Showing 195001 words to 198000 words out of 388641 words
mai ciwo idanunsa na sake ƙanƙancewa tsabar masifar dake cin zuciyarsa, cikin wata irin muryar data bama Qaseem mamaki Jawaad yace, “Qassem ka riƙe girmanka, banason ka kaini bangon da zan sakaka dana sani mara amfani”. Kafin Qaseem yace wani Abu Uncle Sadiq ya ƙaraso wajen. “Ku wane irin shashancine haka kukem mutane anan?”. Jawaad baice komaiba, sai Qaseem ne ya bama Uncle Sadiq amsa da, “Uncle bazaka ganeba, wannan yaron munafukine, wlhy ko rantsuwa nai babu kaffara nasan yanada hannu akan wannan abun daya faru, kuma wlhy dolene ka saki Bilkisu a yau ɗin nan basai gobeba”. Murmushi Jawaad yay cikin taɓe baki ya raɓasu ya wuce batare da yace komaiba.
Ƙarasawa yay wajen su Uncle Nasir ya gaishesu, Uncle Nasir yace, “Kaikuwa ina kaje anta nemanka tun ɗazun Jawaad?”. “Amin afuwa Uncle, naje wani wajene”. “To amma saika kashe wayarka? Minene amfanin hakan?”. Jawaad dai baice komaiba.
Uncle Uwaisu yace, “Amma dai kasan miya faru a wajen ɗaurin aure ko?”. Cikin nuna halin ko in kula Jawaad yace, “Uhmmm na sani”. Ran Uncle Nasir a ɓace yace, “Ka sani? Amma shine dan wulaƙanci katafi wani waje ka barmu da nemanka?”.
Kafin Jawaad yace wani abu Uncle Sadiq yace, “Ya
ya nikam inaga wannan ba maganar nan bace, kamata yay muyi haƙuri yaranan su dawo cikin hayyacinsu sai ayi maganar a nutse a gida kamar zaifi, sannan kuma mu maida hankali wajen neman shi wancan angon da aka ɗaurama Shahudah aure dashi da ita Azeema take kowa”. Duk sunyi na'am da hakan, Jay ya kalli Uncle Nasir a wani yanayi, kamar zaiyi magana sai kuma yay shiru kawai.
Bayan sallar la'asar su Uncle Nasir suka wuce gida harda Dad da Qaseem da aka tilastama dole akan yadace suje su watsa ruwa kodan suji ƙarfin jikinsu, anbar momy kawai wajen Shahudah, Ummie da maman Amina kuma suna tare da Bilkisu, Jawaad bai shiga duba kowaba a cikinsu.
Suna isa gida ya shige sashensa, wanka yay yasha magani saboda kansa ciwo yake masa sosai, duk yanda yaso ya kwanta ya huta hakan ya gagara, ya shiga zagaye bedroom ɗinsa cikin faɗawa wani dogon tunani akan wannan dambarwar da suka wayi gari da ita yau, tabbas yasan kaso mafi yawa na abinda ya faru, musamman akan sarƙaƙiyar ɗaurin auren, sai dai akwai wani al'amarin daya ɗaure masa kai sam ya kasa samun amsa akai, kuma yazama dole ya nemo wannan amsar, Tabbas saiya nemota, itace zata zama tsanin buɗe masa hanyar fahimtar abinda ya kasa fahimta a yanzu da duk sauran jama'a ma. Ya sauke numfashi mai zafi tare da kwanciya a kan gadonsa ƙafafunsa a ƙasa.
Shi da kansa shine ya canja list ɗin ɗaurin aure a masallaci, sai dai daliline mai ƙarfi ya sakashi aikata hakan, kuma duk wanda zaiji dalilinsa anan gaba zai tabbatar abinda yayi shine dai-dai kuma shine ya dace, to amma tayaya zai fahimtar da mutane sukuma su fahimta batare da ya fito da ainahin maganar filiba?. Wannan tambayar itace keta cin ransa da sukarsa a ƙahon zuciya. Barci ɓarawo shine ya sacesa a wannan lokacin batare daya shiryama hakanba, bai farkaba sai gab da magriba, wasu massallatanma har sun fara kiran sallar. Wanka yay a gaggauce yay shiri cikin ƙanan kaya ya fita riƙe da key ɗin mota da wayoyonsa, mota ya buɗe ya zubasu sannan ya nufi massallacin ƙofar gidansu sukai sallar magriba.
Koda ya dawo bayan an idar mota ya shiga ya fice daga gidan.
