Showing 267001 words to 270000 words out of 388641 words

Chapter 90 - KWAI CIKIN KAYA

10 Sep 2025

20691

nai da yawaba amma fuskata tayi fayau, na saka ƙaramar sarka sannan na feshe jikina da turare sosai, kowa ya ganni yaga amarya da gaske, farin gyale na ɗauka shima na saka turare sannan na yafa na fito falon. Gidan tsaf yake babu wani datti, hakan yasa kawai na ɗauki fresheners da turare mai ƙamshi haɗin gida na fesa iya falon nan kawai. Ina cikin fesawar ya fito.
Jin Motsinsa a bayana ya sakani waigawa, kwalliyar tasa ta sakani shagala a kallonsa batare dana fargaba, shaddace ƴar ubansu golden color ya saka, sai maiƙo take da ɗaukar ido, ta samu nutsatstsen ɗinki na zamani da ya fiddo cikar zatinsa mai tabbatar dashi jinin hausawan usul harda su hula......
Saukar iskar da naji a cikin idanuna da ƙamshi Mouth freshener ɗin da ya saka ya sani dawowa hayyacina daga sakin layin da nayi, nai ƙasa da kaina dan naji kunya.
“Gulmammiya kinaso kina kaiwa kasuwa, na miki ƙyaune?”.
Ɗan kallonsa nai na juya ƙeya nace, “Kaɗan”. Murmushi ya saki har inajin sautinsa, ya ɗaura hannunsa saman haɓata ya maido fuskata inda yake, “In har da gaske kike ki kaleni cikin ido kice kaɗan nai ƙyau”. Hannu nasa na rufe fusa da sake juya masa baya ina murmushi. “Baki da gaskiya kenan”. Yay maganar kusa da kunnena yana zame gyalen dana yafa. “Malama niba surukinki bane ai, muje kiga gidanki”.
Shine yaymin rakkiya lungu da saƙo na cikin gidan har ɗakinsa da harabar gidan, gaba ɗaya gidan ya canjamin tamkar ba wanda na taɓa zuwa ɗin nanba, an gyarashi sosai ya canja kamanni. Sai da muka gama zagaye ko ina muka yada zango a wajen cin abinci. Nidai kasa sakewa nai naci saboda yanda yay mugun tsatstsareni da idanu, duk sanda zan ɗago sai naga idonsa a kaina. Da dai na gaji saina kumbura masa fuska, “Nifa wlhy ba television bace ba”. Bakinsa ya taɓe baice dani komaiba bai kuma bar kallon nawaba har muka gama. Ɗakinsa ya koma nikuma na tattarr wajen, na fito masa da abincin maigadi da tunkan mu fara cin namu ya sakani na zuba shima ya fito, agogonsa da links ya miƙomin tare da miƙamin hannunsa. Dukda inajin kunya haka na saka masa links ɗin sannan na saka masa agogon. “Thanks” ya faɗa a hankali yana ɗagemin gira ɗaya.
Kafin nace wani abu maigadi ya doka sallama a ƙofa, kallon ƙofar mukai gaba ɗaya amma shi ya amsa masa, ya amshi kular hannuna tare da nufar ƙofar ya buɗe.
Maigadi ya gaidasa da faɗin, “Alhaji kanada baƙone”. Da ɗan mamaki Jawaad yace, “baƙo kuma malam gambo?”. “Eh Alhaji, harzan masa ƙaryar baka tashiba saina fahimci amatse yake da son ganinka gaskiya, kuma kamar baƙon mai muhimmanci ne”. “Okey, to ga abincinka ina zuwa”. Amsar kular yay dayi godiya ya koma, Jay kuma ya maida ƙofar ya rufe ya dawo inda yabar Bily tsaye tana kallonsu. Wuceta yay ya ɗauka key ɗin motar dake kan centre table, “Bara naje na gaida Alhaji Babba daga nan na leƙa asibi wai Hudah aka kwantar”. “Ya salam” na faɗa cikin damuwa, “Miya sameta kuma? Dan ALLAH kaje dani”. Kaɗan ya kalleni ya ɗauke kansa, “Kimata addu'a daga nan ya isa, kokin taɓa ganin amarya ta fita”. Cikin shagwaɓar da bansan inada itaba nace, “Toni tsoro nakeji wlhy”. “Tsoro kuma?” ya faɗa yana kallona. kaina na ɗaga masa batare dana yarda mun haɗa ido ba. Jin yaƙi magana yasa na sake kallonsa, sai naga niɗin yake kallo ashe shima. “ALLAH na kula kinma rainani” yay maganar yana matsoni, baya nai saurin ja, amma duk da haka saida ya riƙoni. Cikin magana raɗa-raɗa yace, “Ke komai abin tsorone a wajenki halan?”. Nace, “To inason naje naga aunty Shahudah ne”. “Uhhyim shine zakimin ƙarya? to babu inda zakije, ki jira ƙawayenki na nan zuwa zan dawo bazan jimaba dan zanyi magana da ku”. Saurin kallonsa nai da mamaki nace, “Su Ummie?”. Kansa ya ɗagamin. “Miya faru?”. “dan na dawo zakiji ai, ana jirana yanzun”. Ya ƙare maganar da ɗaura bakinsa saman nawa babu zato. ‘Ya salam’ na ambata a zuciyata tsigar jikina na tashi ga yanayin da nakeji na neman tasomin dukda dai yanzuma da sauƙi sosai ba kamar da ba. Sai da yaja kusan minti biyu kafin ya saki bakin ya sumbaci goshina. “Saina dawo”. Kaina kawai na jinjina masa dan na kasa kallonsa. A hankali na furta, ”ALLAH ya tsare”. Inajin yana murmushi. Nidai ban kallesanba har ya fice.
