Showing 153001 words to 156000 words out of 388641 words

Chapter 52 - KWAI CIKIN KAYA

10 Sep 2025

20647

rufamin asiri, kaji tausayin maraicina ka barni da mutuncina, gidanku itace mafakata ta ƙarshe da nake alfahari da ita, idan shaiɗan ya lulluɓe maka ido ka tuzguɗemin ita bansan ina zan dosaba, haramunne a addininmu, sannan cutarwace a garemu, wannan ba shi bane soyayya kamar yanda yake a tunanin yahudu da nasara, ƙoface kawai ta saɓon UBANGIJI, kuma tushen fasiƙanci, daga kama hannuna da kakeson yi a koda yaushe matsala zata fara, tun inaji banason hakan wataran sai kaga shaiɗan ya ƙawatamin nafara jin daɗi, a tafi matakin sumbata, makulin buɗema shaiɗan ƙofa kenan da komai na baɗala zai iya wanzuwa tsakanin namiji da mace, duk takatsantsan ɗinmu wataran kafin mu farga sai akai ga aikata zina, ‘Wa'iyazubillah’. Yah Qaseem namiji da mace duk hukunci ɗaya garesu wajen ALLAH idan suka aikata zina, amma a zahirance ta rayuwar duniya mace itace ke fara ƙasƙanta a idanun al'umma makusantanta dama na nesa da ita, domin itace ke ɗaukar ciki, itace wasu almomi ke fara bayyana a gareta, farko rasa mutunci, ƙasƙanta mutincin gidansu dama ahalinta, tabon da zaita bibiyar rayuwarta har ƙarshen zuri'arta, ita ake fara aibantawa kafin abokin tarayyarta, itace ke rasa mijin aure, ita akafi nunama ƙyama, itace keda rauni. Abin tausayi da tashin hankali ƴa mace na fuskantar waɗanan matsalolin koda ace fyaɗe akai mata. Yah Qaseem indai sona kace da gaske dan ALLAH ka daina min waɗanan abubuwan, wlhy banaso, basa burgeni......”
Qaseem yaja wani bahagon numfashi saboda tausayi da bily ta bashi, harga ALLAH sonta yake da gaskiya ba yaudaraba, ALLAH ne ya jarabcesa da sonta batare daya shiryama hakanba, yanda take kuka sai ya kumajin tausayinta sosai a ransa, murya a sanyaye yace, “Na fahimceki Bilkisu, insha ALLAH kuma zan kiyaye, idan kin amince zanma Dad magana akan aurenmu”.
Sauran hawayena na share tare da kallonsa, ganin ni yake kallo sai na ɗaga masa kai alamar na amince. Ya saki wani murmushi najin daɗi yana sake tsatstsareni da idanunsa farare tas, a hankali ya furta, “Inasonki da yawa Bilkisu na, gara dai nayi na mallakeki kusa dani na huta da wa'azinnan”. Murmushi nayi ina ɓoye fuskata, shima yay ƙaramar dariya yana mai tada motar muka cigaba da tafiya. Hira yaytamin har muka ƙarisa station ɗinmu duk da ba amsa nake bashiba sai dai eh ko a'a da murmushi kuma.
BAYAN KWANA UKU.
A kwanaki ukunnan Boss bai sake shiga harkataba, harna ɗauka gargaɗin Yah Qaseem ne yasa ya barni, tunda ina ganin dai yana sama dashi. Shima a ɓangaren Yah Qaseem na samu sauƙin yawan kai hannunsa jikina da yakeyi, sai dai wasu take-taken Yah Salman a gidan yanzu suke cazamin kai, ya masifar samin idanu, kowane motsina sai ya tanka magana a kai, Aunty Shahudah cema naga dai tayi sanyi, bansan mike damuntaba, amma saina lura kamar bata cikin nutsuwarta.
Ban sake cema baba maigadi komaiba game da zancen Amina saboda saka idon Yah Salman a kaina, amma inata wasu shirye-shirye a gefe nabin matakan da zan gano bakin zaren, dan abinda baba mai gadi yayi ranar yana nan tsaye cak a zuciyata bai gogeba. Da wannan tunaninma yau na fita wajen aiki.
Tunda muka dawo sallar zuhur muna a office ɗinmu da boss ya dunƙulemu, kowa yana hidimar aikin daya dace, yayinda Ni da Ummie muna aikine muna ƴar hirarmu data shafemu, hakama sauran kowa nayi da abokin maganarsa, hakanne yasa ɗakin ɗaukar kananun surutai sama-sama. A bazata naji office ɗin ya ɗauki shiru tamkar ruwa ya cinye kowa, batare dana ɗagoba nai ƙaramar dariya ina faɗin, “Ummie mutuwace ta gitta a office ɗin namu ne?”.
Shiru naji Ummie batace komaiba, hakanne ya sani ɗagowa a tunanina batajini ba.
‘kutumelecy’...............✍

