Showing 198001 words to 201000 words out of 388641 words
ta fara nafilfilinta data saba a zaune saboda ƙafarta bata jimirin tsaiwa.
Wani irin sukur-sukur maman Amina keji a ɗakin, tun tana ɗaukar motse-motsen da takejin a wasa hartakai ta fara waige-waige, tabbas tanaji a ranta akwai wani abu a ɗakin da itama bata iya hasasowa ba, tashi tai ta ɗakko jikkarta datazo asibitin da ita ta ciro Qur'anin da tazo da shi, karatu ta fara cikin suratul baƙara, sai motsin da takeji ya ƙara ƙarfi, ɗa
ga kan da zatai sai idanunta yaci karo da wata irin halitta mai kama da ƙadangare yana fitowa daga ƙarƙashin gadon da bilkisu ke kwance, sai dai kuma shi wannan farine fat tamkar babu jini jikinsa, sannan ƙaton gaske kamar kada ta cikin ruwa, jikinsa sai wata iriyar muguwar walƙiya yake tamkar ruwan dake kwance cikin teku, dukda zuciyarta ta girgiza da kallon wannan halitta mai ban tsoro dake nufota sai bakinta bai daina karanto ayoyin alƙur'anin ba kasancewarta jaruma mai dakakkiyar zuciya, tsayawa yay cak a tsakkiyar ɗakin batare da ya ƙaraso gareta ba, ya shiga goga kansa a ƙasan ɗakin kamar wanda ake duka, kafin kuma ya juya bindinsa har gab da ita ya fuskanci ƙofar fita, da gudu ya fice tamkar an masa umarni. Cigaba tai da karatunta har lokacin ta gaza ɗauke idanunta daga ƙofar. Sam Batool batasan wainar da ake toyawaba, barci take kashirɓan, bily ce dai bazamuce ga halin da take cikiba. Sautin karatun alkur'anin da Mmn Amina keyine ya tada Batool, itama samun kanta tai da shiga bayi tayo alwala, ta idar kenan ta miƙe tana gyara ɗan kwalinta zata fito taga wani ƙaton maciji jajur dashi yana silalawa ta Window toilet ɗin zai fita, ƙara ta ƙwalla tare da fitowa a guje jikinta na masifar rawa. Tazo ta ƙanƙame maman Amina dake cigaba da karatu dukda hankalinta yayi masifar tashi da ƙarar Batool ɗin, tanaji a ranta itama wani gamon tai a bayin................✍
Sannu sannu bata hana zuwa saidai a daɗe ba'a zoba. to aljanin daya canja takarda ya bayyana😂, sai muje zuwa domin jin dalilin Jawaad na canjawar da kuma tayaya ya canja ɗin, da alama kuma ya fara bankaɗo wani sirrine da zai bamu hasken sanin ina muka dosa🚴🏼. ALLAH ya daidaita sahun Jawaad akan lokaci😂, bara na fece nidai kafin ya karyani🚴🏼🚴🏼🚴🏼.
Barkanmu da dawowa, ina fatan kunsha weekend lafiya?.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[12/9/2020, 4:09 PM] HASNA✍🏻: Rasheeda Usman:
Page 24
Godiya ta musamman ga UMMINRASHIDA CARE FOUNDATION, saƙo ya iso gareni, ina muku fatan alkairin nima, tare da godiyan bangirma da jinjina, alkairin ALLAH yakai gareku aduk inda kuke. Nagode da wannan girmamawa taku a gareni, duk da har yazu dai bilyn Abdull rarrafe takeyi, Inai muku so irin trillions ɗinnan😍😍😘😘👍🏻
................Jin Alhaji baba ya fara sauke numfashi Jawaad ya buɗe idanu a hankali, juyi yay domin ya tabbatar barcin baba yay nisa tamkar a cikin barci yake, shiru baiji Alhaji baba ya motsaba, yay murmushi tare da sauka daga gadon a hankali, cikin sanɗa ya fito daga bedroom ɗin, a falonma yanayi yana waiwaye harya fice, gudun matsala yasa yabar motarsa anan ya fice daga gidan baki ɗaya, wayarsa ya ciro a aljihu ya duba time, sha biyu saura kwata, ya maida wayar a aljihu yana furzar da iska. Daga gidan zuwa titi babu nisa sosai, hakan yasa ya taka da ƙafa ya samu napep. Saida suka fara tafiya ya sake fiddo wayarsa ya duba saƙon su Jabeer daya shigo tun ɗazun, ɗan typing yayi kaɗan ya tura musu cewar gashinan a hanya.
