Showing 303001 words to 306000 words out of 388641 words
tace, “Dama kana gidan amma ko tarba babu Anuwar?”. Kafin yace wani abu Umm-Anum tace, “Fushi yake dan ya shirya ƙaryan komawa ƙasanku na ganosa na hana”. Kallonsa mukai da ga ni har Ummu, ya wani ɓata fuska da narketa a shagwaɓe. Dariya nayi kaɗan ina ɗauke kaina. Ummu tace, “Kaga manta dasu Anuwar kaji, lokacin da zamu rama yana zuwa ai”. “Yauwa Ummuna” ya faɗa yana zama kusa da ita ya gaisheta. Nima gaishesa nayi. Cikin hikima yaketa tambayata ina mijina? Da tsokana nikuma nake bashi amsar yana can mun baro. Da nace haka sai ya ɓata fuska ya ɗauke kai. Har raina sai nakejin tausayinsa, dan bamusan mi ALLAH ya ɓoyeba a al'amarin nasu da har suke masifar ƙulafucin juna irin haka.
Bayan sallar zuhur Abbun su Anum ɗin ya dawo gidan, sai da ya zauna suka gaisa da Ummu sannan yake sanar da Umm-Anum gasu takawa nan a falon baƙi a shirya musu abinci akai. Da yake dama tasan da zuwan nasu saita hau shirya komai yanda ya dace, sai dai kallo guda zakai mata ka fahimci kamar a rikice take. Daga ƙarshe ma saita zauna tana mai dafe kanta. Aunty Mahfuzah ce tai azamar ƙarisawa gareta ta dafa ta, “Umm-Anum lafiya kuwa?. Kanta ta nuna mata da hannu alamar yana mata ciwo, Ummu da Aunty Mahfuzah suka kalli juna dansu su Ummu sun sanar dasu komai dama. Addu'a Aunty Mahfuzah tai mata sannan taɗanji ya sassauta mata, amma data miƙe sai tace jiri take gani.
Anuwar ya fita salla bai dawoba, Anum da Bilkisu kuma suna ɗaki suma tunda suka idar da sallar basu fitoba, dan haka basu san wainar da ake toyawaba su.
A falon baƙi Takawa ne zaune da mijin Aunty Mahfuzah abokinsa, sai Jawaad dake zaune a wani irin yanayi mai wahalar fassara, idanunsa sun kaɗa sunyi jazur, ya jingina da kujera saboda jin yanda ƙirjinsa ke wani irin mahaukacin bugu, ga jinin jikinsa sai tsitstsinkewa yake. Takawa ya kafesa da idanu na wasu ƴan mintuna cike da nazari kafin ya sauke gajeren numfashi yana maida dubansa ga Abu-Siddiq, shima ɗin dai kallon Jay yakeyi tun ɗazun cike da nazari, dan tun haɗuwarsu da Abunsu Anuwar gaba ɗaya yanayin Jawaad ɗin ya sake canjawa, shi kansa Abbun su Anuwar ɗin rikicewa yay jikinsa ya hau rawa saboda ganin tsananin kamar Jawaad da Anuwar ɗin, farine kawai Anuwar ya ɗara Jawaad. Duk da daman Takawa yay masa bayanin komai tunma kan suzo ƙasar hakan bai hanashi shiga gigita da ruɗani ba, sai dai baice komaiba bayan gaisuwar daya zauna sukayi, shine ya fita ya sanarma Umm-Anum ɗin da zuwansu shi kuma ya sake dawowa.
Sam ya kasa haƙurin daina kallon Jawaad dake kwance cikin kujera idanunsa rufe, ba barci yakeba amma sam tunaninsa da hankalinsa basa tare da duniyar mutane, da za'a tambayesa wanene shi a wannan lokacin, bazai iya bada amsar komaiba. A wannan yanayin Aunty Mahfuzah da ma'aikatan gidan suka shigo suka shirya abinci gasu takawa.
Duk yanda sukaso Jawaad yaci abinci sam ya kasa, daga ƙarshema yace musu kansa ke masa ciwo, kuma yana ganin jiri, wannan magana ta sake rikita Abbun su Anuwar, dan a irin halin daya baro Umm-Anum kenan itama a cikin gida. Shine yayma Jawaad addu'a, kafin ya sakashi dole cin abincin, gurasa ɗaya yaci da ƙyar ya tsame hannunsa. basu sake tilasta masaba dan sun fahimci bayama cikin hayyacinsa kamar.............✍
Ku lallaɓa da wannan, yau na tashi banajin garin dai-dai nima😩
Gaskiya a rage sakama Jay ido da yawafa ƴan Wattpad😂, dan kunfi kowa iya gulmar Jay na kula, su ƴan Telegram ƴan blue House ne, Yah Qaseem ɗinmu sukafi sama ido da Aunty Hudah🙄😣.
