Showing 177001 words to 180000 words out of 388641 words
Yay shiru yana kallonta kafin ya miƙe yabar wajen.
Cikin ƙanƙanin lokaci barcin Bilkisu yay ƙarfi sosai saboda maganin na saka barci, gashi dama bawani isashen barci ta samu a daren jiyaba, Jawaad kam ya cigaba da ayyukansa har akai kiran sallar zuhur. Tashi yay ya shiga toilet yay alwala ya fito, idanunsa suka sauka akan bily dake takure cikin kujera alamar sanyi takeji. Takawa yay a hankali wajen zamansa, rigar suit ɗinsa dake jikin kujerar a rataye ya cire ya nufeta, lulluɓa mata yay dukda bata rufe har ƙafafuba, cikin barci ta sauke ajiyar zuciya jin ɗumi ya ratsata, ya ɗan lumshe ido ya buɗe yana girgiza kai, sai kuma ya kalli agogo ya nufi hanyar fita da hanzari ganin zai makara salla.
Koda aka fito salla bai dawo office ɗinba ya amsa kiran da Sir Ahmad ke masa a office ɗinsa.
★★-:-:-:-★★★-:-:-:-:-:-★★★-:-:-:-★★
Ƙarfe biyu da wasu mintuna Dad ya isa asibiti, daga airport bai zarce ko gidaba yasa driver ya wuto dashi dan ya matsu yaga jikin mamansa, zuwa lokacin Shahudah ta farfaɗo, sai dai daka ganta kasan tanajin jiki, tayi zuru-zuru, farar fatarta tai jajur musamman fuskarta ma, Dad ya zauna a bakin gadon kusa da ita yana mai shafa gashin kanta fuskarsa a ƙwaɓe tamkar zaiyi kuka dan tausayinta. “Sannu kinji mamana, ALLAH ya baki lafiya”. Hawayene suka ziraro a kumatun Shahudah, ta kama hannun Dad ta riƙe tana magana a hankali saboda nauyin da ƙirjinta yay mata, “Dad bazan samu lafiyaba, mutuwa zanyi, tunda Bb baya buƙatata gara na mutu, Dad cayayfa mun rabu kenan har abada, ya daina sona Dad, Dad mut......” saurin ɗora hannunsa yay akan bakinta yana girgiza kansa, “Mamana bazaki mutuba, ni da kaina zan roƙesa, ko durƙusa masa ta kama zanyi Mamana danki samu farin ciki, indai ina raye a duniya babu ɗayanku da zai nema abu ya rasashi ko menene shi, danku kawai nake neman arziƙi, nai miki alƙawarin saikin koma wajen Jawaad kinji, zaku sake rayuwarku ta jin daɗi fiyema da da har ki haifamin jikoki, nidai abinda nakeso dake ki kwantarmin da hankalinki ki samu lafiya, namiki alƙawarin daga nan ko gida bazaniba office ɗin Jawaad zanje kinji”. Kanta ta ɗaga tana zubda hawaye, tace, “Kaje dan ALLAH Dad, ka faɗa masa ina sonsa, idan ya barni mutuwa zanyi, wlhy namasa alƙawarin ko a daren yau yakeso yamin ciki na haihu gobe, na kuma samin wani jibi, ko ƴaƴa ɗarine zan haifa masa indai zamu kasance tare har abada”. Wata irin kunya ce ta tsargama Doctor jin furucin Shahudah wai ko yau ai mata ciki ta haihu gobe, a ransa yace anya kuwa wannan ƴa da ubane? ‘to irin wannan manya-manyan zance haka babu risinawa’ yaɗan girgiza kansa yana mamakin yanda tarbiyyar yaran hausa fulani keta ƙara ƙuɓucewa a hannun iyayen wannan zamanin, a ganin ko uwa mace ya dace ƴa taji nauyin buɗe wani lafazin a gabanta inba doleba balle uba namiji, gashi ya kula shi Dad ɗinma ko a jikinsa, saima biyema Shahudah da yake sakeyi yana lallashinta da alƙawarta mata samun duk abinda takeso, anya kuwa wannan hanyar ɓullewace iyaye ke ginama ƴaƴansu?, a yanzu tarbiyya da al'adun kunyar da aka sanmu dashi na tangal-tangal ɗin ɓarewa a hannayenmu tamkar kwale-kwale a ƙaton kogi inaga ƴaƴan dake tasowa waɗanda suke jiran amsar tarbiyya a hannun ƴaƴanmu, anya kuwa zamu girbi abinda iyayenmu suka shuka a garemu na alkairi?......
