Showing 165001 words to 168000 words out of 212110 words

Chapter 56 - Ragon Miji

10 Jul 2025

8291

"Allah sarki amira ta rasu dasunan anty abakinta,

fahad da hankalinshi yadan dawo cikin tashin hankali yace "daukota mutafi asibity daukota "

Ya mike tsaye yana nuna mata tatashi,


Faseelat ta kifa kai jikin amira dake jikinta tana kuka mecin rai tace "amira ta mutu amira tatafi "

fahad kamar ansoka mishi mashi yaji yayi sauri ya amshi amira yana dubawa amma ina ta rasu ya kwartsa ihunda seda Aisha tatashi duk karfin maganin datasha kuwa,
Yana kuka yana kiran amira,


Faseelat nata kuka kamar zaa fidda mata rai take cewa "seda nace kadagani, kadagani "


Aisha jin yanata kiran amira yasa zuciyarta bugawa da karfi, kukan dadi daban na tashin hankali daban baa taba hadasu, dagudu ta hito tayi cikin dakin,

Tana shiga taga fahad rungume da amira yana ta ihu da kuka faseelat kuma tana gefen kafafuwan amiran tanata kuka kamar ranta ze fita,

Aisha zuciyarta na up and down very faster ta kalli gefen bakin amira taga jini, ga fahad nata girgizata bata motsi,


Diff komai yatsaya mata tai baya tafadi kasa a su me ,



Sede sukaji karar faduwarta fahad yadago kai da sauri ya ajiye amira yayi wurinta yana girgizata amma shiru yarika kuwwa yana girgizata yana kuka da magana ,


"Aisha kitashi Dan Allah kutashi plssss Aisha!!!! "




Allah sarki rayuwa kullu nafsin zaikatul maut,
amira de antafi Allah yasa meceton su Aisha da fahad ce, 😭


*R. I. P* *our meera we will surely miss you*😭


*da haka kuma nike kira gareku mutane murika kula da yiwa diyanmu addua karmu rika mantuwa, sannan mudena yada diyan mu a media irinsu Insta dasauransu don bamusan iya wadanda zasugani ba har gwamma status me contact dinka kadai zegani kuma nasan inbaka da relation da mutum ba yadda zaai yayi saving number dinka tunda batai mishi amfanin komi ,domin akwai masu kambun baka tun azamanin manzon Allah (S. A. W) wlh wani ko yabon abu yayi sekaga abun ya lalace ko ya mutu gabadaya, balle yanzu duniya tacika da matsafa yan mafiya yan asiri yan tsubbu dasauransu wanda kana nesa se suiya cutar da kai in Allah yaso, yanzu de gashi amira tatafi Allah kadai yasan dalilin mutuwarta, inafatan andau darasi acikin mutuwar amira, nide fatana akoyaushe a novel dinnan ku dauki darussan ciki masu amfani kubar Wanda basu dashi, inafatan ana tsintar wasu darussan boye da basu fito fili ba amma nasan masu hankali sun gansu kuma zasuyi amfani dasu, raggon miji dasauran tafiya ahaka inaganin ina maku tsallake banbi daki daki amma alhamdulillah tunda kuna ilmantuwa da nishadantuwa*


*mudage yiwa diyanmu adduar neman kariya insun girma mukoya musu surikayi da kansu*




*ina mika sakon taaziya ta ga amira fans Allah yajikan mamatanmu musulmai maza da mata amin kuma ina baku hakuri da yadda labarin ze cigaba da tafiya duk kansu akwai darasin da nakeso adauka akansu sede ayi hakuri akan yadda abun ze kasance kuciga da nishadantuwa amma karkumanta kuna ilmantuwa da abinda kaga yayi dede*


*😂nasha wuyar page dinnan ba page din dayaban wuya kamar shi awa 4 ina typing nashi ya kukaga debate yayi? Ayi hakuri da turancin candidate🤣 ahankali muna kara koyo ,acikin maza kukawo oppose na debate din ,ko cikinku mata wadda take mutuwar son mijnta takawo nata debate na opposing that female education is better than male education🤣 ko kuma wadda bata yadda da hakan ba, thank you all enjoyed*







*don't forget to comment saboda aradu na wahala na gwagwatu harseda na nemi temako*😂💃🏼
➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰







