Showing 171001 words to 174000 words out of 388641 words

Chapter 58 - KWAI CIKIN KAYA

10 Sep 2025

20682

kakansa dasu Umma, yadai samu waje ya zauna sannan ya gaidasu.
★★★★★★★
A LADIES MIRROR kuwa lokacin da abinda ID cards ɗin Bily suke ciki ya faɗi akan idon Safah ne, amma sai taƙi magana, sai da ta tabbatar bily ta daɗe da barin wajen sannan ta ɗauka tana faɗin, “Lah Aunty Meenal diba kiga auntyn nan da nace amin irin kitsontace ta yarda”. Duk kallonta sukayi, Amaturrahman ta dalla mata harara da faɗin, “Shine dan iskanci bakiyi maganaba sai yanzun?”. Baki ta tura gaba tana langaɓe kai gefe, “To ai mantawa nayi ko”. Amatullah tai dariya da cewa, “Kai Safah lamarinki sai ke wlhy, saiki bada a ajiye mata dan nasan zata dawo nema”. Da sauri tace, “A'a aunty Ama mu kai mata dai”. Marwah da tun ɗazun bata kula kowaba tanata game a ipad ɗinta ta harari Safah. Ramawa Safah tai, cikin tsiwarta data gada wajen Munaya tace, “Miye kike wani hararana ke kuma malama?”. Lips Marwah ta cije like Sarki Sameer, ta ɗauke kanta batare data tanka mataba.
Duk yanda sukaso Safah ta bada a ajiyema bily saboda idan ta dawo nema ma'aikatan wajen su bata fir taƙi, daga ƙarshe Amaturrahman tayi kiran Ummu ta sanar mata, Sarauniya Munaya dake kishingiɗe a kilisarta ana tausa mata ƙafa ta girgiza kai kawai da lumshe ido, babu abinda Safah ta bari na halayyarta, ta tabbatar kuma akwai dalilin da yasata yin hakan, a hankali tace, “Kubarta tazo dashi, sai a nema yarinyar”. Amaturrahman tace, “Ummu yanzu nan biye mata zakiyi?” yanke wayar Munaya tayi batare da ta bama Amaturrahman amsaba. Dole badan sun soba akabi abinda Safah keso sukatafi dashi bayan an kammala musu kitso su duka kamar yanda Ummu ta korosu suyi badan sunso hakanba..............✍

Maison zuwa gagara badau ya shirya muje gaida Sarki Sameer Saifudden da gimbiya Munaya😉😉lol.

ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏🏻.[11/30/2020, 12:56 PM] HASNA✍🏻: Bilyn Abdull 📚:
Page 16

...............Napep na samu na tare nai tafiyata gidan Inna zainabu. Can nai zamana mukasha hira da Lawusa da a yanzu muke ɗasawa har bayan sallar isha'i sannan na nufo gida.

