Showing 102001 words to 105000 words out of 388641 words

Chapter 35 - KWAI CIKIN KAYA

10 Sep 2025

20648

da tafiyar Jawaad Qaseem ne ya sanar mata komai.
A duk sanda akai mata zancensa danne zuciyarta kawai takeyi, amma kewarsa da ɗunbin begensa kullum sake mamaye zuciyarta yakeyi, batason ya kalleta matsayin mafi arha a mata shiyyasa tai dauriyar riƙe ajinta gam tunda ta ƙetaro kasarsu tai kunnen uwar shegu dashi, sai dai a kullum hotonsa shine abin kallonta, hakama duk wata kafar yaɗa zumunta datasan yanada accaunt a wajen tana bibiyarsa da sunan da ba nataba.
Ta kasa kula kowane saurayi, ta dai yarda kuyi abota amma ba soyayyaba, to kuma dama can dai gaskiya Shahudah bata iskanci, koshi Jay shaidane akan cikakkiyar budurwa ya sameta, dama can iskancinta baya wuce shan minti, amma bata yarda tarayya da waniba, takance wannan mallakin Jay ne tunma a wancan lokacin, to a yanzunma dai da harma yanzu take ɗauka da aurensa kanta tana taka tsantsan, sai dai fa iya shege da duk wani dandali na taruwar wayayyu tana a wajen babu abinda ya dameta, tunda bawai muhimmancin auren ta saniba balle ƙa'idojinsa, a ganinta duk abinda takeyi ƴancinta ya bata damar yin hakan, balle ta dawo inda babu ruwan wani da wani.
A gurguje⛹♀😏
_________________________
BILKEESU
_________________________
Rayuwa tai nisa, sakanni sun zama mintuna, mintuna sun koma awoyi, awoyi sun zama yini, yini ya rikiɗa dare, kafin wani dogon nazari daren ya haɗa kwanakin da suka bada satittikan da suka dunƙulle wattani, sai gamu da shekara ɗai-ɗai har huɗu cif a makaranta, yanzu haka jarabawa biyu kacal ta rage mana kammala jarabawar ƙarshen zangon karatunmu na.
Abubuwa da dama sun faru, wasu a iya tunawa, wasu ko zuciya ta manta saboda hidimomin yau da kullum, mun kwankwaɗi madarar ilimi wadda muke addu'a da fatan ta zamewa rayuwarmu dana ƙasa damu alkairi.
Zakusha mamaki idan kukaji a cikin baƙin al'amuran da suka zoma rayuwata ciki harda soyayyar Yah Qaseem datai ƙarfi a tsakaninmu,
Hoo duniya makarantar makaho, kai mai idonma ba ɗage masa ƙafa takeba, wai ni Bilkisu ƴar baƙa mummuna ƴan ƙwalisar samari masu ji da ƙyawu da ƴan canji a aljihu irinsu yaya Qaseem keso? To lallai dai abin da mamaki, sannan yana buƙatar alamar tambaya, shin sone na gaskiya? Kokuwa sone na sha'awa?.
A wannan kaftawar da zamu farane kawai kowa zai iya fahimtar hakan, danni dai har yanzu baiji amsa tayinsa daga bakina ba.
Dan duk wani salon rayuwa da iya zama da jama'a a yanzu Alhmdllh na san gwargwadon ilimin da UBANGIJI ya bani.
Maza da yawa surar da ALLAH ya bani ke ɗibarsu zuwa gareni, ba wai ƙyawuba, duk da ƙoƙarin killace jikina da nake ban tsiraba a wajen mayu irinsu Yah Qaseem................✍🏻
ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏🏻[8/11, 5:00 PM] Marsy😘: https://youtu.be/gUGygQ5y5pg

*_MANHA HAUSA NOVELS_*


https://youtu.be/xUINNiDdeH0

*_AL-ƘALAMI TV_*


*_Typing📲_*



*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*


*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*


*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_



*_____________________________________*
*_BOOK ONE_*
_Shafi na talatin da ɗaya_
*_____________________________________*