★★★
MASARAUTAR GAGARA BADAU
Koda su Amaturrahman suka iso masarauta sai suka iske gimbiya Munaya tana sashen mai martaba, haƙura sukai akan idan ta fito saisu sanar mata da duk abinda ke faruwa. Safah dai batace komaiba, tana ganin yayun nata sun nufi ɗakinsu ta zare jiki zuwa sashen mai-martaban batare da sun saniba. Sai dai koda ta nema Jakadiya tai mata iso saitace mata gimbiya na tare da takawa, tasan kuma babu mai shiga ganinsa inhar yana tare da matansa. Tarbiyyar da su Safah suka tashi ciki akwai girmama hadiman gidan, dan koda wasa Gimbiya Munaya bata yarda yaranta suce zasu taka koda bawa na gidan yanda suke soba, tsaye take kan tarbiyyarsu daga ita har mai martaba da Mommah. Safah sai ta kwantar da kai cike da shagwaɓa tana lallaɓa jakadiya, harda bata ƙyautar dubu biyar. Baki Jakadiya ta washe, tace, “A uwar masu gida ai dolene nai miki iso, ammafa inhar basa falon farko to saidai kiyi haƙuri anjima saiki dawo.
Safah tace, “Na yarda, amma dai ba falon farko kawai ba, dan ALLAH harna biyu, dan kinsan inhar Ummu na tare da Abbu bazasu zauna a falon farko ba, nikuma maganace mai muhimmanci zanma Ummu”. Rigimar Safah da Jakadiya ta sani yasa ta amince zataje har falo na biyun. Safah na nan tsaye a ƙofar ƙatafaren falon mai-martaba Jakadiya ta shiga domin mata iso. Iyakarta falon farko tai kira ta wayar landline kamar yanda tsarin Sarki Sameer yake. Munaya ce dake masa tausa ta ɗaga, cike da girmamawa Jakadiya ta isar da saƙon Safah. Daga can Munaya zata fara faɗa akan Safah ta jirata saita fito Sarki Sameer yaymata nuni data bari Safah'n tazo, badan tasoba tabi umarninsa.
Cike da ɗoki Safah ta shiga kamar yanda Jakadiya ta sanar mata anbata izini, tun daga falon farko har zuwa na uku bata iske kowaba, hakan yasata wucewa ƙaramin falon da bakowa keda lasisin shigarsaba saisu da iyayensu. Tai sallama a bakin ƙofa suka amsa mata kafin a bata izinin shiga. Sarki Sameer na kishingiɗe a ƙasan lallausar daddumar da
aka ƙawata falon da ita, ya zubama ɗiyar tasa da bazata gaza shekaru sha uku ba ido yana murmushi, itama murmushi take masa tana satar kallon Ummu dake zuba mata harara ta gefen ido. Ganin tayi tsaye taƙi ƙarasowa garesu mai-martaba yakai dubansa ga gimbiya Munaya, hannu yakai yanda Safah bazata ganiba ya Mintsineta, gimbiya Munaya ta ɓata fuska irin taji zafinnan, gira ɗaya ya ɗaga mata yana murmushi da cewar, “Kin tsaremin yarinya da ido takasa ƙarasowa, Ummuna kinga zo naji mike tafe dake?”. Da sanɗa Safah ta raɓa gefe taje ga mai-martaba daya tashi zaune sosai, hannunta ya kamo ya zaunar da ita kusa dashi. Safah akwai shagwaɓa da ƙulafucin iyaye, gashi tsiwarta data gada ga Munaya yasa Sarki Sameer ke tsananin sonta sosai, danshi idan tana abu Munaya kawai yake gani a zamanin ƙurciya. A jikinsa ta lafe tana kumbura fuska, cikin raɗa tace, “Abbu dan ALLAH kacema Ummu tabar hararata ni tsoron idanunta nakeyi, kumafa abu mai muhimmanci zan faɗa”. Murmushi mai-martaba yayi, ya maida dubansa ga Ummu data tsume fuska. “Ummu Please kiɗan saki fuska mana, kinga dai tsoron idanunki mukeji”. Yanda yay maganar cikin marairaice fuska ya sakata yin murmushi ta ɗauke kanta daga garesu.