★★★★★

           Bayan an buɗe taro da addu'a Uncle Nasir ya fara jawabi kamar haka. “Kamar yanda kowa ya sani mun fara tattaunawa akan maganar zaman Jawaad babu aure a kwanakin baya, har takai mukai masa tayin cikin yaran gidannan ko akwai wadda ya keso, sai dai ya nuna a lokacin zaiyi tunani, tun daga wancan lokacin ban sakeji daga gareshiba, to magana ta gaskiya mun gaji da ganinsa yana yawo a gari haka ana zaginmu, shi kansa bama girmansa bane, ƙannen-ƙannen bayansa ma gasunan duk da iyalansu har da ƴaƴa, yakamata Jawaad kaima kanka faɗa, dan lokaci bawai zai zauna jiranka baneba, kai kaɗai Abdul-aziz ya haifa, zamuso ganin ƴaƴanka a duniya kamar yanda mukasan da yanada rai zai ɗokantu da haka shima. A wannan karon ba shawara muke bakaba, umarnine, shiyyasama mukazo da Alhaji Baba domin ya zama shaida, tare da iyayenka, dolene a wannan karon kayi aure, ka zaɓi mace ɗaya a cikin ƴaƴan gidannan koma fiye da ɗayar mukuma zamu aura maka”.
     Jawaad da kansa ke ƙasa yay guntun murmushi domin son ɓoye ɓacin ransa, batare da ya ɗagoba yace, “Uncle ku gafarceni, bazan jaku da nisaba, duk cikin yaran gidannan bazan iya auren kowaba, dan kallon ƙannena nake musu tamkar ciki ɗaya...” da sauri Uncle Uwaisu yace, “Ai tamkar kace, bawai hakan bane, tunda babu ta inda ALLAH ya haramta maka, Jawaad bamason shirme, garama ka zaɓa komu mu zaɓa maka, kokuma ka ɗauki zaɓi na biyu, wato ka maida matarka ɗakinta kuje kuyi haƙuru da juna tunda yarinyarnan ta horu kuma tana sonka”. Yanzu kam kasa daurewa yay saida ya ɗago kansa ya kalli Uncle Uwaisu, kamar zaiyi magana sai kuma yay shiru saboda gargaɗi da Alhaji Baba yay masa da ido, kansa ya maida ƙasa yana sauke ajiyar zuciya.
      Uncle Sulaiman yace, “Son!” ɗago kai Jawaad yay ya kalli Uncle ɗin nasa da yake matuƙar so saboda ƙyawun halinsa, yace, “Na'am Uncle”. “Ko Kanada wadda kake sone?”. Ƙasa Jay ya maida kansa yana motsa laɓɓansa, sai dai babu maijin mi yake cewa, Uncle Taheer ya katsesa da faɗin, “Kai muke saurare Jawaad”. Batare daya ɗagoba ya girgiza musu kai alamar a'a. Shiru falon ya ɗauka kowa ya zuba masa idonu, shi kuma yaƙi kallonsu. Mama Zuhurah da bata da yawan magana tace, “To Jawaad ya kakeso ayi kenan? Yanzu kai kafijin daɗin kullum aita zaman meeting akanka akan maganar kaƙi aure, ka rufa mana asiri ka fidda kanka damu iyayenka daga zargi da zunɗen al'umma kaji, ƴar uwarka na sonka, tayi nadamar kuskuren datai a baya, kayi haƙuri a maida aurenku kaji”.
          Ɗagowa yay zaiyi magana fitowar Shahudah ta katse masa hanzari, gabansa taje ta durƙusa tamkar yanda Mama Atika da Mom suka kitsa mata, ta fashe da kuka tare da kama ƙafafunsa, cikin gurɓatacciyar hausarta da harshen turancin da tafi ƙwarewa ya cinye tace, “Bb dan ALLAH ka gafarceni, wlhy nayi nadamar abinda na aikata, nakumayi alƙawrin bazan sakeba, na yarda zan haihu maka yara komai yawan da kake buƙata yanzun, idan ka barni mutuwa zanyi wlhy, dan ALLAH ka ceci rayuwata Bb...” hannunta ya ture daga saman ƙafarsa yana hararta, “Kima daina ɓata lokacinki, indai haihuwace bana buƙata daga gareki Hudah, karki damu kije kicigaba da cin moriyar ƙuruciyarki kinji, indai nine kima saka a ranki baki taɓa sanin mai kama daniba dan mun rabu kenan”. Fashewa tai da matsanancin kuka yanzunkam fiye da da, dan har ƙasan ranta kalamansa sun masifar sosa mata zuciya, ta dafe kanta dake juya mata, babu zato sai kawai ganinta ƙasa sukai ta yanke jiki ta faɗi. Gaba ɗaya ƴan falon da suka zuba musu ido suka miƙe, shi kansa Jawaad ɗin kallonta yake, dan ya zata salon iskancinta ne, sai daga baya da aketa jijjigata babu alamar rai tattare da itane ya fuskanci babu wasa a lamarinta, gaba ɗaya falon ya rikice, dan iya ƙoƙari anyi Shahudah taƙi farfaɗowa, Mom sai kuka take da sambatu.
       Dole aka kwashi Shahudah zuwa asibiti da gaggawa kuwa, dan wasunsu harsu fidda ran da gaske ta mutu.