............A ɓangaren Shahudah kam taci alwashin sai Jawaad yazo ya nemeta har inda take, dan a nata hasashen gwala rayuwarsa take a haka.
Tasan ɗunbin son da yake mata dolene ya jigatu da rashinta, shekaru biyar ta ɗiba masa cif, sai ya koma ƙaramin mahaukaci a kanta sannan ta bayyana a garesa.
A shirmenta ko ganin ta cinye shekaru biyu bai nemetaba baisa taji a ranta akwai matsalaba, a'a a ganinta kawai ya rasa hanyar da zai iya ganintane, tunda Mummy ta tabbatar mata Jawaad baisan inda takeba har yanzu.
Ita kuma duk motsin Jay Mummy tana sanar mata komai harma Aamilah da Salman, wani lokacinma harda Qaseem, ko dangane da tafiyar Jawaad Qaseem ne ya sanar mata komai.
A duk sanda akai mata zancensa danne zuciyarta kawai takeyi, amma kewarsa da ɗunbin begensa kullum sake mamaye zuciyarta yakeyi, batason ya kalleta matsayin mafi arha a mata shiyyasa tai dauriyar riƙe ajinta gam tunda ta ƙetaro kasarsu tai kunnen uwar shegu dashi, sai dai a kullum hotonsa shine abin kallonta, hakama duk wata kafar yaɗa zumunta datasan yanada accaunt a wajen tana bibiyarsa da sunan da ba nataba.
Ta kasa kula kowane saurayi, ta dai yarda kuyi abota amma ba soyayyaba, to kuma dama can dai gaskiya Shahudah bata iskanci, koshi Jay shaidane akan cikakkiyar budurwa ya sameta, dama can iskancinta baya wuce shan minti, amma bata yarda tarayya da waniba, takance wannan mallakin Jay ne tunma a wancan lokacin, to a yanzunma dai da harma yanzu take ɗauka da aurensa kanta tana taka tsantsan, sai dai fa iya shege da duk wani dandali na taruwar wayayyu tana a wajen babu abinda ya dameta, tunda bawai muhimmancin auren ta saniba balle ƙa'idojinsa, a ganinta duk abinda takeyi ƴancinta ya bata damar yin hakan, balle ta dawo inda babu ruwan wani da wani.




A gurguje⛹‍♀😏


_________________________
BILKEESU
_________________________

Rayuwa tai nisa, sakanni sun zama mintuna, mintuna sun koma awoyi, awoyi sun zama yini, yini ya rikiɗa dare, kafin wani dogon nazari daren ya haɗa kwanakin da suka bada satittikan da suka dunƙulle wattani, sai gamu da shekara ɗai-ɗai har huɗu cif a makaranta, yanzu haka jarabawa biyu kacal ta rage mana kammala jarabawar ƙarshen zangon karatunmu na.
Abubuwa da dama sun faru, wasu a iya tunawa, wasu ko zuciya ta manta saboda hidimomin yau da kullum, mun kwankwaɗi madarar ilimi wadda muke addu'a da fatan ta zamewa rayuwarmu dana ƙasa damu alkairi.
Zakusha mamaki idan kukaji a cikin baƙin al'amuran da suka zoma rayuwata ciki harda soyayyar Yah Qaseem datai ƙarfi a tsakaninmu,
Hoo duniya makarantar makaho, kai mai idonma ba ɗage masa ƙafa takeba, wai ni Bilkisu ƴar baƙa mummuna ƴan ƙwalisar samari masu ji da ƙyawu da ƴan canji a aljihu irinsu yaya Qaseem keso? To lallai dai abin da mamaki, sannan yana buƙatar alamar tambaya, shin sone na gaskiya? Kokuwa sone na sha'awa?.
A wannan kaftawar da zamu farane kawai kowa zai iya fahimtar hakan, danni dai har yanzu baiji amsa tayinsa daga bakina ba.
Dan duk wani salon rayuwa da iya zama da jama'a a yanzu Alhmdllh na san gwargwadon ilimin da UBANGIJI ya bani.
Maza da yawa surar da ALLAH ya bani ke ɗibarsu zuwa gareni, ba wai ƙyawuba, duk da ƙoƙarin killace jikina da nake ban tsiraba a wajen mayu irinsu Yah Qaseem.


