Showing 270001 words to 273000 words out of 388641 words
gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za'a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.[1/2, 11:31 AM] HASNA✍🏻: Billyn Abdul:
Page 41
.................A firgice Mama Atika, Dad, Mom, Uncle Nasir, Uncle Uwaisu, Aamilah, Salman duk suka miƙe baki hangame. Uncle Sulaiman da Uncle Sadiq da basusan komaiba illa cewar ɗan fir'auna ya mutu suka bisu da kallo dansu basusan ɗan fir'aunan ba a zahiri har yanzun. Cikin tsananin firgici da suɓutar baki Mama Atika tace, “Nasiru ba kunce sheɗanin nan ya mutu ba wai?”. Rasa mai bata amsa akai a cikinsu.
Ƙyalƙyalewa da dariya ɗan-fir'auna yay irin ta asalin tsagerun nan da suka gama gawurta a fitsara, ya nuna Mama Atika yana tsuke fuskar tamkar ba shine ya gama dariyar ba, “Ke dai tsohuwarnan anyi ƴar buƙulu, to idanma na mutu ban kwashi garaba ashe kanwa na kawo duniya, koda yake ashefa shirya kasheni akai ko? To anyi tabanza dan shegen taurin raine dani zanyi dogon zamani fiye da naki, a nunamin inda matata take malamai”. Jikin Aamilah na rawa tace, “Brother ga shi nan”. Harara ya zabga mata, “K dan tsohuwarki waye Brother ɗin? Yayah zaki ringa cemin dan gyatuminki hausa zakimin, kujimin faratun banza mai suffar yahudawan farkon ƙarni”. “Kayi haƙuri dan ALLAH yaya bazan sakeba” tai magana tana komawa bayan Jay da yay kunnen uwar shegu dasu kamar baisan wainar da ake toyawaba ta maƙale, Jay wayama yake latsawa abinsa hankali kwance kamar baya wajen. Dariya ɗan-fir'auna ya sake kecewa da ita yana faɗin, “Kaji bayani, da kikace ke tsagerace? Hegiya nifa bar ganinki ƙanwar matata billahillazi jinake kamarfa nai miki eyane dan zaki bada kala a garin maji daɗi. Amma kinci arziƙin musulunci ba'a wannan haɗin. Oga bara na shige daga ciki duk da fa inajin nauyinka fuska kawai zanyi aradun ALLAH na siɗaɗa”. Yay maganar da wani ɗora hannu ɗaya kan ɗaya irin salon nan na gaisuwar gayu ga na gaba dasu. (ALLAH ya daidaita sahunka akan lokaci habibullah😂🤣)
Jawaad da baiko ɗagoba ya jinjina masa kai kawai yana cigaba da aikin latsa wayarsa. Sai da ɗan fir'auna ya shige ɗakin da Shahudah ke kwance sannan Jay ya ɗago yana kallon Dad da yay sagade kamar wani gunkin hanya yana kallon ƙofar, firgigit ya dawo hayyacinsa saboda bugo ƙofar da ɗan-fir'auna yayi da masifar ƙarfi.
Inda Jay yake ya nufa da sauri-sauri yana baza babbar riga, Muryarsa da zafi ya furta, “Inason muyi magana”. Kallonsa kawai Jay yayi baice komaiba, sai dai fuskarsa shima a haɗen take, da ya kai maƙurar da ayanzu zai ɗauki matakin da bai ɗaukaba ada akan kowa. Guntun Murmushi yay da miƙewa yana ɗan kallonsu Uncle Nasir da suka zubo musu idanu. Rai a ɓace Dady yace, “Jawaad!!....” saurin ɗaga masa hannu Jay yayi batare daya kallesa ba. “Karkai saurin harzuƙa, muje waje muyi maganar”. Ɗauke kai Dady yayi kamar bazai sake tankawa ba sai kuma miya tuna oho ya nufi ƙofar fita yana jiyo kukan Momy dake sukar masa zuciya. Tashi Jay yay shima ya fice baiko kalli inda ƴan gidan nasu sukeba balle ya nuna yaji ihun kukan Momy dana Mama Atika.
