Showing 138001 words to 141000 words out of 388641 words
da wannan lamari, ya rasama ta yaya zai fassara al'amarin, maganganunsa da Sir Ahmad kawai ke masa kai kawo a cikin zuciya, tare da zuwansa office ɗin B.G, ya rasa ina zai kama ma shikam? Yana buƙatar ganin su Jabeer tare dashi yanzunan, sai dai tabbas bazai yuwu a station ɗinanba, dan yanzu dukkanin motsinsa abin bibiyane.
Ƙaramar wayarsa ya ɗauka ya turama Hafiz saƙo, kafin ya tura wayar aljihu bayan ya kasheta gaba ɗaya ma, wasu takardu ya ɗiba ya fito a hanzarce, hana kowa ya bisa yayi, ya shiga mota shi da Gimba kawai suka fice daga station ɗin.
Danne-danne yaketa famanyi a lap-top, hakan ya saka gimba kallonsa ta cikin madubi, “Boss! Ina zamuje?”.
Ba tare da ya ɗagoba yace, “A.Y Street”.
Cikin girmamawa Gimba ya amsa, tare da juya kan motar suka nufi hanyar gidan Jawaad ɗin dake anguwar A.Y street.
Sunyi wajen mintuna talatin da zuwa kafin su Aliyu su iso. A falo suka iskeshi har yanzu yanata faman danne-danne a lap-top, a haka ya amsa sallamarsu ko ɗagowa baiyiba ma. Sai da suka zauna da kusan mintuna biyu sannan ya ɗago ya kallesu, kallo ɗaya yayma Rose ya ɗauke kansa, hakan yay bala'in sosa ranta, dan akwai kwallin data shafa, an kuma tabbatar mata idan suka haɗa ido da shi zai haukace mata, yabar kallon kowacce mace da gashin arziƙi sai ita, amma ɗan rainin wayon tun'a station takeson su haɗa ido da shi hakan ya gagara...
“Boss! Lafiya dai ko?”.
Aliyu da ya kafeshi da idanu ya faɗa.
Lap-top ɗin ya ajiye yana faɗin, “Da dai sauƙi Aliyu, an yanka ne ta tashi”.
“Kamar ya?;” suka faɗa cikin haɗa baki su uku, rose ce kawai da bata fahimci hausarba batace komaiba.
Cikin takaici Jawaad yace, “Ƴan uwana wasan jiya ya koma yaƙi, kukan tsuntsuwa mai zanen kanari ya zame mana abin magana”.
Sun fahimci zaurancensa, saboda wannan yana ɗaya daga cikin salonsu, musamman akan aikin da suka samu gamayya da waɗanda basa cikinsu, sai dai basu fahimci dalilin zaurancenba a yanzu, saboda duk sune a wajen babu baƙon ido.
Jabeer yace, “Jay bansan miyasa ka zaɓi ƙin buɗe zancenba, bayan kuma duk mune babu wani bare a cikinmu?”.
Jawaad yace “Nima bansan miyasa harshena ya zaɓi hakanba Jabeer, sai dai saƙon kamar tun daga zuciyane”.
“Idan na fahimta, kamar zuciyarka na ɗarsa maka akwai ɗan baya ga dangi kenan a cikin tafiyar?”. Hafiz yay maganar cikin taraddadi.
Cikin sauke nannauyan numfashi Jawaad yace, “Bani da tabbas, sai dai zuciyata na rayamin akwai idon mikiya a bayanmu”...............✍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻[11/30/2020, 1:02 PM] HASNA✍🏻: Bilyn Abdull 📚:
Typing📲
Page 5
.............Duk Kasa cewa komai sukai, sai idanu da suka zubama Jawaad tamkar wani bakonsu.
Rose da zuciyarta ke tafasa akan rashin kallonta da jawaad baiyiba ta kasa daurewa, ta dubesu baki ɗaya a wani yanayi, “Boss wai mike fauwane? tai maganar cikin harshen turanci da tsare Jawaad da idanu tana fatan ta dace yanzun.
A mamakinta yanzunma dai ƙin kallonta yayi, sai Lap-top ɗinsa ya miƙa mata kawai, ya koma ya zauna tare da ɗaukar tab.. Ɗinsa ya shiga tafa saƙo da hanzari.