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI...
GUDU DA WAIWAYE....
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za'a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[1/14, 5:27 PM] HASNA✍🏻: Typing📲
ƘWAI cikin ƘAYA!!
Bilyn Abdull ce🤙🏻
BOOK TWO
Page 49
..............Kamar yanda Umm-Anum ta saba duk sanda takawa yazo Saudia ya kanzo har gidan su gaisa, domin dai a halin da take ciki su kaɗai takema kallon ƴan uwa, su kaɗai ta sani a yanzu sai mijinta sai ƴaƴan guda biyu, ta mance ita wacece? Ƴar wacece? Daga ina take? Daga ina ta fito?. Wani lokaci hikimar UBANGIJI kan sakata kawo wannan tunanin a zuciyarta, musamman ida tunaninta ya karaɗe ko ina a cikin duniya ta ga babu wanda ta sani sai ƴan Masarautar gagara badau, sai mijinta da danginsa dake anan, hakan kan ɗaure mata kai, sai dai duk yanda taso ta furta da baki kota tambaya bata iyawa. Idan hakan ta kasance takan zauna tasha kukanta ta share hawayenta.
Yauma kamar yanda ta saba ɗin haka ta ƙimtsa ta fito cikin shirin zuwa gaida takawa, idan da Ummu yazo sukanje tare, idan kuma da amaryarsa ne tare itama suke zuwa, sai idan shi kaɗaine yazo sai taje tare da Anum su gaida shi ko Aunty Mahfuzah idan ta shigo. Yau kam sai suka ɗunguma gaba ɗaya, ita, Anum, Ummu, Bilkisu, sai Anuwar daya shigo gidan babu jimawa shima, dan tunda ya fita salla sai yanzu yake dawowa saboda baisan da Takawa sukazo ba balle yay tunanin harda Jawaad.
Sallama sukai a ƙofar ɗakin aka amsa musu da ga ciki, tare da basu izinin shiga, jikin Umm-Anum sai tsuma yake tanata dai ƙoƙarin dannewa da karanto addu'a a zuciyarta. Anum da Bilkisu ne suka fara shiga, sai Ummu sai Umm-Anum, sai Anuwar a ƙarshe. Jay na kwance a kujera idanunsa a lumshe tamkar mai barci, sai dai shigowarsu falon ya saka ƙirjinsa wani irin mahaukacin bugu irin wanda tunda yake a rayuwarsa zai iya rantsuwa bai taɓa jiba, ya buɗe idanunsa a hankali zuciyarsa na wani irin masifaffen tsitstsinkewa. Akan Bilkisu da Anum da suka zauna gefen Abbun su Anuwar ya fara saukewa, ya maida kan Ummu da itama ta zauna a kujerar da takawa yake zaune, sai Anuwar dake tsaye tamkar gunki idanu a ware yana kallon Jawaad, da alama dai yayi sumar tsayene na bazata. Ya maida kallonsa ga dattijuwar mace data juya masa baya suna gaisawa da takawa, tana sanye da baƙar abaya ta naɗe kanta irin naɗin larabawa. Jiyay gaba ɗaya jinin jikinsa na wani bada zuuuu!! Zuuuu! Zuuuu, bazai iya daurewa har saita juyo garesa ba, a matuƙar ɗokance yake da son ganinta duk da cike yake da fargaba da tsoron kar hasashensu ya zama kuskurene kuma ba itaɗin bace ba. Ya miƙe a hankali ƙafafunsa na harharɗewa, yayinda bugun zuciyarsa da fitar numfarfashisa ke fita a matuƙar guje. Miƙewarsa tai daidai da miƙewar Umm-Anum itama fuskarta ɗauke da murmushi sun gama gaisawa da takawa tanason komawa kusa da mijinta ta zauna sai a ɗora firar, dauriya kawai take itama tana danne halin da take ciki. Lokaci ɗaya sukai tsaiii! Suna kallon juna, kallo mai wahalar fassara ga ma'abocin yinsa da wanda ke kallo, kallo mai saka razani da firgici da ban mamaki, kallo mai ɗarsa tausayi ga duk wanda idanunsa zai iya sauka a kansu shima.