Cikin mintuna kaɗan suka iso gidansa na A.Y, sai dai bai bari sun ƙarasa gidanba ya sauka, dubu guda ya miƙama mai napep, yana ya tsaya ga canji amma Jawaad bai saurareshiba yay wucewarsa. Mai napep ya cusa kuɗinsa a aljihu yana faɗin “gaba ta kaini inma bakasan ka baniba”.
Oho Jawaad baisan yanaiba, tunima ya shige gidan. A falo ya iske su Aliyu, kowa da hidimar da yakeyi, ya zauna cikin kujera yana faɗin, “Kuyi haƙuri na rikeku anan ga madams suna jiranku a gida”. Hafiz dake aiki a lap-top yace, “Babu damuwa ango, yanzu dai mike faruwa?”.
Ajiyar zuciya Jawaad ya sauke yana faɗin, “Akan abinda ya farune yau, nasan kuma duk a ƙage kuke da sonjin yadda akayi?”.
Hakane boss. Suka faɗa a tare idanunsu na akansa.
Bayansa ya jingina da kujera yana mai ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya, cikin ɗacin murya yace, “Kamar yanda nasan tunaniku na akan nine na canja komai hakane, nayi ne saboda labari dana samu daga majiya mai ƙarfi akan abinda Momy ta ƙulla ita dasu mama Atika. A zahiri sun tsaida bikin Qaseem ne da yarinyarnan Miemaa, sai dai a baɗini sun tanadarma Qaseem mata batare dashi kansa ya saniba. Azeemar da aka ɗaura aurensa dashi ɗiyace ga Gwaggo Hajarah ƙanwar Momy da suke ɗaki ɗaya”.
Sosai mamaki ya cika zukatan su Jabeer, Hafiz yace, “To amma miyasa sukai hakan?”.
“Wannan itace amsar da nakeson mu nemo nima Hafiz, har yanzu mamaki baibar ɗawainiya da zuciyataba akan wannan al'amarin, miyasa zasu aurama Qaseem Azeema bayan sunsan ga wadda yace yanaso?”. Jabeer yace, “Nidai a nawa ganin kamar dama basason aurensa da Mami ne, sunsan kuma kosun hanashi bazai hanuba, shine suka zaɓi bi ta bayan fage su haɗa masa guda biyu, zaɓinsu da kuma nashi zaɓin”. Hafiz yace, “Maganarka akwai ƙamshin gaskiya Jabeer, to amma idan hakane shi Habib ɗinan miya kawosa cikin wannan al'amarin, sannan wanene shiɗin kuma?”.
Aliyu datun ɗazun baice komaiba yay ƙwafa, “Ni wlhy kusan kawai minake saƙawa a wannan lamarin kuwa; Duk kallonsa sukayi suna jiran ƙarin bayani. ya cigaba da faɗin, “Inagafa su sun tsara al'amarinne akan boss ya auri Shahudah, Qaseem a bashi Azeema, ita kuma Mami su aura mata Habib ɗin, inhar ba hakanne tsarinsuba miya kawo shi habib ɗin a zancen tunda alama ta nuna babu matarsa a cikin list ɗin ɗaurin auren?”. Zaune sosai Jawaad ya tashi idanunsa akan Aliyu, yace, “Aliy wannan maganar taka haka take, abinda yake cin raina anan inhar hakanne to kenan shi Dad bai fahimci Mom batason aure Miemaa da Qaseem ba kenan? Kokuwa shima ta shirya cin dunduniyarsa ne? Tunda ɗiyar ƴar uwarsa ce”. Hafiz yace, “To nima dai abin yasani wannan hasashen, amma kuma idan mukai dubi da yanda ya tada hankalinsa bayan faruwar abun harda suma hakan na nufin baisan su Momyn Shahudah sun shirya hakanba?”.
Shiru duk sukai suna nazarin maganar Hafiz ɗin, Jawaad ya miƙe tsaye hanayensa duka cikin aljihun wandonsa, kallo ɗaya zakai masa ka fahimci ransa a ɓace yake, yace, “Basu kaɗai suka shiryaba, hardasu Uncle Nasir, abinda yasa abin ya tsayamin
arai shine, miyasa shi Uncle Nasir zai zama munafuki a tsakaninmu? Shinefa ya jagorancemu wajen Dad ni da Alhaji baba akan maganar Miemaa ɗin, saboda Ummah ta matsa akan sai dai Alhaji baba ya nemamin aurenta tare da Hudah kodan hakan ya zama gargaɗi gareta, kenan yasan shirinsu da Momy, amma kuma ya amsama Alhaji baba cewar muje muyima Dad ɗin maganar a haɗamin auren Miemaa da Hudah? Sannan sarai yasan Qaseem an tsaida masa ranar aure da Miemaa! ɗin kuma?”.