Assalamu alaikum.
Inason naɗanyi bayani da nake fatan a fahimceni, akan maganar aikinsu Jawaad, inason mai karatu ya fahimci wani abu anan, aikin da muka dangantasu dashi bawai yana nufin ainahin abinda ya shafi ma'aikatan zahirin bane, bamusan komai da ya shafesu ba, tayaya zamuce komai nasu sai ya shigo labarinmu, domin ba'akan hakan muke rubutu ba, da yawanmu ma idan za'a tambayemu bazamuce munsan waɗanan ma'aikatanba kai tsaye, domin su aikinsu bawai a bayyane yakeba kamar ƴan-sanda da dai sauransu da suke cikinmu ba, aikine na wanda kai kanka idan ba wani daliliba bazaka taɓa ka gansu suna yawo gama gari ba ko wani aikinsu a bayyane, so na danganta waɗanan jaruman littafine da hakan saboda mutunci da himma da ƙwazo na irin jami'anmu da mu kanmu bamu saniba, matasanmu kuma su zama masu himma dason bama ƙasarsu gudunmawa da zuciya ɗaya a kowace ƙasa suke ba lallai sai tamu ba, tom inaso ku kalli wannan kawai a matsayin labari bawai lallai abinda yake a zahiri ba, ko yake lallai mu bibiya, matsayinsu, misukeyi? Mizasuyi? Duk iyakarsa labari irin na marubuci {ƙirƙira}, bani da hurumin shiga abinda bani da lasisi a kai, domin bamma sani ba, waɗanan jami'an littafine bawai na zahiri dake aiki a ƙasarmu ba, idan kun kula sam babu wani sunan gari dake nunama a ina suke, ko a wane waje suke, musa a ranmu kawai ƙirƙirarren labari muke karantawa, ilimantarwa, nishaɗi, da faɗakarwa, ba akan kowaba, domin ba'akan kowan mukeyi ba, duk abinda zamu iya ganin yaci karo da waccan rayuwar ta zahiri to kawai fiƙira ce irin ta marubuci bawai dan inada ilimin sani ba ko bibiya balle bincika, ina fatan duk wanda ke bibiyar wannan littafi a ko'ina yake zai kasance maiyin ƙyaƙyƙyawan fahimta akan inda muka dosa, sannan abinda kake ganin na karkace ko shiga hurumin da banawaba ina fatan zakuyi gaggawar dawo dani hanya, ALLAH yasa mu dace, ALLAH kuma ya ƙarama dukkan jami'an tsaronmu lafiya da ƙwazo da nagarta a duk duniyar da suke.🙏🏻

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻[11/30/2020, 12:59 PM] HASNA✍🏻: Bilyn Abdull 📚:
Page 10

    ............‘Kutumelecy’ na faɗa a cikin raina ina saurin janye idanuna dana ware a kansa da tsaida taunar cingam ɗin da nakeyi lokaci ɗaya, ganin yanda ya tsatstsareni da muggan idanunsa.  Zungurin ƙafata dana ɗora saman tebir ɗina Ummie tayi.
     Kallonsa na sake sata sai naga shima idanunsa yanzu akan ƙafar tawa suke harma da sauran ƴan uwana, da sauri na sauke ƙafar ƙasa na nutsu kamar yanda kowa yayi. Bai tankama kowaba ya ida takowa tsakiyyar ɗakin yana binmu da kallo daki-daki, har tsawon mintuna biyu muna a haka tamkar ɗan doka da ƴan gidan kallon ƙwallo ko ɓarayin agwagi, nidai sai faman jan addu'a nake saboda jin yanda zuciyata ke bugawa da sauri-sauri tamkar ko yaushe idan na samu kusanci da shi.
     Ganin bazai tankaba sai muka shiga gaisheshi ɗaya bayan ɗaya, hannu kawai yake ɗaga mana amma bai sake kallon kowaba baikuma amsa mana da bakiba. Yaja kujerar dake gaban tebir ɗin Uchie ya zauna, bamusan mi suke tattaunawaba har kusan tsawon mintuna sha biyar kafin ya miƙe ya fice. Yana fita muka shiga sauke a jiyar zuciya, yayinda wasu suka shiga gulmarsa musamman ma matan cikinmu, nidai sabon cingam na ɓare na jefa a baki na cigaba da sabgar gabana.

