Showing 51001 words to 54000 words out of 212110 words
girgiza kai ko yasamu ya dawo dede, wani irin kishi ne ya taso mishi, yanzu wani namiji yasan komi na faseelat dinshi, yayi squeezing dinta yanda yaso a lokacin da yaga dama, wani yaji yaji ya rika taso mai a makoshi, ya dafe wuyanshi.
Faseelat taji shiru shiru ba reply nan zuciyarta tafara zafi, dama tasani ze rabu daita ne da yagano hakan, ta fashe da kuka tana fadin"karkamin haka fahad "
Da kyar ya samu ya tura mata "why did you do this to me?"
Yaji baze iya typing dinba ya kashe wayar gaba daya ya mike tsaye yafara sintiri cikin dakin, yana ta tunanin yaudararshi da faseelat tayi, duk yadda yake mabukaci duk dare se ankashe arna wannan daren kam ba shaawa ba labarinta, dukda be barci ba gabadaya daren,
Tunaninshi kwata kwata ya kulle yanada kishi sosai bejin zeiya aurar kingin wani, kuma bangare daya na zuciyarshi bejin zeiya rabuwa da faseelat,
Itama batai bacci ba ganin sakonshi ma yakara tabbatar mata da tunaninta ta tashi taita rusa kuka harse da abba yazo bakin window dinta yamata magana akan tai hakuri ta kwanta hakanan.
Tunda asuba aisha ta farka tana mamakin rashin ganin fahad kwance da dalilin rashin yin sex din donko tana off se ya samarwa kanshi natsuwa yake barci,
Ta tashi ta sauka daga gadon dasauri tayo waje daga saman bene ta hangoshi zaune ta sauko ta nufi wurinshi.
[7/12, 11:01 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰
By
*MAMAN MAMY SHALELE 😂*
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
✍✍✍✍✍✍✍
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*
✍✍✍✍✍✍✍
*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*
3⃣8⃣
Kanshi jingine da pillows na kujera tana ta kallonshi taje gefen shi ta zauna, har ta zauna be sani ba ta dafashi ya juyo da kanshi sashen ta yana kallonta tana kallon kwayar idonshi tace "daddin amira lpya? "
Ya juyar da kai tace "mike damunka ne naga ma ko barci ba kaiba "ta dora hannu kan jikinshi taji ko baya lpya
Yanajin ciwo aranshi yace "bakomai wifey kawai jiya na samu headache ne da dare"ya mata karya.
Cikin jin tausayi ta dora hannu kan goshin shi tace "sannu yaya "
Ya daga Kai kurum don ciwon da yakeji yafi na kai zafi, ta tashi "bari nahada maka tea kasha ,kasha magani sorry "
Ta nufi kitchen yabi ta da kallo gabadaya yanzu hankalinshi yakoma kan faseelat meyasa tabari ya kamu da sonta,
Few minutes takawo mishi tea tana bashi abaki tana mai sorry har yagama sha ta bashi magani don yana da bukatarshi ya meda kai ya jingina da kujera, aisha tai fuskar tausayi tace "honey katashi mushiga ciki kadan kwanta kafin kafita aiki "
Ya dan ya mutsa fuska don surutun nata yafara isarshi don yahanashi tunani n mafita Ya dora hannu ya dafe kai yace "aisha plss leave me alone banason surutu "
Cikin jin tausayi thinking that duk ciwon kanne tace "alright I'm going wish you quick recovery "tana ta kallon shi sannan ta juya ta haye sama don tayi salla, se taji itama duk bata lpyan,
Fahad ya meda kai kan pillows ya cigaba da tunani.