Ƙafafun Jawaad sun kasa ɗaukar gangar jikinsa, Mahaifiya ta wuce gaban wasa, jini ba ƙarya bane musamman irin na uwa da ƴaƴa, ko shekara dubu yay baigantaba saiya gane, shekarun data barsa bazai yuwu ya iya manta fuskartaba musamman da ya zam yana kallonta a hoto a koda yaushe, manyanta kawai da ƙiba da haske ta ƙara na alamun girma da jin daɗi. Ƙasa ya zube bisa gwiwoyinsa jikinsa na rawa, kansa na wani irin Masifaffen sara masa tamkar zai tsage gida biyu, cikin rawar harshe da kwararowar hawaye bisa kumatunsa yace, “Ummuna!”.
Umm-Anum dake tsaye cikin mawuyacin hali da ruɗanin zuciya da gangar jiki idanunta kafe akan Jawaad ko ƙyaftawa batayi ta ɗaga hannu da ƙyar tana mai nuna shi da yatsanta manuniya jikinta na wani irin rawa, mai kama da Anuwar ɗinta! Wanene shi? Da ga ina yake? Ya akai kamaninsa da Anuwar ɗinta?! Mutum ɗaya tasan duk duniya yana kiranta da wannan sunan, sai dai wanene? A ina yake? A yaushe ne kuma?. Bakinta rawa yake amma ta gaza furta komai, sai tai luuuu baya zata faɗi.
Wani irin wawan miƙewa Jawaad yayi ya tarota jikinsa, dai dai da zaburowar Anuwar shima yana ƙoƙarin tarota, sai kawai hanunsu ya haɗe waje guda suka tallafota a tare......
Zumbur suma ƴan falon duk suka miƙe tsaye, banda Takawa kawai da ya dake abinsa duk da shima jikin nasa duk yay saƙwat. Da ga can Anum ta ƙwala kiran sunanta cikin kukan da takeyi tun farkon durƙushewar Jay a gaban Umm-Anum. Bilkisu ma hawayen takeyi.
Abin tausayi da tashin hankali daga Jawaad har Anuwar kuka suke suna faman girgiza Umm-Anum da kiranta, Jay na faɗin, “Ummuna! Ummuna Please, Ummuna ki buɗe idanunki ki ganni, nine Jay-p ɗinku ke da Abbah, karkice ba hakaba dan ALLAH, dan ALLAH Ummuna zuciyata zata buga ki tashi ki ganni kicemin da gaske kece ba gizo idanuna keyiba, ba mafarkin dana sabayi bane, ba tunain danake dulmiyawa bane, ki tabbatarmin a zahirance kece tare dani Ummuna, kitashi kiga Jay-p ɗinku yazam Jay-p ɗin gaskiya, Dan ALLAH Ummuna karkice baki ganeniba karkice baki sanibaaaaa”. Yaja (a) ɗin ƙarshe da fashe da wanu irin kuka maiban tausayi da tsuma zuciya yana mai kife fuskarsa saman tata.
Anuwar shima kukan yake yana faɗin, “Umm-Anum ki tashi da ALLAH, ki tashi ki faɗamin shiɗin ɗan uwanmu ne da gaske, wlhy inajin ƙaunarsa mai zafi a raina irin wadda ban taɓama wani mahaluki irinta ba, jinake tamkar zan iya rasa numfashina sabida shi, Umm-Anum dan ALLAH kice shiɗin jininmu ne Ummu”.
Duk wanda yace baiyi hawayeba a parlorn nan ƙarya yake, hatta da Takawa saida yasa handkherchief ya tsane hawaye, Abbun su Anuwar ya saka gefen mayafinsa da larabawa ke sakawa saman kai ya share nasa hawayen, kafin ya taka a hankali shima ya durƙusa a gabansu ya ɗago kawunansu ya rungume a ƙirjinsa yana shafa kansu, fuskarsa ɗauke daɗan murmushi ga ƙwalla da suka sake cika idanunsa, a hankali yakai bakinsa saman kan Jawaad ya sumbata, kafin ya maida akan Anuwar shima ya sumbata. Cikin harshen turanci ya shiga lallashinsu da kalamai masu sanyi. Suna cikin haka Ambulance ɗin da Abbu-Siddiq ya kira asibiti ta iso, mata ma'aikatan asibitine suka shigo su huɗu, da taimakon su Jawaad da har yanzu jikinsa ke a sanyaye suka kamata aka ɗaura a gadon gungura mara lafiya, ma'aikatan asibitinne suka fita da ita, Jawaad da Anuwar suka take musu baya suma. Bilkisu da Anum ma miƙewa sukai da sauri sukabi bayansu. Duk miƙewa suma sukai domin binsu, amma sai Abbun Anuwar yace Abu-Siddiq ya maida su Takawa masauki su huta. Noƙewa Ummu tayi akan ita dai zatabi bayansu itama. Takawa baice komaiba suka fito gaba ɗaya, su Jawaad harsun wuce, su Bilkisu ma basu iskesu ba suna tsaye suna jiran fitowarsu Ummu, Ummu, Aunty Mahfuzah, Bilkisu, Anum suka shiga mota ɗaya suka bisu. Abbunsu Anuwar kuma dasu Takawa suma suka tafi a mota guda.