★★★★★★★

          Tun a gate baba maigadi yake sanarmi

n ai babu kowa a gidan duk suna asibiti aunty Shahudah babu lafiya, hankalina ya tashi sosai, dan haka nai azamar tsayar da mai napep ɗin dake shirin juyawa dan harma ya fara tafiya, shiga nayi na sanar masa asibitin da baba magadi ya sanarmin an kaita. Asibitine mai ƙyau dan na kuɗine, kasancewar bansan ina zan nufaba sai nai kiran aunty Aamilah, saidai bata amsa ba, na sake kira nanma babu amsa, maida kiran nai kan Yah Qaseem, sai da ta kusan tsinkewa sannan ya ɗaga, faɗa masa nai gani a asibitin a ina suke?. Muryarsa a sanyaye yace na jirasa yazo ya shiga dani.
        A yanda na gansa kawai na tabbatar akwai babbar damuwa dangane da aunty Shahudah, kasa daurewa nai na shiga jera masa tambayoyi. Amsa ɗaya na samu daga garesa, shine ta farfaɗo, sai dai sun mata allurar barci, sun kuma hana kowa ganinta sai banzan Jawaad ɗin da taketa sambatun kira. Ta bani tausayi matuƙa, dan na sake fahimtar tsananin son da takema Boss.
           Duk sai da na gaida waɗanda na tarar a wajen, sannan na tambayesu ya mai jiki, sai dai babu Boss babu dalilinsa a wajen, zama nai kamar yanda suke zaune jigum-jigum, kusan mintuna biyar sai naji ƙamshin turarensa. Ɗago kai nai dan tabbatarwa, karaf kuwa muka haɗa ido dashi, ya dalla mani harara sannan ya ɗauke kansa tamkar baiyiba.  Nima janye nawa nai, dan nasan laifina dai bai wuce tafiya bada izininsa ba. Cikin nutsatstsiyar muryarsa dake tattare da alamun gajiya naji yana faɗima Uncles nasa da matansu ya kamata su tafi gida su huta, tunda dai Doctor yace bazasu bari a gantaba har sai zuwa safiya.
          Cike da nazari nake satar kallon yanda wasu suke masa kallon harara dajin haushi a kaikaice, amma a zahiri suna amsashi cike da kulawa, sai al'amarin nasu yay masifar ɗaure min kaina, to amma abinda babu ruwanka ai daɗin kallo garesa, dan haka nai ƙasa da kaina kawai ina sauraren mahawarar da suke akan wanda zai zauna ya kwana, ance Mom taje gida Aamilah ta zauna, sai dai ita aunty Aamilah ta tubure akan tsoro takeji ta kwana asibiti, da sauri Salman yace, “Kedai wawuyace Aamilah, to sai wannan yarinyar tazauna ku kwana ai”. Yay maganar yana nunanu. Da sauri Yah Qaseem yace, “Itakuma aikin tafa? Itadai Aamilah da babu inda take zuwa itace ta cancanci kwana da itan”. Shiru kowa yay, sai kuma daga baya wasu sukai na'am da batun Yah Qaseem ɗin, na saci kallon Boss da uffan baiceba, yama ɗauke kansa daga garemu tamkar baisan mimukeyiba, nikam lamarinsa kan bani mamaki wani lokacin gaskiya.
           Wata mata da nake ƙyautata zaton cikin matan Uncles ɗin nasune ta kawo shawaran haɗa Aunty Aamilah da ɗaya daga cikin yaran gidansu ɗin da wata dattijuwar mai aiki, akan wannan shawarar aka zauna, dan haka duk sai muka fara shirin tafiya. Har mun fito baki ɗaya Mom tace gaskiya bazata iya tafiyaba, itama anan zata kwana, duk kallonta mukai da mamaki, sai kuma naga tsoro akan fuskokin wasu, dan koni naji wani iri saboda ganin Mom na sharar ƙwalla, nasan yanda ƴan gidanmu ke masifar son aunty Shahudah, hakan ya samo asaline saboda so mai tsanani da Dad ke nunamata kasancewar sunan Mahaifiyarsa taci, sai naji a raina kamar zamu iya rasa aunty Shahudah, duk yanda aka lallashi Mom taƙi aminta da hakan, sai kawai aka barta. jinai wani iri, dan tundafa Mom zata zauna nikaɗaice mace zan kwana a gidan, nima da sauri nace to zan zauna a asibitin, da sassafe sai naje gida.
      Harara Yah Qaseem ya dallamin da cewar bazan zaunaba gida zani. Niko na fara roƙonsa akan ya barni, shikuma yaƙi saurarena, kowa kuma yaƙi saka mana baki. Na kalli inda Boss yake tsaye a jikin mota hawaye na gangaromin akan fuska, sarai nasan duk yanajinmu, amma yayi kunnen uwar shegu da kowa, harna yanke ƙauna daga taimakon kowa na tsinkayi muryarsa yana faɗin,
           “Ita Aamilah ta fito ku wuce gidan tare mana, dan sunmayi yawa anan tunda Mom zata zauna, na tabbata sai ma'aikatan asibitin sunyi ƙorafi”.  Harararsa Yah Qaseem yayi, sai dai baiyi maganaba.
      Uncle Nasir ne yay na'am da shawarar Jawaad, dan haka ya aika aka kira Aamilah. Naji daɗin hakan da samun nutsuwa sosai. Daɗin da najine ya sakani matsawa inda yake

