guduwa da rarrafe ba.

Haka ya cigaba da addu'ar neman mafita, dama yaron akwai son ibada ko wacce sallah bata wuce shi. Ko lokacin da yake jeji da ya kwatanci lokacin sallah ya yi koda bai samu ruwan alwala ba a haka yake sallarsa don bai ma san da zama taimama ba bare ya iya ta.

Allah maji roƙon bawa, a kwana na uku da tafiyar Mahmud Likitansu ya samo sandunan bayan shafe tsawon makwanni yana nema. Don haka ya kawowa su Hajiya har gida kamar yanda ya alƙawartawa Mahmud.

Haka ma ya nemi akai shi ga Abdul don ya gwada sandunan ya ga ko zasu ma yaron.

Hajiya ce ta masa jagora har sashen a karo na farko da ta leƙa sashen tun bayan tafiyar ɗan nata. Wannan ma don bata son likita ya zargi wani abu har ya faɗawa Mahmud ne.

A bedroom suka same shi zaune akan tiles ya buga tagumi sai sana'arsa yake ta hawaye.

Da sauri Hajiya ta dube shi "Subhanallah! Abdul me ya same ka kake kuka? Ya ma aka yi ka rame ko baka cin abincin da ake kawo maka ne?"

Kallon zargi likitan ya mata, sannan ya dubi yaron ya ga alamun tsoron hajiyar tattare da shi.

Girgiza kai kawai ya yi alamun tausayawa da mamaki ya ce "Yaro karɓi waɗannan mu gani ko za su maka." Ya miƙa masa.

Karɓa ya yi ya miƙe, sai dai sun masa tsayi kaɗan. Cikin Sa'a kuwa aka yi dace da irin sandunan nan ne masu maɓallai da ake iya ƙara tsawonsu ko ragewa.

Don haka likitan ya rage masa su ta yanda zasu masa dai-dai.

Daga nan ya yi Sallama da Hajiya ya fice daga gidan yana tausayawa wannan yaron da masa addu'ar samun lafiya.

Amma ya ƙudurce a ransa zai faɗawa Mahmud gaskiyar halin da yaron ke ciki, don ga dukkan alamu bai sani ba.

Hajiya kuwa tana ganin tafiyar likitan ta fara tsara yanda zata kori yaron daga gidan ba tare da kowa ya sani ba bare a samu mai bawa ɗanta labari idan ya dawo.

Washegarin ranar tun sassafe ta tashi da shirye-shiryen taron baƙuwarta (Anty Habi) yayarta da zata zo daga Taraba state. Don haka ta yi amfani da damar ta aiki duka ma'aikatanta nesa, yanda zata kori yaron cikin sauƙi.

Hanne kawai ta rage don haka ta ce "Yawwa Hanne zamu yi wani sirri kada ki sake kowa ya ji ko ya ganki a lokacin da kike aiwatar da shirinmu, don ko tun za'a tafi ake shiri ba sai an dawo ba."

Hanne ta ɗaga kai tare da faɗar"Na fahimta aikin sirri ne za'a yi ko?

Eh, yanzu ki je Sashen Son ki tattare duk abinda yake mallakin wannan halittar sannan ki fito da shi a sirrance ki je ki hau abun hawa ku yi nesa sosai da unguwar nan, ta yadda ba zai taɓa gane ta ba bare ya dawo. Kin ji ni koh? Bana son a samu kuskure, ki tabbatar angama da wannan matsalar kafin yaya Habi ta ƙaraso, dama sanduna nake jiran ya samu."

"Haka ne ranki ya daɗe kin ga sai mu gayawa Boss cewar guduwa ya yi ba da sanin kowa ba." cewar Hanne.

Hajiya ta yi murmushi tace "Maza ki je lokaci na tafiya, ki kula bana son a samu kuskure."

Kuɗin abun hawa Hajiya ta miƙa mata sannan ta tsaya don ganin fitowar su.

Cikin zumuɗi Hanne ta nufi sashen tana murnar burinta ya cika.

Duk yanda Hajiya ta faɗa mata haka ta aikata.
Janyo shi ta yi har gaban Hajiya.
Abdul na kuka yana roƙon Hajiya faɗar yake "Don Allah Mama ki temake ni ki banni in rinƙa kwana nan, in yasso da rana in tahi inyo Bara cikin gari in samu abinci amma kat ki kore ni ina son ƙara ganin yayana ina son shi matuƙa."

Hajiya takai ƙololuwar ƙuluwa ta daka mashi tsawa tana faɗar "Yi mun shiru, wato dai so kake ka tona mun asiri a nan unguwar ma kake tunanin yin Bara?

Mai da dubanta ta yi ga Hanne "Zaki fice mun da shi ko sai sun dawo tukunna?"

Ganin yanda ran Hajiya ya ɓaci yasa ta tungume shi ta fita ta ƙofar baya ta tare abun hawa.

Sai da suka yi tafiyar awa ɗaya da kusan rabi a abun hawan, har sai da mai abun hawan ya gaji ya ja ya tsaya tare da faɗar "Malama na gaji da yawo ina zan sauke ki ne wai?"

"Nan ma ya yi ai.' Ta faɗa tana fitowa daga abin hawan fito da Abdul ta yi ta ɗauko masa kayansa ta ajiye masa.

Ta sallami mai abun hawan.
Abdul sai faman kuka yake, dariya ta yi tace "To dodon gidanmu ni na tafi Allah ya kawo wani mai rabon wahalar kamar Boss."

sannan ta taka da ƙafa ta nufi titi don neman wani abun hawan. Ta yi hakan ne don kada a samu wata matsala.