By








*MAMAN MAMY*
*(SHALELE)*




✍🏽✍🏽 *GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION*✍🏽✍🏽✍🏽

We are bearer's of so golden a pen🖊
We write assidiously perceiven no pain
So magical
Our creative golden pen🖊
Be hold our words
A product of our pen🖊
Savour our words
For it will cause you no pain.✍🏽


https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/






8⃣1⃣





*Manzon Allah (S. A. W) yace wanda ya muku alheri to ku gode masa kuma kusaka masa da alheri kwatan kwacinsa ko fin haka idan baku da hali to kuyi masa addua*





*pagyn kine Mrs Ibrahim maman teamalo😍kinasona da diyana kina bamu duk kulawa inasonki sosai da sosai Allah yakawo ranar haduwar mu alherinki gareni yafi karfin fada nagode maki Allah yakara dankon soyayya keda oga yakara budi ya kawo triplets masu albarka luv u so badly dear*






Faseelat na rungume da amira tana kuka shi kuma yana rungume da Aisha yana kukan,

Dogon lokaci aka dauka sunayi abunda faseelat ta lura dashi fahad beiya rudewa ba dan lissafin kanshi kwancewa yake gabadaya,

Tana kuka ta ajiye amira ta tashi tafita tashiga dakinshi takira doctor faith,

tana gama waya daita ta kira umma har lokacin tana kuka da misalin 3:40 umma ta farka tana nafilfili kira ya shigo gabanta yayi mummunar faduwa ta dauko wayar tana dauka tafara jin kukan faseelat,

Tana kuka take magana "umma amira ta rasu amira tatafi tabarmu"

Jikin umma ya mace zuciyarta ta karye dandanan hawaye suka cika mata ido tasamu tace "innalillahi wainna ilaihi rajiun, Allah ya jikanta yasa me ceto ce kuyi hakuri faseelat"

Faseelat bata iya magana ba saboda kukan dake kara tunkudota ta kashe kiran,

Umma tai zaune tana hawaye suma ajiya duk sunga vedion sunata jindadi ashe ajali natafe,

Faseelat ta kira mommy, tana tsaka da bacci jin ringing yayi yawa yasa ta dauko wayar da bacci a idonta ganin son yasa tadan bude ido ta dauka,

jin sautin kuka yasa tatashi zaune faseelat na kuka tace "mommy amira ta rasu"

diff takashe kiran,


cikin mommy kullewa yayi zuciyarta na harbawa da karfi batsayawa hawaye suka cigaba da zubomata, tatashi dasauri daga ita se zane da vest tasaka hijab tafita dakin da keys ahannu ta shiga dakin su ramlat ta tadasu tana hawaye tafada musu sukaita kuka dukkansu suka fito suka nufo gidan,


faseelat na fitowa taji ana danna door bell taje tabude doctor tashigo dasaurinta hankalinta tashe ta haye sama da dangudu faseelat tabi bayanta tana ta kuka,

Doctor nashiga tasamu fahad yarike Aisha yanata kuka tai sauri ta matsa gunta tafara bata temakon gaggawa,

tana jikinshi tafarko da nishi me karfi kirjinta na dagawa sosai idonta a kulle,

doctor tai mata allurar rage pain ta mata ta barci ahankali jikinta ya koma yasaki,

Sannan takoma gun amira dake hannun faseelat sede tana dubata taga ai ta rasu,

ta girgiza kai hawaye nasan zubomata tace "kuyi hakuri mutuwa dole ne kowa se ya mutu kuyi hankuri "da yar hausarta dabata ida gogewa ba,

Tafita dakin dasauri tabar gidan saboda kukannasu jinshi take kamar me,

Tana fita su umma sukashigo sukai cikin gidan suna kuka,

suna shiga dakin suka tarar har lokacin Aisha na jikinshi yanata kuka ga amira a jikin faseelat mommy taje ta amshi amira tana ta kuka su ramlat suka kama Aisha suka kwantar daita kan bed sunata kuka,

ana haka sega umma da tawagarta suma sunata kuka se lokacin megadi yagane mutuwa akai,

suka shiga ciki suna tayi,

se gaf asuba sannan umma ta amshi amira tai mata wanka aka rufamata zane,

Da asuba fahad yafita yafada a masallaci akwai janaizar diyarshi da karfe 7 na safe, mutane sunata mai taaziya duk yabi ya rikice,

