Showing 342001 words to 345000 words out of 388641 words
ya ƙarasa fuskarsa babu walwala, dan duk yanda yaso aro fara'a ya azama fuskar tasa kamar yanda ya saba idan yaje wajen baba ƙaura hakan ya gagara. Cike da girmamawa suka gaishesa har Sir Ahmad.
Kallonsu baba ƙaura yay ya ɗauke kansa yana faɗin, “Kagani har a wajen aikinka ko?”.
Ɗan murmushi Jay yayi da cewa, “Babu komai baba, ai nasan zuwan naka mai muhimmanci ne”. “Hakane” baban ya faɗa yana sake maido hankalinsa garesu sosai. Yace, “Tun da safe na saka a nemomin kai amma hakan ya gagara, ba'a samunka da farko, daga baya kuma ta shiga ba'a ɗagawa”. Kai Jawaad ya dafe, “Dan ALLAH kayi haƙuri baba, wlhy na tsinci kainane a yanayin da komaima bazan iyaba”. “Gudun faruwar hakanne ya sakani yimaka neman gaggawa ai daman, tun bayan wucewarka na tafi jeji ne, acan ma na kwana, dan sai gabannin asubahi na shigo gari, sanda na iso nan har an shiga salla. Na saka a nema min kaine domin isar maka da saƙon abinda idona ya ganomin jiya a cikin jajin nan. Muhammad Jawaad lallai akwai matsala babba dake tunkaroku, da idona na gani, na kumaji da kunnena, gashi rashin samunka akan lokaci ya nunamin alamomin fara faruwar matsalar dana guda ma a yanzun”.
Hankalin Jawaad a tashe yace, “Baba hasashenka duk haka yake, yanzu haka zancen da nake maka anje har gida an ɗauke kakana, akan binciken inda zamu samesa muke”.
“Wannan shine shirinsu na farko dama. Na zauna nayi ƙyaƙyƙyawan nazari mutanen nan ba haka nan suke bibiyarka ba, akwai wani abu aƙasa wanda akwai jininka a ciki, ina nufin cikin zuri'arku akwai wanda ke tare da mutanen nan.....” cike da mamaki Sir Ahmad da Jay suke kallon baba ƙaura. Ya jinjina kansa yana cigaba da faɗin, “Kar kuyi mamaki, neman duniya babu wanda baya ɓatarwa, lallai kamar yanda na faɗa akwai wani abu a ƙasa, dan babu rami miya kawo rami? Bayan abubuwan dana sani ke a hannunku akwai wani abu da kuka ɗakko a wani gida ne?”. Sir Ahmad ya kalli Jay, shima ya kalleshi, sai kuma ya maida dubansa ga baban yana jinjina masa kai. “Akwai wani tukunya baba, wanda.........” ya labartama baba ƙaura da Sir Ahmad komai.
Baba ƙaura da keta faman jinjina kai cike da nazarin maganganun Jawaad ya sauke nannauyan numfashi. “UBANGIJI ya baku kariya sosai to akan wannan aikin, dan suna cikin ruɗani mai girma akan son gano wanda ya ɗauki tukunyarnan, amma sun gaza gano komai, inuwar wadda ta ɗauka ɗin kawai suke iya gani, sannan har yanzu tsafin nasu kuma bai iya nuna musu mahaifiyarka ta shigo ƙasarnan ba. Wannan hikima ce da rahama daga UBANGIJI, inaga iyakar suce tazo shiyyasa komai
ya keta ƙwace musu. A taron da sukai daren jiya sun tattauna abubuwa da dama wanda zarge-zarge da yawa sun sami rinjaye a kai kanka, sai dai a yanda na fahimta na yau sai sun fisu muhimmanci. Dan haka nakeso ku kasance a wajen kai da matarka idan zai yuwu, sannan lallai matsayinku na jami'an tsaro wannan shaiɗancin ya kamata ma ace ku kawo iyakarsa ma baki ɗaya. Dan tabbas kakanka yana tare da su, acanne kawai zaku iya samosa a halin yanzun dama wasu mutanen da aka kai a wajen bisa zalunci da son zuciya”.