A can gefe inda babu mutane ya hango Dad nata kai kawo ransa a ƙololuwar ɓace, Jay yay ɗan murmushi ya ƙarisa. Kallonsa Dad yay ya ɗauke kansa, “Jawaad!! Tun muna ƴar kunyar juna ka saka wannan ɗan iskan yaron ya sakarmin yarinya ta”. Murmushi Jay yayi da tura hannunsa ɗaya aljihu ɗaya kuma ya shafi kumatunsa da gashin saje ke kwance kaɗan saboda yana askewa, “Miyasa kukai tunanin kashesa ne zai baku mafita domin farin cikin ƴarku?. Irin wannan raɗaɗin da kakeji a yanzun, ita kuka shiryama taji mafiyisa Dad, Miye dalilinku na janta jikinku bayan baƙwa buƙatar ta raɓu jininku?........”
Dady ya kallesa da ɓacin rai sosai ya katsesa da faɗin, “Ya ina maka magana akan Mamana kanamin wata banzar magana taka mara tushe?”. Haɗe fuska Jawaad yayi da tura ɗayan hannunsa aljihu cikin ƙoƙarin danne nasa fushin yace, “Banason mu bama juna wahala, dan inhar muka kai ga haka komaima zan bankaɗo babu ruwana, dan haka mu tsaya iya haka ɗin kamar zaifi sauƙi. Batun Hudah na riga na gama da wannan matsalar yanzu tsakanin kune ku da sirikinku. Lokaci yayi da zaku nuna gajiyawar da baƙwaso a gareta na bakomai zaku iya bata ba, ALLAH shike bada komai ga wanda yaso a lokacin da yaso ba mutum ma
i barci, mai mutuwa, mai mantuwa ba. Koda yake, wannan bashi bane matsalata. Minene Ya kai Qaseem China kuma?!”.
“Kai Jawaad!! Tsagerancin naka da su Alhaji Nasiru ke faɗa har yazo kaina nima kenan? Minene matsalarka ko alaƙarka kuma da barin Qaseem ƙasar nan?, Qaseem fa ɗanane, babu kuma wanda ya isa ya sakani koya hanani a kansa, itama bilkisun ba tsoro yasa na bar maka itaba dan inada ikon hanaka auren nata tunda ɗiyar ƴar uwa tace, a hannuna kuma ka ganta. Niba sa'an yinka bane, ka kama kanka kajiki”. Ya ƙare maganar da fara tafiya zai bar wajen.
Jay dake binsa da kallo yay murmushi, “Tabbas kanada iko da ita fiyema da hakan, kuma har gobe ita kallon uba take maka dan ta baka dukkan yarda kai da ahalinka, babu wani laifinku da take kallo laifi sai dai kuskure. Haka take komai nata irin na masu ƙyaƙyƙyawar zuciya ne, tana ƙyautatama kowa zato musamman wanda ya nuna tausayinta saboda a irin rayuwar data tsinci kanta ciki, Dady ka daina tunanin har yanzu al'amarin a rufe yake, na tanadi hanyoyi masu yawa dazan bankaɗo komai harda na Qaseem da kukai ƙoƙarin rufewa dan ina bibiyarsa kuka turasa China”.
Juyowa Dad yay daga tsayuwar da yay tun fara maganar Jay. Idanu suka zubama juna na kusan mintuna biyu kafin Dady yay wani murmushi yana girgiza kansa. Batare da yace komaiba ya juya ya tafi.
Da kallo kawai Jay ya bisa har ya shige, ya lumshe idanu da furzar da huci mai zafi daga bakinsa, batare da yay ƙoƙarin sake komawa cikiba ya nufi motarsa ya bar asibitin
A ciki kuwa tunda ɗan fir'auna ya shiga da maida ƙofar ya rufe babu wanda ya sake jin ɗuriyarsa balle sanin mi yayi a ciki har saida Dad ya koma ciki da kusan mintuna biyar sannan ya fito yana wani ɗan iskan washe baki kamar gonar audiga. tsayuwa yay ya gama kallesu a ɗage sannan ya wuce batare da yacema kowa komaiba, sai wani rangaji yake irin na tsageru tamkar wani bishiyar giginya.
Babu wanda ya iya cewa uffan dan har ransu tsoronsa sukeji, sai da ya kai ƙofa sai kuma ya juyi da sauri, “Af kunga nayi mantuwa zan wuce, Surukina inafa da magana da kai a ina zamu haɗu mu tattauna ta?”. Kafin Dad yay magana Uncle Sulaiman yace, “Haba yarona, hakan duk bai kamataba kaji, koba k.......” Da sauri ɗan-fir'auna ya katse Uncle Sulaiman cikin ɗaga masa hannu da faɗin, “Nifa ka ganninan duk tsagerancina ina girmama masu mutunci, kai Uncle ɗin Ogane mai daraja babba, dan ALLAH na roƙeka ka zama ɗan kallo, dan ko takalmin Oga bazan so na takaba balle kai Uncle ɗinsa”. Uncle Sulaiman ya jinjina kansa kawai batare daya ƙarasa abinda ya faroba, sai dai a ransa yana mamaki. Juyawa ɗan fir'auna yay yana faɗin, “Duk da ni mutumne mai kunya da baya son yawan shiga gidan surukai Zanzo gida na sameka surukina”.
