Showing 150001 words to 153000 words out of 388641 words

Chapter 51 - KWAI CIKIN KAYA

10 Sep 2025

20729

wuce nacin kawai kodan ya barni na tafi, na ɗauki cinya nakai bakina ina ambatar bismilla, ɗanɗanon naman da laushinsa ya sakani lumshe idanuna, ko ba'a faɗaba dama namannan zaiyi ɗankaren daɗi ai, ban ankaraba na laƙume cinyar na sake ɗaukar wata tsoka irin ta haƙarƙarinan, (Damafa inaso shegen gulma ne. Lol) ina gab da cinyeta aka turo ƙofar da azabar ƙarfi aka shigo, a tsananin razane da ganin wanda ya shigo ɗinne ya sakani miƙewa babu shiri ina kallonsa. Shima idanunsa ya zubamin tamkar zai cinyeni da su.
         “Ubanmi kikeyi nan Bilkisu?!!”
Idanuna na lumshe saboda tsawar tashi ta rasha kunnuwana, na buɗe a hankali kansa, cike da dakiya na zubasu a kansa nace, “Yah Qaseem miya faru?”.
       Wata malalaciyar harara ya zubamin kamar zai juye idanunsa ƙasa, ya fara takowa inda nake, taku baifi ukuba tsakaninmu ya rage aka buɗe ƙofar office ɗin aka shigo. Ni da shi duk kallon ƙofar mukai, sai dai shi a take ya janye nasa idon yana jan uban tsaki. Nikam numfashi na sauke a ɓoye dan koba komai na samu kuɓuta daga wannan yunƙurin na yah Qaseem da bansan mi zuciyarsa ke kissima masa yaminba.
         Jay da ya shigo kuwa kallo ɗaya yay musu ya ɗauke kansa ya taka zuwa ga kujerarsa ya zauna.
       A mamakina sai naga yama cigaba da daƙilar Keyboard ɗin Computer ɗin hankalinsa kwance kamar baisan damuba. Shima yah Qaseem ɗin bai tanka masaba ya kalleni yace, “Wuce muje”.
     Jawaad daketa danne-dannensa batare daya ɗagoba yace, “Kai ka kawotane?”. Dogon tsaki yah Qaseem yaja yana damƙar hannuna da faɗin, “Miye na azarɓaɓi ƙaramin tsagera, ai zan dawo kanka idan na gama da ita”. Ya ƙare maganar da fisgar hannuna muka nufi ƙofa. Jinake tamkar na kurma ihu, ‘Nikuma wannan wace fitinace na shigo ciki haka?’..........
      “Wlhy kika fita daga office ɗinan saina saɓa miki kamanninki!”
      Muka tsinkayo kakkausan furucin boss yayinda yah Qaseem ya murɗa ƙofar zamu fice. Bani kaɗaiba hatta da yah Qaseem ɗinma tsayawa daga yunƙurin fitar yay, ya juya yana kallonsa, nidai kaina a ƙasa na gaza kallon kowa a cikinsu, addu'ar ALLAH ya kuɓtar dani daga tsakaninsu kawai nakeyi a raina, dan bansan wazan bijiremawaba? Wakuma zanma biyayya ba?. Yarfar da hannuna yah Qaseem yay ya nufesa, zafin da najine ya sakani durƙushewa a wajen ina sakin siririyar ƙarar azaba.
      Qaseem daya ƙarisa gaban Jawaad ya bugi tebir ɗin gabansa har wasu abubuwan na faɗuwa, “A matsayinka na ubanwa zaka saɓa mata kamannin?”. Ko motsi Jawaad baiyiba balle ya kalli Qaseem, aikin gabansa kawai ya cigaba dayi hankalinsa kwance. A kausashe Qaseem ya sake maimaita tambayar tamkar zai mari Jay ɗin. Ɗago idanu Jawaad yay ya zubasu akan Qaseem, cike da gadara yace, “Qaseem fitarmin daga office!!”.
     “Anƙi a fita, kayi duk abinda kaga zaka iyayi” Qaseem ya maida masa amsa a zafafe shima.
     Jawaad bai sake magana ba, ya miƙe ya nufi Bilkisu dake durƙushe tana hawaye saboda hannunta dake zugi.
     
