Showing 273001 words to 276000 words out of 388641 words
lokacin salla ya ƙwace min. Saida na farayin sallar magriba sannan. Saboda wutar dake akwai sai na jona hand dryer a soket kawai, nai zaman fara busar da gashina.
Karatun Al-Qur'anin dana sakane yasa sam banji motsin shigowarsa ɗakin ba, sai da yay sallama, da sauri na juyo dan banyi tunanin ganinsa ba.
Jay da tun ɗazun yaketa faman sallama ya ɗan tsura mata idanu, daya shigo baiga kowa a falo ba, har yay tunanin nufar nasa ɗakin sai kuma ya nufo nan saboda jiyo sautin karatu.
Towel ɗin dana tsane kai na ɗauka na ɗaura a kafaɗa ta ya ɗan rufemin ƙirji, wanda na ɗaura ɗin kuma sai faman jansa nake ƙasa dan cinyoyina duk a waje suƙe. Ganin ya ɗauke kansa tamkar baiga abinda nakeyinba ya sakani saurin cemasa, “Sannu da zuwa”. “Yauwa sannunki kema”. Ya faɗa yana ƙarasowa cikin ɗakin sosai. Zama yay a bakin gadon yana sauke numfashi alamar gajiya. Daurewa nai na tashi, na raɓa ta gefensa na ɗauka kayana dake saman gadon zan nufi bayi dan na saka sannan na dawo ɗauka masa ruwa da zaman busar da kan.
“Da miye na saurin yin wankan tunda kinsan bai tafiba?”. Maganarsa tazomin a bazata. Cak na tsaya tare dayin ƙasa da kaina dan ni bansan wace amsa zan bashi ba nikam, yaushe yasan nayi wankan to? Anya boss bai gani har hanji kuwa?.
Ganin yanda ta wani tsume waje guda ya sakashi miƙewa yana girgiza kansa, zare rigarsa yayi ya raɓata ya wuce batare da ya sake cewa komai ba.
Ganin ya shige bayi nai azamar saka kayan sauri-sauri sannan na fita na ɗaukko masa ruwa, zaman busar da kan na sakeyi yanzun kam hankalina kwance, saukar laimar ruwa da naji a kan hannuna ya sakani saurin ɗagowa na kalli mirror'n, shine tsaye a bayana, sakar masa hand dryern da yake ƙoƙarin amsa a hannuna nayi ina rumtse idanu, dan wani irin masifaffen harbawa zuciyata tayi, karan farko da naga namiji a tuɓe kamar haka a gabana bayan jazuga da baida wani fasalin kirki irin na zaratan maza. a raina rayawa nake, ‘Wai miyasa maza sam basu da kunya ne? Daga shi fa sai towel iya ƙugu zuwa gwiwa amma ya iya fitowa gabana ya tsaya’.
Jay da duk yana kallon yanda ta rikice ta cikin mirror'n yay guntun murmushi kawai yana ƙarasa busar mata da kan, sai da ya gama tsaf ya ɗauki ribbon ɗin da yaga ta ajiye ya ɗaure matashi tsaf fiyema da yanda zatayi, harda su mata wani ɗan style da brush. Kujerar ya juya ya maido fuskarta inda yake kafin ya miƙar da ita tsaye ya ɗaura duka hannayenta saman ƙirjinsa daketa raɓar ruwan wanka. “Buɗe idonki” ya faɗa babu wasa.
Hannunta dake ɗan rawa tai ƙoƙarin zamewa tana maƙe kafaɗa alamar “Ah-ah”. hannun nata ya maida da ƙyau, yana bin fuskarta da kallo. A bazata ya sumbaci inda batai zatoba duk da akwai riga a jikinta. A take ta waro idanu waje da masifar sauri tare da buɗe baki. Babu shiri Jay ya ƙyalƙyale da dariyar da bai niyyaba, dan yaga tsoron nata fiyye da yanda yake son gani.