Da taimakon su Jay da suma suke a motar Ambulance ɗin aka fidda Umm-Anum zuwa cikin asibitin, abinka da inda kasan darajar ɗan adam, dan danan likitoci sukai mata caa da taimakon gaggawa, yayinda Anuwar da Jawaad ke tsaye aƙofar ɗakin da aka shiga da ita kowanne cike da tsantsar damuwa, kaɗan-kaɗan saisu ɗago su kalli juna, sai dai kowanne ya kasa magana ma ɗan uwansa ko sau ɗaya, dan harsunansu sun musu nauyi, burinsu kawai suga farfaɗowar rabin numfashinsu masoyiyar zuciyarsu mahaifiyarsu abin alfaharin kowa da tinƙaho.
A wannan halin su Bilkisu suka ƙariso suka iskesu, da ga ita har Anum idanunsu sunyi luhu-luhu saboda kuka, Ummu duk tana riƙe da hannayensu. Idanu kawai Jay ya zuba musu amma bai iya cewa komaiba, sai Anuwar ne ya bama Ummu amsar tambayar da tayi akan ina Umm-Anum ɗin. Isowar su Abbu suma ya saka aka basu wajen zama, domin su Abbu sun kasance zuri'a sananniya mai daraja a ƙasar saudia musamman cikin birnin makka, nagartattun malamaine hafizan Al-Qur'ani mai girma, sunada manyan makarantu na addini da cibiyoyin magunan musulunci da suke badawa da sunansu ya zagaye lungu da saƙon birnin na makka da kewaye da saudia ke alfahari dasu a ɓangarori da dama na ƙasar.
Anuwar da Jawaad dai sun kasa zama, sai da Abbu ya kamosu duk ya zaunar tare da zama tsakkiyarsu. Jawaad shi kaɗai yasan irin matsanancin ciwon da kansa ke masa, amma ya daure ya jure, sai dai ta jijiyar kansa data mimmiƙene kawai zaka iya fahimtar yana cikin mawuyacin hali. Hannu Abbu ya ɗaura akan Jawaad ɗin daya kwantar da bayansa jikin kujera ya lumshe idanunsa, hakan ya saka shi buɗe idanun da suke jajur ainun, addu'a ya fara karantowa yana tofa masa a kan nasa, Jay ya maida idanunsa ya lumshe jirin da yakeji na ƙara ƙarfi a cikin idanunsa. Luuuu ya kwanto jikin Abbu alamar shima dai koya suman kokuma wani abun dai daban, saurin ɗagosa Abbu yay yana girgizashi, amma ina numfashinsa yay ɗaf daga ƙirjinsa. Saurin miƙewa Anuwar yay shima jiki na rawa, hakanne ya jawo hankalin sauran suka fahimci abinda ke faruwa. Bilkisu ta cusa kanta cikin cinyoyinta ta sake fashewa da kuka mai tsuma rai. Hakama Anum ƙanƙame Ummu tai ta fashe da kuka tana faɗin, “Ummu shima yayi kamar na Umm-Anum”. Rungumesu Ummu tayi a jikinta daga ita har Bilkisu itama tana ƙoƙarin haɗiye hawayenta, ‘wannan wane irin tashin hankaline haka?’. Ta faɗa a ranta cike da tausayin wannan ahali.
A take shima Jawaad aka ɗaukesa zuwa ɗakin kusa da Umm-Anum aka shiga bashi taimakon gaggawa domin ceto numfashinsa.
★★★★★★
Saida sukai zaman awanni biyu cikin kuka da tashin hankaki sannan suka sami labarin farfaɗowar su, atake duk murmushi ya suɓuce musu, Bily ta saka gyalenta itama tana share hawaye kamar yanda Anum keta faman yi. Ba'a basu damar shiga ba dan duk ance suna buƙatar samun hutu musamman ma Umm-Anum da jikinta ya manyanta.