nace, “Thanks you Sir”. Banza yaymin tamkar bai jiniba, sai daƙilar waya yake abinsa, na ɗaga ƙafafuna zanbar wajen naji yace, “Uhm”. Kallonsa kawai nai sau ɗaya nabar wajen zuwa motar Yah Qaseem daketa antayomin harara tamkar idanunsa zasu zubo ƙasa.

             Tunda muka tafi yah Qaseem keta zabga jarabar da babu wanda yasan kanta, daga ni har Aunty Aamilah da Yah Salman babu wanda ya kulashi, yana gama fakin kowa yay ficewarsa, dama nice farkon fitama nai cikin falo dan banaso ya tsaidani, nayi masifar gajiya wajen hutu kawai nake buƙata. Ina shiga ɗakina na murza key, na zaresu na ajiye saman mirror tare da jikkata dana cire a kafaɗa. Idanuna har lumshewa suke saboda gajiya, haka na daure nayo wanka da alwala na fito, daƙyar na iyayin shafa'i da wutiri na faɗa saman gado, sama-sama ma nai addu'a sai barci.
            
                     Cikin barci na ringajin saukar numfashin mutum a jikina, na buɗe idanu a razane ina ambaton ‘Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un’ tabbas a jikin mutum nake, na buɗe baki zan ƙwalla ƙara aka dafe bakin da hannu, cikin wata irin murya da bantaɓa jin mai itaba a gidan ake magana da shafamin jiki, “Bazan iya saduwa dake baƙya cikin hankalinkiba kamar sauran, shiyyasa na zaɓi baki damar farkawa, kiyi haƙuri ki bani haɗinkai cikin sauƙi bilkisu, samunkine kaɗai ya ragema cikar burina yanzun, karki lalatamin tanadina na tsahon shekaru, nai miki alƙawarin zan biki a sannu bazan cutar dakeba kodan son da nake miki, sannan zaki moru da tagomashi mai yawa a gareni saɓanin sauran da basu sami komaiba sai baƙin ciki, tun farko kece tsanin nasarata da na ɗauku dakon jira tsahon lokaci”.
            Tsabar tashin hankalin da nake ciki sai zufa nake kwararwa dukda ac dake aiki a ɗakin, jikina wata irin muguwar rawa yake da ɗaukar azababben zafi lokaci ɗaya, gashi ya rufemin baki, hawayenma sunƙi fita daga idona sai zuciyata ke kukan, duk addu'ar da tazomin bakina yi nake da taimakon UBANGIJI na.