Boss ya cika bakinsa da iska ya furzar yana taunar lip ɗinsa na ƙasa da ƙarfi. Kallon Sir Ahmad dake fahimtar dukan maganganun nasu a baibai yayi. sai kuma ya maida ga baba ƙaura yana faɗin “Babu damuwa baba, amma kana ganin ita zuwa da ita bazai zama haɗari ba?”. Ƴar dariya baba ƙaura yay yana kallon Bilkisu data fito da waya a hannu ta doso su, “Babu wani haɗari insha ALLAHU, matar nan taka akwai sirrika tattare da ita waɗanda ALLAH kaɗai yasan tushensu, amma haka kawai nakeji a raina kamar sunada nasaba da taka ƙaddarar. Amma ita ɗin ba jami'ar tsaro bace?”. “Eh jami'ar tsaroce, irin aikinsu ɗaya”. Sir Ahmad ya bama Baba ƙaura amsarsa. Baba ƙaura ya sake faɗaɗa murmushinsa “Ka barta itama ta nuna bajintarta a aikinta da ƙwazon da ALLAH ya bata, ALLAH yana tare daku a dukkan al'amuranku insha ALLAHU. kudai kuci gaba da gayama ALLAH”. A tare suka jinjina masa kawunansu da faɗin insha ALLAHU baba. “Karkuji komai, wannan tafiyar tafi ta farko sauƙi insha ALLAHU, ta wani ɓangaren kuma tafi waccan haɗari, dan haka runduna zaku haɗa mata da tafi ta farko indai aikin zakuyi da gaske” ya ƙare maganar dai-dai da isowar Bilkisu wajen.
Rissinawa nai na gaida baba ƙaura da banyi tunanin ganiba anan, ya amsamin cike da fara'a da kulawa. Cikin girmamawa na miƙama Sir Ahmad takardar hannuna da aka aikoni na kawo masa. Amsa yay yana dubawa, ni kuma na maida dubana ga boss da yanayinsa ya bani tsoro. Da ido nai masa alamar ‘Lafiya?’. Kansa yaɗan girgizamin kaɗan yana lumshe idanunsa dake jajur.......
Sir Ahmad ne ya katse mu da faɗin, “Jay inaga yanzu haɗa rundunar da zamu tunkaru jejin ne ya dace, bara na nema mana jirage masu saukar angulu yanzun nan, sai ku haɗa kayan operation ko”. “Okay Sir” Jay ya faɗa cike da karsashi na jami'i mai cikakkiyar lafiya da zafin nama..
Tare muka koma da baba ƙaura office ɗinsa inda su Jabeer keta aiki cike da zafin nama da ƙwarewa. Boss ya ɗan bigi tebir da zafi-zafi yana faɗin, “Ayi shirin fita operation mun gano inda suke insha ALLAHU”. Duk juyowa sukai suna kallonsa da mamaki, harni kaina kallon nasa nake, amma sai ya ɗauke kai yana nufar telephone ɗin dake saman table ɗinsa yana jero sunayen waɗanda za'a kira yanzun nan”.
Cike da bin umarni Aliyu ya fice zuwa office ɗinsa domin aiwatar da komai, shima bayan yayi waya da wani da bansan ko wanene ba ya ajiye yana kallona da nufar ƙofa yace na biyosa ni da Dawood da suka dawo da Oga Aliyu yanzun.
Store ɗin station ɗin muka nufa, inda acan muka iske Sir Ahmad da wani ogan mu shima suna haɗa bindugu. Muma aikin haɗa wasu makaman aka sakamuyi. Mamaki ya kuma cika zuciyata, duk yanda nake hasashen al'amarin da alama ya wuce nan, nasan Boss mutum ne mai muhimmanci a hukumarnan tamu, ya cancanci a nuna masa kowanne irin halacci akan taɓa ahalinsa, amma yanda ake shirin fita operation ɗin sai nakeji a raina kamar ya zarce na maido kakansa kawai. Cikin mintunan da bazasu gaza talatin ba duk wani shiri an kammalashi, duk jami'in da aka buƙaci gani ya amsa kira, a mamakina harda su Ummie su dukansu, Rose harma dasu Ada, sai sauran jami'ai na departments ɗin da ba namuba ma. Dukanmu mun kasance cikin Uniform ɗin aiki, dan boss ma da yake sanye da kayan gida a da sai gashi ya fito cikin Uniform harsu oga Jabeer da Sir Ahmad ɗin kansa. An bamu bullet proof jacket duk mun sassaka, kafin oga Hafiz ya rarraba mana bindugu harda kibiya ga waɗanda suka samu horo na musamman a kanta, wasu kuma wuƙaƙe naga an basu manyan takubba, sosai mamaki abin yayta bamu mu baƙin shigowa hukumar, dan zan iya cewa wannan shine operation na
farko gagarumi da za'a fita damu..............✍
Da ace zan iya sai nabi wasunku da bulala goma-goma a ɗuwawu aradu🙄, wlhy nafiku son naga na kammala buk ɗin nan🤦🏻. Uzirin daya riskeni ya wuce dukan tunanin mai hasashe, yanzunma dauriyace kawai dason ganin na faranta muku, saɓanin wasunku da bakunansu ke furta abinda bai daceba a gareni😢🚶🏻.