Karfe 6:30 amira tafito tana kuka tana saukowa ya bude mata hannu cikin kasala, taje ta rungumeshi
Yace "what? "yana shafa kan amira
Tana hawaye tana nunamishi saman bene tace "it's mom that woke me up from my sleeping "
Yace "sorry sorry kinsan zakije school yau gobe weekend bazaa tadaki ba okay? "
ta daga kai yace "oya go and get ready to school "
ta juya ta tafi, wai amira har tasan ta kai karan momynta saboda yanda taga ubanta na sonta,
bangaren khalil shima be barci ba saboda bakin ciki yana ta jin dama be saketa ba, hjya ta rikeshi akan ya kwana nan, tana ta jaddada mishi cewa ya cire faseelat a rai ba macen aure bace,
Wannan yakara tada mishi hankali da kuma maganganun faseelat na karshe datace zata iya fadawa halaka,
Faseelat baccin asuba ya dauketa tai ta barci har 9 kwankwasawar kofar dakinta ya tadata gaban ta na faduwa taje ta bude a tsorace taga ummi tsaye idanunta duk sunyi ja, faseelat taja baya zaton ta ko kara bugunta tazo yi,
Ummi tace "kifito kije kici abinci kiyi salla "fuska daure ta juya,
Hawaye suka zubowa faseelat dukda taba tawa ummi rai amma ta damu da cikinta, ta koma ta zauna tana share hawaye gabanta na tsananta faduwa tuno last chart dinsu da fahad jiya,
Seda tai minty goma tafito ta shiga toilet tai wanka tafito ta nufi daki,
Abul ne ya kira ya omer yafadamishi abinda yafaru, hankalin ya omer ya tashi jijiyoyin kanshi duk suka fito,
Har suka Gama waya da abul,
Cikin sauri ya kira ummi ta dauka murya sanyaye, cikin rarrashi da ladabi yace "ummi kiyi hakuri dan Allah komi kikagani a rayuwa rubutaccene ki dena sa damuwa ki kwantar da hankalinki ke kadai garemu ummi kat wata cuta ta kamaki "
Ummi tace "to Omar hakuri dole ne amma faseelat bata kyauta min ba "
Yace "kiyi hakuri ummi ki dena fushi daita kinsan fushinki matsala ne arayuwarta "
Tace "to nadena omer "
Yace "Nagode ummi da kika fahimceni, Allah yasa haka shine yafi zama alheri "
Tace "amin de "
Sukai bankwana cikin jin haushin faseelat ya omer yayi dialing number dinta,
Tana cikin saka kaya taji kiran dasauri taje wurin wayar tazata fahad ne se taga ya omer cikin jin nauyi ta dauka tana kame kame
yace "faseelat abinda kika ga ya dace da rayuwarki kenan? Tun kafin abunnan nafada miki matsalar shi amma kika ce zakiiya, yanzu aurenku wata 8 kinfito miye amfanin hakan? The sad news ma wai kina fira da wani, yanzu duniya inta tashi fada cewa kawai zaai ankamaki da wani, haka kikaga yamaki ko? Ki bata mana suna ki batawa kanki har yaya da jikokin ki se anmasu gori? "
Ta fasa kuka "Dan Allah yaya kuyi hakuri bansan yaakai haka tafaru ba kabawa su ummi hakuri fushi suke dani, Allah yaya banyi komi ba kawai natsaya da shine awaje "
Yace "wa yace kifita din? Faseelat kinsan fa malaiku na tsinewa macen da tafita batare da izinin mijinta ba "
Tace "yaya I'm sorry, hankali na ya gushe bansan abinda nake ba lokacin "tana cigaba da kuka.
yace "alright naji kimin shiru kinaji?"