اَللَّهُمَّ إِنَّا نَجْعَلُكَ فِي نُحُورِهِمْ، وَنَعُوذُ بِكَ مِنْ شُرورِهِمْ .
“Allahumma inna naj'aluka fee nuhoorihim wana'oothu bika min shuroorihim”.

       Ya ALLAH! Mu mun sanya ka a gabansu, kuma muna neman tsarinka daga sharrace-sharracensu.

اَللَّهُمَّ أَنْتَ عَضُدِي، وَأَنْتَ نَصِيرِي، بِكَ أَجُولُ وَبِكَ أَصُولُ وَبِكَ أُقَاتِلُ.
“Allahumma anta 'adudee, wa-anta naseeree, bika ajoolu wabika asoolu wabika oqatil”.

        Ya ALLAH kai ne mai karfafa ni, kuma kai ne mataimakina, da karfinka ne nake yin dabarun yaki, kuma da karfinka ne nake kai hari, kuma da karfinka ne nake yin yaki.

حَسْبُنَا اللهُ وَنِعْمَ الْوَكِيلُ.
     “Hasbunal-lahu wani'mal-wakeel”.

ALLAH ne mai isar mana, kuma madalla da shi abin dogaro.

اَللَّهُمَّ رَبِّ السَّمَوَاتِ السَّبْعِ، وَرَبِّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ، كُنْ لِي جَارًا مِنْ (فُلاَنٍ)، وَأَحْزَابِهِ مِنْ خَلاَئِقِكَ؛ أَنْ يَفْرُطَ عَلَيَّ أَحَدٌ مِنْهُمْ أَوْ يَطْغَى، عَزَّ جَارُكَ، وَجَلَّ ثَنَاؤُكَ، وَلاَ إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ.
    “Allahumma rabba s-mawati s-sab'i wa rabba-l-'arshi-l-'azimi. Kun li jaran min  (fulanin) wa ahzabihi min khala'iqika, an yafruta 'alayya ahadun minhum aw yatgha. 'Azza jaruka, wa jalla thana'uka, wa la ilaha illa anta”.

       Ya Ubangijin sammai bakwai, kuma Ubangijin Al'arshi mai girma, ka kasance mai tsari gare ni daga wane dan wane, da dukkan rundunarsa daga cikin halittunka kar wani daga cikinsu ya yi gaggawar azaba a gare ni, ko ya ketare haddi, kariyarka ta buwaya, kuma babu abin bautawa da gaskiya sai kai.

اَللهُ أَكْبَرْ، اَللهُ أَعَزُّ مِنْ خَلْقِهِ جَمِيعاً ، اَللهُ أَعَزُّ مِمَّا أَخَافُ وَأَحْذَرُ، أَعُوذُ بِاللهِ الَّذِي لاَ إِلَهَ إِلاَّ هُوَ، الْمُمْسِكِ السَّمَوَاتِ السَّبْعِ أَنْ يَقَعْنَ عَلَى اْلأَرْضِ إِلاَّ بِإِذْنِهِ، مِنْ شَرِّ عَبْدِكَ فُلاَنٌ، وَجُنُودِهِ وَأَتْبَاعِهِ وَأَشْيَاعِهِ، مِنَ الْجِنِّ وَاْلإِنْسِ، اَللَّهُمَّ كُنْ لِي جَاراً مِنْ شَرِّهِمْ، جَلَّ ثَنَاؤُكَ وَعَزَّ جَارُكَ، وَتَبَارَكَ اِسْمُكَ، وَلاَ إِلَهَ غَيْرُكَ " ثَلاَثَ مَرَّاتٍ.
“ALLAHU akbaru. ALLAHU a'azzu min khalqihi jami'an. ALLAHU a'azzu mimma akhfu wa ahdharu. A'udhu billahi lazee la ilaha illa huwal mumsikis samawatis s

ab'i an yaqa'na 'alal-ardi illa bi'izinihi, min sharri 'abdika  (fulanin) wa junudihi wa atba'ihi wa ashya'ihi minal-jinni wal-insi. Allahumma kun li jaran min sharrihim Jalla thana'uka wa 'azza jaruka, wa tabaraka smuka, wa la ilaha ghayruka”.