Maganar Dad ta katsema Doctor tunaninsa, ya miƙe yana mai ranƙwafawa ya sumbaci koshin Shahudah da kumatunta, sannan ya shafa kanta cikin sigar lallashi da nuna tsagwaron soyayya da ƙaunar da yake mata yace, “Ki kwantar da hankalinki Mamana, yanzun nan zanje na isar ga saƙonki ga bb'n ki kinji, ki cire komai a ranki indai Jawaad ne kamar kin samu”. Kaita gyaɗa masa, murya a sanyaye tace, “I love you so much my Daddyna, duniyata, farincikina”. Cikin jin daɗin kalamanta Dad ya sake shafa kanta yana murmushi, yace, “I love you more mamana sanyin idaniyata, ki bani awa ɗaya kacal zan dawo miki da zance mai daɗin gaske”. Kanta ta ɗaga masa tana lumshe idanu tare da murmushi.
Dad ya matsa daga gaban gadon tare da kamo hannun Aamilah dake tsaye jikin Window tana kallonsu, “My autana zo mana”. Baki taɗan tura gaba tana ƙoƙarin ƙwace hannunta, tace, “Bayan bakama kulaniba sai mamanka”. Jawota yay jikinsa ya rungume yana murmushi, “Waneni da ƙin kula autar Mom, ayi haƙuri bazan sakeba ihuyim”. Kanta ta jinjina masa kafin ta taso daga jikinsa tana kallon fuskarsa, cikin magana a hankali dankar Shahudah taji tace, “Dad dan ALLAH kasaka mai shegen taurin kan nan yay sanyi, kaga sister tana cikin damuwa, son da take masa yayi yawa tausayi take bani”. Murmushi Dad yayi ya shafa fuskarta, “Karki damu autana, insha ALLAH komai yazo ƙarshe kinji, bara naje na dawo kafin Mom ɗinku ta dawo”. Kanta ta jinjina masa, shikuma ya saketa ya fice.
★★★★★★
A station kuwa, bayan an fito salla Rose ce ta nufi Office ɗin Jay domin kai masa wasu takardu, tai knocking dan batai tunanin bai dawoba, jin babu amsa kusan sau uku saita tura ta shiga, dan sarai tasan randa yakejin wulaƙancinsa haka yakeyi, takuma tabbatar yana kallonta ta cctv. Babu kowa a office ɗin sai ƙamshinsa, saita shiga waige-waige, hangen kamar mutum a kwance a kujera ya sata takawa ta nufi wajen, ƙirjinta yay masifar bugawa saboda yin tozali da fuskar bily dake barci tana sauke numfashi a hankali tabbacin lafiya ta samu, ga rigar boss lilliɓe a jikinta. Cikin gurɓataccen hausanta ta lailayi ashariya ta direta tana kaɗa jiki da hura hanci, kafin takai hannu da nufin finciko bilkisu ƙasa, dan ta rantse yau sai tayi maganin shegiyar baƙar yarinyarnan koda boss zaiyi markaɗenta ya murza a turmi jininta ya zama mai, tsokarta da ƙashinta da fatarta su zama tunkuzar ƙuli-ƙuli.............✍
To baza'ai tankaɗe da rairaya a gabanaba Rose nayi nana🚴🏼. Yau words dubu uku harda ɗari uku da hansin da hida nayi yanda zaku karanta har lahadi🤭🤫🤥🤐.