Bilkisu tai saurin duƙewa tana matse hannayenta duka biyu a ƙirjinta tare da cusa kanta duka a cikin cinyoyinta tana murmushi, dan ita kanta tabama kanta dariyar abinda tayin. Ga kunya mai tsanani akan abinda yayi ta lulluɓeta. Kafaɗunta ya kama ya ɗagota yana murmushi, duk yanda yaso su haɗa ido taƙi, daga ƙarshema saita ɗora kanta a ƙirjinsa ta ɓoye fuskar. Rungumeta yay da duka hannayensa yana murmushi tare da shaƙar ƙamshin da gashinta keyi da jikinma nata ya lumshe idanu. Kusan mintuna biyu suna a haka sannan ya zauna a bakin gadon ya ɗaurata saman cinyarsa. Fuskarta ya ɗago yanda zata kallesa duk da dai tanata faman yin ƙasa da idanu amma tana ganin fuskar tashi. Laɓɓansa ya nuna mata da ɗan yatsa yana wani ƙanƙance idanunsa. Kafaɗa ta maƙe da sake maida kanta a ƙirjinsa.
“Ni ai sai nayi” yay maganar yana yin baya dasu a kan gadon ya birkiceta ta koma ƙasa. A take idanun bily sukayo waje, hanata dukkannin dama yay ya shiga yin yanda yaso da ita.
Kiran sallar isha'i ne ya ƙwaci Bilkisu a hannun Boss, shima da ƙyar, dan daga kiss sai salon ya nema canjawa. Tunda ta samu ya barta ta cusa kanta cikin filos. Baice da i
i buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za'a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
ta komaiba shima ya fice yana murmushi. Ɗakinsa ya nufa ya sake ɗaura alwala da canja kayansa zuwa blue jeans da t-shirt itama Blue, ya saka turare kaɗan da ɗaukar wata ƴar ƙaramar bindiga ya saka a gefen ƙugunsa sannan ya fito. Ɗakin Bilkisu ya koma. isketa yay ta fito daga toilet fuska a jiƙe alamar alwala tayo. Ruwan data ajiye masa ɗazun ya ɗauka yana sha idonsa a kanta. Kofin ya ajiye yana kallon agogon hannunsa, “Bara naje za'a shiga salla, idan an idar zan ɗan ƙarasa wani waje insha ALLAH kafin goma zan dawo.
Da sauri Bilkisu ta kallesa idanu cike da ƙwalla, “Dan ALLAH mu tafi tare, nidai tsoro nakeji”. Yanda ta kumbura baki taso bashi dariya, amma sai ya danne abinsa ya taka zuwa inda take tsaye, fuskarta data duƙar yasa hannu ya ɗago, acan ƙasan maƙoshi yace, “Kin taɓa ganin amaryar kwana ɗaya a gidan miji ta fita?”. “To ai babu wanda zaisan na fita tunda dare ne”. Fuskar tata ya saki yana ɗan ɗage kafaɗa, “Okey, ki shirya kafin na dawo salla saimu je”. Cike da murna ta amsa masa da to. Goshinta ya sumbata ya juya ya fice yana murmushi dan wayo kawai yay mata ba dawowa zaiyi ba.
Ana idar da salla Jay ya fito daga massallaci, motarsa da dama ya bari a waje bai shiga da ita gida ba ya shiga ya bar anguwar, kai tsaye address ɗin da dattijon nan ya bashi ya nufa, anguwace irin sabuwar anguwarnan da uncompleted building sukama fi yawa, sai dai inda gidan drama'n yake anɗan gaggama wasu gidajen dan wajen harya fidda santa ɗoɗar, bakajin hayaniyar komai saina Genretor ɗin da suka kunna da ƴar hayaniyarsu alamar basu gama zuwa ba, akwai ƙwayayen wuta a waje da suka haska kusan rabin layin, sai mai Nama daketa faman haɗa wuta, gefensa mutum biyune ɗaya mai ruwa ɗa kayan drinks, sai saurayi da budurwa dake can gefe suna hira, sai kuma masu shiga da fita cikin gidan ɗai-ɗai dan yanzu suke kan zuwa. Waya ya ɗauka yay kiran wani abokinsa da ya kasance ainahin police, saida suka gaisa ya gama tsokanarsa da ango-ango, sannan Jay yace, “Auwal kuna garin nan amma tsageru har suke da lasisin buɗe wuraren iskanci irin haka?”. Daga can Auwal yace, “Haba dai Jay, kaima kasan hakan bazai kasanceba”. “Gashi kuwa na gani da idona, akwai wani gidan Drama a sabuwar anguwar nan data kusa haɗewa da jan-ɓauna, inason ƙarfe goma da rabi kuzo wajen kuyi kamen kan mai uwa da wabi”. Bai jira cewar Auwal ba yace, “Mu kwana lafiya” ya yanke wayar. facemask ya ɗauka ya saka tare da facing cap, kallon kasan yayi a madubi ya tabbatar komai yayi kafin ya fito bayan ya kashe motar. Sai da ya tabbatar babu wanda yaga fitowarsa sannan ya nufi gidan.