“To tabbas kam wannan matsalar daga nan take boss, Uncle Nasir yasan komai, amma kam bai ƙyautaba, dan nikam ina bala'in ganin girmansa wlhy saboda yanda ya riƙeka, ashe ba har zuciya bane, wannan wane irin zumincine muke fama dashi a wannan zamanin?, kaga yanda aka cukurkuɗe abu saboda kawai buƙatun wasu dason faranta musu, kuma duk idan kaje ka dawo zaka fahimci ita Mami itace akai shirin sakawa a tsaka mai wuya, miyasa sukaso mata wannan mugun ƙullin to?”.
Duk hankalinsu suka maida ga Jawaad da yay shiru yana nazarin kalaman Jabeer na ƙarshe akan uncle Nasir da maganar ƙullin da akaso yima Bilkisu. Cikin son maidosa hankalinsa Hafiz ya zunguresa, kallonsa yay. Hafiz yace, “Mi muke ciki yanzun? Dan ko game da Mami muna buƙatar bincike mugano gaskiyar maganar Jabeer, mizaisa suyi shirin cutar da ita?”.
Guntun Murmushi kawai Jawaad yay ya koma cikin kujera ya zana, kwantar da bayansa a kujeran yana mai lumshe idanunsa, a hankali ya furta, “Wannan shine dalilin zamanmu anan, dan inaji a raina wannan ƙiyayyar da sukaso nuna mata tawuce naƙin son aurenta da Qaseem kawai, akwai wani abu da bamu saniba, dan haka inason sanin anahinma alaƙarta da mutanen gidan”.
Jabeer ya ajiye cokali yana faɗin, “Kamar ta taɓa gayamin Dad yayan mahaifiyartane ubansu ɗaya, kaga kuwa bazai wuce Momy ta ƙitaba akan ƴan ubancin dake tsakanin Dad da mamata, sai dai kuma zata iya yiwuwa ɗin akwai wani abu a ƙasa damu bamu saniba harsai mun bincika tukunna”.
“Kai lamarinfa akwai ɗaurekai, sannan akwai lauje cikin naɗi, aganina tunda basa sonta da ɗansu su rabasu kawai basai sun zalinceta sun haɗata aure da wanda bata saniba”. Hafiz yay maganar cikin takaici.
Aliyu yace, “Kai dai bar son zuciya Hafiz, amma harma nawa Mami take da za'a mata irin wannan muguntar? Yanzu dai boss mikace kai akan batun? Tunda dai ALLAH yasa ta fita daga tarkonsu, yanzu aikin farko dake gabanmu shine Qaseem da Shahudah, baƙaramin yaƙi zasuyi a kankaba da Mami tunda. Shin Ka sanar musu kaine ka canja sunayen ne?”.
Jawaad da duk yake saurarensu cike da nazari yace, “Eh na sanarma Alhaji baba ɗazun, na nuna masa nine na canja, nakuma saka masa zancen Azeema ciki, na tabbatar zuwa safiya zai nema su Uncles da maganar, mukuma sai muyi amfani da wannan damar”.
“Amma Boss baka ganin ka ɗaure kanka da yawa? Taya za'ai ka amshi laifin kai tsaye bayan bamusan mike a ransuba game da batun?”. .
Muryarsa cike da damuwa yace, “Jabeer hakan shine kawai hanya mai sauƙi da zamu bama koma waye ƙafa, sannan Bazaka ganeba, rikicin tsohon nan ya wuce dukkan tunaninka, gara nafito na faɗa masa gaskiyar maganar, harfa ya kafamin sharaɗin saina saki Miemaa, yanzu dai nagama da matsalarsa”.
Dariya sukayi a tare, cike da tsokana Jabeer yace, “To tsakani da ALLAH gaskiya Alhaji baba ya faɗa, ka bama Qaseem matarsa”. Banza yayma Jabeer ɗin, ya miƙe yana kallon agogon hanunsa, “Kunga ɗaya harta wuce, mu tsaida maganar iya haka, zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu nasan Alhaji baba zaisa ai zama akan batun, anan zan fahimci yaren kowa, daga nan saimu ɗora da abinda ya dace kawai”.