Har yakama hanya liman yabishi yasa meshi cikin nuna tausayi yace "alhaji fahad kuyi hakuri da rashin da kukayi, Allah yana son masu hakuri nasan hawaye dole ne saboda shakuwa da yaro manzon Allah (S. A. W) ma yayi hawaye a lokacin da Ibrahim ya rasu amma kuyi hakuri ku dangana se Allah yabaku wasu masu albarkan dama shiyabaku ita kuma ya amshi kayanshi in kukayi hakuri seyabaku ladar hakurin ya musanya maku da wasu kuma inamaku albishir da cewa yara zasuyi ceton iyayensu ranar kiyama insha Allah zaku hadu a aljanna "yana maganar cikin tausasawa,

fahad seyaji hakuri yazo masa lokaci daya, yace "nagode malam Allah yajikan mahaifa "

liman yace "amin "sukai musabaha ya tafi,

fahad na zuwa gida yakira abokansa na kusa yafada musu, yasa akakawo likkafani akaimata sutura,

dandanan mutuwar amira tabazu cikin garin,

7 dede aka kai amira makwancinta mutane ne birjik don fahad mutum ne me kyauta da muaamala da mutane wasuma besan suba duk sunzo,

kowa yatafi amma shi yana duke wurin kabarin yana kuka,

sabeer da shima mutuwar ta girgiza shi har hawaye yayi yaje yakamashi yasashi mota suka nufi gida,

Ahanya yanata bashi hakuri da nasiha har yayi shiru,


Bayan anfita da amira umma takoma gida itada mommy sauran kuma sunanan dangin mommy kau sun cika gidan,

Faseelat haryanzu bata samu natsuwar yin waya tafadawa yangidansu ba,

Ana haka Aisha tafarfado tana hawaye masu zafi, zuciyarta na matsanancin ciwo,

Anty salma suka medata dakinta suka bata magani takasa cewa komi se hawaye data ketayi baadadi,

Su fahad na dawowa yasamu cikin gidan duk ankafa rumfuna na zaman gaisuwa,

yaje ya zauna mutane sukaita mishi gaisuwa,

Zuwa 12:00pm har yan kasashen waje sunji labarin mutuwar amira yara mate dinta sunata kuka wadanda jiya ta burgesu sunata yi,


Karfe daya da wani abu mutane suntafi sabeer ma yatafi yayi wanka fahad yashiga gidan ta kitchen,


Faseelat suna zaune falo inba kukan ta ba ba abinda akeji anyi rarrashin anyi ban bakin taki hakura,

Da fada Anty salma tace"ke da Allah kimana shiru munafukar banza munafukar wofi kin damu mutane da kukan munafunci dan ace kinason amira to kinason ta din muguwa kawai wa ma yasani ko ke kika kasheta yarinya ba ko ciwon kai sede asamu ta mutu"

su lady duk shiru sukayi, dangin mommy akai mata ca wasu nabada hakuri,

Fahad da yadanji wasu maganganun be gama jiba ma yahaye sama saboda idan yatsaya bakaramar matsala zaasamu ba,

Faseelat ta tashi tahaye bene dagudu tana kuka tashiga daki tai zaune saman kujera ta hade kai da gwiwa tanayi,


fahad da yashigo daukar wayarshi yafito yazo wurinta ya zauna ya medata jikinshi yana rarrashi,

faseelat tai shiru sede hawayen sunki tsayawa,

cikin dauriya ya dago fuskarta yana kallon fuskar yace "kiyi hakuri kidena kuka honey amira yanzu haka tana aljanna kidena zubar da hawayenki ki sawa zuciyarki hakuri, kuma kiyi hakuri da abinda anty tayi kidaure ki kulle idonki da kunnenki a cikin zaman gaisuwar nan har agama domin dangin mommy basuda halin kirki kiyi hakuri kinji kidena kuka yanakara dagamin hankali "

tanata ajiyar zuciya hawaye na kara zubomata, saboda tsananin sonta besan lokacin da yasa harshe yana lashe mata hawayen ba "

lady data biyo bayan faseelat dama kofar nabude ta hangesu kan kujera dayake sun bata baya setaga kamar ma kiss suke, takoma da baya tana tunanin jarabar yayannata,

dakyar yasamu tai shiru tashiga wanka ,shikuma yatafi dakin Aisha,

sadiya na gefenta yahau gadon yana kallonta yace "ki yi hakuri Aisha amira mutuwarta yafi rayuwarta domin tana cikin rahmar Allah ayanzu haka "

Aisha da hawayen sundena ma fitowa saboda tashin hankali ta lumshe ido kawai batare da tace komi ba,