Da wannan albishir ɗin suka sami ƙwarin gwiwar tafiya yin sallar la'asar da lokacinta yayi, kowa ya shiga miƙama UBANGIJIN al'arshi kukansa dan shine masanin duk wani sirri dake a binne tare da rahama ga bayin da aka zalunta kuma suka jurema jarabawar rayuwa batare da nuna ƙosawarsu ba. Sosai yin sallar ya ɗan basu ƙwarin gwiwa suka dawo asibitin, Abbu ya roƙa takawa akan suje su huta haka nan tunda ance sun farfaɗo ai. Daƙyar Ummu ta yarda, Bilkisu kam ƙasa tai da kai tana hawaye alamar batason tafiya. Takawa yay murmushi da yima Ummu alamar a barta anan ɗin da ido.
Hakan kuwa akayi, bayan sun shiga sun duba su Jawaad da Umm-Anum suka tafi akabar Bilkisu da Anum da Anuwar anan, sai Aunty Mahfuzah, takawa kuma da Ummu da Amintacciyar baiwar Ummu da Abu-Siddiq suka tafi, sai Anuwar da Abbu suma suna nan. Suma dai bayan wucewar su takawan duk sai suka shiga suka dubasu suka sake fitowa suka zauna zaman jiran farkawarsu da musu addu'oi.
Kasa haƙuri Abbun su Anuwar yayi yaɗan farama Bilkisu wasu tambayiyi game da Jawaad da ita kanta, danshi tabbas yana kallon wasu abubuwan na Bilkisu masu mugun kamanceceniya da Umm-Anum, tafiya, murmushi dama abubuwa da dama tun a wancan zuwan nata, hakan sai yasa kansa ya ƙara kullewa ya shiga tambayarta ko auren zuminci akai musu ita da Jawaad?. kanta a ƙasa ta bashi amsa da “A'a”. Ya tisa (a'a) ɗin nan ta bilkisu a ransa yafi sau dubu, dan shidai gaskiya bai yardaba akwai abinda ita Bilkisun bata saniba maybe, musamman yanda yake mata tambayoyin da amsoshin da take bashi. Anuwar dai da Anum da Aunty Mahfuzah na binsu da kallone da saurarensu.
A haka lokacin sallar magriba yayi itama suka tashi suka gabarta, sun dawone suka iske Jawaad ya tashi, Abbu ne yace Bilkisu kawai ce zata shiga, badan Anuwar da Anum sunso ba suka haƙura.
Tunda na shigo ɗakin idanuna a kansa suke, shiko nasa a lumshe tamkar mai barci har yanzun, yana kwance ne, amma yanzu an ɗago gadon sama ta wajen kanshi yanda kwanciyar ta bada style kamar yana a zaune. Na cigaba da takawa a hankali na ƙarasa garesa, Zama nayi dai-dai saitin fuskarsa tare da ranƙwafawa na sumbaci goshinsa, hawayen da suka cikamin ido suka ziraro suka ɗiga akan fuskarsa. Buɗe idanun yayi a hankali tare da riƙo hannuna cikin nashi, kallon cikin ido mukaima juna, wasu hawayen suka sake silalo mani na tausayinsa, abinda ban taɓa gani daga garesaba sai yau, (kuka) Boss ne gwanin dauriya da shanye abu yay kuka, kai mahaifiya dabance a rayuwar kowanne ɗan adam, mahaifiya tafi gaban wasa, mahaifiya mutum mafi daraja sama ga komai ga ƴaƴa. Na ayyana a raina ina matsawa jikinsa na kwantar da kaina a ƙirjinsa ina fashewa da kuka, dan nima haka kawai sai naji ƙaunar tawa mahaifiyar da kewarta, Innata gatana, innata abar alfaharina da tinƙahona harma da taƙama a dukkan daƙiƙa ta rayuwata.
Jawaad da shima wasu zafafan hawayen da babu zato suka silalo masa ya ɗaura duka hannayensa saman bayanta ya rungumeta a jikinsa. Sunkai tsahon lokaci Bilkisu na kukan da shashsheka ta kasa ɓoyesa, Jawaad na kukan zuci da hawaye masu zafi da raɗaɗi. Buɗe ƙofar da akaine ya saka Bilkisu saurin ɗagowa dan ta zata su Abbu ne, shima babu musu ya saketa ta miƙe yana share hawayensa, itama nata ta shiga sharewa da bakin mayafin jallabiyar. Nurse ɗin daya shigo ya nema afuwarsu, dan ya jima yana sallama da knocking babu amsa, hakanne ya sakashi shigowa direct, dan tun daga can waje ta cctv'n da suke amfani