Sassanyar ajiyar zuciya na sauke tare zubewa a kujera daɓar na dafe kaina, wlhy abun mamaki yake ban, boss fa! Kai rayuwa bata rabo da abubuwan al'ajabi. Naja kusan mintuna biyar a haka kafin na miƙe naje ɗakinsa dan na gyara. Sosai ɗakin yake ƙamshin turarensa daya fesa yanzun, tsaf na gyarashi na saka fresheners sannan na koma kicin na ɗauraye kwankina da mukaci abinci shima naɗan gyara abinda bai minba.


Koda Jawaad ya fito sai ya iske baƙonsa cikin rumfar bunun dake harabar gidan maigadi ya kawosa, ƙarasawa yay yana faɗin, “Ai bammayi tunanin kai bane Munkaila”. Baƙo mai suna Munkaila daya miƙe domin girmamawa ga Jay yay murmushi, “Nine wlhy Oga barka da fitowa”. “Yauwa sannunka da zuwa” Jay ya faɗa yana zama tare da masa nuni daya zauna shima. Cikin girmamawa Munkaila ya gaishe da Jay kasancewarsa ogansa, file ɗin gabansa ya miƙa masa yana faɗin, “Oga dukkan abinda kake buƙata gashi, harma da abinda bakaceba dukna haɗo maka”. Kai Jay ya jinjina masa da faɗi, “Sannu da ƙoƙari” yana buɗe file ɗin. Da hotuna ya fara cin karo waɗanda sukai masifar ɗaure kansa dan harda Alhaji baba tare da mata biyu wadda ɗaya a ciki takasance kakarsace mahaifiyar su Ummah da shima a hoto ya santa, kallon Munkaila yay kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya maida file ɗin ya rufe.
Munkaila yace, “Oga akwai matsala ne?”. Kai Jay ya girgiza masa, “Babu matsalan komai, yaya maganar wancan aikin?”. “Shima ina gab da kammalawa oga, saboda naga ka matsu da wannan ma shiyyasa na dakata da wancan”. “Shikenan kayi ƙoƙari shima ka haɗamin shi a satin nan, ga wannan ka saka mai nima nayi aljihun nawa yay ƙasa”. Godiya Munkaila yayi sosai sannan suka fito a rumfar. Jay ya shiga mota shikuma ya fice dan mashin ɗinsa na daga waje bai shigo da shiba.
★★★★★
Fitar jawad babu jimawa su Ummie suka isa gidan amarya Bilkisu, Ummie, Zuhrah, Rebecca, Nazifa. Duk da jiya suka rabu da juna tuni suka haukace da ihun murnar ganin juna, suka saka bily tsakkiya da tsokana kala-kala, tun tana musu shiru dai harta koma ramawa itama dan taga shirun nata bazai sa su barta ba.