Kallo kawai suka iya binsa dashi harya fice tamkar wasu wawaye babu wanda ya iya sake tanka masa.
___________________________
Ɓangaren su Bilkisu kam sunsha firarsu cike da nishaɗi kasancewar sun daɗe basu sami damar irin wannan haɗuwar ba, abincin da driver ya kawo daga gidan Ummah babba suka ci, dan Nabeelah ƙin biyosa tayi dan tazata Jawaad na gidan. Sai dai batasanma yana tafe zuwa gidan nasu ba, dan bayan sallar azhar can ya nufa. Tana falo zaune tana kumburin fushin Ummah tace taje tai kitso yay sallama. Ai da wani shegen gudu ta kwasa sai ɗakinta ta garƙame ƙofa. Hakan datai ya saka kowa fahimtar laifi tai masa.
Zama yay suka gaisa da Ummah tare da musu godiyar hidima da gajiyar taro, Aunty Batool ma ta gaidashi da tambayarsa bilkisu. Anan yaci abincin rana suka ɗan tattauna da Ummah akan abinda ke faruwa, kuka rurus Ummah keyi na farin ciki da al'ajabi, kai ita kanta tana mamakin irin yanda takejin Bilkisu har cikin jinin jikinta da ɓargo, san nan tana hango abubuwa da yawa dake mata kamanceceniya da jininta tattare da Bilkisun amma tarasa wacece?, wato jini ya wuce gaban wasa duk inda yake. Tace, “Jawaad bazan iya haƙuri ba gobe idan ALLAH ya kaimu zaka ganni a gidanku”. Murmushi Jay yayi, “To ai Ummah itama bata saniba, bamason ta san komai yanzun har sai mun bincika sauran
abinda ke faruwar tukunna, dan kinga al'amarin yazo da ruɗani a ciki”. Shiru Ummah tai na wasu sakanni, cikin sauke ajiyar zuciya tace, “Hakane kuma Jawaad, rashin faɗa matan yanzu yanada amfani, dan ko ƴan gidanku karmu bari su sani yanzun sai mun gama sanin komai mu kanmu”. Jay yace, “Insha ALLAHU Ummah bazasu sani ba”.
Baibar gidan Ummah ba sai kusan ƙarfe uku na rana. Daga nan gida Ummah ƙarama yaje itama, itakam harma tafi Ummah Babba shiga ruɗani, saboda ita mutumce mai ƙarancin juriya akan farin ciki ko ɓacin rai, duk wanda ta tsinci kanta a ciki saika ganesa tattare da ita. itama dai ya jima anan suna tattaunawa, dan saida akai sallar la'asar sannan ya baro gidan.
Gida ya nufa dan a gajiye yake ga barci yanaji sosai cikin idanunsa. Dai-dai traffic light ta tsayar dashi idonsa ya hango masa ɓaleru cikin mota, wanda ke a bayan motar ya kalla ya ɗauke kansa, sai kuma yay saurin sake kallon motar. Abinda ya faɗo masa a raine ya sakashi saurin ɗaukar wayarsa ya shiga WhatsApp, saƙon gimba da har yanzu yana nan ya kunna, ya maimaita dai-dai inda gimba yake sanar masa sunan Alh...Alh..k......
