Showing 48001 words to 51000 words out of 388641 words

Chapter 17 - KWAI CIKIN KAYA

10 Sep 2025

20704

Inna Asiyar ce kuwa inna”.
“Ɗiyar Asiya? Kai ina ka samota haka?”
Inna ta faɗa cike da mamaki.
Murmushinsa ya faɗaɗa, tas a yanda muka haɗu jiya sai ya sanar mata, sai jinjina kan mamaki takeyi, ta juyo gareni tana tambayata daga ina nake haka har shi Shu'aibu ya ganoni?.
Da farko nayi niyyar faɗa musu gaskiya, amma yanayin Inna da naga har sannan bawani ɗokin ganina taiba saina canja zancena kawai, na faɗa musu iya abinda zasu iya amsata game da nemnsu kawai na fitoyi dan nagaji da zama ni kaɗai.
Kai inna ta jinjina, babu ko jin nauyina tace, “Amma kai Aibo kana ganin riƙon babbar budurwa kamar wannan bazai zamar mana wani tawayaba? Mu dai ba kuɗin aurar da ita ke garemu ba kaima kasan haka, ga ɗan karen kishin matarka da batason ganin wata mace ta raɓeka, inaga mu taimaka mata da wani abun ta koma inda ta fito tai haƙuri kamar yanda kowa keyi a nasa gida.
Murmushi nayi mai ciwo hawaye na taruwa cikin idona, wato sai yanzu na fahimci abinda yasa dangina ke gudun ɗaukata, ashe hidimar aurar danice damuwarsu kawai, to nida banida ko saurayi wane maganar aurena za'ayi kuma?, maganar shu'aibu ta katseni.
“Haba inna, wannan wace irin maganace haka, koba komai ai Bilkisu abar tausayice, ALLAH kuma shine zai buɗa mana mu sauke dukkan nauyinta gwargwadon iko, dan riƙe maraya ba ƙaramin alkairi bane da falala ga bawa, amma yanzu sai kowa ke gudun hakan, kifa tuna mahaifinku ɗaya da inna Asiya, na tabbata kuma da itace a raye zata riƙe naku ƴaƴan ai, sa......”
“Nikam naji gwanin iya magana, tunda kaji ka gani ta zauna ga fili nan, ni dama dai kai nake tausayi, tunda dukkan ƙarfin riƙe gidannan kaine keyi”.
Cikin jin daɗi yace, “Nagode da amincewarki inna, ALLAH ya tayamu riƙo”.