    ALLAH shi ne mafi girma, ALLAH shi ne mafi buwaya daga dukkanin halittarsa, shi ne mafi buwaya daga abin da nake jin tsoronsa kuma nake shayinsa. Ina neman tsarin ALLAH, wanda babu abin bautawa da gaskiya sai shi, mai rike sammai daga su ruguzo a kan kasa sai da izininsa, daga sharrin bawanka  (ya ambai sunansa), Ya ALLAH! Ka zamo mai tsari gare ni daga sharrinsu. Yabonka ya girma, kuma kaiyarka ta buwaya, kuma alherin sunanka ya yawaita, kuma babu abin bautawa da gaskiya ba kai ba”.
            
        Duk da na rigada na sadaƙar tawa ta ƙare ban fasa karanto addu'oinba ina faɗama ALLAH kukana, koda a wani wajen bana haɗa kalmomin dai-dai saboda ruɗani karantowa nake, wata razananniyar ƙara mukaji a dukkanin illahirin gidan, hakan ya saka koma waye sakarmin baki ya miƙe a firgice kamar yanda nima na samu damar ƙwalla tawa ƙarar saboda firgita da nayi, ɗif naji kunnuwana sun daɗe banajin motsin komai, dukda ɗakin a duhu yake dunɗum, jinai an sake rungumeni an fashe da kuka, yanzunkam a tare muka ƙwala ihu da koma wanene duk da naji jikin ya banbanta dana wancan, ɗakin sai naga yana wani irin juyamin tamkar ina cikin hajijiya, rumtse idanuna nai da ƙarfi na sake ƙwalla ƙarar da ni kaina bansan iyakar ina muryata ta tsaya ba a gidan, daga nan ban sake sanin mi duniyar ke cikiba kuma.

           Duk wanda yake a cikin gidan kunnensa saida ya jiye masa ƙara maiban tashin hankali da tsoratarwa da aka ƙwala da farko a wannan dare, wadda taɗauki adadin mintuna biyar kafin ta gushe ihun bilkisu ya biyo bayanta, Aamilah da ɗakinta ke kusa dana Bilkisu ce ta fara fitowa a razane saboda kiɗimar data shiga na tsoro itama, cikin lalube ta afko ɗakin bilkisu batare data saniba itama tana ihun, fitar sautin ihun bilkisu ne ya bata damar isa inda take suka ƙanƙame juna suna kuka maiban tashin hankali. A daidai lokacin da Qaseem da Salman harma da kuku suka shigo sashen suma a razane, dan duk wanda yake gidan yaji ƙarar farko, sannan a yanzu yana jiyo ihun su Aamilah dake nuna alamar tsoratar da sukaice ta gusar musu da hankali suka tsinci kansu a yanayin. Kuku ne ya samu damar kunna fitilar ɗakin haske ya gauraye ko'ina, dukansu kansu Bilkisu sukayi, dan hakan yayi daidai da ɗaukewar numfashinta daga gangar jikinta.
            Babu mai iya musalta tashin hankalin da suke ciki a wannan dare, kan kowa ya kulle daga abinda ya faru, cikin ƙarfin hali Salman ya ɗakko ruwa ya miƙama Qaseem dake taya Aamilah jijjiga Bilkisu, bai tsaya yayyafa mataba ya bulbule matashi kawai a fuska, wani nannauyan numfashi Bily ta kawo, sai dai jikinta babu alamun ƙarfi, ta buɗe idanu a hankali ta kalli kowa sai kuma ta maida ta lumshesu hawayen da bata samu yiba ɗazun suna ziraro mata a kumatu masu ɗumi.
       Sama-sama nake iya jiyo muryar yah Qaseem daketa jeramin sannu shida Aamilah da Kuku, bandaiji muryar Salman ba sai daga baya, tsahon wasu mintuna muna a haka kafin barci yaɗan fara fisgata, addu'a nake buƙatar ko yaya wani ya dinga karantowa yana tofamin kozanji sauƙin abinda nakeji a jikina tamkar ana kunna garwashin wuta,


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login