Showing 60001 words to 63000 words out of 388641 words
sauke nannauyan numfashi lokacin daji ƙarfin ƙamshin turarensa gab da ita.
Ta bishi da kallo tana sake yabama kwarjininsa da cikar zati da ALLAH yay masa, tasan sarai ya ganta, amma jiba yanda ya basar abinsa.
Murmushi tayi ta miƙe tana gyara zaman wuyan rigarta.
Itama ƙyaƙyƙyawar ce ba laifi, gata doguwa masha ALLAH, yanda take tafiya cikin zafin nama tana juya dukkan illahirin jikinta zai tabbatar maka da tasamu isashen training wanda ya haɗu da ainahin halittar yanga ta ɗiya mace.
Kanta tsaye ta nufi Office ɗin Jawaad, wanda kowa yasan bata da shamaki da hakan.
Yana zaune a kujerarsa yayinda wani ke tsaye a kansa yana masa bayani akan aikin daya sakashi, har Rose ta zauna bai kalleta ba, dan idonsa nakan wasu takardu ne, itama batace komaiba ta dai zauna tana saurarensu.
Sai da wancan yakai aya sannan Jawaad ya ɗago yana kallonsa da rikitattun idanunsa da mafi yawan lokuta ke tsorata duk wani maison kawo masa wargi.
“Aikinka yayi ƙyau, sannan yana tafiya dai-dai, yanzu dai kafin dare a tababbar an kamo min Ɗan Lawan da yaransa baki ɗayansu, sannan itama kanta Kande barikin a kamomin ita tare da wiwi ɗin dasu ɗan lawan ɗin ke kai mata ajiya”.
“Okey sir” ya amsa yana mai sara masa, takardu biyu Jawaad ya miƙa masa, ya amsa yana ƙara sara masa sannan ya fice.
Lokacinne Rose ta miƙe tai salute ɗin Jawaad dake haɗe takardun daya baza bisa tebir ɗin waje ɗaya, fuskarsa ta sake tsukewa alamar babu wasa, a dake yace,
“Ban saniba yanzu ko zaki maida hankalinki ga aikinki, kokuma zaki cigaba da ɓata lokacinki akan farautar soyayya?”.
Ido Rose ta lumshe tana sakin murmushi mai sauti, ta kuma ƙamewa tare da sarama Jawaad a karo na biyu, “Boss duk zaɓin daka bani zan riƙe”.
Ɗago ido Jawaad yay ya kalleta, mikuma ya tuna sai ya saki wani guntun murmushi yana girgiza kansa. Ya jawo drawer ɗin gefensa ya fiddo bindiga ƴar ƙarama mai ƙyau, saman tebir ɗin ya ajiyeta idonsa akan Rose da itama kallonsa take ko ƙyaftawa babu, yaɗan bugi bindigar kaɗan sannan ya turata gabanta cike da salo.
Itama cikin nata salon ta ɗauka ta wurwurata tare da buɗeta. Babu komai a cikinta, hakan ya sakata sake kallon Jawaad daya maida hankalinsa ga latsa Computer ɗin saman tabir ɗin.
Ba tare daya kalleta ba yace, “Riƙe soyayya a wajenki tamkar riƙe bindiga ne babu bullet a cikinta, kinsan kuwa a garemu jami'an tsaro sam bindigar bata da amfani, domin ba bindigar bace ƙarfinmu harsashin cikinta ne, shima kuma yana amfanine idan an samu ƙwarewar iya harbi. Karki yarda a karo na biyu kiyi sakaci da damarki, Jawaad akwai mai shi”.
“Hummm” ta faɗa cikin ƙunar zuciya ba tare data iya cewa komaiba.
Shima bai sake cemata komanba tsawon lokaci kafin ya miƙe zuwa ga wata kanta, yabi tarin files ɗin cikinta da kallo, da alama dai kwanan wata yake dubawa, har idonsa yakai inda yake buƙatar zuwa sannan ya zaro wata takarda, mazauninsa ya dawo fuska a tamke ya miƙa mata, “Ki samu su Jabeer da wannan file ɗin zakuyi magana”.
“Okey Boss” ta faɗa cikin rissinawar girmamawa gareshi tana amsar file ɗin. Sai da ta sake salute nashi sannan tai ƙoƙarin ficewa.
“Ji mana” Jawaad ya faɗa yana bin Rose da kallo.
Juyowa tai ta kallesa, da ido yay mata nuni da harsasai (bullets) kusan goma daya ɗora a tebir ɗin.
Dawowa tai da baya ta kwashe tana faɗin, “Thanks you boss”.
Baice da ita komaiba, saima maida hankalinsa yay ga kallon Computer harta fice.