Wannan shine yazama sanadin zqmana a wannan gida, duk da bajin daɗin zaman nakeba hakan ya fiyemin akan naje naita raɓe-raɓe harna cigaba da gamo da irin gidajen su Uwargida masu dulmiyar da imanin bawa zuwa halaka.
Babu mai sakarmin fuska inba Shu'aibu ba, shi kuma ba yini yake a gidanba, a hankali dukkan aikin gidan ya dawo kaina, sam bani da wani hutu inba dareba shima sai kowa ya rigani kwanciya.
Lawusa matar Shu'aibu ta mugun tsanata, ni zan dafa abincin gidan amma idan tazo rabo ɗan kaɗan take zubamin, wani lokacinma saita gama rabon zatace ta manta dani, sai dai ace na kankare ƙanzon.
Duk da agaban Inna ake komai uffan bata ce mana balle ta nunama Lawusa batai dai-daiba, koda yake na lura Inna tsoron Lawusa takeyi, dan haka zatai ta mata rashin kunya amma bata iya cewa batai dai-daiba, sai idan taimata abinda yay mata zafine sosai zakaji ta faɗama Shu'aibu, shiko iyakarsa yace tayi haƙuri ta bar Lawusar da halinta kawai.
Wannan zama nasu na bani mamaki sosai.
Ban fahimci abinda yasa gidan yake hakaba sai da ƙanwar yaya Shu'aibu Sa'a tazo gidan yini a ranar da nake cika wata guda a cikinsa, itakam hannu biyu ta amsheni, sai murna take matsayina na ƴar uwarta.
Akan Lawusa namin masifa nazo na ɗaura abincin rana sukai faɗa da Sa'a, tace ban ɗorawa ita da take aure a gidan ta fito ta ɗaura, da yake Inna batanan sai babu wanda yace Sa'a batai dai-daiba, nicema naita bama sa'a haƙuri akan tabari kawai nayi, amma fir tace bazanyiba.
Nanne ta zauna ta bani labarin ai Yaya Shu'aibu ba son Lawusa yakeba, Inna ce ta haɗa auren saboda Lawusa ƴar ƙawartace, yanada wadda yakeso amma inna tace bazai aureta ba sai Lawusa.
A lokacin babansu na jiyya baida lafiya, shiyyasa aka rasa mai goyama Shu'aibu baya, dole ya auri Lawusa badan ya soba, bayan bikin da sati biyu kuma babansu yarasu, daga nan Lawusa ta fara ma Inna rashin mutunci a gidan, inna ko bata iya ce mata komai, yanzu haka aurensu shekara uku kenan, amma ko ɓari Lawusar bata taɓa yiba sai rashin mutunci, sai dai duk wannan tijara tata tana tsoron Shu'aibu, ita kuma Sa'a bata raga matane.
“ALLAH ya ƙyauta” kawai na iya faɗa naja bakina na tsuke.
Sai yamma lis Inna ta dawo gidan, Lawusa ta kwashe ƙarya da gaskiya ta faɗa mata a kaina, Inna ko ta rufeni da masifa hardasu gori akan daga taimakona da sukai shine zanzo na watsa musu gida.
Ran Sa'a ya ɓaci akan wannan abu, Shu'aibu na dawo ta kwashe komai itama ta sanar masa, shiko ya balbale Lawusa da masifa har takaisu ga marinta.
Kuka da ihu taita kurmawa akan mari guda ɗaya, yayinda bakinta keta danƙarama Shu'aibu zagi ta uwa ta uba, ta haɗa kaya zata tafi Inna taita roƙonta da bata haƙuri, sai da ƙyar Lawusan ta haƙura saboda tana bala'in son Shu'aibu, batason rabuwa dashi sam.
Ni daga baya ma abin nasu dariya ya koma bani dan na lura dama Lawusa bason tafiya takeba, farfaganda ce kawai.
Sam abinda akemin a gidan sai baya damuna sosai, komai kuma suka buƙata ina musu dan a zauna lafiya, ban taɓa ɗaga kai na kalli wulaƙancin da Lawusar kemainba sam, a ganina ba laifinta bane ai, haka ƙaddarar rayuwata take.....



________________________
JAWAAD
_________________________

Yau ma dai Jawaad bai kwana gidanba, koda ya baro wajensu Aliyu Office ya koma, acan ya raba dare yana aiki, daga baya ya fito, amma saima ya rasa ina zai dosa, sam baya buƙatar komawa gida, dan bayason yawan ɓacin rai a yanzu, yana buƙatar nutsuwa ta musamman akan gudanar da wannan aikin da yake fatan nanda kwana biyu ya kammala shi insha ALLAHU.

Gidan dasu Jabeer suke dai ya sake komawa, ya iske har sunyi barci, dan haka ya buɗe wani ɗakin ya shiga ya kwanta, bama wani barci sosai yayiba aka kira asubahi.
Su Hafiz duk sunyi mamakin ganinsa a gidan, sai dai tunda bai basu fuskar da zasu tambayesa komaiba sai basuce ɗinba.
Suna dawowa daga salla duk da barcin dake cin idonsa bai kwantaba.
Zama sukai yana musu bayanin abinda kowa ya kamata yayi a ranar yau.

Coffee da Jabeer ya dafa musu da kansa kowa yake sha, Jawaad ya ajiye kofin hannunsa yana faɗin, “Dolene yau muyi komai da azama, dan guri na sake ƙure mana. Ni zanje gidan Alhaji kokino na gana da matarsa, Jabeer kaikuma filin jirgi ya kamata kaje ka sake mana bincike a cctv ɗinsu, Aliyu da Hafiz ku kamo mana drivern Alhaji Kokino da ƙaninsa wakili, dan hardashi akaje tarbosa filin jirgi, shima inada alamar tambaya a kansa”.
A tare duk suka jinjina masa kai, sai kuma kowa ya miƙe domin zuwa ya shirya...............✍🏻



https://youtu.be/5xN4SGMIzME

*_ALƘALAMI TV_* takuce, maza ku garzaya kar ayi babu ku, Please a danna mana subscribing domin nuna mana ƙauna ta musamman🥰🤙🏻.