Gani nai Aliyu ya ɗago ya kallesa, yay masa wani salo da ido tare da cije baki, murmushi Aliyu yayi kawai ya maida kansa, kafin ya miƙe yabar falon, hakama Jabeer da Hafiz duk ya tura musu suma, Hafiz shima tashi yay ya fita, Jabeer kuma ya koma kusa da Rose dan kawai ya ɗauke hankalinta da aikin da Jay ya bata itama.
Bayan fitar su Aliyu da kusan mintuna tara ya miƙe yabar falon ya nufi bedroom ɗinsa. Sai da ya kulle ƙofar kafin ya ciro ƙaramar wayarsa yay kiran Hafiz.
“Hafiz yaya? An dace kuwa?”.
“Ba'a daceba Boss, amma ga shawara mana?”.
“Micece shawarar taka?”.
“Mu bincika kowanne manhajar yanar gizo ko zamu dace wani ya ɗauka, kasan yanzu ba'a raba mutane da ƴan ɗauke-ɗauke a waya, maganar gano wanda ya kaima su B.G kuma ba abune mai sauƙiba ace yanzu da gaggawa, sai dai mu canja shawara ta wannan gaɓar”.
“Na fahimceka Hafiz, yanzu kayi duk yanda ya dace, amma inaji a raina koma wanene yakai wannan bayanan yana da kusanci damu Hafiz, amma banason zargin kowa”.
“Boss zargi dolene, kuma koma wanene ya daɗe a jikinmu, a sannu zamu cinmasa da ƙarfin ƙudirar UBANGIJI, dan shine ke haska mana hanya a dukkan lamuranmu”.
“Insha ALLAHU Hafiz, yanzu dai sai na jika”.
Yana yankewa yay kiran Aliyu shima, sai dai daga ɓangaren Aliyun an dace, dan ya turo masa dukkan bayanai akan Bilkisu da abinda ya shafi shigowarta hukumar tasu, da horon data samu, da ƙwazon data nuna tun a wajen horaswa, alaƙarta da Qaseem, sai dai babu wani bayani kafin zuwanta gidansu Qaseem ɗin, hakkanne yaɗan tsayama Jawaad a zuciya, har yakejin dolene ya sake binciken, dan karfa nan gaba ta zame masa ƘWAI CIKIN ƘAYA kuma kamar yanda ƴan bayan fage ke hasashe.
Daga ɓangaren Hafiz ma an dace daga baya, dan kuwa cikin amincin ALLAH ya samo bidiyon faruwar komai tun daga lokacin da Bilkisu ta kaima motar masu laifin caffa kafin zuwansu, har zuwa sanda abubuwa suka lafa.
Yaci karo da Bidiyon ne a wani chennal na youtobe, bayan ya shiga manhajar Google yay Searching, sai dai abinda ya bashi mamaki yana kammala sauke video'n akan manhajar ta youtobe wanda ya ɗora ɗin ya saukeshi daga accaunt ɗin, hakan sai yay bala'in ɗarsa mamaki a zuciyar Hafiz, harya kasa haƙuri ya kira Jawaad ya shaida masa.
Murmushi Jay yayi yana shafa kansa, “Ba abin mamaki bane Jabeer, musamman idan mukai la'akari da babu wata kafar yaɗa labarai da dama ta saki bidiyon mai tsawon hakan, sai wasu ɓangarori da dukansu iya inda muke musayar wutane kawai”.
Hafiz yace “Hankalina sam bai kaiba sai yanzu kam, koma miye yake a ɓoye ALLAH zai bayyanashi ai, mudai domin ALLAH mukema ƙasarmu aiki, duk mai yunƙurin daƙilemu kuma ALLAH zai mana maganinsa”.
“Insha ALLAHU kuwa Hafiz” Cewar Jay cike da takaici.
Kafin dare duk sun haɗa bayanan da ya kamata akan maganar, sun tura iya waɗanda Sir Ahmad ya umarcesu zuwa Office ɗin, L.G, sauran kuma sun adana a wajensu domin ya zame musu hujjar kare kai, hatta da bidiyon suma gutsira sukai suka tura, sauran kuma suka adana a wajensu.
_______★__________
SHAHUDAH
_____________________________
Tunda suka fara zuwa gidan rasuwarnan sau ɗaya taga Jawaad, harga ALLAH ita kuma dominsa take zuwa, a tunaninta idan suka haɗu zai matuƙar rikicewa da ganinta, musamman ma yanda ta sake canjawa da ƙyau mai ƙayatarwa, sosai ta gama shirya shika-shikan rama dukkan abubuwan da yay mata kafin ta yarda da buƙatarsa ta komawa gidansa.