_________________________
Asibiti yay niyyar fara zuwa saboda Uncle Sulaiman daya tilasta masa yaje, to amma wannan bayanan da Munkaila ya kawo masa yanzun sun ruguza komai, burinsa kawai ya dangane da gidan Alhaji Babba. A waje yay fakin motarsa ya shiga shi kaɗai, Alhaji babba na zaune a falo hannunsa riƙe da Jarida Jay ya shiga da sallama. Ɗagowa yay yana kallonsa fuska ɗauke da murmushi, cikin tsokana yace, “A lallai wannan angon da gaske bahausa ya aura, ashe ba gidan jiya ya komaba”. Jay dake murmushi ya girgiza kai kawai yana zama, “Wannan itace tarbar da zakamin ma na baro matata na taho ganinka da farar safiyar nan”. Alhaji babba yay dariya irin tasu ta manya yana faɗin, “Ja'iri kenan bakifa ya buɗe”. Gaidashi Jay yayi yana murmushin tsokanar da kakan nasa ke masa. Sai da suka kammala gaisuwar da tambayar lafiyar juna da amarya Bilkisu kafin jay ya buɗe file ɗin da Munkaila ya kawo masa, hotunan ciki ya fiddo gaba ɗaya ya miƙama Alhaji Babba shi kuma ya maida hankali ga duba bayanan cikin file ɗin.
“Sa'adatu! kuma?”. Alhaji babba ya faɗa da alamun bazata. Kallonsa Jay yayi amma baice komaiba. Alhaji babba yace, “Jawaad kana nufin matarka nada alaƙa da wannan ta hoton?”. Zama Jawaad ya gyara sosai yana maida dukkan hankalinsa ga kakan nasa, “Baba abinda bincike ya nuna min kenan, sai dai nima kaina a kulle yake musamman da ganin hotonka a tsakkiyar mata biyu bayan mata ɗaya nasan kanada ita kafin Mama Maryam”. Shiru Alhaji babba yay na wasu mintuna kafin ya sauke ajiyar zuciya, yace, “minene sunan mahaifin nata?”. “Adam makaho” Jay ya bashi amsa a taƙaice. Nanma shiru Alhaji babba yay na wani ɗan lokaci yanata faman jinjina kai da murmushi a fuskarsa kafin yace, “Abin akwai ɗaure kai da ban al'ajabi”. Jawaad yace, “Miyasa zai ɗaure maka kai bayan na fahimci kasan wani abu”. Murmushi Alhaji babba yayi mai ciwo da sake maida hankalinsa ga hotunan guda biyar, ɗaya shine da mata biyu a jiki sai jaririn yaro da alamu suka nuna ranar sunansa aka ɗauki hoton ma ƙila, ɗaya kuma matane da miji matar gurguwa sai mijin da alamu suka nuna makaho ne, sai hoto na uku jaririyace nannaɗe cikin farin showal da gani kaga sabuwar haihuwa, hoto na huɗu, mata da minjin nan ne da jaririyar, na ƙarshema dai mata da mijinne sai bilkisu a tsakkiyarsu da bazata wuce shekaru goma sha biyarba. Ya ajiye hotunan yana kallon Jawaad da ƙyau. “Akwai abinda ku baku saniba Jawaad, mahaifiyarka cema kawai zata iya sanin wani abu itama ba duka ba dan a labari ta sani. Ba Amina da Maryam kawai na taɓa aureba, na taɓa auren wata matar mai suna Sa'adatu. Kafin aurena da Amina Sa'adatu itace yarinyar da naso aura dan itace muke soyayya amma iyayena suka ƙi, bakomai ne ya sakasu ƙinba sai kasancewar Sa'adatu batajin magana, duk da yarinyace da bata wuce shekaru goma sha biyarba a lokacin mutane kan jefeta da kalmar ƙarancin tarbiyya, Sa'adatu ta tashi a gidansu bata da uwa a hannun kakarta ta tashi, hakan yasa ta tashi sangartacciya da batajin ƙwaɓa, a dalilin ɗan karatun da aka sakata na boko wanda a wancan lokacin iyakamu maza kawai keyinsa yasa idanunta buɗewa dan ita kaɗaice mace a cikinmu, Sa'adatu ji take tafi kowa a ƴammatan yankinmu dama gata ƴar gata kuma babanta shine maigari, ALLAH ya jarabceni da sonta fiye da yanda kake tunani har takai naima iyayena maganar aurenta. Amma sai mahaiyata tace sam batasan wannan zanceba tama rigada tamin mata Amina, na ɗaga hankalina matuƙa a lokacin amma dole na haƙura muka rabu da Sa'a ina kuka tanayi. Hakan ya zafi kakarta har tayi alwashin sai nayi nadamar yaudarar jikarta da nayi. Babu wanda ya ɗauki alwashinta wani abu aka ɗauramin aure da Amina ta tare. Banason Amina