★★★★★★
Ina idar da salla na koma bakin gado nai zaman jiransa, ganin shiru-shiru sai kawai nahau yin game a waya, hamma na farayi ɗai-ɗai alamun inajin barci, nayi guntun tsaki da kallon agogon ɗakin, tara saura minti ashirin, zamewa nai na kwanta tare da jan filo na ɗaura kaina na cigaba da game ɗin, tun ina ƙoƙarin damƙe wayar dake neman suɓuce min harna yaddata batare dana saniba.
A firgice na farka jikina na wani irin ƙyarma, ‘innalillahi wa'inna ilaihirraji'un’ na shiga ambata ganin ɗakin dunɗum da duhu bayan kuma nasan fitilar a kunne take, dariyar da aka tuntsure da ita ta sakani sake firgicewa nahau laluben gadon.....
“Bilkisu! Kenan mai gadon zinari, wato ke amarya ko? Azatonki zaki iya tsere minne? Ke da kina tunanin na barki? Wannan gurɓataccen tunanine bilkisa, na rantse miki yau saina amshi abinda ya kasance cikar burina dan bazan rasa komai a dalilinki ba wannan gangan ne hhhhhhhhhh!!!!!!!!.................✍
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI...
GUDU DA WAIWAYE....
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gama
[1/4, 2:46 PM] HASNA✍🏻: Page 42
..................Inda mai naman nan yake ya tsaya, batare da yayi magana ba ya miƙama mai-naman 1k tare da nuna masa naman. Kallonsa yay a ƙufule, “Haba malam, ya zakazo waje babu ko sallama ka miƙomin dubu wai na baka nama? An faɗa maka ni irin sakarkarun masu saida naman nan ne da kuke rainama hankali, nibanma taɓa ganinka a gidannan ba, kai wane?”. Jay ya danne takaicinsa cikin salon maganar kurame yay masa nuni wai shi bebe ne”. Mai nama yace, “Oh to yanzu naji batu, kasan rainin tsagerun gidannan ne bazan iya ɗaukaba shiyyasa kaima nai zaton kalarsu ne, na duka kake so?”. Kai Jay ya jinjina masa. Mai nama ya fara yankowa yana sawa a takarda da raira ƴar waƙarsa ta shata mai taken “Natsaya ga annabi Muhammadu.......” Jay dai kallonsa yake da nazarin wajen harya kammala yanka masa, amsa yay da masa godiya ya juya zai tafi, sai kuma ya juyo da sauri irin kamar yayi mantuwar nan. Ƴar takarda ya ciro a aljihun wandonsa ya miƙama mai nama. Mai nama ya amsa da faɗin, “Miye kuma wannan? Nifa kunsan ba wani boko nayiba amma kuyitamin wani lagude-laguden jaraba. Kai Hamusu zo duba mi ya keso kuma?”. Wanda aka kira Hamisu dake gaban lemuka ya amsa da “To baba”. Takardar ya amsa ya duba sannan ya kalli mai naman, “Baba wai gidan Ɗan Alhaji ya keson a nuna masa”. Shiru mai naman yay yana kallon Jawaad, mikuma ya tuna oho masa sai ya washe baki, “Af to inaga irin abokansa ne daya ɗan gayyato, kasan yau zaiyi ajo”. Jinjina da hannu Jay yayma Mai nama irin ka gane ɗinan. Mai-nama ya sake washe baki da nunama Jawaad wani gida dake can kusan ƙarshen layin. Cikin alamar maganar kurame yayma Jay yay masa godiya da nufar inda aka nuna masan.
Rufe gidan yake dan haka ya ƙwanƙwasa, sai da yay sau kusan baƙwai sannan akazo aka ɓuɗe cike da masifa.