Tai tsit tana goge face yace "kitashi yanzu kije kibawa ummi hakuri ki tabbatar ta hakura zankira abba zamuyi magana se kuma ki tanaji abinda zaki fadawa baba babba don yana kan hanya "
Tai tsit tafara raba ido batare da sunyi bankwana ba yakashe kiran,
Ta tashi jiki mace ta nufi dakin ummi bata ciki tafito tai dakin abba ta sameta tana gyaran dakin,
Ta zube kan gwiwoyinta kanta kasa ummi ta juyo tana kallonta faseelat tafara magana "ummi kimin hakuri dan Allah, wlh banyi zina ba nade fita wajen amma ban aikata komi ba, dan Allah ummi wlh bazan iya jure ganinki cikin fushi da damuwa ba "tahade hannayenta gu daya,
Cikin nazari ummi tace"ni nayafe miki faseelat bakin ciki na kawai da kika rasa miji kamar khalil, wai faseelat me kika rasa wurin mijinki da har zaki kula wani? "
faseelat ta kara dukar da kai tasaka hannu ta share hawayen da suka zubo,
ummi tace "inajinki ki fadamin me kika rasa bakida wanda zaki fadawa inbaniba"faseelat tace "ummi kiyi hakuri na barshi ne a matsayin sirri a zuciya ta "
Ummi tai kasake tana kallonta daga jin maganar faseelat ta san akwai wani abu kuma she want to know it,
Ta matsa ta jawo hannun faseelat ta zaunar daita gefenta tace "faseelat dama kinada wani sirri wanda mamanki bazata iya ji ba? "
faseelat tai shiru kanta kasa ummi ta dafata tace "ki fadamin inajinki "
murya na rawa tace "ummi khalil be taba kusanta ta ba ko yaso hakan baya iyawa"
Ummi taja salati tana tafa hannu tana kallon faseelat tace "kice anyi baaiba kenan, natura ki can ina tunanin zaki samu natsuwa ashe gwara ma kina gidannan don bazaki yi wani abun gaba na ba ,to ke miyasa baki fadamin ba aida tuntuni an nema mishi magani tunda be lpya, shine ke kuma kika dauko hanya marar bullewa ko? "
Faseelat ta girgiza kai "Allah a, a ummi "
Ummi tace "bari na kira alhaji nafada masa inshirya inje gidan hjyar muyi magana "
ta mike zata tashi faseelat ta riketa tana girgiza Kai tace "a, a ummi wlh in ina tareda khalil zan fada wani hali, ummi haryanzu banijin kwayar zarra na sonshi a zuciya ta, na miki biyayya ne kawai dan Allah ummi abar maganar khalil dan Allah "ta hade hannu
Ummi tai kasake tana kallon faseelat can zuwa tace "Allah yasa haka shine mafi alheri "
faseelat tace "ummi karki fadawa abba dan Allah "ta langwabe kai
Ummi tace "naji,kitashi kije kici abinci ki saki ranki kuma, sede ina rokon ki da ki kara rike darajarki faseelat karki bawa kowa kanki se mijinki Dan Allah "
faseelat tace "Tom "tana daga kai ta tashi akunya ce tabar dakin,
Ummi ta girgiza kai ita kadai ta daga kai ta kalli sama tace "Allah ka temakeni ka tsaremin diyata "
Faseelat nashiga daki takira fahad yana ganin kiran yaki dagawa yanzu so yake ya cire ta daga zuciyar shi kawai Saboda bazeiya aurenta ba, shawarar da yabawa kanshi kenan,
Tana ganin be dauka ba hawaye suka kara zubo mata tace "nasani nasan haka zakamin"
Khalil ko yakasa fita school hjya taita magana sannan ya tashi ya fita ,
Be koyi nisa ba ya juyo don ya manta wayarshi,ya shigo cikin gidan bako sallama ya shiga ya dauko wayar jin abinda hjya kecewa ne yasa shi dakatawa
Hjya na tunanin ya tafi ta dauko waya ta kira rakiya, rakiya ta dauka suka gaisa,
Hjy tace "rakiya khalil de ya saki matarshi "
Rakiya tace "to barka kunfita lpya "
Hjy tace "to inaso kije malan ya karya asirin nan tunda ansamu ta fita dan aure nakeso na mishi kwanan nan"
rakiya tace "yanzu ko zan shirya in tafi amma ki tanadar min kudi na "
Hjy tace "bakomi kudi ba matsala bane"
Rakiya tace "se nazo tow "ta kashe wayar,
Hjya tace "to ba gashi ba salamun salamun anrabasu"