_________________________


Uzirin gaggawa ya sakani dawowa gida a weekend ɗinnan domin ɗaukar abinda na manta, babu wanda yasan da zuwana, dan motar haya na shigo.
Tun isowa gidan namu gabana ya faɗi, dan kuwa da motar ƴan sanda naci karo, na tura ƙaramar ƙofar gate na shi da sassarfa, dama dagani sai handbag ɗita.
Zan shigo ƴan sandan zasu fita, dan haka suka bani hanya saboda na riga na kawo jiki, koda na shigo sukuma sai suka fice, na bisu da kallo kafin na maido kan Amina dake ta faman kuka ga mamanta itama tanayi.
Sai Dad da Mummy dake tsaye sunata faman faɗa akan maza su Amina su fice musu da ga gida, inba hakaba zasu bama ƴan sandan da suka fice dama su tafi dasu.
Gaba ɗaya ban fahimci yaren kowa a cikinsuba, na sake maida dubana ga Yah Salman dake kan mota zaune yana wani munafukin murmushi, Aamilah na daga gefensa tana latse-laste a waya.
Nai saurin ƙoƙarin riƙo hannun Amina da suke ƙoƙarin fita, amma sai ta fisge a fusace harda bigemin hannu ta fice.
‘Lallai akwai matsala’ na ambata a zuciyata ina binsu da kallo har suka fice......
Kiran da Dad ke minne ya katse tunanina, na sauke ajiyar zuciya ina nufarsu hankalina duk a tashe da tunanin mi akaima Aminar?.
Ina isowa gabansu Dad abinda ya fara faɗamin shine, “Ƴata rabu da waɗancan masherantan mutanen kinji, dan ba mutanen arziƙi bane masheranta, duk ƙyautatawar da mukaima rayuwarsu sai suka ƙare da nemanmu da sharri”.
Duk da bansan kan al'amarinba sai naji kalamun dad basumin daɗi ba, dan haka nai murmushin yaƙe kawai ina faɗin, “Wani abune ya faru Dad?”.
Kafin ya bani amsa Mummy ta katsesa da sauri, “Daga shigowarki Bilkisu, ki shiga ki huta mana koma minene zakiji daga baya”.
Kaina kawai na iya ɗaga mata, suka shiga ni kuma nabi bayansu.
Dad dake zama a kujera yay min tambayar lafiya nida nake ƙoƙarin zana jarabawa ta ƙarshe nazo gida?.
Sai da na durƙusa a gabansu na gaishesu sannan nai masa bayanin abinda ya kawoni.
Ganin ya gamsu da maganatane ya sakani miƙewa na nufi ɗakina, dan duk tunanina a dagule yake da abinda na gani, sam zuciyata ta kasa yarda su Amina ne basu da gaskiya. Akwai dai abinda tabbas shi Dad bai saniba an ɓoye masa.
Har nai wanka na fito domin cin abinci wannan lamari na sukata, babu kowa a falon na wuce kicin, a can ɗinma ban samu kowa ba, to dama wa zan gani? Amina ce dai da kuku kuma ga ayanda na iske gidan.
Babu komai a kicin ɗin, amma da alamun dai anyi abinci, fitowa nai dan na san yana Dani, ilai kuwa a can na hangosa, tunani baisa hankalina ya fara kaiwa canba.
Ɗiba nai na koma ɗaki kawai, duk da uwar yunwar da nakeji sai kuma nama kasa cin abincin, dan laumata ɗaya jal na ajiye cokalin ina sake karanto damuwar dake tattare da Amina.
Amina ta taka rawar gani a rayuwata ta gidannan, dan ta soni a lokacin da kowa ya tsaneni, ta ƙaunaceni a lokacin da kowa ke ƙyanƙyami na, to ni tayaya yanzu zan sami nutsuwa a halin da take ciki?.
Bani da ikon fita gidan a yanzu, amma nayi alwashin zuwa anjima ko a sacene sai naje gidansu Amina.
Da ƙyar naci rabin abincin dana ɗebo, na zuba tagumi ina cigaba da saƙawa da kwancewa.