Safah ta gyara zama ganin Ummu tabar harararta tace, “Abbu kasan miya faru a inda mukaje kuwa?”. “Saikin faɗa Ummuna”. duk abinda suka iske na rikici a gidansu Bilkisu shi Safah ta zauna tsaf ta zayyanema mai-martaba da Ummu, sosai abin ya basu mamaki, sai dai basuce komai akan batunba Ummu tace, “Tunda kin gama faɗa tashi kije idan na fito zanyi magana dasu Amaturrahman”. Sosai Safah ta kumbura harda hawaye, tace, “Abbu kajifa ni bandani za'ayi maganar bayan aunty nace”. Murmushi takawa yay yana mai girgiza kansa, ya shafa kanta yana faɗin, “Ai dolenema ayi magana da magajiyar Ummu, bayan ma kece kika kawo zancen”. Cikin ɗoki tace, “Yauwa Abbunmu shiyyasa nake sonka, bara naje na faɗama Mommah itama”. Kafin wani cikinsu yay magana ta fice da gudunta.
Ummu tace, “ALLAH dai ya shiryeki Safah, nikam bansan irinkiba”. Murmushi takawa yay tare da ɗora kansa saman cinyarta, yakai hannu ya shafi kumatunta yana mai lumshe idanu, “Dukfa rawan kan Safah a wajenki ta gada, kinsan kawai dai shi ɗan gado idan ya gaji abu saiya zarta mai shine”. Murmushi gimbiya Munaya tayi itama tana shafa kansa, tace, “Kaikuma gashi baka mantuwa yallaɓai”. Sosai ya buɗe idanunsa a kanta yana mata wani sassanyan kallo, cije lips ɗinsa da yay tare dayin ƙasa-ƙasa da murya kamar mai tsoron ajisu yace, “Yallaɓiya ai Sameer bai cancanci mantawa da ƙuruciyarki ba, kin bani wahalafa da yawa madam”. “Kamar yanda nima ka baniba”. Dariya sukayi a tare. Saida suka tsagaita takawa ya tashi zaune sosai idanunsa akan gimbiyar tashi. Yace, “Ban fahimci zancen Safah ba, mike faruwane?”. Cikin nutsuwa gimbiya munaya ta zayyane masa komai akan farkon haɗuwar Bilkisu dasu Safah ɗin a wajen Saloon ɗinta, har tafiyarsu yau domin kaimata l'd cards ɗin da Safah ta zama sanadin ɗakkosu. Shiru baice komaiba tsahon wasu mintuna, itama Ummu bata sake cewa komaiba. Harma ta sakin zancen sai y jeho mata tambaya akai “Toke yanzu mi kika fahimta a zancen nata kenan?”. “Eh to inason nasamu ƙarin bayani wajensu Amaturrahman ne, daga nan sainaga idan maganar nada muhimmancin da zamu shiga ciki, dan na lura a zancen Safah kamar ita yarinyar ba ƴar gidan bace”. Kansa ya jinjina mata kawai, daga nan suka saki zancen suka cigaba da hirarsu.
_________________________________
Kai tsaye asibiti Jawaad ya nufa, Ummie ta wuce gida tun ɗazun bayan zuwansu Batool da Jawaad ya kira Ummah babba ɗazun yace taje asibiti ta kwana a can wajen Bilkisun, babu musu batool ta amsa sukazo tare dasu Ummah suka duba Shahudah da bilkisu, su su Ummah sai suka koma gida akabar batool din anan, da Nabeelah ma ta tubure nan zata kwana tana ta hawaye ganin halin da Bilkisu ke ciki, harda rantsuwar saita rama mata, saida ummah ta lallabata saboda sunyi yawa, kuma Jawaad tunda ba ita yaceba idan yazo ya sameta tasan kaniyarta zaici ne..
Batool na zaune suna ɗan hira itada maman Amina aka
n abinda ya faru yay knocking ƙofar, a zatonsu Doctor ne ya dawo. Ganin Jawaad ya saka Batool mamaki, dan cayayma Umma sai da safe zai dawo daga inda yaje, zatai magana yay saurin saka yatsansa saman baki alamar tai shiru, shirun kuwa tayi. Ya gaida Maman Amina cikin girmamawa dan dama sunsan juna tun lokacin da take aiki gidansu Shahudah kafin ta barma Amina saboda matsalar ciwon ƙafa data isheta. Takawa yay zuwa gaban gadon da Bilkisu ke kwance dama tunda ya shigo idanunsa a kanta yake, baya ganin fuskarta saboda ta juyama ƙofar baya. Cikin dabara maman Amina ta fita daga ɗakin.
Ta inda bily ta juya fuska Jay ya zagaya, tsaye kawai yay ya zuba mata manyan idanunsa da sukai jazur da ɓacin rai, tsawon mintuna uku kafin ya kalli Batool dake tsaye itama tana kallon bilyn. Cikin ɗacin murya yace, “Waye yay mata wannan dukan?”. Itama Batool muryarta da alamun baƙin ciki ta bashi amsa da cewar, “Su Aamilah ne akace, inason dan ALLAH kaci uban yarannan Brother, saboda wannan abin da sukai tsabar cin zaline ai da hauka, yaran gidannan naku sam tarbiyya bata ishesuba na lura, mtsoww!”.