ALLAH ka gafartama iyayenmu🙏🏻😭
[2/12, 7:51 PM] Wasila: *_ƘWAI CIKIN ƘAYA!!_*
*_Bilyn Abdull ce🤗_*
_ASSALAMU ALAIKUM MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR... 🙋🏿♀️🙋🏿♀️INA KUKE NE? 🔊🔊KU MARMATSO, DOMIN ZAMAN JIRA YA KARE, HAZIKAN MARUBUTAN NAN DA SUKA HADA HAZAKA DA KAIFIN TUNANI SUN SAKE ZAGE DAMTSE SUN ZO MU DA WASU SABBIN SALON RUBUTUN SU, WADANDA ZASUWA’AZANTAR, SU NISHADANTAR, KANA SY DILMIYA KU A KOGIN KAUNA, BASU TSAYA ANAN BA SALON RUBUTUN SU YA SAKE ZUWA DA SABBIN TSARE TSARE NA DARUSSA DABAN DABAN, DA KUMA HANYOYIN GYARIN JIKI DA WAJE._
_KADA KU MANTA MARUBUTAN ZAFAFAN DAI SUNE WADANDA SUKA YO MUKU HAR KASHI BIYU A SHEKARAR 2020 DATA GABATA,: WUTSIYAR RAKUMI DA GUDU DA WAIWAYE NA BILYN ABDULL. 2-DAURIN BOYE DA ALKAWARIN ALLAH NA SAFIYYAH HUGUMA.3-BURI DAYA DA QAUNAR MU NA MAMUH GEE-4- SAUYIN KADDARA DA DAURIN GORO NA HAFSAT RANO. SAI 5-KAI MIN HALACCI DA IGIYAR ZATO NA MISS XOXO.._
_A WANNAN SABUWAR SHEKARAR TA 2021 MA HAZIKAN MARUBUTAN SUN SAKE DAWOWA DA WASU SABBIN DA’DADAN LITTATTAFAN NASU:_
_1_
_* SAFIYYAH HUGUMA* MARUBUCIYAR KUNDIN KADDARA DA ABADAN TAZO MUKU DA SABON LITTAFIN TA MAI SUNA: *(SIRADIN RAYUWA)💜*_
_2_
_*HAFSAT RANO* MARUBUCIYAR GUGUWAR SO DA RUHI DAYA, TA ZO DA SALON NATA LITTAFIN MAI SUNA: *(ABINDA KE CIKIN ZUCIYA..*)💘_
_3_
_* MAMUH GEE* MARUBUCIYAR TARAYYAH DA EZNAH, TAZO DA SABON ZUWA MAI SUNA: *(MIN QALB)❤️.*_
_4_
_*MISS XOXO* MARUBUCIYAR NAUFAL DA SAIFUL-ISLAM, TA YUNKURO DA WANI MAI SUNA: *(KIBIYAR AJALI)*💜_
_5_
_SAI MARUBUCIYA *BILLYN ABDUL* WADDA TAYO MUKU KWAI CIKIN KAYA, DA CIKI DA GASKIYA TA YINKURO DA WANI MAI TAKEN: *(YANKAN BAYA)*💝_
_RIGIJI GABJI DUKKAN WADANNAN LAGWADAR DADADAN LITTAFAN BIYAR ZASU ZO MUKU NE INSHA ALLAHU AKAN FARASHI MAI RAHUSA KAMAR HAKA;_
Duka BIYAR 5 zaku samesu akan garabasar naira 700 kacal,
Guda hudu 4 Kuma 500,
Guda uku 3 Kuma 450,
Guda biyu 2 Kuma 400,
Guda daya akan 300.
Ma'ana
Each one is 300
2 is 400
3 is 450
4 is 500
5 is 700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO- *0812652655*
ACCOUNT NAME- *HAFSAT LAWAN GAMBO*
BANK NAME: *ACCESS BANK*
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*+234 903 234 5899*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
*09033181070*
Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO
TEAM#ZAFAFABIYAR🔥
Page 59
..................Motoci na alfarma aka aika daga masarauta domin tarbo su Abbu a airport kamar yanda aka aika tarbar su Umm-Anum, sai dai su masarauta aka wuce dasu, inda acan ɗinma suka sami tarba ta musamman da mutuntawa ga mai martaba sarki Sameer Saifudden da iyalansa, harma da ƴan majalissar sarki baki ɗaya. A yanda masarautar take yau ko ba'a faɗa makaba kasan anyi manyan baƙi a cikinta, waɗanda suka isa suka bunƙasa. An baje musu abinci na alfarma na ƙasarmu masu daɗi da daɗaɗa zuciya.
