Showing 3001 words to 6000 words out of 212110 words

Chapter 2 - Ragon Miji

10 Jul 2025

8287

tattaro natsuwarsa bakinsa na dan kyarma yace "Assalamu alaikum"


firgigit ta dawo hayyacinta still zufa na karyo mata se kace mejin kashi,

Tana mazurai tace "sannu da zuwa shigo ciki"

Wani iri yaji jin muryarta yayi tsaye itakuma tashiga cikin zauren gidan ya bita zalalo zalalo kamar rakumi da akala.

Har cikin zauren babban zaure ne dan already har an ajiye sit din roba biyu tai tsaye ta juyo sannan yakaraso tana nuna masa kujera tace" bismilla "

Ya haye ita kuma tasa gefen gyalenta ta share wata zufa data tsiyayomata ganin kafafunsa Sun dan baud'e kadan,

jiki sanyaye taja kujera ta zauna ta dukar da kai sam bata kaunar ganinsa, beyi mata ba, mi zatayi da baki?dogo kamar ba samude sam baze yiwuba.

Tunanin ta yakatse ne da yafara magana voice dinsa na vibrate saboda yadda yake jin tsoro yace "sannu malama faseelat, Da farko de sunana khalil shekaruna 35 ina teaching a all brighters academic, Hjy ta ta umarce ni nazo naganki mu dedeta ina fatan zamu fahimci juna ni da ke "

wata iriyar murya ce dashi gatanan de, ita kuma faseelat tana son miji me siririyar murya shi ko gata de, kamar wadda aka mara tashiga jijjiga kai, shiru ne ya biyo baya can ta tuna bata kawo masa drinks ba, ta tashi ta kawo masa dudu milk ta tsiyaya a cup ta mika masa, yayi kurba daya ya ajiye shiru beda abin fadi kanta na kasa amma duk dagowar da zatayi seta ga ita yake kallo,

Can zuwa yayi karfin halin cewa "kibani no din wayarki "

Faseelat gabanta na faduwa tana inda inda tace "ni banda waya"

yayi shiru can yace" ba damuwa inafatan nasamu karbuwa? "

tai shiru can zuwa ta daga kai

Yace "Alhamdullilah se na sake dawowa ko? "

Haushi ya kashe faseelat se tambaya yake kamar tsohon makaho ta dago tace "ihhhhhh"

Aiko yayi shiru ya tashi tsaye"ni nawuce "

Afili tace "tow agaida Hjy, a Zuci tace agayas "

yajuya yafita daga zauren takara bin bayanshi da kallo kuttt se yanzu ta lura rigarshi ta wuce gwiwa tsabar tsawo

Ta kai minty 5 zaune sannn ta tashi tai cikin gida,

Shiko Karon farko da yafara fira da mace dadi kawai yakeji yanda ya sameta ya tada babur dinshi yayi gida.

Faseelat nashiga cikin gida da sallama ummi ta amsa, zuwa tai zata wuce ummi tashiga daki ta kwanta ko ta samu ta dawo dede,

ummi tana kallonta tace "zo nan faseelat"

Tana daga kafa daya kan daya kamar wadda kafar taiwa dayi tazo gun ummi ta zauna,

Ummi tace "ya kukayi"

Faseelat ta sosa kai tare da cewa "naam"

ummi ta harareta tace "eh "

Sosa kai faseelat ta fara labbanta na kyarma tace "ummi beyi kama da mijin da nikeson aure ba "

ummi tarika jifanta da mugun kallo can tace "dan ubanki har wani kalar mijin da kikeso kika tsara? wallahi faseelat ki shiga hankalinki tom,"

Faseelat ta zumburo baki gaba "wlh ummi bani sanshi baki ganshiba beda kyau ko kadan "

ummi ta rike haba "faseelat? Dan kina ganinki fara shine zaki ce haka, ke kekikayi kanki haka hala? To kamar yadda kike haka fara shima haka Allah yayishi baki kuma haka yakeson ganinshi "

faseelat ta matso hawaye "Allah ummi ni banisonshi "


ummi tace "rufemin baki kar in mazgeki, dan kinsamu ze temakamiki ma wa yataba cewa yanasonki? Dankawai ze rufa miki asiri? To barikiji wlh inkinga baayi aurennan ba to abbanku ya binciko wani mummunan hali atare dashi ne ko in Allah ya kaddara
Ke ba matarshi bace amma ina tabbatarmiki se anyi bikinnan "