        Tsayuwar mutum kawai naji a kaina, cikin bada umarni yace, “Tashi”. Miƙewa nai babu musu, na saci kallonsa, ganin shima kallon nawa yakene yasa na janye nawa ina goge fuska, kafin ya sake wata magana yah Qaseem yazo ya shiga tsakkiyarmu, ”Wuce muje” ya faɗa yana nunamin hanya, haushin murɗamin hannu da yayne yasa naƙi motsawa. Ganin naƙi motsawarne ya sake hasalashi ya

ɗaga hannu zai saukemin mari.
         Rufe idona nai da sauri naja baya saboda masifar firgita da nai da ihun da yaymin akai, na ƙanƙame jikina ganin ya ɗaga hannu zai makeni, shirun da naji yasani ɗago kaina kaɗan naga miya hanashi dukan nawa da yay niyya.. Saurin waro idanu nai waje ganin boss riƙe da hannun Yah Qaseem da ya ƙara kumbura sai hura dogon hancinsa yake.
       “kika fita saina karyaki a office ɗinan Miemaa” boss yay magana a dake  kamar yanda na fahimci halittarsace yin magana kai tsaye koda a gaban wa yake. Saurin duƙar da kaina nai saboda tsatstsareni da yay da idanu, nai baya daga kusa dasu cike da tashin hankalin sakani tsakkiya da sukai.
        yah Qaseem ya fisge hannunsa dake cikin na boss ya kai hannu zai damƙoni ina ƙoƙarin matsawa. Cikin matuƙar zafin nama boss ya fisgi yah Qaseem ɗin gefe, hakan sai ya bani damar mannewa a bango na sake musu kuka kawai, dan zuciyata bazata iya ɗauka ba.

          A cikin tsagwaron fushi Qaseem ya damƙi wuyan rigar Jawaad zai shaƙeshi, “Amma kasan zan iya illataka ko?”.
     Murmushi Jawaad yayi yasa hannu ya ture hannun Qaseem dake damƙe da wuyansa, cikin halin ko in kula yace, “Ka illatanin mana Qaseem, kai wai wace irin banzar zuciyane da kai haka? Mace zaka ɗaga hannu ka daka?”. A matuƙar masife Qaseem yace, “ina ruwanka? Miye matsalarka?” baki Jawaad ya taɓe yana watsa hannayensa da ɗage kafaɗa yace, “Banda” ya ƙare maganar da juyawa zai koma kujerarsa. Saurin maidoshi baya Qaseem yay, hakan ya saka Jawaad tsayawa sai dai bai juyo ya kalli Qaseem ɗinba, ƙoƙarin danne zuciyarsa yake dan bayaso su raba hali gaban yarinyarnan kamar yanda ya kula Qaseem yana buƙata. Cikin nunashi da ɗanyatsa Qaseem yace, “Wannan ya zama na farko kuma na ƙarshe da zaka sake saka Bilkisu! cikin lamarinka, itaɗin matar dazan aurace, ya rage naka ka kiyayi ko kaci gaba”.
       Rumtse idanu Jawaad yayi saboda jin yanda Qaseem ya ambaci sunan mahaifiyarsa gatsal, ya juyo a hankali yana kallon Qaseem cikin ido, cikin ƙunar zuciya yace, “Ko wacece ita a wajenka baya gabana, sai dai kai kasani baka isa hanani sakata aikin dana gadamaba tunda har tazo station ɗinnan a ƙasana, kasa a ranka yanzu aka fara wasan kuma, ina gargaɗinka Ka kiyayi  kai hannu kan mace da nufin duka”. ya ƙare maganar a wani irin yanayin rainin wayo. Hakan sai yay masifar sake fusata Qaseem, a tsawace yace, “Matsayinka na ubanwa?”..............✍
     

Qaseem team & Jawaad team banda faɗa kuma 🚴🏼🏋🏼🤼🏼😂😖.