Tun kafin tafiya ɗakko su Abbu Gimbiya Munaya tasa Amaturrahman ta nema Number Jawaad, amma taƙi shiga sam, ta kira ta Bilkisu kuma ba'a ɗagaba. Hakan ya bata mamaki matuƙa, dan tasan dai ai su Jay ɗin sunsan da zuwansu Abbu, a yanda suka tsara al'amarin kuma daga tarbo su Abbu a airport zasu wuce masarauta ne harsu Umm-Anum ɗin, bayan su Abbu sunci abinci sun huta sai su ɗunguma baki ɗayansu gidan Alhaji Babba, daga can idan dare bai rufaba zasu ƙarasa family house ɗin su Jay. To amma gashi har lokaci ya shige babu Jawaad ɗin babu dalilinsa.
Basu ji halin da ƙasar take ciki ba sai sai kusan isowar su Abbu da awa ɗaya da rabi sannan takawa ya samu kiran waya daga gwamna akan ya buɗe television yaga tashin hankalin da a yanzu shima aka faɗa masa game da manyan mutane da ake ganin mutuncinsu a ƙasar, babban abinda ya razana gwamna kuwa harda wasu a abokansa masu manyan muƙamai kuma a gwamnatin tasa.
Al'ajabi daya kume sarki lokacin daya buɗe tv kasa ƙwaƙwaran motsi yayi, dan shima ɗin ai akwai waɗanda suke matuƙar gaisawar zuminci a cikinsu sosai..........
_________________
ASIBITI
____________
Hankalin su Mom a tashe suna jiran fitowar Dr Tayyeb daga ɗakin da aka saka Mama Badiyya kira ya shigo wayarta daga mai aikinsu. Kamar bazata ɗagaba sai kuma mita tuna oho mata ta ɗaga wayar.
A matuƙar ruɗe Talatuwa dake kuka ta zayyane mata abinda ya faru game da zuwan wasu mutane da sukace su ƴan sandane har gida suka tafi da kuku da maigadi.
A tsawace Mom tace, “What!! K bansan shirme da hauka kinji, ubanmi suda suke gida kullum zasu aikatama ƴan sanda harsuzo gida su kamasu?”. cikin kuka talatuwa tace, “Wlhy hajiya da gaske nakeyi, yawwa gama wannan da kikacemin shine babban yaronku nan yazo gidan”. Da mamaki Mom tace, “Waye? Kina nufin Qaseem?”.
“E...e...eh shi hajiya, wanda hotonsa ke a falo sanye da baƙaƙen kaya tare da Alhaji”. Jikin Momy har rawa yake wajen ambaton, “Da gaske Qaseem, yaushe suka barshi ya fito to? Kinga bashi wayar muyi magana nima gani nan zuwa gidan yanzun nan”. “T..t...to hajiya, bara nakai masa”. Talatuwa ta faɗa tana ɗan gudu wajen bin bayan Qaseem dako kallon inda take baiyiba ya haye sama ɗakin Dad direct. Yana kama handle ɗin ƙofar tana ƙarasawa garesa, da rawar jikin tsoro ta miƙa masa wayar tana faɗin, “Alhaji ƙarami sannu da zuwa, gashi inji hajiya zakuyi magana”. Wani mummunan kallo daya kaɗa hanjin cikinta ya zuba mata, cikin daka tsawa yace, “Ɓacemin da gani kona halakaki wlhy”. Zabura Talatuwa tayi da gudu tabar saman, yayinda Momy kuma taji komai ta cikin wayar, ita kanta tsawar Qaseem sai da ta sakata cire wayar daga kunnenta ma.
Bata iya cewa sauran ƴan uwanta komaiba ta nufi hanyar fita daga asibitin da hanzari, duk faman tambayarta lafiya? da sukeyi bata juyoba balle ta amsa musu harta fice. Da kanta taja motar tabar asibitin zuwa gida.