🗣 *_RANAR KUKE JIRA YAU GATA TAZO📻📻💃🏻💃🏻💃🏻_*


*_ZAFAFA 👭🕴🏻👫, DA TAMBURANMU GAMU MUNZO💃🏻💃🏻💃🏻📻📻_*


*_MASOYA MUKE KIRA DAN KUWA MUNZO💃🏻💃🏻🤫😉😂_*


*_Dan dan dan dan dan, ina masoyan suke?, ga fa ZAFAFAN BIYAR sun sake faso muki da wani SABON KAFCE mai tsuma zuciyar abokin tafiya_*

_ZAFAFAN dai nan nakune, waɗanda suka barbaje basirarsu a littatafai biyar da suka shuɗe, masu saka nishaɗi da tada kunnuwan mai karatu sama tamkar yana tailunar kilishi😉_.

*_Kunsan wanima abin jin daɗi kuwa? To wlhy ina mai tabbatar muku KAFCEN wannan lokacin ya ɗara na farko, domin kuwa madarar basira zasu kwarayar, tare da nagartaccen ilimi mai garɗin dabino_*

_Maza ku garzayo dan kaɗan ya rage a fara al'amura, farar takarda da biriknmu duk riƙe suke a hannu, hallaruwarku guri gudane zai bamu ƙwarin gwiwar suburbuɗo muku daɗaɗan labaranmu kamar haka._👇🏼


_*IGIYAR ZATO.....*:- Na marubuciya Hafsat (miss xoxo), labarin soyayya mai ƙyatarwa, cakuɗe da tsagwaron cakwakiyar ruguntsumin abin al'ajabi_.



_*ƘAUNAR MU:-* Na Mamu gee, labarin madarar soyayya ƴar asali da babu sirkin ruwa a cikinta, ga wata sambaɗeɗiyar zumar zaƙin daɗi mai saka zuciya zumuɗi._


_*ƊAURIN GORO...:-* Na Hafsat rano, Kitumurmura kenan, amma ta lobayyar baje basirar ƙofofin zukatan masoyan da suka samu ɗaurewa bisa makirci ta cakwakiyar maƙiya_


_*ALƘAWARIN ALLAH:-* Na Safiyya huguma, labari mai tsagwaron nuna jarumtar masoyan da ƙaunar gaskiya ke ambaliya da dulmiya cikin tsantsar ƙauna, dukda ɗunbin zagon ƙasar da ake tafka musu._

_*GUDU DA WAIWAYE....:-* shi ya kawo mugun zato. inji masu iya maga. Na Bilyn Abdull, labari mai ɗaure da sarƙaƙiya a zukatan masoyan da yarda ta amince musu kasancewa a inuwa ɗaya, amma tsagwaron cakwakiya da hargitse-hargitsen ƙaddariri suka tarwatsa hakan._


*_Tabɗi jan, wannanfa shine ZAFAFAN, to kai mai karatu tayaya zaka tabbatar zafafanne?, bari na baka satar amsa😁👇🏼_*


_*Amsar itace😉*👉🏻 ƙoƙarin mallakar ZAFAFA ta tsafta tacciyar hanyar sanƙamawa jagororin tafiyar kuɗi kamar haka.👇🏼_.

_*NAIRA 500*, mabuɗin mallakar litattafan ne gaba ɗaya biyar hankalinka kwance_

_*NAIRA 450*, Zata mallaka maka littatafai huɗu._

_*NAIRA 400*, tikitin mallakar littatafai uku_.

_*NAIRA 300*, zai baka lasisin mallakar littatafai biyu_.

_*NAIRA 200*, Na mallakar littafi guda ɗayana._

*_Kunji wata rahusa ƴan uwa? Yo duk saukinnan saiki zauna daɗaɗan labarannan guda biyar su wuceki duk da gwanayenki ne mamallakansu?🤔😳_*.