Aikinsa ya cigaba dayi, duk da zuciyarsa na tunanin halin da yabar Shahudah jiya da dare, tana bashi tausayi saboda wahalar da cikin yake bata, amma bayason nuna mata hakan koda a fuska ne.
Ƙarfe huɗu da wasu mintuna ya fito massalaci ya zarce office ɗin boss ɗinsa domin amsa kiransa.
Bayan nuna girmamawarsa garesa ya zauna kamar yanda ya bashi izini.
“Jay yaya dai? Na jika shiru, ko akwai matsala ne?”.
“A'a Sir, babu wata matsala aiki yana tafiya dai-dai, a yanzu haka zancen da nake maka insha ALLAHU ƙiris yama rage”.
“To Alhmdllh, banason aikinnan ya shige satinnan, dan yanzu hakama wata ta taso kuma”.
Kallonsa Jawaad yayi da son jin ko minene?.
Ya cigaba da faɗin, “Akwai wani mai kayan miya anguwar ƴan kilishi daga can ƙasan layin, majiya mai ƙarfi ta kawo mana alamar tambaya a kansa, saboda gagarumin fashin da akayi satin baya gidan Alhaji Sulaiman, Qaseem aka ɗora akan case ɗin, sai dai naga baiyi wani serious ba sam, yamafi maida hankalinsa akan wannan case ɗin da ayanzu nasan kai kama kusa kammalashi”.
“Okey Sir, yanzu mikakeson nayi ni akai?”.
“Case ɗin nakeso ya dawo hannunka Jawaad, dan waɗannan ƴan fashin bincikenmu ya nuna sunada laifuka masu yawa, amma basu barin kowacce damar da za'a gane sune, sai yanzune muka ɗan samo bakin zaren”.
“Na gane sir, to amma an buɗema case ɗin file ne?”.
“No, nabar komai a hannunka, dan banida shakku akanka sam”.
Kai Jawaad ya jinjina masa, “To amma sir kozan iya sanin wanda ya kawo sirrin?”.
“Mizai hana Jay”.
Murmushi Jawaad yayi, dan har zuciyarsa yana ƙaunar ogan nasa, ALLAH ne ya ɗaga darajarsa a hukumarsu, da kuma ƙoƙarin ogan nasa, dan ƙarancin shekarunsa basukai ace yana a kujerar da yakeba a yanzu, amma saboda manyan ayyukan da sir Ahmad Barewa ke bashi yaketa samun cigaba, har takai yanzu yana cikin jami'an da hukumar ƴan sanda ta DSS ke ji dashi saboda ƙwazonsa, da salon aikinsa, duk da kuwa ta wani ɓangaren yana zagayene da maƙiya masu burin taɗosa ƙasa a kullum.
Ya daɗe a Office ɗin suna tattaunawa kafin ya fito.
_________________________
“Ke kuwa yaushene zakiyi hankali mamana?”. Hajiya Humaira ta faɗa saboda faɗowa kanta da Shahudah tayi tana barcinta.
Baki Shahudah ta zumɓura tana faɗin, “Ni Mummy inada hankalina, wai wacece a ɗakina kuma?”.
Baki Hajiya Humaira ta taɓe tana sakkowa daga saman gadon tare da jan tsaki, “Ƴar uwarkuce”.
“Ƴar uwarmu fa mommy? Waccan baƙar yarinyar?”.
“Ita ɗinfa, ɗiyar ƙanwar dad ɗinkj Gurguwarnan da kika taɓa ƙonawa da shayi wani zuwa data taɓayi kuna primary lokacin, koda yake dawuya dai ki tuna ma”.
“Tab wlhy mummy ban mantaba, shine Dad ya jajubo mana ƴarta? Itama gurguwarce halan?”.
“Ko ɗaya, lafiyarta ras itakam, mamar tata ta rasune ai, shine ya kawota nan wai tayi karatu”.
Dariya sosai Shahudah take kwasa harda kwanciya, cikin dariya take faɗar tab ɗi, “Wannan mummunar ce za'aima gatan karatu? Irin waɗannan ko a makarantar ma mi suke ganewa yo? Amma kuma shine ama rasa inda zata zauna sai ɗakina” ta ƙare maganar da kumbura baki.
“Uhm, ke bakisan tsiyar da mukasha akan hakanba da shi, yanzu dai karkice komai ki bar mata ɗakin, ke sai a gyara miki na kusa dani, dan idan kikace wani abu akanta komai zai iya faruwa, ya ɗauki son duniya ya aza a kanta waishinan mai riƙon amana”.
Sosai lamarinnan ya zafi zuciyar Shahudah, harda ma dad ɗinsu wani maganar rashin tarbiyya, na zata Hajiya Humaira zata kwaɓeta sai naga kawai tayi dariya.