Yatashi yafita yayi wanka ya tafi masjid,


Yan group din su Aisha naganin post na cewar amira ta mutu jikin hotunan jiya an rubuta rest in peace suka rika karyatawa nan suka fara kiranta sadiya tace musu gaskiya ne nan sukaita kira gaisuwa sede sadiya ta dauka,


seda faseelat tagama salla takira umma tafada mata, ba jimawa umma ta zo itada fadila su ya omer ma dasauran suka taho gaisuwa,

bayan ta musu gaisuwa tatafi gidan umma ta mata da gidan mommy sannan takoma gida,

Malaman amira suma segasu mutane anata shige da fice wangame gate din gidan akayi dan samun hanya,


ranar bawanda yaiya shan ko ruwa da faseelat da fahad Aisha ko dole suketa bata magani,



da daddare mutane na jiran cigaban labarin amira wadanda basu saniba sede sukaga sauyi,

yau aichatu Ibrahim mousa itace me gabatarwa suma mutuwar ta basu tsoro tace "Allah yayiwa amira fahad rasuwa yarinyar da ta anshi kyautuka 5 jiya,zamu nuno muku cigaban tattaunawar jiya da wadda mukayi yau da makusantan ta "

Bayan angama labarai tace "a Nigeria Allah yayiwa amira rasuwa a jiyan da daddare ta mutu ne batare da ciwo ba zamu kalli cigaban rahoton jiya da kuma wurin taaziyarta ayau "

Aka nuno malaman su na yabonta wurin meda hankali a karatu da kuma kokari sannan aka nuno sabeer da dazun dole yayi magana da suka sameshi wurin gaisuwa,

sabeer yace "Allah ya mata rahma iyayenta sunyi rashi amira yarinya ce meshiga rai fatan Allah ya jikanta yaba iyayenta hakurin rashi "

se aka nuno anty salma tana ta hawaye tace "ba ciwo bakomi ta rasu munafatan Allah yabasu wadanda suka fita "seaka dauke gun akadan hasko hotunan amira lokacin da take Amsar gift na can baya dana jiya, daga karshe aichatu tace "Allah yajikanta ya mata rahma muna ma iyayenta taaziya, dafatan sauran yara zasuyi koyi daita da haka ni aichatu Ibrahim nakecewa mukwana lpy daganan London "tadan matse lips irin yadda takeyinnan 🤣kafin adauke wurin,



Mutane sunata roka mata gafara aka kuma cigaba da yada vedion ta da pics wasu ma seyau suka gani,


bayan week jamila tagama wanka tahadu ta tsumu, khalil Allah yakara masa budi ya siye mota da dalleliyar motarshi maroon color yaje dauko jamila,jamila batasan da motar ba yadece zezo su tafi sega mota Taita murna suka kamo hanya suka taho,

bakinta yaki rufuwa khalil se satar kallonta yake yana murmushi tana rikeda lil khalil ta kalleshi tace "yaya wannan surprise haka kayi amarya bakafadamin ba wlh nayi murna sosai Allah yakara budi "

Yayi dariya yace "da amarya ce aida bakinnan naki seya tabo batsari daga katsina saboda yadda zaarika kara mishi tsawo"

Tai dariya tace "yaya kenan kishi fa halass ne yinshi "

yace "eh amma bana hauka ba "

Tace "wai miye ma na firar ni kadai zan zauna dakai nasan bazaka min kishiya ba ai saboda kana sona sosai "

Khalil yace "hakane nadade da afkawa cikin kogin sonki, me kika tanadarmin ne? "

Tace "ai yaya baa magana semun hadu kawai "ta rufe fuska tana dariya,

yace "Allah? "


ta daga kai yace "I'm happy yanzu de zamu biya gidan musa semuwuce gidan hjya dan tayi missing naku daganan semu tafi gida"

jamila tace "Tom Allah yakaimu lpy,


bayan sun isa gidan musa aka tarbesu hannu biyu ancika musu gaba da kayan sha da fruit sukadan sha sannan musa da khalil suka fita da jamila da matar musa sukadan taba labari sukai exchanging numbers sannan khalil yamata flashing tayomata rakiya suka tafi,

suna shiga gidan hjy jamila ta bude baki tana sallama "assalamu alaikum hjy ga mijinki nakawomiki "

hjy tafito daga daki tana faraa tace "maraba da ku kunsha hanya sannunku"


jamila ta mika mata lil khalil tana dariya tace "hjy inawuni mun sameku lpy?"