_Maza garzaya ki sanƙama ƴan kwabbanki ta wannan asusun bankin domin mallakar zafafa masu sanyaya zuciyar mai karatu._

*_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_*


2260792279
_MARYAM SANI_
_ZENITHBANK_

saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇
*07067124863*

*_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇

*09032345899*


_Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_


Mucigaba da shakatawa da wannan kafin a fara kafta WASAN😁👉🏻📻



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻*_Typing📲_*




*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*


*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*


*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_


*______________________________________*
*_BOOK ONE_*
_Shafi na goma sha bakwai_
*______________________________________*


.............A gaggauce yay shirin cikin Suit kalar ruwan goro mai duhu, sai rigar ciki data kasance ruwan bula mai haske, yanada kaya a gidan, saboda duk randa Shahudah ta haɗa masa zafi to nan ne wajen fakewarsa ya samu nutsuwa, shiyyasa yake da abubuwan amfaninsa.
Turare ya fesa kaɗan ya fito yana ƙoƙarin ɗaurama hannunsa a gogo, rigar suit ɗin ta sama rataye a hannunsa dan bai sakaba.
Su Aliyu dake zaune a falo cikin shirin fita suma suna jiransa duk suka miƙe idonsu a kansa.
Jabeer ya kama hannun da Jawaad yake ɗaurama agogon yana ƙarasa ɗaura masa.
Bai musaba ya miƙa masa hannun yana maida hankalinsa ga Hafiz.
“Hafiz ka kulafa sosai, dan ƙaninsa ɗinnan shegen wayone dashi, duk wani motsinsa inda yake zuwa, da wanda yake mu'amula da dai komai nasa ku sani, a koda yaushe yakan nuna yanason yayan nasa fiye da kansa”.
Ya ƙarasa maganar dai-dai Jabeer na gama ɗaura masa agogon, yace, “Thanks”.
Kai kawai Jabeer ya ɗaga masa, sukai ƙoƙarin ficewa.
Jawaad na gaba suna binsa a baya su uku, dolene ka gansa su burgeka sosai, dan kallo ɗaya zakai musu ka tsinkayo tsantsar jarumtar aikinsu a fuskokinsu.
Gimba ya gaishesu cikin girmamawa, sannan ya buɗe ma Jawaad mota ya shiga.
Suma sauran kowa mota ya shiga, Jabeer shi kaɗai, Hafeez ma shi ɗaya.
Sai Aliyu da ya shiga kusa da Jawaad zasuje gidan Alhaji kokino tare.
Shiru Jawaad na kwance a bayan mota, kansa kwance jikin kujera. yayinda idanunsa ke buɗe yana kallon titi.
Dai-dai danja ta tsayar dasu idonsa ya sauka akan wata mahaukaciya dake tsaye bakin titi tanata soshe-soshe, kafeta da idanu yayi ko ƙyaftawa bayayi, Gimba da Aliyu da basusan mike faruwa ba suna ɗan magana jefi-jefi, gimba yaja motar sukai gaba.
Jawaad yasa handkherchief ya tsane hawayen da suka cika masa idanu, yanajin kewar mamansa sosai, irin yanda bakinsa ma bazai iya furtawa ba, ya lumshe idanunsa yana magana a hankali akan laɓɓa wanda inba kusa da shi kakeba bazakajiba.
“Boss mun iso”
Gimba ya sake maitawa Jawaad da yay nisa cikin tunani sam baisan harma sun samu damar shigowa harabar ƙaton gidan Alhaji kokino ba, Aliyu da gimba harsun fita a motar sai shi kaɗai.
Numfashi mai nauyi Jawaad ya sauke yana kallon Gimba da idanunsa dake a rine da damuwa?.
Baice komaiba ya ziro ƙafafunsa ya fito, agogonsa ya ɗan kalla kafin ya maida kallonsa ga dogon ginin benen gidan,
“Ali muna buƙatar ai mana iso fa”.
“Yes Boss, ai mai gadin ya shiga ya sanar musu ma”.
“Ok” Jawaad ya faɗa yana tura hannayensa biyu cikin aljihun wandonsa kamar maijin sanyi.