amma ita tana sona kuma mace ce mai haƙuri da kawaici, a zamanmu tasha wahala kafin na ɗan fara fuskantarta, aurenmu da Amina yakai shekara shida amma bata taɓa ko ɓariba, a wancan lokacin dan mace takai shekara goma ma bata haihuba babu mai damuwa da hakan balle ya zama abin magana shiyyasa nima ban taɓa damuwaba. Zuwa lokacin Sa'a itama tayi aure amma ba a wannan garin namu ba, wani ɗan uwanta mai kuɗi aka aura mata, sai dai kuma hankalinta na kaina dan haka shekararta uku ta kashe auren ta fito da yarinyarta guda safara'u, a lokacinfa na tsaya kai da fata saina auri Sa'a dan sonta na nan daram a raina. Zakasha mamaki idan nace maka Amina itace taita kai kawo ga iyayena har mahaifiyata ta amince na auri Sa'a. A farkon shigowar Sa'a gidana ta kwantar da kanta tanama Amina biyayya kamar gaske, amma tunda muka wayi gari ta samu ciki sai abubuwa suka fara canja salo, raini da wulaƙanci babu wanda take ragewa bataima Amina shi ba a bayan idona, amma a gabana babu abinda ya sauya na ladabin da take mata da. Sam ban fahimci zaman kisan mummuƙen da akeyi a gidana ba dan Amina ko a fuska bata taɓa nunaminba har ALLAH ya sauki Sa'a lafiya ta haifi ɗa namiji wanda yaci sunan kakana Adamu. Bayan haihuwar Adamu ne na fara fuskantar akwai matsala a zaman nasu, dan wataran na shigo a bazata na iske Sa'a nama Amina gorin haihuwa. Ranar nayi tamkar bansan Sa'a ba saboda biji-biji nai mata tare da dogon gargaɗi na saki ɗaya. Kamar Sa'a ta nutsu bayan wani lokaci saita dawo da halinta na rashin arziƙi har ƙawaye take kawowa suna haɗuwa cin zarafin Amina. Cikin amincin ALLAH Sa'a bata yaye Adamu ba saiga Amina da ciki. Munyi murna sosai fiye da zato, ganin Amina itama ta samu cikin da ake mata gori sai Sa'a ta sake sabon salon iskanci, Amina dai bata kulata dan ta bama banza ajiyartane. Cikin ikon ALLAH itama cikinta yakai haihuwa ta haifi mace wadda taci suna Bilkisu (mamanka kenan) dariya Sa'a taitayi alokacin da faɗin ai dai itace a sama tunda namiji gareta, Amina dai bata kulatan, bata yaye Bilkisu ba sai ga wani ciki, Sa'a kuma shiru, hankalin Sa'a ya kuma tashi ainun da wannan ciki na Amina harta sake haihuwa bata barta ta hutaba, a wannan haihuwarma dai mace ta samu itace Wasila (Ummah babba). dukda Sa'a ta nuna bata damuba tunda Amina mace ta sake haihuwa saita kasa daurewa, tashiga ƙananun magana Amina tai mata asiri haihuwarta ta tsaya, tun ina tsawatarwa har al'amari yafi ƙarfina na saki Sa'a saki biyu ya zama uku dan al'amarinta ya isheni. Wannan saki yama dangina daɗi yama nata zafi dan dangina dama babu mai sonta sai ƙalilan a cikinsu. Nayi ƙoƙarin na amshi Adamu amma kakar Sa'a tace ban isaba, duk hanyar data dace nabi suka hanani ɗana, acewarsu kishiya bazata riƙe musu yaroba wataran ta kashesa. Rabuwarmu da Sa'a da shekara guda Amina ta sake haihuwar mace dai again, wadda taci sunan Rahamah (ɗiyar Alhaji babba wadda ta rasu) haihuwar Rahama babu jimawa kakar Sa'a ta rasu, alokacinne na shirya amshe yarona dan banaso ya tashi da kalar tarbiyyar gidansu, sai dai a randa naje nai magana da mahaifinta washe gari aka nema Sa'a aka rasa ta gudu da Adamu. Neman duniya anyi babu wanda yaga Sa'a, munɗauki tsahon lokaci muna nemanta amma babu Sa'a babu labarinta. Har kuma ALLAH yayma Amina rasuwa ta barni da ƴaƴa huɗu duk mata ban sakejin ko labarin Sa'a ba balle yarona, kullum yana a raina, dan harda Maryam mun taɓa yin labarinsa”.
Ajiyar zuciya Jawaad ya sauke yana mai jinjina al'amarin a ransa, yace, “to Amma baba miya nisantaka da danginta harmu bamu taɓa saninsu ba ballema shi labarin Uncle ɗin? Tunda gashi dai alamu sun nuna shi Uncle ɗin ya dawo gida har yay aurema kenan ya haifi Miemaa”.