Akan hanyar momy na nufar gida ta fahimci garin babu lafiya, dan kuwa babu abinda take gamo da shi a tituna sai matsanancin holdup. Mafi yawancin inda traffic light suke an haɗa cinkoso a wajen sosai, ga jirage masu saukar angulu da keta yawo na kaikawo a sararin samaniya, wasu ma daf da mutane suke. Ratse ta ringayi ta cikin anguwanni tamkar yanda wasu motocin taga sunayi. Da ƙyar ta samu kanta a anguwarsu, tai fakin motar a ƙofar gida batare data kasheba saboda wani bahagon ruɗani da ta sake karo da shi kuma, ƙofar gate ɗinsu a buɗe take, ga jami'an tsaro sun zagaye gidan, cikin sake shiga ruɗani ta afka cikin gidan da sassarfa tamkar zaga kifa, ananma wasu jami'an tsaron ta sake cin karo dasu a cikin gidan, talatuwa na durƙushe gefe tana kuka ita da mai bayin fulawa.
“Kai lafiya?”. Mom ta faɗa hajijiya na neman ƙwasarta zuwa ƙasa. Wani cikin ƴan sandanne ya bata amsa da faɗin, “Hajjaju wannan gidan yana a hannun hukumane a yanzun, akwai bincike da za'azo ayi a cikinsa daga yanzu zuwa kowanne irin lokaci”. Cikin tsawa da hucin ɓacin rai, “Mom tace kuɗin ubanwa muka sata to? Muba ƴan siyasaba ba ma'aikatan gwamnati ba, amma za'a turo mana jami'an tsaron binciken almun dahana da dukiyar ƙasa?”.
“A'a hajiya, mu ba jami'an tsaron almun dahana bane ba, jami'an tsarone na farin kaya, da kuma amincewar Sir Qaseem Ali muke anan bisa Umarnin Sir Jawaad Abdul-aziz Yusuf”. “Qaseem! Da Jawaad kuma?”. “Hakane hajjaju” ya sake bata amsa kansa tsaye.
Wata ashariya da momy ta manta tama iyata ta kwaso ta dire bisa ƙasa tanayin wurgi da jikkar hannunta, ta shaƙo wuyan police ɗin tana huci, a take sauran suka zagayeta da bindiga. Murmushi Munkaila yayi yana ɗaga musu hannu alamar su barta, ya kalleta fuska babu wasa zaiyi magana ta tare numfashinsa. “Kai shashasha kasan mi kake faɗa kuwa? Ina Jawaad da Qaseem ɗin suke?”. Ɗan murmushi yay mata yana zame hannunta a wuyansa ya gyara rigarsa, “Sir Qaseem yanzu ya fita, Sir Jawaad kam yana filin daga”. Sake rikicewa kanta ya nemayi, batare data nutsu wajen fahimtar inda batunsa ya dosaba ta fice a gidan tamkar wata mahaukaciya.
Mota ta sake shiga tabar anguwar batare da tamasan kalar tunanin daya dace ace tayiba, kanta tsaye station ɗin su Jawaad ta nufa, sai dai ɗan karen holdup ɗin da take fuskanta a yanzun ya zarece na ɗazu data riska tsakanin asibiti zuwa gida............
___________________
JAY-QAS
________________
Koda tawagar su Jawaad suka iso cikin gari cike suka iske station ɗinsu da manyansu da ƴan jaridu, abu na farko da suka farayi shine gabatar da sallolin azhar data riskesu a can da kuma la'asar da a yanzu aketa yinta.
Suna idar da sallar ƴan Jarida sukai musu caa aka, Jay dai bai saurari kowaba daga shi har Sir Ahmad da sauran manyansu.
Cikin son ƙure mutane irin na ƴan jarida ɗaya a cikinsu ya juya ga masu ɗaukar rahoton gidan tvn su yana magana a harzuƙe. “To jama'a kamar yanda kukai hasashe dai hakanne ta kasance, dan kuwa munga alamar rufa-rufar da muka saba gani ga jami'an tsaronmu idan laifi ya shafi manyan ƙasa yau gashi ta tabbata, to ta yayama zasu yarda su buɗe komai wa duniya bayan daga kawunansu sai surukansu da abokan iyayensu dama iyayen nasu. Haka za'a kifemu bayan kwana biyu muji shiru, bayan kuma tarin gawarwaki da mutanen dake a cikin mawuyacin hali da aka amso a hannun waɗan nan miyagu ƙuru-ƙuru duk mun gansu. ALLAH dai ya ƙyauta, dama ba sabon abu bane irin wannan a ƙasarmu ta gado. idan kaga ana yayata mai laifi da cecekuce da tada jijiyar wuya ga jami'an tsaro to talakane ya aikatashi, amma idan su masu faɗa ajinne suka