“Wai wane shegene yake bugama mutane gida haka? Sai kace ya bada ajiya ko an ci masa bashi, idan akai haƙuri dai ai zan fito ba sai ansama lokacina ido b.....” hankaɗa shin da Jawaad yay ya koma baya ya hanashi ƙarasa maganar, zai sake magana Jay ya ɗaura hannunsa saman baki yace, “Shiiiiii”. yana ɗaga rigarsa bindiga ta bayyana, jiki na rawa ɓaleru ya saka hannu ya toshe bakinsa yana faman zare idanu. Ƙofar Jay ya maida ya kulle bayan yay wurgi da ledar naman daya shigo da ita, ya sake kaima ɓaleru wani bahagon bugu tare da damƙo wuyan rigarsa ya miƙar dashi tsaye. Batare da yay magana ba ya nuna masa hanyar cikin gidan. Jikin ɓaleru na rawa ya shiga kaɗa kai tamkar wani ƙadangare.
Gidane madaidai ci yasha tiles har a jikin bango, ga hasken wutar Genretor da alamu suka nuna na gidan drama ɗinne aka jawo masa har nan, ƙofar dake buɗe suka shiga, budurwar dake kwance saman katifa tsirara ta miƙe da sauri zaune tana jan bedsheet ɗin saman katifar ta ƙudundune kanta ciki zata zabga ihu.......
“Idan baki rufemin shegen bakin kiba saina ragargaza ƙasusuwanki wlhy!!”. Jay yay magana cikin kaushin muryar da ta saka budurwar cusama bakinta bedsheet ɗin tana zare idanu hawaye na ƙwarara, jikinta sai rawa yake.
Jawaad ya maida kallonsa ga ɓaleru da duk hankalinsa ke kan wayoyinsu dake zube a ɗan table na glass ƙarami dake gefe. Ƙafa Jawaad yasa ya taɗesa ya faɗi ƙasa tim, cikin zafin nama ya shiga sauke masa maruka a fuska da hannu bibbiyu. A take ji da ganin ɓaleru suka gushe, gashi babu damar yin ihu yana tsoron bindiga. Sai da Jay ya jigatashi da maruka ya tabbatar ya fita hayyacinsa sannan ya barshi. Budurwar daketa gunjun kuka da faman ɓoye fuska ya kalla, “K zoki kashemin duk wayoyin nan....”. Kafinma yakai ƙarshe harta miƙe zaram tana damƙe bedsheet ɗin da ƙyau jikinta na rawa, wayoyin uku manya ta kashe sai ƙarama ɗaya. Yace, “Ina taki?”. Nuna masa ɗaya daga cikin manyan tayi, ukun kuma tace, “N..na nashi ne sauran”. Ɗauke kai Jay yay batare da ya sake cemata uffan ba, ya ɗauki Coc dake ajiye yanata raɓar sanyi ya ɓalle murfin, saman fuskar ɓaleru daya suma ya juyeshi, a take ɓaleru ya kawo numfashi. Wani marin Jay ya sake sauke masa a fuska. Take ya dawo hayyacinsa ya fashe da kuka yana share jinin da yake fita daga hancinsa yana sauka masa kan baki, “Dan ALLAH malam minai maka kake min irin wannan dukan? Idan kuɗi kakeso ko nawane zan baka, nidai karka kasheni dan girman ALLAH, kag.....” sake wanka masa wani marin Jawaad ya ƙarayi tare da ɗora ƙafarsa ɗaya kan katifar ya ranƙwafo kansa da nuna masa fuskar wayarsa. “Wanene wannan?”. Ɓaleru da jikinsa ke rawa ga jini nata fita masa ta hanci da gefen baki yace, “Ni...ni ban sanshi ba wlhy”. “Baka sanshi ba! Kace baka sanshi ba?!!”. “Eh wlhy oga bamma taɓa ganinsa ba”. “Yayi ƙyau” Jay ya faɗa yana miƙewa da tattare hannun rigarsa sosai yay sama. Har Ɓaleru ya fara murna an barsa sai kawai ji yay Jay ya cakumo masa wuya ya miƙar dashi tsaye da ƙyau. Mahaukacin duka ya shiga masa da babu algus, yanda yake bugun nasa zai tabbatar maka zuciyar ƴan mazan a wuya take. Sam baya sauraren roƙon da ɓaleru ke masa da kukan karuwarsa. Saida yay masa lilis sannan ya hankaɗashi ya faɗa saman katifar kansa ya daki bango Ƙummm!!!!. Dafe kan Ɓaleru yay da sakin wata wahalalliyar ƙara, saiga jini sharrrr. Jay ya sake cakumo wuyansa ya shaƙesa da ƙyau da hannu guda, ɗayan kuma ya sake nuna masa hoton Gimba dake tare dashi da suka ɗauka a gidan gonarsa wani zuwa da suka taɓayi tare. Yace, “Har yanzu dai baka sanshin ba?!”. “Dan ALLAH ka tausayamin oga ka daina dukana karka halakani na sanshi, Abokina ne sunanasa Gimba garinmu ɗaya”. Ɗauke fuskarsa Jay ya sakeyi da mari yana faɗin, “Ɗan iska kake son maidanine da?”. “Na tuba dan ALLAH kayi haƙuri bazan sake maka ƙarya ba”. Miƙewa Jay yay tsaye ya kaima Ɓaleru harbi a ƙafa da tofa masa yawu, sai faman huci yake, jiyake tamkar ya kashe banzan nan ko zaiji sauƙin raɗaɗin da zuciyarsa ke masa.