hjy tace "lpy lau ya mijina sarkin kuka koyadena kukan "

Jamila tace "ai yadena hjy "

sega khalil yashigo yakara gaida hjy suka shiga ciki,

Jamila ba kunya tatashi ta zare hijab ta bude fridge ta dauko ruwa da lemu takawowa khalil ta dauka tasha,

hjy na rikeda lil khalil tace"jamila ki dauko muku abinci mana a kitchen "


khalil yace"aa barshi hjy akoshe nake wlh "


hjy tace "to in ita tana cifa "

khalil da ya matsu suwuce gida su hadu chamber yayiwa jamila magana da ido dan yasanta acici tana iya cewa tanaci ,

jamila tace "a, a nakoshi hjy "

sannan sukadanyi fira suka tafi su biyu suka gyara gidansu lil khalil na goye yayi bacci ta kwantar dashi suka shiga wanka ko a toilet sunsha love sannan suka dawo bedroom suka cigaba da faranta ran juna, kunsan in aka dade baa haduba kowa dokin kowa yake kusan 1hr sukayi suna romance and sex,

daganan suka cigaba da rayuwarsu hankali kwance, khalil yabar ma zuwa shago, jamila kuma duk intaje gidan hjy ita take mata girki da share share dan takara samun nasiha wurin mamanta na ta kara kyautatawa uwar mijinta, hakan yasa khalil yakara sonta fiyeda baya, itama hjy sonta take sosai don tayi hankali yanzu,




Saura 2days bikin su lady gyara sukasha ciki da waje, umma me gyara takira ta musamman tana gyaramata yan matanta, faseelat ma tayi iya kokarinta wurin temaka wa lady da kayan matsi itama ladyn tadade da yin wasu da tagani a media sude gidansu faseelat basa wata hidimar biki domin haryanzu basu gama fita daga alhinin rashin amira ba ,

Dasu akai hidima amma sama sama ran biki akadaura aure Lady da Hussein safiiya da Hassan salma da rayyan,
Wurin kai amarya basu faseelat amma faseelat ta musu nasiha sosai ta basu shawara,

Yan kai amare suka hau jirgi se Egypt amma su tarba ta musamman da dare sukai dinner wanshekare aka medosu,


da dare angwaye duk Sun meda amaren cikakkun mata, lalle Allah yayi gaskiya da yace shi me afuwa ne kuma me rahma da jinkai domin ya ma lady rahmar dukda laifinta na baya ,ta gyara kanta sosai mijinta saurayine kuma Allah yarufa mata asiri don be gane komi ba shi yana kukan dadi ita kuma tana kukan murna domin yadda taji yanata kokarin shigarta se da kyar yashiga ko zafin bata ji dukda akwai, shiko da yagama yayita rarrashinta,

Itama safiyya tasha wuya wurin mijinta don begane kofar ba da tsiya yaganota ya afka,

Salma ko tagane kurenta tasha kuka sosai don mijinta yanada mata memakon tasamu saukin abun se yazama tafi dukkansu shan wuya domin rudewa yayi ,yayi zaton da waccan yar hannun yakeyi seda taga likita, wanshekare kuma duk suka tafi Las Vegas honey moon,


Gidan tsit yake kowace na bangarenta basuko san fitowa waje kayan wasan amira na daga musu hankali domin sukan tuno ta yanzu sati biyu da rasuwarta kuma har yau fahad be kara kusantar matansa ba don shaawar ma bayaji dukkansu rarrashin juna sukeyi,

Ba abunda ke hada faseelat da Aisha se a dining su gaisa shikenan, dayake tariga bata sakarmata fuska wannan yasa faseelat bata damuba,

da rana ne misalin karfe 2 suna zaune suna lunch
Sede duk cokalar abincin suke don zaman dining ma yana kara tuno musu amira,

Kowa plate din gabansa kadai yake kallo,

Aisha duk tarasa natsuwarta gani takeyi kamar bazata kara haihuwa ba abincin ma bata kwantar da hankali wurin yinshi wani lokaci gishiri yadan hau wani lokaci tayishi ba gishiri ba magi itace tayi girki yau,


fahad ma yanzu mugun son yara yake yasan da ba amira kadai bace agidan dabasu damu haka ba,


faseelat da so daya tasa abincin bakinta taji zuciyarta na tashi don miyar kifi ce wani

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login