Tunda ta fita sai nima na kasa daurewa na fito falo na zauna, kusan awa ɗaya ina wajen zaune duk damuwa ya rufeni, dan bansan dalilinta na fita da gudu ba.
Aunty Aamila ta fito daga ɗakinta cikin figigiyar rigarta ta barci, wadda kaɗan ta zarta cinyarta.
Kallo ɗaya taimin taja tsaki ta wuce tebirin cin abinci.
Lamarinta baya damuna nikam, hakan yasa ko sashen da take bamma kallaba.
Ina zaune a wajan Mummy da baƙuwarmu suka fito, na gaida Mummyn cikin girmmawa kamar yanda na saba.
Amsawa tayi itama cikin nuna halin ko in kula, aunty Shahudah kam bamma isheta kalloba, hakan ya tabbatar min itama dai bazan samu karɓuwaba a gareta kenan, ban damuba, dan ba yaune karon farko dana fuskanci hakanba.
Zuwan Aunty Shahudah gidan yaɗan sake takurani, saboda wulaƙancin da takemin yafi na kowa muni, ko abu na taɓa ita bazatayi amfani da shiba, a cewarta karna gogama ɗan cikinta Munina, nakanyi murmushi aduk lokacin da naji furucinta.
Takai inhar tana falo zaune takance bazan zaunaba wlhy, banaja da ita saina tashi na fita kona koma ɗaki, kaida kazo cin arziƙi miye naka na zaƙewa?.
Kwannanta uku a gidan, duk da kuwa tun a daren da tazo naji suna tafka bala'i da mijinta a waya akan kwannan nata, dan naga tanata magana a zafafe akan dan tazo gidansu zata kwana dole saita sanar masa.
Da alama ma yanke mata waya yayi kafin takai zancen ƙarshe, dan kuwa sai faman faɗin, “Hello hello takeyi, daga ƙarshe cikin takaici tai jifa da wayar saman kujera tana masifa iya iyawarta akan ya kashe mata waya.
Itako Aunty Aamila sai zugata take akan wulaƙancin da yake mata yayi yawa, ni dai banji ƙarshen zancenba na shige ɗaki, dama daga kicin nake na zubo abinci, suko suna a tebir zasuci nasu.
________________________
Ran Jawaad ya ɓaci da ya dawo ya iske Shahudah bata gida, hakanne ya sakashi kiranta amma saita sanar masa tana gidansu, ya tambayeta da izininwa? tahau kansa da masifa, shine kawai ya yanke wayar ba tare daya gama saurarenta ba.
Sam bayason jin zafinta da yake ya cigaba da girmama cikin ransa, dan haka ya tashi yay shirin fita dukda kuwa lokacin ƙarfe tara da rabi na dare, kuma dawowarsa gidan kenan ko hutawa baiyiba.
Da kansa yaja motar dan yabama gimba damar zuwa ya kwanta ya huta.
Kansa tsaye gidan dattijuwarnan ya nufa, yanabin address ɗin da su Hafez suka bashi dalla-dalla.
A ƙofar madaidaicin gida ya tsaida motar dajin tabbacin nanne, dankuwa duk abinda aka kwatanta masa a jikin gidan ya gansa, kashe motar yay sannan ya fito cikin nuna alamun tsantsar gajiyar dake tattare dashi.
Ya kulle motar amma sai bai fitoba ya fara ƙoƙarin yin kira cikin ƙaramar wayarsa.
Bugu uku aka ɗaga, “Gani a ƙofar gida” ya faɗa idonsa akan murfin gidan.
Bansan amsar da aka bashiba daga can naga dai ya kashe wayar yana fitowa a motar, bindigarsa ya ɗauka ya tura a aljiyu sannan ya rufe murfin motar yana mai kulleta gaba ɗaya.
Dai-dai nan dattijuwa mai aiki gidan Alhaji kokino ta fito sanye da lulluɓi.
Da hannu tai masa nuni alamar su shiga, babu musu ya bita, bayan yaɗan wawwaiga bayansa yaga babu alamar kowa a wajen, dukda ma anguwar babu wani isashen haske saboda rashin wutar lantarki.
Gidan bawani babba bane ammafa yasha gyara, dan fes yake sannan kuma da gani babu ƙananun yaran da zasu ɓata.
Zama yay a farar kujerar roba dake ajiye a bangon yamma da yake ƙyautata zaton kicinne, itama ta zauna a ƙofar kicin ɗin bayan ta kawo masa tea tamkar tasan yana buƙatarsa a halin yanzu.
Godiya yay mata kuwa ya ɗauka yana sha.
“Bani da tabbas amma inaji a jikina kasan inda Alhaji yake”.