Da dai Abdul ya ga tabbas ta tafi, ga shi gurin shiru-shiru ba kowa, irin bayan garin nan ne ba kowa sai wanda hanya ta biyo da shi.

Ɗaukar kayansa ya yi cikin ƙarfin hali ya matsa gaba, nan ya samu ɗan wani ɗakin langa-langa da gani irin na masu gadi ne ko 'yan ci rani da basu da muhalli.

Don haka ya shige ciki tare da ajiye kayansa ya bazama cikin gari don yin Bara ko ya samu abinci don yunwa yake ji sosai.

@@@@@@@@

Bayan barinsu gidan da kamar awa Uku Anty Habi ta ƙaraso.

Da murna Hajiya ta tare ta tuni ta manta da wani Abdul kowa ya dawo sai shagali ake.

Anty Habi na tsaka da cin abincin taron baƙin da aka mata.
A hankali suka fara jiyo-hayaniya da iface-iface abun sai ƙara daɗuwa yake da kaɗan-kaɗan.

Nan fa hankalin Hajiya ya fara tashi dama gata da ɗan banzan tsoro kuma tana da hawan jini.

Zuwa can aka callara wata ƙara mai Masifar ƙarfi da take barazanar fasa masu dodon kunne......


Hmmm! Tofah readers meke shirin faruwa a gidan Hajiya ne?🤔🤔

Ina Abdul ya nufa, rayuwar Bara zata riƙe shi kuwa?

Waima shin ina labarin Hajiya Hasina da yan uwan Alhaji Munir?

Shi kanshi Alhaji Munir ɗin meke faruwa da shi?🤔🤔

Don samun wadannan amsoshin ku juri bibiyar alƙamin Ummu inteesar don jin ya zata kaya.



Kada ku manta more comment more typing.










UMMU INTEESAR CE😍🥰❤️❤️


*HALITTAR ALLAH CE*

🧑🏻‍🦼🧑🏻‍🦼🧑🏻‍🦼🧑🏻‍🦼🧑🏻‍🦼

*(Labari mai taɓa zuciya, da sanya imani da tsoron Allah a zuciyar mai karatu)*

*ALƘALAMIN: RUƘAYYA IBRAHIM LAWAL (UMMU INTEESAR)*


*MARUBUCIYAR: SOYAYYAR MEERAH*
*Y'AR GANTALI*
*RIKICIN MASOYA*
*A SANADIN KAMA*
*RASHIN GATA*
*WATA ƘAWA*

*AND NOW*
*HALITTAR ALLAH CE*


Ga masu buƙatar na tallata masu hajojinsu a shafukan littafina dama shafukana na sada zumunta kamar instagram, whatsapp, telegram, facebook da sauransu sai su tuntuɓe ni ta wannan number __08109634202__

Kowacce irin haja je gareka zamu tallata ma cikin rahusa insha'allah.

________________________________


*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com


https://www.youtube.com/channel/UCXPmzqpUDDjUfBUkYwadf4w

_*Ku danna mana subscribe kana da kararrawar sanarwa mu gode.*_


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


PAGE 59-60

Nan fa mutanen dake gidan suka birkice, yaya Habi ta ajiye cokali tana neman guduwa amma ina! Kafin ta gudun abun ya ƙaraso.

A kiɗime Hajiya ta ɗaga kanta don ganin menene ke wannan Masifar ƙarar. Wani curin dunƙulallen abu ne a hankali yake ƙara girma har faɗinsa ya mamaye ilahirin inda yake. Zuwa can kuma ya rabu gida goma.

Hanne da tashin hankali ya korota daga kitchen ta nufo falon, a nan ta tarad da sabon tashin hankali. Amma duk da haka bata yi kuskuren komawa kitchen ba, domin kuwa duk abinda ya koro ɓera har ya faɗa wuta ba ƙaramin abu ba ne.

A hankali waɗannan curin suke mulmulowa sai hayaƙi suke fitarwa ga wasu sautukan Muryar yara iri-iri dake fitowa daga curin. Suka nufo inda yaya Habi, Hajiya da Hanne suka manne waje ɗaya don tsoro..


Wani tsalle yaya Habi ta daka, tana yin sa'ar ƙetare abun ta yi wuf ta faɗa ɗaya daga cikin ɗakunan dake falon ta rufo da makulli tana mayar da ajiyar zuciya.

Hajiya kuwa ganin curin na nufo ta, tun bai ƙaraso gare ta ba hankalinta ya gushe ta fadi a gun kafin ta kai ga suma ta ji wata mummunar murya na faɗar "Kin tsani ganin Musakai a rayuwa koh? To kishirya don kina dab da tsanar kanki." Daga haka aka bushe da matsananciyar dariya mai ƙara birkita birkitacce.

Kafin idonta su ƙarasa rufewa ta hango bayyana wata mummunar halitta a gabanta mai ido ɗaya saman hanci da wani wagegen baki. tsaya faɗa maku munin halittar bata lokaci ne don tafi Abdul muni nesa.

Haka halittar ta ƙarasa ga hajiyar ta rungume ta. A take idon hajiyar ya rufe ruf alamun ta suma.

Hanne kuwa yau taga tashin hankali da bata taɓa ganin irinsa ba. To wai duk me wannan abun ke nufi? Me ya janyo musu wannan masifar? Tana tsaka da wannan tunanin ta ji an sure ta anyi sama da ita.
Waige-waige ta hau yi tana ƙwala ihu amma bata ga abinda ke riƙe da ita ba. Kawai ta ganta a sama.

Can kuma aka makata ga ƙauren ƙofar falo ta faɗo a galabaice.

Zahirin siffar Abdul ce

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login