________________________________

               A gidan su Jawaad kam taron meeting Mom ta tara da ƴan uwanta, sunɗau tsahon lokaci suna tattaunawa akan Jawaad da maganarsa da Shahudah, duk da dai da farko Uncle Nasir yaso bijirewa, a cewarsa suma sunada ƴaƴan da zasu bama Jawaad ɗin ai ya aura. Shahudah ta kiya musu hankalin da bai kamata su sake sakata a sabgarsu ba.
       Kuka mama Atika ta fasa musu, tare da ɗakko musu maganar data saka suka nutsu waje guda.
        “Munsan Sabira tayi laifi da tafka kuskure a baya, amma kuyi haƙuri munada tabbacin zuwa yanzu ta magantu za'a samu gyara musamman idan mukai dubi da yanda take son yaron, amma ni na yarda da shawarar Nasiru, mu fara ma Jawaad maganar auren wata a cikin yaran gidannan, idan ya nuna rashin amincewa saimu tirsasashi ya maida Sabira ɗakinta, dan baikamata mu zubamasa ido yana yawo sakaka babu aureba, shekararsu kusan biyar kenan da rabuwa, amma yaƙi aure, inba neman matan banza yaron nan yakeba yaza'ai mutum mai lafiya kamarsa ace yanaƙin aure?, su waɗancan dangin uwar tasa sakarkaru da yake tsoronsa sukeji sun gaza masa magana kuma, tomu bai kamata mu saka masa idoba, dan kuwa mune duniya zata zaga basuba, amma yaya kuka gani? Danni dai shawarace na kawo matsayina na uwa a gareku, da Badiyya nada isashiyar lafiyama tare zamuyi muku, yanzu saiku zauna ku yanke shawara a tsakaninku” ta ƙare maganar da tashi ta fice daga falon.
     Duk binta sukai da kallo harta fita, Uncle Sulaimam ya sauke numfashi yana faɗin, “Nidai ƴan uwana na yarda da maganar mama, dan nidai zaman Jawaad bayamin daɗi a haka, da Abdul-aziz nada rai bazai zubama gudan jininsa ido kamar yanda mu muka kasa riƙe amana mukaiba, duk da bana zargin Jawaad da neman mata, dan mu shaidane akan tarbiyya da sanin yakamata na yaron nan”. Duk shiru sukai basu ce komaiba, wasu na hararsa ta gefen ido wasu na ƙunƙuni a cikin rai, dan suma sunsan ƴaƴan Mama Badiyya sam nasa tare da burinsu a gidan, su kaɗaine masu ƙaunar Jawaad dan ALLAH badan dukiyarsaba. Jin shirun yayi yawane ya saka Mom yin magana. “Nima na aminta da maganar mama, kuma ina goyon bayan ɗan uwana Sulaiman”.
         Daga maganar Mom sai kowama ya fara faɗar abinda ke ransa, daga ƙarshe dai suka ajiye shawara akan zama da Jawaad ɗin idan ya dawo aiki da wuri yau, kokuwa weekend idan ALLAH ya kaimu.

_________________________________

             A makare yau Jawaad ya tashi a wajen aiki, saboda fitar da sukai shi da Hafiz zuwa wani waje da yamma, basu dawoba sai bayan magriba, akwai abinda zai ɗauka a office shiyyasa suka dawo, amma da daga inda sukaje gida zai wuce. Bayan ya tattaro abinda zai ɗakko a office ɗin nasa sai yaga lokacin sallar isha'i ma yayi, dan haka suka tsaya sukai a station ɗin.
           Koda suka fito yunwar dake cin cikinsa yasa yace su tsaya wajen wani haɗaɗɗen gashin kaji, gimba ya amsa masa da girmamawa.  gimba ne ya fita domin