Faseelat ta dora hannu akai "nashiga ukkuna ummi dan Allah ki temakamin "

Ummi tace "temakon da zanmiki knan in aurar dake "


Faseelat tafasa kara tana kuka sosai ummi ko tatashi tabata wuri tace "ai seki tayi "

"wayyo Allah na ni wlh bansonshi "
Hardasu majina saboda kuka sallamar abbansu ne yasa ta gudu wurinshi ta rungume "abba dan Allah banisonshi karku auraminshi "

cikin mamaki yace "share hawayenki diyata "

Tasa hannu ta goge still wasu na biyowa yace "bawanda ze miki auren dole kinaji ki wuce kije ki kwanta "

Faseelat ta wuce sundum sundum ummi tafito daga kitchen "amma de alhaji kasan bazanji kunya nai magana biyu ba nariga na amsa musu yanzu mi kakeso nacema uwarsa ince bata sonshi? "

Abba cikin sanyin murya yace "haba asiya kibi komi sannu mana, wai ma duka Nawa faseelat din take ne? Duka fa yanzu shaekararta biyu da graduate, kibari komi asannu akebinshi ai yau suka fara haduwa may be su dedeta zuwa gaba"

Faseelat dake labe tace "wlh aa banisonshi bazan so sa ba harabada "sede bawanda yajita dayake ta Shiga daki

Ummi tace "hmmmm"

Tashige kitchen

Shiko abba ya shige daki yana girgiza kai, yarasa daliin ummi da ta kagara ta aurar da faseelat.

faseelat kan gado ta mike tanata sharar kwalla har bacci ya kwasheta.


shi ko malan mudi da farin ciki ya isa gida,

Bayan ya shigar da babur dinshi yawuce dasauri dakin Hjyarsu Hjyar na tsefe gashinta da rabi yafara zama furfura ya shiga, Hjy saratu ta dago tana kallon fuskar shi tagane yana cikin farin ciki,

Ya zauna tare da cewa "Hjy kiniya zabe wlh tayi komi yayi dede, gata da kyau ga iya wanka "
Hjyar tai dariya" marar kunya kawai, aibaka isa aure ba "

Yayi shiru yana dariya "toya ita faseelat yanayinta ta amince? "

yace "eh Hjy "

"to yaushe Zaka koma? Kukara ganawa, kafin atura su kawu "

yace "gobennan Hjy "

Hjy tace "hmmmm Allah ya kaimu, sede dan Allah ka natsu kuma ka rika yimata kyautuka saboda takara sonka sannan kuma ka san maganar da zakurika yi "

Yace "to "


Yakagara gobe tayi


*nace da akwai matsala kufa? 🤣*
[7/12, 10:58 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰







Writing by *MAMAN MAMY*




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*





5⃣




*Dedicated to SIS ZULAIHAT RANO*



Ya kagara gobe tayi ko yakara ganin kyakkyawar fuskarta.

Wasa -wasa har dare faseelat taki tafito waje, ummi de ta share ta su abulkhair suna ta tambayarta sede ummi tace bacci take ,

Har abba ya dawo gida bayan ishai ummi da abba suna daki suna fira while ishak abul da Mubarak na tasu firar, dan auta ya kasa hakura da rashin ganin ta ya leka dakinta tayi rubda ciki amma ba bacci take ba, abin duniya ne kawai ya sha mata kai, ganin idonta rufe yasa yaja mata kofar,

Dakin abba ya shiga ya samu ummi ya zauna gefenta "ummi kode ya faseelat bata lpy? Naga tundazu da rana bata fito ba yanzu naje dakinta na ganta kwance har yanzu "

Ummi tace "to bana ce maka bacci take ba? Ka tashi kaba mutane wuri "

Yace "to ummi kode a tado ta ni wlh gidan ba dadi da babu ita "

Ummi tace "kai kasani ai "


Abba yace "wai tun dazu bata fito ba? Kuma kika kyaleta haba Hjy kinsan fa ulcer na iya kamata "

"to ya kake so na mata? Ko so Kake naje na rarraso ta tunda na mata laifi "