Ina Bil-Qas team nidai😜🤫🤸🏼.

ALLAH ka gafartama iyayenmu🙏🏻
[11/30/2020, 1:01 PM] HASNA✍🏻: Typing📲

ƘWAI cikin ƘAYA!!

Bilyn Abdull ce🤙🏻

BOOK TWO

Page 9
............A matsayinka na ubanwa?” cewar Qaseem a fusace.
Cike da rainin wayo Jay yace, “Lokacine zai nuna maka”.
Jabeer da ya shigo office ɗin kusan mintuna biyar da suka shuɗe, amma jaraba ta hanasu ganinsa yay gyaran murya.
Duk kallon ƙofar mukai, Cikin nuna alamun tamkar baima fahimci mike faruwa a office ɗinba ya kalleni tare da miƙamin kwalin dake a hannunsa, “Momcyn mu kikai wannan Office ɗin MM; daga nan ki wuce ƙasa naga ana nemanki”.
Kaina na ɗaga da sauri, na amsa kwalin na fice ina mai godema ALLAH da zuwan oga Jabeer da yay belina hannun waɗanan zakunan.
Babu wanda yay magana tsakanin Jawaad da Qaseem ɗin har Bilkisu ta fita, Jabeer ya maida kallonsa kansu yana ɗan murmushi, “Haba basawanmu, ya zaku saka yarinya tsakkiya kuna yaƙi? Ai saiku rikitata, miye nata a ciki tunda batasan miye tsakaninku ba?, yakamata kumata adalci, aiki take kamar yanda kuke aiki, ku sakata abinda zaku sakata matsayinku na waɗanda suke sama da ita, amma bawai ku sakata tsakkiya akan abinda ke zukatanku ba”.
Juyowa Jay yayi, kamar zaiyi magana sai kuma ya girgiza kansa kawai ya juya yana mai ɗaura hannunsa a kafaɗar Qaseem ɗin yaɗan bubbuga kaɗan ya koma mazauninsa. Binsa da kallo Qaseem yay cike da takaici da baƙin ciki, a ransa yana rayama kansa inhar Jawaad yay gigin cigaba da kutse a al'amuran Bilkisu wlhy wannan karon sai ya karta masa rashin mutuncin da bazai taɓa mantawa da shiba har ƙarshen numfashinsa, yaja tsaki tare da harar Jabeer ya fice daga office ɗin..
Jabeer dake binsa da kallo ya girgiza kai kawai sannan ya juyo ga Jawaad da ya cigaba da harkar gabansa, ƙarasawa yay ya zauna yana ɗora wayarsa a tebirin Jay ɗin, “Boss dan ALLAH son yarinyarnan kakeyi ne?”.
A bazata maganar ta zoma Jawaad, dan haka babu shiri ya ɗago idanunsa da sukai sirkin jaa da ƙara girma ya watsama Jabeer ɗin wata uwar harara, sai kuma yaja tsaki ya maida kansa ƙasa.
Jabeer ya haɗiye dariyarsa yana gyara zamansa, “ALLAH ba wasa nakeba Jay, kuma idan hakan ta kasance wlhy zanyi murna, dan nutsuwar yarinyar na burgeni, g......”
“Motsoww! Jabeer banason shirme, wace irin banzar maganace wannan, Please banaso karka sake”.
Hannu Jabeer ya haɗe waje guda alamar ban haƙuri, Jawaad ya kuma hararsa ya ɗauke kai. Shidai Jabeer yay murmushi kawai, cikin son kauda zancen yace, “Yanzu nakeji su Sir Ahmad sun sake shiga meeting akan batunnan”.