amsowa, kasancewar wajen ba baƙonsu bane akaima gimba tarba ta sanayya, kamar yanda Jawaad ya bashi umarni takeaway biyu akayi sai fura da yogurt masu sanyi aka saka ɗaɗɗaya a ciki, gimba ya bada kuɗin sannan ya dawo mota suka ƙarasa gida.
         Ganin da sauran mutane da keta shigi da fici a sassan gidan sai ya bashi mamaki, a ganinsa dai tunda anyi addu'an bakwai mikuma mutane keyi tunda ba taron biki bane. Saurin kauda abin yay a zuciyarsa dan a ganinsa hakan ba huruminsa bane, yaso shiga sashen Uncle Usman ya gaida Mama Zainab matarsa kamar yanda yakeyi kullum tunda akai rasuwar, sai dai a matuƙar gajiye yake, ga masifaffiyar yunwa dake cin hanjinsa.
         Tare suka shiga sashensa da gimba dake ɗauke da tarkacensa, bayan ya ajiye masa a falon ƙasa yay masa sallama ya fita, shima bai iya ƙarasawa bedroom ba ya yada zango a falo, sai da ya huta na wasu mintuna sannan ya miƙe ya haura sama, duk da yana buƙatar fara cin abinci haka ya daure, dan shi mutumne mai yawan cin abinci, idan bai samu bane dai yakanyi haƙuri kawai. Ɗakin barcinsa ya ƙarasa ya watsa ruwa, kusan ƙarfe tara ya fito tsaf dashi sai baza ƙamshi yake. Ya shiga kicin ya ɗakko kofi da filet, a falon ƙasa ya zauna ya kunna tv domin kallon labarai, yana kallonne yana cin abinci, lokaci-lokaci kuma yakan amsa waya idan an kirashi, ya daɗe zaune a falon har aka kammala labaran kafin ya miƙe yay ciki dan yana matuƙar buƙatar hutawa.

SHAHUDAH

      Saboda son haɗuwa da Jawaad yasa yau taƙi binsu Mom gida, a cewarta nan zata kwana, Mom bata hanata ba, suka tafi ita da Aamilah kawai saboda Salman ne yazo ɗaukarsu dama ba driver ba.
     Wajen ƙarfe goma ta kammala kwalliyarta, tai shiga cikin kayan barci masu taushi da ƙyau, dan sunyi masifar fidda mata surarta, sai ƙamshi take kamar jikar gidan mai turare, a ranta ta ƙudiri aniyar maido hankalin mijinta kanta yau, dan ta gaji da wannan wasan ɓuyan da sukeyi, ta kuma shirya karɓar cikin da yake buƙata. (Karku manta Shahudah batasan Jawaad ya saketa ba fa😥🤦🏻, ɓoye mata shine kuskuren dasu mom suka tafka).
     Hijjab ɗin mama Atika da ya kai mata har ƙasa ta ɗauka ta saka, babu kowa a sashen na mama Atika, itama tayi barci ma tun ɗazun, kai tsaye Shahudah ta nufi sashen Jawaad tanata zuba murmushi, dan ita kaɗai tasan abubuwan data shirya masa, yau ɗinan basai gobeba sai ta zautar da gayen nan, ta sake sakin tattausan murmushi lokacin data murɗa ƙofar taji ta buɗe. Jawaad ya manta shaf bai rufeba ya haye sama, sai da ta gama ƙarema falon kallo, komai tsaf tamkar ba namiji ke zauneba, tasan Jawaad yanada tsafta, sam bayason ƙazanta, duk jin kan nan nasa baya ƙyashin tashi yay shara yay morping wa sashen,, ya samu wannan horonne a zamansa da kakarsa Mama maryam, hatta da girki Jawaad ya iya, kawai rashin isashen lokacin kai ne ke hanashi yi. batasan miyasa bayason masu hidimaba. Ta sake sakin murmushi kafin ta fara taka steps ɗin a hankali tana wani yauƙi saikace tarwaɗa, a falo ta cire hijjab ɗin ta jefa saman kujera, ta kuma gyara rigarta da gashinta sannan ta nufi hanyar ɗakinsa.

       Jawaad kam a gajiye yake matuƙa. hakan yasa yana shigowa bayan yay brush da alwala yay adduar barci ya kwanta, bai wani jima da kwanciyaba barci yay gaba dashi, fitilar gefen gado ce kawai a kunne, itama ta ɓangare ɗaya, hakan yasa ɗakin yay dim babu haske sosai, bai kumayi dunɗum ba. Shahudah data murɗa ƙofar ta shigo a hankali ta sauke ajiyar zuciya tana mai shaƙar ƙamshin da ɗakin keyi, komai na Bb'n ta daban yake dana kowa, bata ganin fuskarsa, dan ya juya ma ƙofar bayane, sannan ya lulluɓa da bargo saboda uban AC'n daya ƙure ɗakin da shi, ‘ko tsoron murama bayayi’ ta faɗa tana ɗaukar remote ɗin acn ta rage ƙarfinsa.
       Jawaad da baisanma hidimar da akeba barcinsa yake hankali kwance da mafarki mai daɗi, hakan yasa yaketa faman sauke numfashi a hankali. Ya sauke ajiyar zuciya lokacin da Shahudah ta hawo gadon a hankali ta kwanto bayansa bayan ta ɗaga bargon ta shiga, itama ajiyar zuciyar ta sauke ƙwallan kewarsa na taruwar mata a idanu, jitake tamkar ta haɗiyesa ta hutama kawai. Cikin salon data shirya masa a wa