Duk sunyi na'am da jawabinsa, kowa ya miƙe yana tattare kayansa kafin su fito, Jawaad tare suka tafi da Hafiz zai ajiyeshi gidan Alhaji baba saboda hanyarsa ce shi, su kuma su Aliyu kowa ya shiga motarsa.
★★★★★
Da sanɗa Jawaad ya shigo bedroom ɗin duk dan karyay motsin da zai tada Alhaji baba, a bazata yaji yace, “Daga ina?”. Tsam Jawaad yay ya kasa ƙarasawa, cikin sauke ajiyar zuciya yace, “Nafita akan wani aikine”. Alhaji baba baice komaiba, hakan yasa Jawaad
nufar toilet dan ya watsa ruwa.
_________________________________
A asibiti kam daƙyar mama ta kwantarma Batool hankali, Cikin sarƙewar numfashi da tsananin tsoro tai mata bayanin abinda ta gani a toilet, shiru maman Amina tai tana nazari da haɗa komai a mizanin daya dace, a fili kuma sai tayi murmushi tana mai girgiza kanta, cikin bama Batool ƙwarin gwiwa ta umarceta akan ta tashi tai sallarta koma minene ALLAH zaiyi maganinsa. Jiki a sanyaye Batool tabi umarnin Mama.
Haka suka kusan kwana akan abin salla suna gayama UBANGIJI damuwarsu, gabannin asuba bilkisu ta farka tana ambaton a bata ruwa. Fita Batool tai ta kira Doctor'n daya kwana duty, babu jimawa suka dawo tare. saida ya tabbatar babu wata matsala tare da Bilkisun sannan yace su bata ruwan tasha.
Tunda ta kafa kai a babban goran ruwan da Batool ta saka mata a baki sai da ta shanyesa tas sannan ta ɗauke kanta, dukansu kallon mamaki suke mata hatta da Doctor ɗin kansa, sai dai babu wanda yace komai.
murya a sanyaye tace, “Mama zanyi sallah”.
Taimaka mata batool tai ta sakko a gadon, mama ta rakasu har toilet ɗin ta sirkama bilkisu ruwan wanka da ruwan dake cikin flask, fita batool tai, mama ta taimakama bilkisu tai waka da gasa jikinta dukda tana ta noƙewa saboda kunya. Itako mama sai tayi kamarma bata gantaba. Bikisu taji daɗin wankan sosai, takumaji karifin jikinta, sallolin dake kanta ta shiga ramawa harda sallar zuhur ɗin jiya data tabbatar batayita cikin nutsuwaba.
★★★★★★
Zuwa 10:30am na safe dukkan mai alhakin tofa albarkacin baki akan wannan matsalar ya hallara a gidan Dady, bisa umarnin Alhaji baba daya buƙaci hakan, dan yanason jin gaskiyar magan akan abinda Jawaad ya faɗa masa gameda zancen Azeema da yace sunsani. Jawaad yana jerin waɗanda sukazo a farko-farko dan tare yake da Alhaji baba, hakan kuwa yaso bama kowa mamaki dan sunsan halinsa sarai da iya ƙin zuwa wajen meeting akan lokaci saiya gama shanya jama'a, amma yau abin mamaki sai gashi cikin masu sakkon zuwa.
Bayan isowar Imam da wasu daga cikin manyan massallacin da aka ɗaura auren Salman da Qaseem daya rame sosai tamkar wanda ya kwana biyu yana jiyya suka shigo suma, ya ƙara haske da tsayi abin tausayi, Jawaad dai baiko kalli inda Qaseem yakeba, amma shi Qaseem sai binsa yake da wani irin mugun kallo tunda suka shigo.
Imam ne ya buɗe taro da addu'a, a kuma dai-dai lokacinne Shahudah da Mom da suka taho daga asibiti bisa matsawar Shahudahn suka shigo suma, wajen zama suka samu idon Shahudah akan Jawaad tana mai kwarar da hawaye, itama harta rame kwana ɗaya kacal. Bayan imam ya kammala addu'oi ya ɗaura bayani da cewar, “Nasan kowa dake nan yana neman amsar tambayarsane a gareni, wadda yinin jiya har zuwa dare na ɓata lokacine wajen nemota nima amma har safiyar yau ban samo amsarba, narasa wannan wane irin cuɗaɗɗen al'amarine mai sarƙaƙiya, a hasashena har junnu saida na kawo dukda bani da tabbacin haka balle hujja, ban saniba shin ko a cikinku wani nada amsar da nima nake cikin ruɗani da bulayin nemanta?”.