Barkanmu da juma'a, kar'a manta da saka bayin ALLAH a addu'ar juma'a😥🙏🏻.
Musha weekend lafiya😍😘🚴🏼
ALLAH ka gafartama iyayenmu🙏🏻😭Bilyn Abdull 📚:
Page 18
...............“Wannan shine kuskure mafi girman da zaki aikata a rayuwarki inhar hannunki ya sauka kanta!!”.
Kakkausan furuci daya karaɗe illahirin office ɗin da kunnuwan Rose kenan a lokacin da hannunta ke gab da kaiwa jikin Bilkisu da batasan Rose ɗin na kantaba ma, dan barci take cikin kwanciyar hankali da jin daɗi, harma ta manta a inda take kwance.
A firgice Rose ta janye hannunta tare da ɗago idanunta da juyowa domin tabbatar da abinda take zato, ilai kuwa shine fuska a murtuke babu alamar wasa tattare dashi balle sassauci, ya saki hannunsa dake harɗe a ƙirjinsa yana cigaba da watsa mata wani mugun kallon daketa tsitstsinke jijiyoyin jikinta da hanjin cikinta, “Mi kike shirin yi da?” ya faɗa muryarsa cike da tsanarta irin wadda bata taɓa ganiba a gareshi. Da ƙyar Rose ta haɗiye ɗan yawun data tattaro a maƙoshinta, tace, “Ni babu abinda zanyi, kawai dai na shigone na ganta anan kwance____” “Shine zaki tada ita saboda a kanki take kwance?”. Yay saurin ƙarasa mata zancen data ɗakko yana tsatstsareta da idanu. Fuska ta sake tsukewa cikin tsananin kishi tace, “Ni wlhy yarinyarnan batai minba”. Wani banzan kallo sama da ƙasa yay mata ya ɗauke kansa yana faɗin, “Saiki kasheta ai”. Kamar zatai kuka tace, “Amma boss wai miye haɗinka da ƙwailar yarinyarnan? dako mace bata gama zamaba ma”. Tsaki yayi ya juya zaibar wajen yana faɗin, “Duk abinda ke ranki shine tsakaninmu, kozaki hana?”. Tamkar rose zata fasa kuka tabishi da kallo, yana zama Su Hafiz na shigowa da sallama, hannun Aliyu ɗauke da leda mai tambarin gidan abinci, duk kallon Rose sukai ganinta tsaye tamkar gunki tana kallon Jawaad da tamkarma baisan da itaba, ga fuskarsa a matuƙar ɗaure alamun zuciyar na kusa, mai tsautsayi ya taɓa a fashe masa ita. Hafiz ne ya fara janye idanunsa daga kan Rose ya sauke akan Bilkisu dake kwance tana barcinta lulluɓe da rigar Jay, har yanzu ko motsi bataiba dukda ihun da yayma Rose ɗazun, kafin suma su Jabeer su lura da ita. Babu wanda yace komai a cikinsu, shi kuma Jay baiko ɗago yama kallesuba balle su saran zai tanka.
Aliyu ya matsa inda Jay yake ya ajiye ledar yana faɗin, “Ga abinci, kasa munje munata jiranka a wajen ashe kai kanama nan ka manta damu Boss”. Ɗago ido Jay yay fuska a yatsine ya harari Aliyu batare da yace komaiba, shi dai Aliyu zama yay abinsa bai kulashiba, Jabeer ma yaja kujerar kusa da Aliyu ya zauna yana haɗiye dariyarsa, dan ya lura Rose suman tsaye tayi a wajen kokuma ta samu gushewar hankaline na wasu mintoci.