“Kasan na faɗa maka dama akwai damuwa tun hanani aurenta da akai a farko, sannan koda mukai aure danginta sunajin zafin mahaifiyata dani kaina, badanma sunso Sa'a ta dawo ta aureni ba, bayan guduwarta kuma sai abubuwa suka sake ƙwaɓewa suka ɗaura laifin akan Amina ce tai mata kurciya tabar gari saboda ita ƴaƴanta matane Adamu kuma namijine, dalilin wannan sheɗancin nasu nema yasa nayo nesa dasu na dawo nan dan lokacin garin bai haɗe ya zama babba ba gaba ɗaya kamar yanzun, ahankali abubuwa sukaita canjawa dangi makusanta sunata ƙarewa, shiyyasa kusancin namu ya sake taɓarɓarewa ma baki ɗaya tunda wanda za'aiyi dominsa babu shi tare dasu”.
Kai kawai Jawaad ke iya jinjinawa amma ya kasa magana, Alhaji babba ya katse shirun nasu da faɗin, “Duk da na daɗe banga Adamu ba tun yana yaro amma ƴarsa sai ta ɗakko kamanin Rahamah sosai musamman tana yarinya fiye da nasa kamannin, dan ni randa na farama ganinta a asibiti kamannin Rahamah na gani tattare da ita bana Adamu kawai ba, hikimar UBANGIJI kenan mai tsara yanda yaso a lokacin da yaso, Jawaad yanzu kenan Adamu baya raye?”. Cikin damuwa Jay ya jinjinama Alhaji babba kai, “Ta faɗamin mahaifinta ya rasu bayan rasuwar mamanta kusan shekara bakwai kenan ana cikin na takwas, kuma a yanda bayanai suka nunama kenan anan ɗin ya rasu, to amma abinda yama ɗauremin kai sufa danginsa ma suna nuna tamkar bashi da wata alaƙa da ɗiyar tasane fa, wannanne dalilin daya raunana zumincinsu ya dawo gefe yana rayuwarsa shi da matarsa kawai da yarinyar, kuma ko bayan rasuwarsa abinda yasa sukai watsi da ita kenan sai dai batasaniba ita”.
“Jawaad ban gane basu da alaƙa ba, duk wanda ya kalli matarka aiko yaga jinin Adamu ai”. “Gaskiya ne Baba, a hoton dai kam daka gani kasan jinsa ce, nima inason zuwa da kaina garesu naji miyasa suke nisantashi da abinda alamomi suka nuna nasa ne?”. “Bakai kaɗai zakajeba Jawaad, tare zamuje ai, dan nima ina buƙatar amsoshi da yawa a garesun”. Sun daɗe suna tattaunawa akan batun kafin jay yayma Alhaji babb sallama ya tafi asibiti.
★★★★★★
Tunda ya shiga asibitin sukai masa caa da idanu, shiko ya fuske abinsa fuska a ɗaure ya gaidasu da tambayar jikin Shahudah, kafin ya shiga ya dubata tana barci har yanzun, dan data farka suke sake mata wata allurar barcin tunda taƙi kwantar da hankalinta ta saurari kowa, ta dage sai an kira mata Jay.
fitowa yay daga ɗakin ya dawo wajensu da nufin yimusu sallama ya kama gabansa, amma sai mama Atika ta dubesa cikin gadara fuska babu wasa tace, “Mun gama magana da ƙannen ubanka yau bayan sallar azhar za'a maida aurenka da Sabira, kuma gobe idan ALLAH ya kaimu zata tare koda ba'a sallameta daga asibitin ba”.
Wani lallausan murmushi Jay ya saki da ya bama kowa al'ajab da mamaki, dan ba murmushin sukai tunanin gani daga garesa ba. Ya kalli mama Atika da ƙyau yana tura hannayensa cikin aljihun wandon shaddarsa da gyara tsaiwa yace, “Shi kuma mijinta yaya zakuyi dashi”. Yay maganar da maida kallonsa ga ƙofar shigowa.
Gaba ɗaya suka maida kallonsu ga ƙofar inda ɗan-fir'auna ke tsaye akan ƙafafunsa ya warke sarai sai tabbunan raunikan da yaji waɗanda basu gama bajewa da ƙyauba.............✍
(Kana basu pepe da ginger ɗan bilkisu da Abdul-Aziz mijin bilkisu🤣😂🚴🏼)

______________________
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI...
GUDU DA WAIWAYE....
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login