Sai dai abin mamaki da al'aj
abi dukkan tunaninta sai bai zama gaskiyaba, dan kuwa ko a randa suka haɗu kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa, komai kuma a kan idanun Mom ya faru, dan suna a falon mama Atika ne a washe garin rasuwar ya shigo da baƙi su Sir Ahmad da sukazo gaisuwa. Sarai idanunsa sun gane masa Shahudah, amma sai ya ɗauke idanu cikin nuna halinsa na ko'in kula da abu.
Abin ya sosa mata rai sosai, amma saita danne da yaƙinin ƙila yayi hakane saboda ganin suna cikin jama'a. Koda suka koma gida sai basuyi maganar da Mom ba, saboda kowa ya dawo a gajiye wajen bacci yafi buƙata. Washe gari kuwa kwalliya tayi ta musamman dan Jawaad nanma babu sa'a, dan har dare da suka baro gidan bata sakashi a cikin idanunta ba, washe gari kuma suna isowa gate ɗin gidanne motar Jawaad ɗin ke fita da alama ya nufi office ne. Waɗanan akasin da akaita samune suka jefata a cikin damuwa har yau ta kasa daurewa.
“Mom kinga abinda Bb ya kemin kuwa? Bayan ya kamata ace ya nuna zalamarsa da kewata na shekarun da muka kwashe bama tare”.
“Huhm” Mom ta faɗa tana shafa kan Shahudah dake saman cinyarta, dan kuwa suna cikin bedroom ɗin Mama Atika ne ita da Shahudahn kawai, dan ta fahimci ɗiyar tata na tare da damuwa, yau tunda sukazo gidan ta shigo ɗakin Mama Atika bata sake fitaba, shiyyasa ta biyota, sai ta isketa cikin damuwa, hakanne ya sakata zama ta dora kan Shahudah a cinyarta tana shafawa, itakuma take bata labarin ruɗanin data shiga akan tarbar data samu daga wanda batai tsammaniba daga Bb ɗinta (Jawaad).
Mom ta haɗiye abinda ya tsaya mata a maƙoshi tana sake yamutsa sumar Shahudah'n, “Kar taurin kan yaron nan ya ɗaga hankalinki fiye da haka Shahudah, ki barsa, ni da kaina zan sauke masa wutar dake ci a kansa, bara dai a gama hidimar rasuwarnan kinji”.
Kai Shahudah ta ɗaga mata cike da shagwaɓa, har ƙwalla na sakko mata a kan kumatu tace, “Amma Mom wane mataki zaki ɗauka to?”..
Mom ta share mata hawaye tana murmushi, “Karki damu Shahudah zaki gani, kedai sonake kicigaba da kwantarmin da hankalinki, nan kusa kaɗan zaki dawo ɗakin mijinki”.
Kai Shahudah ta ɗaga mata tana murmushi da rungume mom. Murmushi mom tayi taci gaba da lallashinta cikin so da ƙauna.
Nikam nace, “Mai uwa a gindin murhu baya cin tuwonsa gaya ai Shahudah😋😜🤸🏼.
..::..★__________★..::..
BILKEESU
____★..::..★__________★..::..★____
Kwanaki huɗu cir bana zuwa Office ina gida ina jiyyar hannuna, yayinda kullum Ummie ke tare dani, ƴan gidanmu kuwa basa yini suna gidan rasuwa, barci kawai ke kawosu gidan. A kwana na biyar nai shirin komawa aiki, dan naji sauƙi sosai, a kuma daren ranarne Yah Qaseem ya dawo, nayi farin cikin dawowar tasa, dan nikaina nasan idan nace banason Yah Qaseem na yaudari kaina, a ƴan kwanakinan da bayanan sosai nayi kewarsa.
Tun a daren yake jeramin tambayoyi akan hannuna, bai samu amsa ko ɗaya ba daga gareni sai murmushi kawai.
Koda muka tashi da safe ma dai bai fasa sonjin musabbabin ciwonba, da naga ya damu sai kawai nace masa tsautsayine ya gitta mani a wajen aiki, badan ya yardaba ya ƙyaleni kawai, kasancewar yau zan koma aiki nima sai na bisa muka tafi tare kamar yanda muka saba kafin yay tafiyar.