________________________
Bilkisu! Kenan mai gadon zinari, wato ke amarya ko? Azatonki zaki iya tsere min ne? Ke da kina tunanin na barki? Wannan gurɓataccen tunanine bilkisa, na rantse miki yau saina amshi abinda ya kasance cikar burina dan bazan rasa komai a dalilinki ba wannan gangan ne hhhhhhhhhh!!!!!!!!.
Hannu nasa na toshe kunnuwana domin nisanta jina daga shaiɗaniyar dariyarsa, na fashe da kuka ina jan jikina baya, “Kaji tsoron ALLAH bawan ALLAH, koda kai aljanine na tabbata kasan akwai hisabi tsakaninmu ƴan adam da ku, minai maka ne kakeson ganin bayana? Ka tunafa ni matar aurrece yanzun, dan ALLAH na roƙeka karka wulaƙantani, ka barni da mutuncina.............”
“Kima daina ɓata yawun bakinki madam, babu wani roƙonki dazan taɓa saurara, keɗin kaddarace mai girma a gareni, makullin cikar dukkanin burkana. Kinsan illa nawa kikaimin ne?!!” yay ƙare maganar a tsawace da cafke wuyana ya shaƙe. A take jikina ya fara rawa na fara ƙoƙarin fisgo numfashi cikin kakari. Hankaɗani yay na bigi fuskar gadon. Azaba ta sakani fashewa da kuka na riƙe wuyana da duka hannu biyu. Wani irin matsanancin fushine ya tasomin jin dariyar da yake sake ɓaɓɓakawa yanzu ma, nace, “Ƙarya kake azzalumi, idan ka isa ka daina ɓoyemin kanka, matsoracin banza da wofi kawai, Bazan sake roƙoka ka barni ba koda hakan na nufin zakai nasara a kaina ɗin, sai dai na ɗauki alwashin in ALLAH ya yarda, inhar ƙazamin jikinka ya kasance shine ƙaddarata, nima nice zan zama ƙaddarar mutuwarka, dan da hannuna zan kasheka a ɗakin nan, a wannan daren la'ananne ALLAH fasiƙi kawai!!!”.
“Hhhhhhh!!” ya shiga sake ɓaɓɓaka dariyarsa mara daɗin ji da tafa hannayensa. Gaba ɗaya ɗakin ya ɗauki sauti hakan yasa na kasa fahimtar taka maimai inda yake. “Da ƙyau Bilkisu, da ƙyau!, ashe kema kin fara koyon jarumtar mijin naki?, nine zaki kashe, ni ni ninan kikejin zaki iya ki kashe.....?!!!” naji an sake damƙar wuyana an shaƙe.
A take jikina ya fara rawa, nasa hannu na daki cikinsa cikin gushewar hankali, dukda alamu sun nuna yaji zafi bai sakeni ba, sai ma dannani da yay baya ya maƙureni jikin fuskar gadon ya haye kaina. “Zanyi abinda ya kawonin, ada nayi niyyar barinki a raye tamkar sauran kicigaba da rayuwa kema, to amma tunda kince ke tsagerace saina shayar dake gidauniyar azabar mutuwa, k har wacece? Nawa kike? Da zaki zamewa rayuwata matsala.......”
Yanda naima Jazuga ne ya shiga dawomin a rai, duk da shaƙar da