Khalil jiyayi kamar ze zube awurin, irin kamar an cire mishi duk kuzarin jikinshi, yasamu dakyar yaja kafa ya fita yana fita ya koma gefen gidansu da baranda jiki ya zauna ya duke yana kuka, all this while asiri na tare dashi be saniba, the sad news ma uwarshi ce tasa amishi, wannan wace irin rayuwa ce, duk raini da wulakanci da yasha awurin faseelat ashe mamanshi ce sila, se yanzu yake hango wasu abubuwa da yakasa tunanin su a baya, gaskiya ya cutar da faseelat wata takwas ba saduwa, ya kara fashewa da kuka, shikenan burinta ya cika ya rabu daita, an rabashi da masoyiyarshi wacce yake mutuwar so, meyasa ma be rabu daita ba tun can baya ba?base yanzu da takara shiga ranshi ba, se ya tuna wata magana da alhaji ya taba yi mashi gab aurenshi yace "khalil mahaifiyar ku nada tarin matsaloli ta cika son kanta da yawa batada tunani ko kadan kuma zata iyayin komi a rayuwa inde zataci wa gurinta, ina nufin komi "ya kada kai alhaji be karya ba hjya batada tunani ko kadan ,shikadai yaketa maganganun zuci yana kuka maras sauti,
Wasa -wasa har laasar yana wurin yakasa tashi gabadaya kamar an cire masa lakka ga wani ciwon kai da ya tasomishi, ba azahar bare laasar yana zaune shikadai,
Ana haka yaji karar mashin be juyo da wuri ba yana juyawa yaga mace ta shiga gidan su, cikin karfin hali ya tashi yabi bayanta,
Yayi tsaye bakin kofa yana saurarensu,
Cikin tashin hankali da jimami rakiya tace "hjya naje wurin malam bansame shi ba nafito wani ke fadamin wai ya rasu wata daya da yawuce"
Hjya ta mike tana raba ido ta dora hannu kan bakinta
rakiya tace "bawani abu hjya ki kwantar da hankalinki ai akwai Islamic chemist seki nema mishi ilajis sihir"
Hjya ranta ya baci ido rufe ta cakumo rakiya tana fadin "nide wlh kin cuceni inama bantaba saninki a rayuwa ta ba, kinsani nayiwa dana asiri many times inaganin damuwarshi amma na share Allah yaisa tsakani na dake duk ta dalilin muguwar shawararki na rasa mijina na tabbatar ranar nan yaji komi muke cewa ya hadiyi zuciya ya mutu ke ko ga mijinki da yaranki can gida hankali kwance ......."
Khalil jiyayi kamar an zare mishi rai wani zafi ya ratsa zuciyarshi ya fadi kasa,
jin kurummmm kawai sukayi hjya na zare ido ta saki rakiya tayo waje, rakiyar ma tabiyo bayanta suna fitowa sega khalil kwance Kasa jini na fita daga kanshi saboda faduwar da yayi,
Hjya jiki na rawa ta kwala kara "innalillahi wainna ilaihi rajiun nashiga ukku ni saratu "ta dora hannu biyu saman kai.
hmm mata kenan baku tashi kiran Allah se masifa ta taso,
Allah yasa khalil yana raye
,team khalil atanaji makara da likkafani 😂🏃🏽♀🏃🏽♀🏃🏽♀🏃🏽♀🏃🏽♀🏃🏽♀
.
[7/12, 11:01 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰
By
*MAMAN MAMY*
3⃣9⃣
Dasauri taisa gunshi ta tallaboshi tana kuka "khalil dan Allah katashi karka tafi kabarni "
Rakiya hankali tashe tai waje ta taro me napep da temakonsu akasashi ciki suka tafi asibity, rakiya naganin Sun wuce tai gida hankali tashe don ita aganinta temakon hjya tayi,
Sun isa hospital aka wuce dashi emergency room ana bashi temakon gaggawa,
Hjya na waje nata kuka ta kira kanin babanshi tafada mishi nan take ya taho hospital din, takira siyama tafada mata, kafin kace me sega siyama cikin asibitin hankali tashe tana ta kuka suka rungume juna da hjya sukai tayi,
Lokacin da kanin mahaifinshi yazo shine yayi ta basu hakuri sannan suka dena kwarar bakin yin kuka amma basuiya tsayar da hawayen su ba,
Acikin theater room ko khalil be farfadoba, jin zuciyarshi na harbawa dasauri alamun da ranshi sukai masa wasu allurori tareda yi mishi dinki a inda kan shi ya bugu sannnan aka fito dashi aka wuce dashi bedrest,
Tunda aka fito dashi hjya takara shiga tashin hankali domin kwance kawai yake ba mara barsa da gawa,
Tsoro ya shigeta sosai ta tashi tai waje tai alwala ta dawo dakin tafara kawo nafilfili tana rokon Allah ya tashi kafadun danta.
Da isha'i baba babba yazo gidan su faseelat gashi ga ummi ga abba aka kira faseelat, faseelat gabanta faduwa kawai yake tazo ta zauna,
Baba babba yana harararta don duk amfada mishi abinda akai yace "faseelat abinda kika zabawa kanki kenan? Ki kaso aurenki ki dawo gida ko? Wai kece ke gayyato maza gidanki? "
Faseelat tana girgiza kai tace "dan Allah kuyi hakuri wlh bazan sake ba "tana zubda hawaye.