Jawaad dake ƙoƙarin kai kofin shayi bakinsa ya dakata yana kallonta, leɓensa na ƙasa ya tura cikin bakinsa yana tsotsa tare da kafeta da wani kallon nazari na seconds biyar, sai kuma yay murmushi yana ƙara damƙe kofin shayin da hannu biyu yakai bakinsa ya kurɓa.
Itama kallonsa takeyi har yanzu, sai dai bata sake cewa komaiba.
Jawaad ya cigaba da shan shayinsa kawai idonsa na kallon yanda iska ke kaɗa labulen ɗakin matar.
Yasha kusan rabin kofin shayin sannan ya ajiye yana sauke ajiyar zuciya, idonsa akanta.
“Mama shekararki nawa kina mata aiki?”.
Murmushi dattijuwa tayi tana kallonsa, “Yarona ai mai son kama fara sammako yakeyi”
“Hakane” Jawaad ya faɗa yana shafa kansa cikin murmushi.
“Miyasa take ɓoyemin kanta har yanzu?”.
“Bani da wannan amsar a zahiri da baɗini”.
Kansa ya rausayar kawai, idanunsa na sake rikiɗewa zuwa ja sosai, sai haɗiyar numfashi yake da zafi, hakan yasaka zuciyarsa gudu tare da tsitstsinkewa.......
Mama ta katse masa tunani da faɗin, “Ta bani saƙo na baka”.
Ɗago kansa yay ya kalleta, amma baice komaiba.
“Tace ka sadaukar, a cikin hakan akwai alamar tambaya? Idan kabi diddigi zaka fahimta”.
“Zanyi biyayya, sai dai zan cutu kuma”.
“Shiyyasa nazo maka da maganin hakan”.
Miƙewa Jawaad yay yana kallon agogon hannunsa, “Ina saurarenki, dan lokacina ƙararrene”.
“Karka damu nima komai inayinsa da ƙa'ida. iya ruwa fidda kai, amaryar alhajice mafitarka”.
Jawaad ya juyo yana kallon dattijuwa hannuwansa duka a cikin wandon jeans ɗinsa, “Mimene nata burin?”.
“Kisa da mallakar abinda ya tara”.
Kansa ya jinjina yana murmushi, ahankali ya furta “Abin birgewa”.
Kallonsa mama tayi tana murmushi itama.
Takowa yay ya dawo gabanta yana ɗan jingina da bango, yace, “Shine kikaji a ranar da kika faɗi kenan?”.
Cikin sauke numfashi mama tace, “Kusan haka yarona, sai dai tsoron ya gauraya ne da cin amanar aure, kuma da makusancinsa”.
Hannu ɗaya Jawaad ya ciro a aljihu yana mai shafa fuskarsa, “Idan babu kuskure a hasashena auren manufa tayi da haɗinkan ƙaninsa kenan?”.
“Hasashenka yana kan dai-dai, kamar yanda sukuma ka ruguza musu nasu a ranar da Alhaji zai dawo daga tafiya shi da ita”.
“Zan samu dukkannin bayanan?”.
“Ƙwarai kuwa, harma da wanda baka tambaya ba” tai maganar tana kunce ƙullin haɓar zaninta ta ciro wani ɗan abu ta miƙa masa.
Amsa yay yana sauke numfashi, “Nagode ƙwarai da gaske mama. A sanar mata ina buƙata matuƙa, sannan ke kuma yaushe aikinki zai ƙare a gidan?”.
“Eh to, inada zaɓi biyu ne, sannan dama ɗaya kacal, a koda yaushe za'a iya nemana a rasa”.
“Shikenan, ni zan wuce, a daren yau zan ƙulle bakin zaren”.
“Kariyar ALLAH ta tabbata a gareka tareda rahamarsa akowane lokaci”.
“Amin ya rabbi mama, nagode sosai, da safe Yazeed zai dawo gida”.
Murmushi kawai tai masa, shikuma ya fara taku cike da kasala ya fice daga gidan.
Buɗe motarsa yay ya shiga sannan ya rufe kansa, ya buɗe hannunsa dake rumtse da abinda mama ta bashi, idanu ya tsira masa yana kallo, kusan mintuna uku sannan ya ajiye yana tada motar ya fice daga anguwar.
Tuƙi yake amma hankalinsa kashi sittin baya a wajen, gefen titi ya samu jikin wani ƙyamiz yay fakin motar, ya cire babbar wayarsa a caji ya danna kiran Jabeer, bugu ɗaya ya ɗauka, sai dai yanda yaji muryarsa ya bashi tabbacin ya fara barci ne.
“Barci kake?”.
Jawaad ya faɗa a ƙasan maƙoshi.
Daga can Jabeer yace, “Wlhy kuwa barcine ya figeni a falo