Baice da Batool komaiba, sai dai yanda fuskarsa ta ƙara tsukewa zakasan lallai ran ƴan maza sun ɓaci, tsahonsa ya rage tare da ranƙwafowa akan bily da duk batasan anaiba, yakai hannun damarsa a hankali gefen kumatunta da yafi ko ina kumbura, motsawa tai tare da yatsine fuska alamar taji zafin taɓawar da yay ɗin, ya sauke nannauyar ajiyar zuciya yana mai janye hannunnasa. Tsaye ya miƙe idonsa har yanzu akan Bilkisun yace, “Mi Doctor yace yanzun?”. “Sunyi magana da Ummah, bansan miyace mataba gaskiya”. Bai sake cewa komaiba ya cigaba da kallon Bilkisu na tsahon lokaci, kafin ya sauke numfashi da zare hannunsa ɗaya daga aljihun wandonsa ya ɗauki file ɗin daya gani a drawer gefen gadon, saida yagama dube-dubensa sannan ya ajiye yay ficewarsa batare da yacema Batool komaiba. Itama da kallo kawai ta bisa, haka kawai yau takejin matsanancin tausayin ɗan uwan nata da ya kasance shi ɗaya tilo, babu wa babu ƙani, babu iyaye baki ɗaya sai dangi.
Magana yaje sukai da Doctor, ko kallon ɗakin da aka kwantar da Shahudah baiyiba yay ficewarsa daga asibitin, daga nan gidan Alhaji baba ya nufa.
Kiraye-kirayen sallar isha'i da akeyine ya sakashi shiga massallaci, saida aka idar ya shiga gidan. Shima Alhaji baban shigowarsa kenan babu jimawa, Jawaad ya zauna ya gaishesa, amsawa Alhaji baba yay idonsa akan jikam nasa. fuskar Alhaji a ɗaure baba yace, “Daga ina?”. Batare da Jawaad ya kallesaba yace, “Gida”. “Ɗazun kumafa da akaita nemanka a wajen ɗaurin aure?”. “Aiki naje”. Alhaji baba yace, “Humm aiki? Kenan bakasan miya faru a wajen ɗaurin aureba ma?”. Kan Jawaad a ƙasa dan yaƙi yarda su haɗa ido da kakan nasa yace, “Na sani, ninema na canja list ɗin ai”. Idanu Alhaji baba ya ɗago daga littafin addu'oin dake hannunsa ya kafe Jawaad ɗin da kallo, cikin sake ɗaure fuska yace, “Ai nasan bazai wuce kaiɗinbane daman, miyasa kai hakan?”. Kallonsa Jawaad ya ɗago yayi sai kuma ya ɗauke kansa yana wani ɓata fuska, dama yasan ko kowa bai gano shi bane da wuri Alhaji baba sai ya gane.
Alhaji baba yay ƙwafa yana maida kansa ga littafin da faɗin, “A hatsabibancinka dana sani hakan ƙaramin abune a gareka Jawaad, amma ince tun randa mukaje gidan Alhaji Ali akan maganarnan ya tabbatar mana da ɗansa zai aurama yarinyarnan kace ka haƙura?”. “Hakane baba, kamar yanda na faɗa a gabanku na haƙura na barmasa da gasken na haƙuran, sai dai kuma dalilin daya biyo bayane yasa na canja shawara”. Ran Alhaji baba ya fara ɓaci, dan haka cikin zafi yace, “Kasan zan iya saɓa maka ko Muhammad? Har wane irin banzan dalili ka riƙe da bazakazo ka sanar minba kafin ka yanke masa hukunci? Banason wannan shegen taurin kan nakafa kaima ka sani”. Sosai idanun Jawaad suka sake kaɗawa sukai jajur, jijiyar kansa dukta fito ruɗu-ruɗu, yasan duk sanda zaiyi abu saiya zo ya sanarma Alhaji baba, dan a halin yanzu shine kawai ke iya nuna masa ɓacin rai idan ya aikata ba dai-daiba kuma ya tsawatar masa akan ya kiyaye gaba, to amma akan wannan shi kansa baisan miyasa zuciyar
sa taƙi aminta da ya nema sharar kowaba akan batun har sai bayan ya aiwatar..........
“Ina maka magana ka tafi tunani”. Jawaad da maganar Alhaji baba ta maido hayyacinsa yay ajiyar zuciya, cikin sanyin murya yace, “Nayi laifi kayi haƙuri, amma zuwa nan gaba kaɗan zaka fahimci hakan danai shine dai-dai baba......”