Bayan sallar isha'i na fahimci gidan yayi shiru, a hankali na leƙo falon, babu kowa a ciki, yau ko tv ma ba'a kunnaba, cikin sanɗa na nufi kicin, ta ƙofar baya na fita a hanzarce zuwa harabar gidan, nanma sai da na wawwaiga na tabbatar babu mai kallona sannan na nufi gate.
Baba mai gadi ya taso yana tambayata ina zanje, saurin masa alamar yay shiru nayi, murya ƙasa-ƙasa nace, “Gidansu Amina zanje baba, dan ALLAH ko wani ya tambaya karkace na fita, duk da nasanma da wuya asan bana nan”.
Kansa ya ɗagamin, ni kuma na fice da sauri...............✍🏻





*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻
[8/11, 5:00 PM] Marsy😘: https://youtu.be/gUGygQ5y5pg

*_MANHA HAUSA NOVELS_*


https://youtu.be/xUINNiDdeH0

*_AL-ƘALAMI TV_*


*_Typing📲_*



*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*


*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*


*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_



*_____________________________________*
*_BOOK ONE_*
_Shafi na talatin da uku_
*__________________________________*


................Duk wanda ya sanni zaisan inada damuwa tun dawowata gida, a kwana na uku da dawowata mukai ɗaya a cikin jarabawar data rage mana, ranar ƴan uwana suka nunamin ɓacin rai sosai akan abinda nake ɓoye musu, dan badan taimakon Nazifa dake kusa daniba da babu abinda zan rubuta sai shirme a takardata.
Ba komai zai jawo hakanba kuma sai halin da nake ciki na ɗunbin tausayin Amina da fargabar tawa rayuwar idan na koma zaman gidan yanzu.
Ganin sunyi fushi na basu haƙuri, sannan na ɗora da faɗin,
“Ƴan uwana kuyi haƙuri, zan aikata muku babban laifi na canja burinmu nason zamowa ƴan jarida, yanzu na gane ba wan nan bane abinda nake buƙata, martaba da kare sauran ta ƴan uwana itace abar buƙatata”.
“Wace magana kikeyi haka bily, mu bamu fahimceki ba” Rebecca ce mai maganar.
Zama nai da ƙyau na shiga zayyano musu abinda na gani a gida, wanda inaji a raina cewa na manto abinda na koma ɗaukane dan na iske wannan iftila'in, dan ƙila daban ganiba babu mai bani gamsashen labari.
A take naga duk sunyi murmushi mai ciwo, Nazifa ta miƙe tabar wajen tana kuka.
Da kallo mamaki na bita, dan bansan manufar kukan nata ba, “Nazifa!”
Na ambaci sunanta, hakanne ya sakata tsayawa cak sai dai bata juyo garemu ba.
Miƙewa nai tsaye na taka zuwa gareta na dafa kafaɗarta, “Nazifa miya sakaki kuka a wannan maganar?”.
Sai da taja wasu sakanni kafin ta juyo gareni, sosai take hawaye wasu nabin wasu, ta dafa tawa kafaɗar tana sake fashewa da kuka mai ciwo. Ban hanata ba, hakama sauran ƴan uwana babu wanda yay mata magana.
Rebecca dake bayanmu tsaye tace, “Bilkisu, kukan da Nazifa keyi kukane namu mu duka, duk da dai ke mun ɓoye miki dalilin kukan tuni, sai dai maganarki ta yanzu ta sosa mana inda ke mana ƙaiƙayi harma da tuna mana abinda ya shuɗe”.