Abba yace "yaro dan rarrashi ne in kika lallabata se ki shawo kanta amma bata haka ba, kinsan faseelat na da saukin kai ai "

"Alhaji kabarta kawai in yunwa ta kusa kasheta zata fito, nifa duk abinda nakeyi saboda ita ne yarinyar nanfa da kake gani kusan kullum se tayi mafarki, taya kake tunanin hankalina ze kwanta tana zaune gidannan gwara ai mata auren tun kan ai abun kunya "

Abba yayi shiru yana nazari,yace"eh ki de bita a sannu, wa ma ta gado inbake ba da jarabar tsiya in baayi miki 3 rounds ba baki koshi "ya ida yana dariya

Tace "eh naji din ai kai ma shine da har kake iya yin ukkun "

Suka sa dariya Mubarak fa yadade da barin wurin tunda aka korashi.

Ummi nata zuba ido faseelat zata fito cin abinci amma bata fito ba, se kuma tafara shiga damuwa.

Itako faseelat muguwar yunwa takeji ga, zazzabi da ya rufeta kwance kawai take tanata tunanin yadda zatayi rayuwa da khalil.

Can 12am samarin duk sunyi bacci ummi tafito daga dakin abba har zata wuce se kuma ta shiga dakin faseelat,

Tana kwance rubda ciki still ummi ta matsa "ke bana hanaki kwanciya haka ba?"

faseelat ta birkita ba tare da ta dago ba

Ummi tace "wai dani faseelat zaki fushi ?dan kawai ina fadamiki gaskiya? Ya kikeso nayi ne? So kike nabarki na zuba miki ido? Bayan ga hanya Allah ya kawo, haba faseelat wlh kinbani mamaki da har zaki bijirewa magana ta shi dake namiji ya amince da umarnin mahaifiyarsa, amma ke kinkasa ".

faseelat ta fashe da kuka tana sheshsheka ummi tace "aa kidena kuka faseelat bazan takura miki ba tunda bazaki iya aurenshiba shikenan gobennan zankira uwarshi in fadamata bakisonshi tunda burinki ki kunyatar dani, ni wlh daace kinada wanda kikeso da baabinda zesa na matsa miki amma keda bakida kowa ihhhhm? Dama ace ke lafiyayya ce amma kinada larura ki duba fa yanayinki faseelat, shikenan anfasa auren ki tashi kije kici abinci "

Ummi ta juya zata fita faseelat na kuka ta kira sunanta "ummi "!

Ummi ta waiwayo ta cigaba da cewa "Dan Allah ki hakuri baniso ranki ya baci karki fushi dani "

"bazanyi fushi da keba faseelat sede ki sani zaki sani cikin zullumi da tunani dan wlh inde ban aurar dake ba banida kwanciyar hankali "

Faseelat daga kwancen de take magana cikin rashin tunani tace "na yadda ummi zan aure shi inde zakiji dadi "

Ummi tace "dako kinfaranta min rai dan inada tabbacin bazaki kuka ba in Allah yaso"

faseelat tace "na amince ummi kuma kiyi hakuri da bata miki rai da nayi "

ummi tace "bakomi Allah ya miki albarka ki tashi kici abinci karkijawa kanki ciwo"


Faseelat tace "bazan iyaba ummi masassara nake tun dazu "

ummi tace "subhanallahi "tana hawa kan gadon ta fara tattabata gabadaya jikinta rau yake har kafafunta, ummi tace "sannu kinji bari na kawo miki magani "
Ta tashi ta fita wani kuka ne yazowa faseelat ita kanta tasan ta amsa ne kawai amma tasan haka zatai ta rayuwar hakuri harabada, tasa hannu ta share hawayenta yanzu de koba komi ta farantawa mahaifiyarta rai da tun tasowarta tana ganin yadda take fifita ta akan yanuwanta.

Motsin da taji yasa ta kara goge fuskarta ummi tashigo dauke da tray ta ajiye ta bude flask ta debo taliyar hausar da ta dafa da daddare ta dora kan bed ta debi ruwa ta ajiye sannan ta zauna bakin gadon tace "tashi ga abincin diyata "

Faseelat na ciza baki ta yunkura ummi taida tadata zaunen jikinta har kyarma yake saboda yunwa,

Ummi tafara bata abincin a baki da yake tana jin yunwa taci abincin sosai sannan ta bata magani ta koma ta kwanta se sannu ummi ke mata sede ta daga kai, tashi ummi tayi taja mata kofa tana mata seda safe.


ko bayan fitar ummi faseelat kuka ta rikayi ga bacci ya kaura cewa idanunta,
Ba abinda take tunani se fuskarshi da jikinshi tana tunanin yadda zasuyi rayuwa tare wuri daya gida daya daki daya gado daya.