nnan dare ta fara yawo da hannunta a jikinsa, Jawaad dai bai motsaba, amma da alama jikinsa na karɓar saƙwannin Shahudah kamar yanda tai fata. Mafarkin da Jay keyi da saɓanin Shahudah yay dai-dai da abinda take masa a zahiri, hakanne yasa ta samu haɗin kan gangar jikinsa har takai ya gyara kwanciyarsa yana sake rungumeta, hakan yayma Huda daɗi kuwa, ta ƙara ƙaimi kan abinda takeyi, kamar wasa saiga tafiya tayi nisa a tsakaninsu, dan tuni ya fara maida mata murtanin sumbatarsa da takeyi.
          Yanda take sauke numfashi ne da sauri-sauri akan fuskarsa ya sakashi farkawa, dan kuwa tabbas wannan al'amarin ya wuce a mafarki kawai, a matuƙar razane ya hankaɗeta daga jikinsa yana ambaton “Innalillahi wa-inna ilaihirraji'un. Wace ƴar iska ce haka ta shigomin ɗaki?”. Yay maganar yana ƙoƙarin kunna fitilar ɗakin.
       Shahudah daya jefar gefe duk da taji zafi tai ƙoƙarin tashi zaune tana sauke numfashi a gwame, hasken daya gauraye ɗakin ne ya basu damar ganin juna. Kansa ya dafe yana ƙara ambaton “Innalillahi....” Shahudah ta matso jikinsa tana neman kwantawa a kafaɗarsa ya sake tureta a fusace, “Wai ke wane irin dabbanci ne wannan? shin baki da hankaline Hudah?”. Tabbas maganganunsa sun mata zafi, amma saita daure cikin dakewa da tsiwarta tace, “Dan nazo wajen mijina zakacemin banda hankali?, to ka ɗauka ni da kai duk mun zama mahaukatan”.
      Karon farko Jawaad ya waro idanu waje, yace, “Miji!?, Hudah rashin ilimin addinin naki harya ƙara faɗaɗa haka? Kinga bani da lokacin wannan haukar tashi ki fitarmin daga sashe kafin na saɓa miki kamanni, kuma wlhy wannan yazama na farko na ƙarshe da zaki sake shigomin nan”.
       Kuka Shahudah ta saki, ta nuna kanta tana faɗin, “Yanzu nan tsanar da kaimin bb har ta kai haka? To wlhy babu inda zanje, dan inada haƙƙi a kanka ai, duk ma abinda zakayi sai kaitayi, amma ka sani niba ƴar iska bace, amma wlhy da tuni naje na nema wani namijin a waj.......”
      Mari ya kai mata tai saurin kaucewa, cikin daka tsawa yace, “Tashi ki fita a ɗakinan kafin na raba kanki da wuyanki wawuya kawai!!”. Saurin sauka tay a gadon, dan yanda ya harzuƙo ɗinan zai iya maketa, batasan ma bashi da wannan ƙarfinba a yanzu, dan ta sakashi a kwale-kwale. Da ƙyar Jawaad ya iya sakkowa a gadon saboda tashin hankalin da Shahudah ta sakashi, duk ƙoƙarin kame kansa da dauriyar da yakeyi yau ta kwanto masa liƙi, ya murzama ƙofar key ya dawo saman gadon jiki babu ƙwari. Gaba ɗaya kansa ya toshe, yama gaza yin tunani akan Shahudah.
       Duk yanda Jawaad yaso yayi barci a wannan daren ya kasa, gashi maganin da yake sha ya barsa a office saboda ya ƙare ya sayosu jiya, sai kuma ya manta bai ɗakkoba, ya watsama jikinsa ruwan sanyi yafi sau shidda kafin asuba, sosai mararsa ke masa masifar ciwo, ko sallar asuba bai fitaba a ɗaki yayi, sai bayan ya idarne barci ɓarawo ya sacesa, shima a matuƙar wahale yayisa.
       
         Shahudah kuwa da kuka rurus tabar sashen zuwa sashen mama Atika, a falo ta zube tacigaba da kukanta har barci ɓarawo ya saceta.
  

_______________________________

                       Yau ma har muka fito Office banga kowa a cikin ƴan gidanba, cikin nishaɗi muke ƴar firarmu da Yah Qaseem har muka iso, saida na rakashi har office da tarkacensa sannan na fito nima zuwa namu.
       Ummie bata isoba, hakan yasa na


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login