Jawaad da kansa ke durƙushe yana aiki yace, “Basai suyi tayiba tunda basu da tunanin kansu sai abinda aka ɗorasu a kai”. Jabeer yace, “Wlhy Jay ni mamaki suke bani ma, saboda ALLAH maimakon subama yarinya ƙwarin gwiwa akan abinda ta fara sai kawai su ɓige da tsugunne-tsugune, kai yanzu mi kake tunani akan batun?”.
Kallonsa Jay yayi fuska a taɓe, sai kuma yaja tsaki ya maida kansa ga abinda yakeyi, “Tunanin mizanyi akan wannan shirmen Jabeer, iyakaci suce zasu dakatar da ita na wani lokaci ta huta, ko su canja mata wajen aiki ai dai ko? Tunda basu isa suce ta ajiye aikiba akan hakan”.
“To ai babu wanda ya kamata kabari ya kasance a ciki” cewar Jabeer yana kafe Jay da idanu.
Shiru Jawaad yay bai tankaba, tsahon mintuna biyu harma Jabeer ya fidda rai da samun amsa sai yaji yace, “Akanmi zan hana ni kuwa? A matsayina kuma nawa? Dukansu ogannina ne, suna sama dani nesa ba kusa ba, to mizan iya musu kona hanasu?”.
“Jay! Saboda ina ƙwaɗayin yarinyar ta shigo tawagarmu”.
“Humm” Jawaad ya faɗa a taƙaice.
Jabeer da ya fahimci amsar kenan sai ya cigaba da faɗin, “Ba ƙaramar nasara bace hakan a garemu Jay, dan inaji a raina zata ƙara kawomana nasarori, amma kadaiyi tunani akan hakan”.
Ƙin cewa komai Jawaad yayi, hakan yasa Jabeer sakin zancen shima ya ɗakko masa na aikin da suka fara yau kawai, ananne Jay ɗin kuma ya bashi dukkan attention ɗinsa suka shiga tattaunawa.
★★★★★★★
lna fitowa daga office ɗin MM naci karo da Ummie, bansan miyasa na tsinci kaina da gyara yanayinaba na sakar mata murmushi, hararata tayi ita kuwa tana fusgar hannuna mukai gaba. Masallaci muka nufa dan lokacin sallar zuhur yayi.
Bayan mun idar da sallane mun fito Ummie ke tambayata akan ina naje? Mi kuma ya sami kana?. Ban wani ja zancenba na bata labarin abinda zan iya, sai dai ban bata labarin miya faru tsakanina da yah Qaseem ba da kuma ceton da boss yay min a hannunsa yanzun.
Sosai naga mamaki a wajen Ummie tattare da labarin nawa, harna kasa haƙuri nai mata tambaya, tai ƴar dariya kawai da cewar, “Abunne da mamaki ALLAH, wannan mutum mai fuska kamar hadarin tsakkiyar damina ɗin?”.
“Ba abin mamaki bane Ummie, ni kawai na danganta lamarin da abinda ya farune ranar, ganina yake kamar wata jarumar gaske, baisan lamarin duk buge bane kawai” sosai Ummie ta kwashe da dariya cike da shaƙiyanci, nakai mata duka ta kauce tana cigaba da dariyarta, sai da tai mai isarta sannan ta dawo tana bani haƙuri muka shirya, daga haka muka cigaba da tsokanar junanmu da aikin dake gabanmu kuma.
Har lokacin tashi yayi ban sake saka boss da yah Qaseem a idanunaba, dama bai zama lallai na gansunba kasancewar bani da hurumin hakan sai idan sune sukaso, haɗuwarmu a inuwa ɗaya dama sai da ƙwaƙwƙwaran dalili. Haka kawai na tsinci kaina da tsoron bin yah Qaseem, sai kawai nabi Ummie ta saukeni a gida