“Dai-dai ɗin ƙaniyarka, ka sakar musu yarinya ta auri wanda suka zaɓa mata, shikuma wancan habibun halan shima kaine ka kawosu shi da Azeemar? Tunda kasan har cikin ranka bakason maida yarinyarnan miyasa ka amincemin zaka maidatan?”.
“Baba nifa bani na kawosuba, su Uncle Nasir pretending kawai suke akan maganar suma, dan sunsan wacece Azeema, tunda da saninsu aka ƙulla aurama shi Qaseem ɗin ita, sannan sakin yarinyar zai zama babban kuskurene, akwai wani abu da suke ɓoyewa akan yarinyar, ka bani damar bincikosa sanan, na yarda inhar nine banda gaskiya ka ɗauki kowane hukunci”. Shiru Alhaji baba yay yana kallon Jawaad da nazarin kalamansa a ƙwaƙwalwa, kusan mintuna biyu suna a haka shiru kafin Alhaji baba ya ɗauke kansa daga kallon Jawaad ɗin ya maida ga littafinsa, “Ka dainamin ɓoye-ɓoye, ka fito fili kasanar min abinda ke faruwa?”. Ajiyar zuciya Jay ya sauke da faɗin, “Duk abinda zan faɗa a yanzun zai iya zama kuskuren abinda yake a zahirin gaskiya ne, nima a yanzu bakomai na saniba baba, sai dai insha ALLAH zan binciko duk abinda yake a binne nanda ƙanƙanin lokaci insha ALLAHU”. Tsagwaron gaskiya Alhaji baba ya hango a kalaman Jawaad, hakan yasa bai sake cewa komaiba.
Miƙewa Jay yay ya nufi bedroom ɗin kakan nasa yay kwanciyarsa.
Alhaji baba ya bisa da kallo har saida ya shige, tabbas ya fahimci akwai abinda Jawaad ke ɓoyewa, kuma da alama yanada alaƙa da Uncles ɗin nasa, bazai matsa masaba akan sai yaji komai a yau, dan yasan idan yana fushi takura masa akan abu sake busar masa da zuciya yake, sai dai yasan duk abinda Jawaad ya dage a kansa to lallai akwai abinda ya hango a cikinsa, shi kansa akwai mafarkan da yake a kwanakinnan suna damunsa, ya kuma rasa ina suka dosa?, abin mamakin shine kullum mafarkin maimaita kansa yakeyi, kayi mafarki sau ɗaya sannan ka sake maimaitashi gobe, har tsahon wasu kwanani dolene kasaka masa alamar tambaya koda kaso tureshi a ranka. Tsahon lokaci yana zaune a falon yana tunani bai shiga ɗakinba sai kusan sha ɗaya, lokacin tuni Jawaad yay barcima shi. Shirin barcin yay shima ya hau gadon, idanu ya tairama Jawaad dake barci fuska a ɗaure alamun cikin ɓacin rai yay barcin, Alhaji baba ya sauke numfashi tare da shafa kan jikan nasa, a ƙasan ransa yanajin tausayinsa, gefe kuma yana jin matuƙar tsoron irin hatsabibancin Jawaad da rashin tsoro, yana tsoron kar wani yay amfani da wannan halayyar tasa ya cutar dashi wataran. Da waɗanan tunane-tunanen fal ransa yay barci shima.
★★★★★★
Bayan tafiyar Jawaad Maman Amina ta dawo ɗakin, macece ita mai yawan ibada dama, bata wasa da ibada ko kaɗan, dan haka koda ta dawo saita ɗauro alwala takoma gefen bilkisu ta zauna a kujera dan ganin wata irin zufa da Bilkisu keyi mara dalili, gashi sai mutsu-mutsu take kamar wadda aka saka cikin wuta, Batool kuwa tana gadon mara lafiya ɗaya daya rage a ɗakin tai kwanciyarta itama. Addu'oi maman Amina taita tofama bilkisu dan zufar ta bata mamaki da tsoro, gashi akwai fanka a ɗakin tana aiki kuma, bakuma wani uban zafi akeba a garin balle ace, da alama dai mafarki Bilkisun keyi. Ahankali-ahankali gumin ya fara tsanewa daga goshin bilkisu, ta koma sauke numfashi ahankali saɓanin da datake yinsa da sauri-sauri, takuma nutsu waje ɗaya. Tajima tana mata addu'ar har kusan ƙarfe ɗaya kafin ta miƙe ta shimfiɗa abin salla