Ganin an basu hanya ya harba motar gaba hankalinsa nakan motar su ɓalerun, gefen titi ya gangara yabi motar da kallo harta ɓacema ganinsa, a fili ya furta ‘Tabbas Alhaji Kokino Gimba kake nufi’ yay maganar da ɗan dukan sitiyarin motar yana cije lip ɗinsa na ƙasa da ƙarfi, kafin ya furzar da huci mai ƙarfi ya kife kansa a sitiyarin na kusan tsahon mintuna bakwai. Tabbas inhar tunaninsa nakan dai-dai matarnan ce, to minene alaƙarta da Gimba?. Bashi da mai bashi amsa, dan haka wayarsa ya ɗauka yay kira, bugu biyu kuwa aka ɗaga daga can cike da girmamawa. Bai tsaya sauraren gaisuwarba yace, “Hameed kana tare da ɓaleru ne yanzu haka?”. Daga can aka amsa masa da, “Yes Sir, ai da naga ma irin sabuwar motarka a traffic yanzu har na ɗauka kaine”. “Kaga manta da wannan, wa yake ja a motar?”. “Alhaji Sadi Kokino ne sir” “Ka tabbata shine?”. “Wlhy shine Sir”. Shiru Jay yayi yana murza goshinsa, ya sauke zazzafan numfashi da faɗin, “Amma kacemin Drivern Mr Gebrail ne ai?”. “Wlhy Sir tunda na fara aikin nan tare da shi nake ganinsa, ni kaina yau da naga ya ɗauki Alhaji Kokinon nasha mamaki, shiyyasa ban gazaba wajen bibiyarsu”. Sitiyari Jay ya sake daka da ƙarfi, “Hameed akwai matsala, kodai sun shirya bada ƙafane dama dankar a bibiyesu, kokuma sunada tabbacin akwai mai bibiyarsu, yanzu haka suna ina?”. “To Sir nikam ka sakani a ruɗani, amma gamu a anguwar Sanni zasu shiga wani gida mai farin gate”. “Maza kabar wajennan Hameed, kuma duk abinda ka gani bai makaba ka tabbatar ka kirani, gobe idan ALLAH ya kaimu kazo ka sameni a A.Y street”. Cikin mamakin da babu damar tambaya Hameed yace, “Okey Sire”. Yanke wayar Jay yayi ya maida akalar kiran ga Jabeer, yana ɗagawa shima bai saurari tsokanar da yake masaba ta ango ango yace, “Jabeer kuna Office ne?”. “Eh muna Office, lafiya naji muryarka haka?”. “Jabeer inason yanzun nan ku bincikamin Number da Gimba yay wayar ƙarshe da ita a randa aka ɗaukesa, a ina mai ita yake yanzu haka? Sannan macece ko namiji?”. “Okey boss ina zuwa”. Yanke kiran Jawaad yayi ya tada motarsa yabar wajen, kansa tsaye tashar da ake hawan motar garin su Gimba ya nufa. Nesa da wajen yay fakin tare da kiran Dattijon nan a waya. Mintuna uku kuwa basu cikaba sai gashi. Motar ya buɗe masa ya shiga sannan ya maida ya rufe. Saida suka gaisa Jay yace, “Ka tabbatar yarinyarnan tana mana aikin da muke buƙata?” “Sosai kuwa Alhaji, ai itama kanta batasan aiki take manaba a kansa, yanzu haka ɗazun take sanarmin wai yau zasuje wani gidan dirama wani mawaƙi zaiyi wasa na musamman akan soyayyarsu da ɓalerun”. Murmushi Jay dake ɗan wasa da yatsun hannunsa saman sitiyari yayi, “Address ɗin wajen, sunan mawaƙin, time ɗin da zai shiga wajen da tashinsa?”. Dattijo yay ƴar dariya da faɗin, “Ai Alhaji kamar dama nasan zaka tambaya duk sai da na samo waɗanan amsoshin kaf, gasu a rubuce”. Amasar takardar Jay yayi yana jinjina kai, ya ciro kuɗi ya miƙa masa yana faɗin, “Ga cikon kuɗin aikinka nagode”. Baki a washe dattijo yac
e, “Nine da godiya ai Alhaji, ALLAH ya ƙara buɗi na alkairi, idan wani aikinma ya taso wlhy a kawo zanyi”. Jawaad baice komaiba sai murmushi kawai.