Hafiz yay guntun tsaki yana harar Rose, “Ke kuma lafiya kika wani tsaya ƙiƙam kamar wata dogariya?”. Numfashi Rose ta kawo cikin dawowa hayyacinta, ta watsama Hafiz harara kafin ta nufi ƙofar fita batare data tankama kowa a cikinsu ba, jikinta sai rawa yakeyi. Tana fita Jabeer ya kwashe da dariya, duka Hafiz yakai masa ya duƙe, Jay ya galla masa harara da faɗin, “Dilla malam miye haka?”. “Me nayi ni?” cewar Jabeer dake rama harar da Jay yay masa, ya cigaba da faɗin, “Kai ka dace da wannan tambayar baniba boss, sai neman haukatar da yaran mutane kake kana wani cijewa, gwara idan son yarinyarnan kake kafito ka sanarma duniya ka kuma shiga cikin ƴan takara ko Rose ta dawo hankalinta, kuma ka kwana da sanin Qaseem son yarinyarnan yake, yasin ka tsaya kallon ruwa ƙwaɗone zaima ƙafa, saboda gida ɗaya suke kwana suna tashi, dan a ruwa kake kusa da kada malam”. A fusace Jay da dama kaɗan yake jira ya miƙe, ƙofa ya nunama Jabeer yana huci, “Tashi ka fita a office ɗinan Jabeer kafin nama rashin mutuncin da bazaka taɓa mantawaba, banason wasan banza kaima ka sani ko”. Miƙewa Jabeer yay yana taɓe baki, yasan fitar tasa shine mafi alkairi dan Jawaad a wuya yake, shikuma idan yay zuciyar da har ɓacinta ya fito a muryarsa kai nesa dashi yafi komai alkairi, idan ya huce da kansa zai nemeka yay maka bayani harma daban haƙuri idan yasan yamaka abinda bai daceba. Ficewa Jabeer yay yana murmushi da girgiza kai. Jawaad ya koma ya zauna yana ƙwafa, sai kuma ya miƙe ya nufi toilet yabar su Hafiz dake binsa da kallo.
A sanyaye Aliyu yace, “Sonta yake amma kamar shima bai fahi
mci hakaba Hafiz”. Cikin damuwa Hafiz ya bama Aliyu amsa da cewar, “Na daɗe da fahimtar haka Aliy, ba fahimtace baiyiba kuma shima, sarƙaƙiyar dake cikin al'amarin yarinyarne yake sakashi ƙoƙarin haɗiyewa, sai dai kuskuren daya kasa tunawa shine, ba kowanne irin SO bane yake haɗiyuwa lokacin da ake buƙata, wani koda ka korashi da ruwan haƙuri dana juriya a maƙoshi yake tsayawa ya tsaida dukkanin muhimman al'amuranka wucewa cikin zuciya da ƙwaƙwalwa, ni kaina na waiga ta kowacce kusurwa bashi da wani magoyin baya akan al'amarin yarinyarnan sai sashe ɗaya, shi kuma baida wani ƙarfin iko akan hakan”. ajiyar zuciya Aliyu ya sauke mai ƙarfi yana dafe kansa, sai kuma ya ɗago ya kalli Hafiz dake kallon inda Bilkisu take, yace, “Minene mafita yanzu Hafiz? Jay yana buƙatar mace a kusa dashi sosai ta kowanne ɓangarema kuwa, yarinyarnan kuma tanada mafi yawan nagartar data dace ta zame masa abokiyar rayuwa, mizai hana mu bashi shawarar ya sanar mata ABINDA KE RANSA”. Numfashi Hafiz ya sauke yay shiru na wasu sakkani yana nazari da bubbuga yatsansa akan baki, ya kalli Aliyu yana kaɗa kai, “Aliyu ita kanta yarinyarfa bamuda wani ƙwarin gwiwar samun goyon bayanta, dan tayi nisa wajen son ɗan uwanta, sannan bana tunanin zata iya barin Qaseem kodan halaccin mahaifinsa a rayuwarta ta ɗauki waninsa, shiyyasa nace maka akwai sarƙaƙiya takowacce kusurwa, Kasan Jabeer yanada fiƙira akan irin waɗannan al'amuran, sai dai shi matsalarsa saka wasa a dukkan lamarinsa, bansan lokacin da zai dinga kallon abu mai muhimmanci a muhallin daya dace ba, amma mubari zuwa weekend sai muyi zamana musamman akan maganar”. Cikin gamsuwa Aliyu yace, “Shikenan ALLAH ya kaimu”. Fitowar Jay daga bayi fuskarsa jiƙe da ruwa ya sakasu yin shiru, babu wanda yace dashi komai yazo ya zauna a kujerarsa, Hafiz ne ya fara miƙewa yana faɗin, “Bara muje zuwa anjima ma dawo muyi maganar idan ka samu lokaci”. Kai kawai jay ya ɗaga amma baice uffanba.