Yah Qaseem na gama daidaita fakin motarsa wani jami'inmu na isowa wajen, ya isarmin da saƙon kira daga office ɗin B.G, maganar da jami'in yazo da itane ya sakamu kallon juna ni da yah Qaseem ɗin.
Idanuna na janye daga cikin na Yah Qaseem daya tsatstsareni da kallon tuhuma, da ƙyar na haɗiye yawun da ya tarumin a baki, dan girman office ɗin mai kiran nawa na kalla da kuma tunanin minene dalilin kiran?.
Yah Qaseem da har yanzu idanusa ke kaina da alamar tambaya na kuma kallo, ya gyara tsaiwarsa yana mai jehomin tambaya,
“Bilkisu mikike ɓoyemin ne?”.
Da sauri na girgiza masa kaina, “Wlhy Yah Qaseem bana ɓoye maka komai, nima bansan minene dalilin kiranba, amma bara naje najiyo”.
Ban jira amsarsaba na bar wajen cikin tafiyar sassarfa, zuciyata sai bugu take da sauri-sauri, dan inaji a raina wannan kiran bana lafiya bane ba, musamman
idan nai dubi da ƙaramin matsayina a hukumar.
Koda na iso sai da na jira aka bani izinin shiga sannan, wannan shine karon farko da zan shiga office ɗin a rayuwata, ba shi kaɗai bane a cikin office ɗin, jinai wani abu ya tsargamin daga saman kaina har zuwa yatsan ƙafata, na aro jarumtar dole na yafama kaina tunda bansan minene dalilin kiranba. Na miƙa musu gaisuwa cikin girmamawa kafin na zauna inda aka nunamin.
Tambayar farko da aka jefamin ta sakani ɗago idanuna na kallesu badan na shiryama hakanba, ba firgici ne ya sakani kallon nasu ba, nutsuwace ta zomin saɓanin yanda na shigo a rikice, dan kuwa a nawa tunanin inhar akan rikicin daya faru kwanaki biyar da suka wucene banga wani abin kuskure dana aikata a cikiba, zamana na gyara na fara amsa musu tambayarsu da iya gaskiyata dana sani.
Yanda Bilkisu ke amsa musu kowacce tambaya kanta tsaye babu ko ɗigon firgici ko rawar harshe ya sakasu kafeta da idanu, su kansu iya zallar gaskiyarta suke gani a saman fuskarta da furucinta.
Sun mata tambayoyi sosai, domin sake tabbatar da gaskiyar tata suka sake maimaito mata dukkan tambayoyin da sukai matan a farko, abinda ta faɗa daga farko shine ta sake maimaitawa saboda hakan shine gaskiyarta.
Kusan awa ɗaya da wasu mintuna suka sallamoni na fito, a raina sai juya wannan al'amari nakeyi...
_____________________________
JAWAAD
Zaune yake a office yanata aikin duba wasu tulin takardun dake gabansa yaji knocking ƙofa, siririn tsaki yaja dan baya buƙatar kowa a irin wannan lokacin, izinin shigowa ya bada batare daya ɗago ba balle kallon wanene?.
Ƙamshin turarenta kawai ya bashi amsar wacece, harta zauna bayan gaisheshi da tayi bai ɗago ɗinba, a haka ya amsa mata.
“Mi kike buƙata?”
Ya faɗa yana cigaba da aikinsa batare da ya ɗago ɗinba.
Duk da taji haushi sai ta danne, abinda ta gani kuma ta jiyo game da kiran Bilkisu da akayi office ɗin B.G ta zayyane masa, karon farko da ya ɗago ƙyawawan idanunsa ya sauke akan rose, sai dai baice komaiba. Duk da tsawon kwanaki kenan tana buri da buƙatar irin wannan kallon daga garesa saboda kwallin da take sakawa na jawo hankalinsa kanta sai ta kasa jurewa, dan wani irin kwarjininsane ya kuma cika mata idanu da gangar jikinta, tai azamar janye idanun nata ƙirjinta na wata irin harbawa.
Har lokacin idon Jawaad na akanta, ya cigaba da ƙare mata kallon nazari har kusan mintuna biyu kafin ya janye ya maida ga aikinsa.
Ɓoyayyen numfashi rose ta sauke, daga can ƙasan ranta kuma wani daɗi na sake mamayeta, dan kuwa dai tasan ta gama da taurin kan Jay kamar yanda bokanta ya sanar mata, inhar suka haɗa ido wannan kwallin na idonta to lallai tagama da mallakarsa har abada, ba kuma zai sake kallon kowacce maceba bayan itaɗin.