Kallonta nayi sannan na maida gasu Ummie, kukan da Ummie take har yamafi na Nazifa, dan numfashinta har sama yake tamkar zai shiɗe ta fusgosa da ƙyar.
Hankalina ya sake tashi mtuƙa fiyema da da, nace, “Ƴan uwana ku buɗemin abinda kuka rufemin ko zuciyata zata samu sukuni dan ALLAH”.
Shiru sukai kusan na mintuna biyu, kafin Zuhrah tazo ta kama hannuna dana Nazifa zuwa inda muka taso.
Duk zama mukai har Rebecca.
Zuhrah tace, “Bilkisu kinsan dai mun taɓa baki labarin ƴar uwarmu data rasu sanadin sikila ko?”.
Cikin ɗaga kai nace, “Tabbas anyi haka”.
Zuhrah ta share hawayenta yana riƙo hannuna, “Bilkisu tabbas ƴar uwarmu nada sikila amma sanadin baƙin cikin fyaɗe ta rasu”.
Cikin matuƙar razana na zabura, har taune harshe nake wajen ambaton “Fyaɗe fa kikace Zuhrah?”.
“Tabbas fyaɗe Bilkisu, ni Nazifa nida ita akaima Fyaɗe a cikin gidanmu sunje mini weekend ita da Ummie, amma abin mamaki da al'ajab sai aka rasa wanda ya aikata mana wannan ta'asa, dan kuwa kamar yanda kika bamu labarin nan sai da aka bugar da Amina muma haka akai mana wlhy. Babu kalar binciken da ba'ayiba amma har yanzu babu wani bayani, kwannamu uku a asibiti ƴar uwarmu ta rasu saboda yanayin jikinta bayason wahala, da kuma dai ƙarar kwana. Bilkisu wlhy ba ɗiyan talakawa kawai akema fyaɗe ba, sannan ba mata kawai ba, harma da maza, ƙanin Rebecca an masa fyaɗe ta hanyar luwaɗi shima kuma ya rasu”.
Kasa magana nai saboda kuka, jikina sai tsuma yake, hakan yasa na miƙe a fusace ina nunasu, “Amma duk da wannan abubuwan da suka faru da rayuwarku kuka ɓata lokacinku wajen tsara burinku akan business kawai? Rayuwa a hannun ALLAH take, amma baka yanke ƙauna daga rahamarsa, shiyyasa a kullum muke zama masu buri, kuyi haƙuri duk da ni ɗiyan talakawace, ban tashi gidanmu naga kuɗiba hakan bazaisa na cigaba da zama a cikin burinku ba gaskiya”.
Dukansu kallona sukai, bance musu komaiba naja takarda da biro nai rubutu na tura a tsakkiyarsu.
Dukansu kallon takardar sukayi, kafin su maido kallonsu gareni.
“Wannan daga yau ni Bilkisu Adam makaho shine burina, ban isa canjawa gaba ɗaya ba, amma ko alwashin dana ɗauka akan Amina da Nazifa da ƙanin Rebecca da ƴar uwarmu data rasu suka cika naci riba”.
Rebecca ta kamo hannuna ta ɗora nata, itama tace, “Daya yau nima Rebecca ina tare fake Bilkisu”.
“Nima ina tare daku” cewar Nazifa tana aza hannunta akan na Rebecca, Ummie da Zuhrah ma duk suka ɗora tare da bamu goyon baya.

Wannan shine sanadin burinmu, a haka muka ƙarasa jarabawar data rage tare da bikin karramawa da aka gudanar.
Ranar Dad da kansa yazo ɗaukata shi da Yah Qaseem.
Nayi farin cikin ganinsu, haka suma sun tayani farin ciki.
A gidanma nayi mamakin tarbar dana samu daga Mummy.


*_RAYUWA SABON TAKU!_*

.............Dole na kira yanayina na yanzu da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login