Se asuba bacci ya dauketa, ummi na Gama azkhar taje ta gaida abba yake tambayarta jikin faseelat da yake wurinshi ta amso maganin tace dasauki ta fita dubota, tana shiga ta tada ta faseelat bude ido kawai tayi ummi tace "ya jikin "tana tabata faseelat tace "dasauki "

Ummi tace "naji haryanzu da fever din kitashi ki salla inje in hado miki tea kisha kisha magani "

Faseelat tace "I'm off"

Ummi tace "kinada pads ne? "

Faseelat tace "eh amma beda yawa "

"OK anjima zanba Mubarak yasiyo miki wata tashi kije ki kimtsa ko kinji dadin jikin "

faseelat tace "to "ta mike ummi taga har tangadi take ummi tace "zakiiya wankan kuwa "

Faseelat tace "eh "tafara bin bango ummi takamata ta kaita toilet sannan tai kitchen,

Da dai daya yanuwanta suka rika shigowa suna mata ya jiki kafin su bar gidan, shi ko Mubarak harda hawaye danba karamar shakuwa sukai ba daita.

Bayan tasha tea din da magani ta koma ta kwanta,

Can wajen 12pm ummi nata aikace aikacenta wani yaro yazo yace ana kiran faseelat .

Ummi ta danyi jimmm sannan tace "gatanan zuwa "

Yaro yaje ya kai sako

itako ummi tashiga dakin faseelat har lokacin tana bacci ummi tafara tapping dinta tana kiran sunanta faseelat ta bude ido, tana kallon ummin.

Ummi tace "ki daure kitashi ki dan kimtsa ga khalil can yazo "

Faseelat gabanta ya bada dudum, tasan datace bata iyawa ran ummi ze baci dan dole ta mike tsaye ummi tace "zade kiiya ko? "

Faseelat tace "eh ta jawo hijab har kasa ta saka ai gwara tajema ta kara ganinshi maybe jiya batai masa kallon tsaf ba.

Tana saka hijab din tafita ummi ta girgixa kai tana kallon yadda take tafiya a kasalance.

Faseelat na fita taganshi a.....




Next page loading........
[7/12, 10:58 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰





By



*MAMAN MAMY*



https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



6⃣




*Dedicated to SIS ZULAIHAT RANO*




a zaune kan roba-robar shi kallo daya tai mashi ta dauke idanunta, jikin bango ta jingina kanta na kallon sama ta cije baki saboda Marar ta data murda ,

Shi ko yana ganin fitowar ta ya mike tsaye yana gyara riga ganin ta jingina a bango tana ya mutsa fuska yasa shi jin badadi,

Bakomi yasa faseelat dauke kai ba se dan ganin kara jiya da yau, shadda ce jikinshi fara kall ya kawo farar hula akanta ga takalmi fari, wayaga balbela🤣
Shi gashi baki abin se ya dagule, itada tafito ganin canji se taga gara jiya, shaddar se sheki take tsabar fari.


Shi ko be samu ganin fuskar taba saboda kanta na facing up ganin Sun kusa minti ukku yasashi cewa "barka da fitowa"

Batare da ta sauke kanta ba ta dan juya shi ta zuba mai jajayen idanunta wanda suka kumbura saboda rashin barci da kukan da tasha ,

Yace "subhanallah, faseelat lpya kike? "

Ta juya sannan tace "ban lpya "

Cikin jimami yace"miyasameki?"

Tace "fever"tana tabe baki.