Sakanni kusan ashirin bai tankaba, bai kuma sake kallonta ba. Takaici ya sake mamaye zuciyar rose, ta buɗe baki da nufin yin magana ya miƙe tsaye, bindigarsa da wayoyinsa dake saman tebir ya ɗauka ya tura cikin aljihun Blue jeans ɗinsa, tare da ɗaukar tab... ɗinsa a hannu. “muje” ya faɗa batare da ya kalleta ba.
Binsa tai da kallon mamaki, harya buɗe ƙofar office ɗin ya fice, dole itama ta tashi da hanzari ta bisa, a ranta tana ayyana cewar ‘Yau ƴan wulaƙancinne a kansa kenan?’.
Fitowar Jay daga office yay dai-dai da fitowar Bilkisu daga sashen office's ɗin su B.G, kaɗan ya rage suyi karo, kasancewar hanyar data haɗa shataletalen office's ɗin ɗayace kafin su ƙarasa su hau lifter da zata kaisu kasa.
Da sauri naja baya ƙirjinna na motsawa, cikin dakewar harshe da banyi zaton inada shi ba nace, “Kayi haƙuri dan ALLAH , bansan ka taho bane”.
Ƙyawawan fararen idanunsa ya zubamin kansa tsaye, kusan sakan biyar tamkar zai cinyeni dasu sannan ya janye batare da yace dani komaiba. ya raɓani zai wuce, hakan yasa na matsa baya na bashi hanya, tafiya ya fara tare da faɗin, “Biyoni”..............✍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
[11/30/2020, 1:03 PM] HASNA✍🏻: Bilyn Abdull 📚:
😂🤣😂🤣😆😆😆Kunsan miyasa nake dariyarnan? Akan yanda kuke ganin kamar bily tsoron Jay takeyi, dukfa halin da take shiga shiba fahimta yakeba, hasalima kallon miskila idan kun lura yake mata, akwai masu samun kansu a irin yanayin bily akan wani ko wata, sai daga baya suke fahimtar dalilin shigarsu irin wannan halin, itama bily lokaci zai warware mata komai har muma mu sami amsa, ina muku fatan alkairi aduk inda kuke, sosai Comments naku na sakani nishadi da sani typing kodama ban niyyaba.
I love you wujiga-wujiga irin trillions ɗinnan🤸🏼🤸🏼🤸🏼 😍😘😍😘😍😘🤗.
Page 6
Ko kaɗan ban fahimci dani yakeba, musamman dana waiga naga rose data fito daga office ɗinsa a bayanna, wani kallo naga ta watsamin mai kama da takaicin tabi bayansa. Numfashi na sauke mai nauyi na shafa ƙirjinna dai-dai saitin zuciyarta dake harbawa da sauri-sauri, duk da na fahimci kallon da rose tai mani sai hakan bai dameni ba, dan bata ita nakeba. Nima fita nai daga wajen, na fito ainahin harabar station ɗin domin nufar sashenmu.
“Ɗi! Ɗi! Ɗi!!” gimba ya danna mata horn kamar yanda Jay ya bashi umarni.
Duk da naji horn ɗin hakan baisa na fahimci da ni akeba, saboda idan akai dubi da sauran jami'ai irina daketa kaikawo a harabar wajen, kowa da hidimarsa.
“K! Wace irin daƙiƙiyace da baƙya fahimtane? A haka kike tunanin zama jami'ar tsaron al'umma!!?”
Maganar Rose a tsawace ta shiga dodon kunnena ina gab da shiga lungu da zai sadani da office ɗinmu. Da sauri na juyo, idona ya sauka akan rose dake huci da jifana da kallon takaici mai nunin tsana. Duk da naji zafin kalaman datai amfani dasu a gareni sai na danne saboda tana sama da ni, a ladabce nace, “Kiyi haƙuri maa! Bansan dani kike ba”.
Tsaki rose ta buga, tare da juyawa tabarni a wajen, wani jami'i dake tsaye kusa damu ya kalleni da tausayawa, dan shi dai yarinyar tunda tazo station ɗin ɗabi'unta birgesa sukeyi, ganin ban fahimci manufar rose ba sai yay min fassara akan nabi bayanta maybe kirana akeyi.
Godiya nai masa, kafin nabi bayanta cikin nutsuwata,