Baba babba yace "to ai shikenan tunda ya sake ki kuma yayi dede wannan hukuncin da ya miki, amma kisani ranar da ya dawo yace ya medaki ranar zaki koma kinajina? "
Ta daga kai tana share hawaye yace "tashi kibawa mutane wuri mutuniyar banza kawai "
Ta tashi dasauri tana tuntube tabar dakin tana isa dakinta tafasa kuka ta jawo wayar ta takara kiran fahad wayar nata ringing har ta tsinke be daukaba ,ta cigaba da kuka ita yanzu duk tashin hankalinta be wuce rabuwa da fahad ba.
Wasa wasa har seda akai 2 days sannan khalil ya farka idanunshi suka sauka kan hjya dake zaune tana ta lazimi, tana ganin ya Bude ido ta matso tafara hawaye ya juyar da kai don ba yason ko ganinta ta riko mishi hannu cikin nadama take cewa "khalil dan Allah kamin hakuri ka yafemin na zalunceka, wlh rakiya ce ta cuceni dan Allah kayi hakuri nayi hakanne don kada na rasa ka "
Yana ji tana magana be juyo ba, tunani kawai yake wace irin uwa ce Allah yabasu da ita da kanta zata cutar dasu,
Hjy ganin ya kyaleta tasaka kuka harda shesheka, jin sheshshekarta ya juyo da kanshi Yana kallonta se lokacin hawaye suka fara zubomishi, daace wani ya masa wannan abun baze ji ciwo ba akan yadda yakeji yanzu,
Kukan hjya bakaramin tabashi yake ba, baze iya u
jure ganin wadda ta dauki cikin shi tasha wahalar haihuwarshi tana kuka ba,
Yana rumtse ido ya damke hannuta hjya ta bude ido da sukai ja tana kallonshi,
Cikin dauriya yace "kidena kuka hjya ni nayafemiki duk abinda kikamin, da wanda nasani da wanda bansaniba ki share hawayenki, komi kikamin bazan mance matsayinki awuri na ba, kuma bazan iya biyanki abunda kikamin, na dauki wannan abun da yafaru a matsayin kaddara ne, haka Allah yariga ya tsaro kuma lokacin mutuwar alhaji ne yayi shiyasa ya rasu, ina rokonki ki kwantar da hankalinki kidena Damuwa zan warke da yardar Allah adduar ki kawai nake bukata "
Hjya ta dago hannunshi ta dora a fuska tana kara fasa kuka na nadama, ita ta riga ta sani Allah be bata yaya masu halinta ba shiyasa take kara godiya ga Allah akodayaushe,
Khalil yanajin dumin hawayenta suna bin hannunshi yace "plsss hjya ki dena zubar da hawaye yanamin ciwo a raina"
hjya tai shiru tana share hawaye kanta kasa, khalil kallonta kawai yake, su siyama suka shigo room din, yana ganinta ya dan Saki murmushi dukda azabar ciwon da yakeji, siyama ta matsa tana mashi ya jiki,
Sati biyu khalil yayi asibity sannan aka sallamoshi, duk yabi ya rame tunani barkatai sun hanashi sukuni, shi da kanshi yake rokon Allah duk salla akan ya cire mishi son faseelat saboda samarwa hjya kwanciyar hankali, amma da ba haka ba da tuni ya meda princess dinshi dakinta, gabadaya yanzu gidan hjya ya dawo kwata kwata besan ganin ko tunanin abinda ze tuno mishi da faseelat,
Shiru shiru hjya bata kira ummi ba ,don ummi nata tunanin zasu kira amma shiru ganin har anyi 1 month basu neme suba akaje aka kwaso kayan faseelat aka siyar, ummi nata tunanin cewa khalil zargin faseelat yake shiyasa be medata dakintaba sam bata bawa hjya laifi ba,
faseelat se rama take tana ganin rabuwa da fahad abu ne me sauki ashe ba sauki abun, gashi dukda ya shareta abinda yake nuni da bayasonta amma takasa hakura kullum seta kira amma baya dauka ta tura message a what's up yana viewing ammaba reply sosai hankalinta ke tashi, kwata kwata