★★★★★
Bayan sallar magriba ina zaune a saman abin salla ina azkar aka turo ƙofar ɗakina aka shigo, kaina na ɗaga ina kallonsa, yanda fuskarsa ke a tamke saida naji gabana ya faɗi, amma sai na dake abina nace, “Yah Qaseem ka dawo?”. Baice dani uffanba sai wata uwar harara daya makamin, ɗauke idona nai tamkar ban ganiba, ya ida shigowa cikin ɗakin yana bin ko ina da kallo, bakin gado ya ƙarasa ya zauna, hakan sai ya sakani jin wani iri, dan kuwa ni kaɗaice a gidan, koda na dawo ban iske kowa ba, su mom basu dawo daga gidan rasuwaba. A daƙile yace, “Waye ya maidoki gida?”.
Kaina tsaye nace, “Ummie ce, na jiraka naga baka fitoba gashi magrib ya gabato, sai kawai na biyota”.
Shiru yay tamkar bazaice komaiba, sai numfashi yake saukewa da sauri-sauri, hakan yasani tsira masa ido, “Yayah lafiya kuwa?”.
Wata harara ya sake danƙaramin kamar idonsa zai faɗo ƙasa, “Uwar miye haɗinki da shi Jawaad ɗin? Da har zaku fita tare? Ban miki Warning akansa ba?”.
Zamana na gyara sosai akan abin sallar saboda jin ƙafata ta fara yami, duk da na lura bawai maganar wasa yakeminba inata ƙoƙarin dakewa.
Bansan yanda zan bashi amsa ya fahimtaba, amma ni banajin kuskure nayi tunda akan aikine ai. “Dake nake magana Bilkisu!!”. Saurin kallonsa nayi danjin yanda yay maganar a kausashe, nace, “Aiki muka fita fa”.
“Aiki? Duk jami'an dake cikin Station ɗin babu wanda zai ɗauka suje aiki sai ke?”.
“Yayah ni wlhy ban saniba”.
Saida yasake watsamin harara dayin ƙwafa sannan yace, “Su kuma waɗannan kayan na jikinkifa da nagani ɗazun? Ina kayan da kika fita dasu daga gida da safe?”.
Kaina tsaye nace, “A wajen aiki da muka fita ne a mistake jikinmu ya ɓaci, to shinefa sai... Sai... Sa.........”
“Sai ubanmi? Bilkisu!!”.
“Sai Rose ta bani wasu kayan na zanja”.
“Harda ita kuka fita?” yay maganar cikin kakkafeni da idanu. “Eh” na bashi amsa cike da ƙwarin gwiwa.
Karon farko da yaymin murmushi, ya sakko daga saman gadon ya zauna kusa da ni sosai ya tanƙwashe ƙafafunsa (Dan zuciyarsa tayi sanyi jin basu kaɗai bane, amma hakan ba yana nufin zaiƙi saka musu ido bane ba). Yanda muka samu kusancine ya sakani matsawa baya kaɗan, baice komaiba, saima hannuna daya kamo cikin nashi, nai ƙoƙarin amshewa amma sai ya hanani damar yin hakan, murya a sanyaye yace, “Bilkisu!”.
Amsawa nai idona na kawo ƙwalla, dan banason kama hannuna da yayi......
“Kinsan kuwa yanda nake sonki da kishin ganin wani ya raɓeki?”. Shiru nai bance komaiba, shima bai jira amsata ba ya cigaba da faɗin, “Daga yau karna sake ganinki da Jawaad, idan kuma ba hakaba to lallai zan saɓa miki kuwa! Domin koba aurenki zanba yayankine ni, dolene na saka miki ido gudun karki lalace”.
Yanda ya ƙare maganar sai yaban dariya, a raina nace, ‘Kaima ka samu dama ai lalatanin zakai’, amma a fili sai, nace, “Yayah nifa banice naje wajensaba, bayan na fito daga kiran da akai minne mukai karo dashi a hanya, shi kuma ya fito daga office ɗinsa, shine yace na biyosa, da farko ma bansan dani yake ba sai da ya sake aikowa sannan, amma dan ALLAH kayi haƙuri”.
Murmushi yay min yana jinjina kai, yace, “Nasan dama ba laifinki bane, amma zan takama al'amarin birki tunkan yay nisa kinji, ina sonkine da yawa shiyyasa bazan juri ganinki da waniba ballema maƙiyina Bilkisu...”