Fitar su Aliyu babu jimawa Dad ya iso station ɗin su Jawaad, ba'a bashi damar shigaba saida ya kira Jawaad a waya, tamkarma Jawaad bazai ɗauka wayarba sai wani tunani yazo masa a rai, hakan yasa bayan wayar ta katse yabi bayan kiran Dad shi ya kirashi. Koda ya sanarmasa yana gate sosai mamaki ya kasheshi, amma sai yabama securitys ɗin umarnin a rako Dad office ɗinsa, shaf ya manta da Bilkisu dake kwance tana barci.
Bai nunama Dad komaiba yay masa tarba ta mutuntawa, bayan sun gaisa ya bashi ruwa Dad ya fara magana cikin karyar da murya. “Jawaad”. Yanda ya kira sunansane ya sakashi ɗaga kai ya kallesa, ya amsa da “Na'am”. “Jawaad wajenka nazo gwiwoyina a ƙasa da tarin magiya da roƙon da idan kamawa tai na duƙa a gabanka zanyi hakan. Dan ALLAH ka tausayama Mamana ka dubi al'amarinta, bazan musamaka ba akan ita mai laifice damu kanmu, sai dai ince dan ALLAH mu manta da baya domin ta shuɗe, wlhy ina mai tabbatar maka duk wautar dake kan Mamana a yanzu babu ita, dan ta gurzu da horonka, ka tausayamin kodan ciwon dake tare da ita na hawan jini da likita ya sanar mana, badan tanada sauran shan ruwaba faɗuwar da tai jiya a gidanku likita ya tabbatar mana da sai ta kamu da paralysis, wlhy yarinyarnan tana sonka fiye da yanda kake zato ko tsammani........” Jawaad da kansa ke ƙasa yace, “Kayi haƙuri Dad ban katsekaba, da Huda na min irin wannan son da bazata guji haɗa zuri'a daniba, yakamata mu fahimci Hudah ta huce sahun ƙuruciya yanzun, bai kamata ace duk abinda yazo zuciyarta tai tunanin aikatashi shine mafi dai-dai a rayuwarta ba, sannan kuma abinda takeso ace dole saita samesa, dolene duk inda akwai take wataran za'a samu babu. batason haihuwa yanzun miyasa ta yarda tai aure? Bata shirya zama kamar kowacce macen aureba miyasa ta zaɓi muyi aure? A ganina da sai ta bari sai lokacin da duk ta shirya waɗan nan, Dady ni bahaushene, uwata bahaushiyace, mahaifina bahaushene, dukkanin dangina hausawane sai fulani, addinina shine musulunci, addinin iyayena da dangina duk musuluncine, tayaya Hudah take tunanin zan biye mata na ajiye dokokin UBANGIJINA na ɗauki son zuciyarta?, tayaya take tunani zan ajiye al'adun yarena dana tashi
cikinsu na ɗauki ra'ayinta data aro a wajen wasu?, ai duk duniyar da zan shiga dady ina alfahari da abubuwannan guda biyu, YARENA ADDININAH, banajin kunyar nuna kaina a gaban kowanne mahaluki da tambari kasancewata musulmi, dan rahamace babba a gareni da wofantar da ita babbar asarace da bata da madadi duniya da lahira, a duk duniyar dana shiga zan kira kaina bahaushe, koda wanda nake tare dashi baitaɓa jin sunan yaren hausa ba ma zan tabbatar masa da yaren ya fara saninsa a lokacin kuma nai masa AlFAHARI dashi saboda yarena ne, shine harshen da UBANGIJINA yafi ganin ya cancanta na fito a ciki ya zama abin maganata, to mizaisa na ƙyamacesa saboda yaren wasu da ko za'a kashesuma basusan nawa ba, wlhy Dady idan ka cire LARABCI daya kasance yaren MANZON ALLAH (S.A.W) to babu wani yare da yakai muhimmancin dazan fifitashi sama da yarena na HAUSA, duk yaren da kaji yafita a harshena saɓanin LARABCI da HAUSA to inayinsane saboda lalurar mu'amulla da mutane badan ina kallonsa a saman nawaba. Kayi haƙuri Dad mubar wannan maganar kawai, ku tayamu addu'ar ALLAH ya bama kowa dai-dai da ra'ayinsa ni da ita, dan nikam Hudah tafi ƙarfina”.