Dattijo na fita kiran Jabeer na shigowa, ɗagawa yay yasa a kunne batare da yayi magana ba. Daga can Jabeer yace, “Tabbas Boss mace ce, sunan da tai register layin dashi shine Safara'u Hashimu, kakanta Bala, sunan mahaifiyarta Indo, kakaninta na wajen uwa Hassan da Baraka, shekarunta sittin da huɗu a duniya, asalinta ƴar garin Tsamiya ce, yanzu haka alama ta nuna ana amfani da layin a anguwar Habbun.........” Jay ya katsesa da faɗin, “Habbun kuma? Ba garin nan bafa kenan?”. “Kwarai hakane”. Baya Jay yay ya jingina da kujerar yana furzar da huci, kafin yace, “Hasashena ba dai-dai bane kenan?”. Daga can Jabeer yace, “Kai minene hasashen naka da?”. “Jabeer akwai wata mata lokacin case ɗin nan na Alhaji kokino mun haɗu da ita a gidansa idan baka mantaba itace ta taimakemu sosai har muka ɗauke mata yaro mai suna Yazeed, da ina zargin itace Gimba ke magana a gidan Alhajin nan da bai ƙarisa faɗaba”. “Tabbas Boss hasashenka ba kuskure bane, tun a wancan lokacin naso nace muku kodai Alhaji Kokino Gimba ke nufi, dan na taɓa ganinsa a ƙofar gidan farkon fara maka aiki lokacin bikinmu da Surayya, kasan matar Alhaji kokino ƙanwar maman tace, yanzu abinda za'ai shine kabani daga nan zuwa safiya insha ALLAHU zan bincika komai”. “Okey babu damuwa, shima yaron nan yau insha ALLAHU zan kamashi dan na kula akwai wani abu damu bamu saniba”. “A'a haba boss, ka bari wani a cikinmu ya kamashi mana, karka shigarma Mami lokacinta, amma mika hasaso mana”. “Da kaina zan kamashi Jabeer, dan akwai saƙon da nakeson bari a kamun nasa, abinda na hasaso kuma sai mun haɗu zamu tattauna”. Ya kashe ƙittt batare da ya jira amsar Jabeer ɗinba.
Wayar Bilkisu ya kira, sai da ta kusa tsinkewa ta ɗaga dan bata kawo a ranta shi bane, ba Number data sani bace. Shiru tai taƙi magana, dan haka shi yay sallama. Yanda ta amsa sallamar ne yasashi fahimtar ta gane wanene yanzun, zamansa ya gyara da ƙoƙarin dai-daita muryarsa dake cike da ɓacin rai, “Am sorry kicema ƙawayenki suje kawai zan haɗu dasu zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu, wani uziri yane ya riƙeni gaba ɗaya shiyyasa ban dawo ba”. Murya a sanyaye bily tace, “To zan faɗa musu, amma bakaci abinciba fa, haka kake yawo da yunwa?”. Idanun Jawaad ya lumshe yana murmushi, ji yay duk ɓacin ran da ya tarar masa a ƙirji yana guduwa, yace, “Karki damu da anyi magriba zan dawo isha ALLAH, jin muryarki kawai tasa nama ƙoshi, ke dai ki shirya amsar angonki kawai ƙanwar Jay.......” ƙittt ta yanke wayar daga can.
Jawaad ya girgiza kansa yana murmushi har kumatunsa na loɓawa, motar ya tada yay gaba har lokacin murmushi ya gaza barin fuskarsa.
___________________________
Tunda su Zuhrah suka wuce sai naji gidan duk babu daɗi, ga wani motse-motse da naketa famanji amma narasa takamaimai a ina nake jinsan, nai jarumtar dakewa dan bana son na ruɗar da kaina, sai kuma na koma ganin tamkar gittawar inuwoyi ta jikin Windows, da farko dai naso fita na leƙa waje, sai kuma wata zuciya ta gargaɗeni dayin hakan, yanda kaina ya farayin nauyine yasa na jawo wayata na kunna karatun Al-Qur'ani mai girma, a hankali nutsuwa ta fara saukarmin, naji kaina ya saki na koma normal, gidan kuma yay wani irin yin tsitt mai ban mamaki, babu motsin nan sam, ko ƙarar na'urorin dake aiki da wutar dake a kwai duk bakajin ƙararsu, ban ɗauki hakan komaiba na cigaba da zama a falon har aka fara kiraye-kirayen sallar magriba, Miƙewa nai da shirin sake wanka, dan ɗazun lokacin sallar azhar da zanyi salla ganin ɗingon jini yasa banyi ba, amma yanzu dana duba gab da su Ummie zasu wuce kuma ya sake ɗaukewa, dama nasan ɗazun nayi gaggawar yin wanka dan ƙa'idane sai bayan sallar azhar nake wanka ko la'asar duk da lokaci kan ɗan canja min wani watan.
Wayar na ɗauka na shige bedroom, Kayan da zan saka na fara cirowa a drawer na ajiye, dan waɗan nan dazan cire ɗin jini yaɗan ɗiga a sket ɗin kaɗan sai yanzu na kula ma. Batare dana kashe karatunba nabar wayar a saman gado na cire
kayan na shiga bayin, ban jimaba na fito gudun kar