Ya ƙare maganar a hankali yana matsowa jikina sosai, gabana ne ya shiga faɗuwa, nai ƙoƙarin ja da baya amma sai hakan ya gagara saboda riƙon da yaymin bana wasa bane, sannan ƙarfina da nasa ba ɗaya bane, matsananciyar rawa jikina na fara sabida ƙoƙarin kawo fuskarsa kan tawa da yake, na shiga girgiza masa kai ina hawaye, roƙonsa nakeson yi, bakina sai motsawa yake amma na kasa furta komai, ya riƙe kaina da ƙyau yana ƙoƙarin ɗora bakinsa kan nawa na ƙwalla ƙara.
Da sauri ya sakeni shima yaja baya saboda tsorata da ƙarata, jikina sai ɓari yake na tashi a guje na shige toilet ɗina na banko ƙofar harda murza key. ‘innalillahi wa inna ilaihirraji'un’ naketa ambata, wace irin masiface kuma wannan ni Bilkisu, kuka na shiga rusawa a bayin sosai, duk da inajin ƙwanƙwasa ƙofar da yaketa famanyi yana kiran sunana da bani haƙuri banko tankashiba, kusan mintuna talatin naji shiru alamar yabar wajen, ban buɗe ƙofarba har sannan sai bayan wani lokacin sannan na buɗe kaɗan na leƙa, babu kowa a ɗakin saima ƙofa dana gani buɗe alamar ya fita, komawa nai toilet ɗin na ɗauro alwala na fito, sai da na sakama ƙofar key kafin na tada sallar isha'i.
Haka nai kwanciyata da yunwa ban fitaba duk da inajin motsin su mom da suka dawo kusan ƙarfe goma, ina idar da sallar asuba nai shirin barin gidan, dan gwarama na shiga gidansu Amina daga baya sai na wuce wajen aikin, bazanbi yah Qaseem ba. Sauri-sauri na kammala na fito, gabana ya faɗi ganinsa zaune a falo yana shan shayi alamar dai shima harya gama shirinsa, yanda ya tsatstsareni da idanu kuma ya sakani tsayawa cak nai ƙasa da kaina, “Kizo kisha shayi mu wuce, dan sauri nake yau”.
Bance dashi komaiba na wuce zuwa kicin, kaɗan na haɗa tea a kofi na zauna a kicin ɗin ina sha, dan kuku ma bai kai ga fitowaba, saurin kallon ƙofar nai jin an shigo, nai masa kallo ɗaya na ɗauke kaina gefe, baice komaiba nima banceba, sai ajiye kofin da nai na nufi ƙofa, matsawa yay ya bani hanya, a ɗarare na raɓashi na fita yabi bayana.
Badan raina yaso ba na shigar motar Yah Qaseem yau ɗinnan, shiru motar babu mai cewa komai ni da shi, ko redio bai kunnaba, tuƙi yake a hankali kamar bayaso, mun ɗanyi nisa da gida ina lafe a jikin kujera da karanto addu'ar neman tsarin ALLAH daga shaiɗanin dake ingiza zuciyar yah Qaseem ga abinda bai daceba gareni naji motar kamar ta tsaya, idanuna dake cike da barci na buɗe, naɗan waigo na kalleshi, ganin ni yake kallo sai na janye idanuna ina sake gyara zama, wlhy bazan ɓoye mukuba a tsorace nake, bani da ƙarfin dazan kare kaina ga murɗaɗɗan namiji irin yah Qaseem koda ace yay shirin cutar da nine, cikin dauriyar dole nace, “Yah Qaseem lafiya muka tsaya?”.
Ajiyar zuciya ya sauke a hankali, har lokacin inajin idanunsa na yawo a kaina, sai dai baice komaiba, kusan mintuna biyu suka sake shuɗewa, a bazata na tsinkayi muryarsa, yace, “Kiyi haƙuri Bilkisu akan abinda ya faru jiya, banyi hakan da niyyaba tunda kinsha faɗamin baƙyaso”.
Ajiyar zuciya na sauke inajin daɗin kalamansa, na share hawayen da suka zubomin, ba tare dana kallesa ba nace, “Na haƙura Yah Qaseem, amma dan ALLAH ka


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login