Jikin Dad duk yayi sanyi da maganganun Jawaad, dan kuwa dukkan abinda ya lissafa matsalace mai tushe da shima yanada kaso mafi yawa wajen ƙirƙirarta ga ahalinsa, to amma yanzu bata wannan akeba, matsalar mamansa itace gaba da komai. Ya nisa cikin girgiza kai da raunana murya fiye da farko yace, “A karo na babu adadi Jawaad zan kuma cewa kayi haƙuri, ina mai tabbatar maka a yanzu zaka sami mamana a yanda kakeso kuma kake buƙata”.
Shiru Jawaad yay yana mai kallon Dad cike da tausayi, dan yasan shine ginshiƙin ruguza gidansa wajen sakaci, gashi a yanzu abinda ya raina yayi gawurtar da al'amarinsa yafi ƙarfinsa amma shi baima fahimtaba, cike da girmamawa yace, “Kayi haƙuri Dad zanzo gida na sameka idan na tashi aiki insha ALLAH, wannan maganar bata nan baceba, ALLAH ya zaɓa mana abinda yafi alkairi”. Shiru Dad yay ya kasa tashi, dan gani yake tamkar Jay yawo da hankali zai masa, saboda yasan taurin kan yaron da kafiya idan ya juyama abu baya, tun yana yaro ya fahimci wannan shegiyar halayyar tattare dashi, shiko buƙatar ƴaƴansa bai haɗata da komai a wannan duniyar ba. A bazata Jawaad kawai sai yaga Dad tsuggunne gabansa yana faɗin, “Jawaad dan girman ALLAH karka wofantar da maganar n....” da sauri Jawaad ya miƙe jikinsa har rawa yake ya tanƙwaɓe wayarsa dake kan desk ɗinsa ta faɗi ƙasa, baibi takantaba ya kama hannun Dad yana faɗin, “Ya ilahi, Dad dan ALLAH ka tashi, minene kakeyi haka? Wlhy na tabbatar maka zanzo muyi magana a gida” da ƙyar Jawaad ya samu Dad ya tashi tsaye, gaba ɗaya al'amarin yana neman birkita masa ƙwaƙwalwa, wane irin ubane Dad? Wane irin kalar mugun so ne wannan yakema ƴaƴansa? Abin yayi yawa matuƙa, kowanne iyaye nason ƴaƴansu amma na Dad yana neman wuce hankali. Shidai Jawaad sai ya koma lallashin Dad ɗin ya samu suka fita yay masa rakkiya ya tafi, gaba ɗaya kansa a cinkushe yake, harma ya fara masa wani masiffen ciwo tacan ciki.
Koda ya dawo office da shashshekar kukan Bilkisu ya fara cin karo, tun shigowar Dad ta farka, dukkan maganganun da Dad