Yace "ayyyah "da karfi wadda tasa seda ta mike daga jikin bango saboda yadda gabanta ya fadi, Ya cigaba da cewa "Allah shi sawwake shi baki lpya "

Faseelat kamar ta dora hannu aka tasa ihu haka takeji, ashe ba karamar illa takeso taiwa Kanta ba ko magana be iya ba, shi ga bahaushe wani abinda ta dan lura dashi shine kamar maganarshi daga hanci take fitowa.

yakatse mata tunani da cewa "ga wannan"

Ta kai kallonta ga ledojin da yake miko mata, daya babba daya karama, dan dole ta mika hannu ta amsa can ciki ciki tace "Nagode"yayi kamar be jiba sema yace "dama zuwa nai mugaisa gashi bakya jin dadi yanzu ni zantafi se munyi waya ga waya nan da sim da komi "

Batare da wata murna ba ta kalli ledar hannunta ta yamutsa fuska.

Yace "se anjima agaida ummi "

ta juya kawai ta shige gida tana saka da warwara , yadda zata kuma ganinshi in ya dawo dan kullum kara gano muninshi takeyi.

tana shiga gida ummi tayi shimfida kan barandar gidansu kafafunta a mike tana huce gajiyar hidimar da tasha, ta je ta kwanta kan kafafunta,

Ummi tace "sannu faseelat kode mutafi asibity? "

Ta girgiza Kai ummi ta kai dubanta ga ledojin da suke zube ta jawosu tana fadin "shi ya baki wannan?"

Faseelat ta daga kai idonta na kawo ruwa batare da ummi ta dubeta ba ta Fara bude ledojin, daya cosmetics ne kawai ciki, danginsu perfume, Nivea lotion, roll on, powder irin big pack dinnan wadda Zaka samu su concealer da foundation, da janbaki duk a ciki, se lip gloss.

dayar kuma waya ce ciki me suna infinix hot 6, ummi tace "aaa!masha Allah Allah yasa alheri, faseelat kinga kaya ko? "

faseelat da duk abinda zaa daga wani kululu ke tokare mata makoshi tace "ihhhhm "

Ummi tace "to ga waya faseelat tunda wayarki tasamu matsala har yau alhaji babba be aiko da wata ba toga khalil ya hutar dashi "

faseelat ta mike tsaye zata wuce dakinta dantagaji da jin maganganun ummi, kawai wayar tafara ringing, ummi tace "zo zo gashi har ya kira ashe a bude take "

Faseelat takoma ta amsa kamar zatai kuka tashige daki tana shiga ta danna ta a key dif ringing ya tsaya ummi duk a tunaninta faseelat ta dauki wayar ne, kiran na yankewa shiru be sake kira ba faseelat ta tabe baki,

Ta haye gado tana tunanin rayuwar da zatayi nangaba,

Hannunta ta dora kan kirjinta taji yadda yake fat..fat ta fara hawaye.


khalil yana be koma gida ba se 2pm dan daganan school ya wuce,

Yana shigarda mashin dinsa yayi hanyar dakinsa Hjy saratu da ke alwala zatai salla tabar alwalar tana bin bayanshi da kallo har ya kusa shigewa Hjy tace "kai zonan khalil"

ya juyo yaisa wurinta dan slope din dakinta da take kai anan ya zauna tana kallonshi tace "lpya kake naga ka dawo haka kamar marar lpya? "

ya cire hular kanshi yana fifita yace "Hjy naje gidansu faseelat na sameta bata da lpya sosai "

Hjyar tace "ummm se akai yaya? "

yace "shine nakeji nima bani lpyan "

Hjy saratu tai kasake tana kallonshi shi kuma dagaske yake maganarshi ,Hjy tace "to Allah ya sawwake ,saboda bata lpya shine kake wannan yaushin? kamar ba namiji ba, tashi da Allah kaban wuri "

Memakon ya tashi se yace "Hjy yaushe zakije ganinta? "

ta banka mai harara "se ran da na shirya "

"to me ze hana kije yau? "

Cikin haushi tace "saboda ban ga dama ba "

Ze kara magana tace "aa da Allah kyaleni fita xanyi yanzu idan na dawo zan biya ingano tan "

yace "tom "ya mike zakadai -zakadai ya shige dakinshi, wata kan jiya daga jiya zuwa yau faseelat ta zama wani bangare na cikin jikinshi, ku jifa 😂kunsan irin su dasaurin shiga hannu ,

wayar shi ya fiddo a aljihu ya kara kiranta bata dauka ba faseelat lokacin ma batasan inda kanta yake ba dan gabadaya masassara ta rufeta tana cikin bargo tana kyarma lokacinma ummi na wurinta zaune

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login