Kusan mintina uku sai ga mai gadin ya dawo, shine yay musu jagora har ƙaton falon baƙi dake a cikin gidan, sannan yay musu sallama ya fita.
Zamansu baifi na mintina ukuba wata dattijuwa ta shigo ɗauke da ƙaton tire, ta ajiye sannan ta risina ta gaishesu, cikin kulawa Jawaad ya amsa mata.
Tana fita babban yaron Alhaji kokino ya shigo cikin kayan barci, da alama ma tasoshi akayi daga barcin, dan yanayinsa ya nuna hakan.
Hannu ya bama Jawaad suka gaisa tare da Aliyu da Gimba, sannan ya samu waje ya zauna hankalinsa akan Jawaad.
“Yallaɓai ko an samu wani ƙyaƙyƙyawan news ne haka?”.
Jawaad dake zaune ƙafa ɗaya kan ɗaya ya girgiza masa kai yana gyara zamansa, “Babu wani labari mai nuni da nasara abokina, yanzu ma munzone dan inason ganawa da dukkan jama'ar gidannan idan babu damuwa”.
“Babu damuwa yallaɓai, barama kaga naje na tattarosu”.
Kai Jawaad ya jinjina masa cikin lumshe idanu, ya miƙa hannu ya amshi system ɗinsa dake a hannun Aliyu, saman cinya ya ɗorata yana ƙoƙarin kunnawa. A haka jama'ar gidan suka fara shigowa cikin sallama.
Jawaad bai ɗago ya kalli kowa ba a cikinsu, danne-dannensa kawai yake a lap-top.
Kowannensu mazauni ya samu, budurwar da tunda ta shigo idonta ke a kan Jawaad ta miƙe daga inda ta zauna tana faɗin, “A yallaɓai ko shayi ai kwasha, dan da alama kunyo sammakon barin gida”.
Ɗan murmushi Aliyu yay kawai, Jawaad kam ko motsi baiyiba balle zancen ɗagowa, zata fara ƙoƙarin haɗa shayinne Aliyu ya ɗan kalleta yana girgiza kansa, “No Please barsa kawai”.
Da sauri Uwargidan Alhaji Kokino dake ƙoƙarin zama ta katsesu da faɗin, “A'a haba dai, in kuka ƙi kuwa bazamuji daɗiba sam”.
Murmushi kawai Jawaad da ya kallesu yayi, amma baice komaiba, dan haka shema'u ta cigaba da haɗama su Jawaad shayin, cike da yanga ta kalle Jawaad kamar shi kaɗai kawai take gani a wajen tana faɗin, “Asa shuga da yawa?”.
“Spoon ɗaya ya isa” Jawaad yay magana a taƙaice ba tare daya kalleta ba.
Koda ta kammala tazo miƙa musu sai da fara bama Jawaad, saboda neman magana saida tai yanda hannunsu ya gogi juna, hakanne ya saka Jawaad ɗago idanu ya kalleta, yanda ta kafesa da natane ya sakashi yin luuu da nasa cikin salon isa irin na mazan da suka isa ya janye daga nata yana faɗin, “Thanks” a hankali.
Tai murmushi saboda jin daɗin godiyar da yay mata, wajen zamanta ta koma bayan ta bama Aliyu da Gimba suma, inda take facing ɗin Jawaad da har yanzu bai kai shayin bakinsa ba yana cigaba da danna lap-top ɗinne.
Amaryar Alhaji kokino ce ƙarshen shigowa cikin shiga ta alfarma, ta samu waje nesa da kowa ta zauna.
Sai lokacinne Jawaad ya janye system ɗin daga saman cinyarsa yana maida hankalinsa garesu.
Shayin yakai bakinsa kafin ya basu dukkan nutsuwarsa yanayin gyaran murya.
“Zakuyi mamakin cewar da nai a tattaromin ku duka, so amin afuwa idan na shiga rayuwarku da yawa. Dama dai akan maganar Alhaji ne, maganar gaskiya a koda yaushe lamarin nan sake rikitar damu yakeyi, musamman idan mukai dubi da lafiyar ALLAH suka baro filin jirgin, ku kuma gashi kunce bai shigo gidannan ba, sai labarin rashin ganinsa aka kawo muku”.
“Hakane kam yallaɓai, mu kanmu mun rasa yanda zamu kwatanta al'amarin gaskiya”.
Kai Jawaad ya jinjina yana duban Amaryar Alhaji.
“Hajiya kece kuka dawo da Alhaji daga tafiya ai?”.
Zamanta ta gyara sannan cikin isa


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login