Shiru falon yayi babu wanda ya iyayin koda tari, sai shashshekar kukan Shahudah kawai ke tashi. Uncle Nasir ne yay ƙarfin halin bama Shahudah umarni akan ta tashi ta fita. kafaɗa ta maƙe alamar bazata tashinba, ta koma jikin Momy ta lafe tana masa kallon harara dukda kasancewarsa wan uwarta. Babu wanda ya iya sake cewa komai game da tashin Shahudah, dan kuwa anga iyayenta basu tankaba alamar basu da damuwa da zaman nata su. Jawaad yay gyaran muryar da kowa ya maida hankali kansa, batare da ya kalli kowaba yace, “Imam kayi haƙuri, babu ta inda zaka iya samo amsar sarƙaƙiyar jiya kaida duk wanda keda alhakin sanin sirrin massallacin nan. Ni dasu Momy mune kawai masu wannan amsar, dukda inada tabbaci da yaƙinin bayanmu wasu sunsan komai koda ba duka ba”. kaf falon babu wanda bai sagade yana kallon Jawaad ba, yayinda Momy ta miƙe zumbur tana nunashi, “Amma kai dai Jawaad anyi shaiɗanin yaro, a gidan ubanwa nake da amsar? Ni dama tun jiya da akace an nemeka an rasa nasan kaine shaiɗanin daya dace a nema dukka
n amsoshinnan a wajenka.......”
Murmushi Jay yayi, sai dai baice komaiba, hasalima kansa a duƙe yake bai kalli kowaba har yanzun. Alhaji baba ne ya tsaida Momy jin tanata aibanta masa jika, “A'ishatu, inaga mubashi dama muji ina maganganunsa suka dosa kafin mu yanke hukunci koda na furucin bakine, mudukanmu nan a ƙage muke dason jin amsa, yakamata muji yaya akai aka kwana a ragaya bayan munsan shirinmu a tandun mai ne”. Magana Momy zata sakeyi Qaseem yace, “Momy Please ki zauna miji munafurcin dazai faɗa”. Ƙwafa Momy tayi ta koma ta zauna saboda gargaɗin da Uncle Uwaisu yay mata da idanu.
Shirun da akaine ya saka Jawaad ɗagowa, yace, “Inaga kafin warware dukkan sarƙaƙiyar massallaci yakama musan wacece Azeema da aka ɗaurama Qaseem aure da ita? Domin wannan shine kawai zai zama mabuɗin buɗe mana gaskiyar abinda muke son sani baki ɗaya”. Tsit falon yay saboda bugawar da zukatansu sukai a lokaci ɗaya babu zato ko tsammani da zuwa furucin Jawaad ɗin a garesu. Alhaji baba ya katse shirun da cewar, “Banda abunka Muhammad Jawaad muma ai duk amsar da muke nema kenan akan Habib da Azeema?”.
Jawaad yace, “Hakane Alhaji baba, amma ina ganin karmu jata da nisa, domin su Uncle duk sunsan wacece Azeema da Habib, idan ka cire Imam da jama'arsa, kai da Uncle Sulaiman, Uncle Sadiq, Qaseem, kune kaɗai kuke neman ƙarin bayani”. Uncle Sulaiman yace, “To mukam saiku amsa mana kunata sake dilmiyar damu a hasashe”. Fuskar Uncle Nasir a matuƙar ɗaure cikin kafe Jawaad da idanu yace, “Mikake nufi da waɗanan kalaman naka?”.
Jawaad yace, “Babu abinda nake nufi Uncle, kawai dai ina son kowa ya fahimci daga ina matsalar take harshi Qaseem ɗin da aka ɗaurama aure.......”
Cike da masifa Momy ta sake katse Jawaad da faɗin, “Inma wani munafurci ka ƙulla kai zai ƙaremawa, inace dai sokake kace mune muka haɗa auren Azeema da Qaseem batare daya saniba, to ai mun isane, yarinyar da ya kawo yanason zai aura batai manaba, tayaya idan shi baisan ciwon kansaba mu zamu biye masa duk muzama mahaukatan?”.
Cikin ɓacin rai Jay yace, “Amma miyasa ni da nazo neman a bani na aura kukace Qaseem shi zai aureta?”. Yanzukam tamkar Momy zata mari Jawaad ta bashi amsa a matuƙar zafafe “Saboda Shahudah tafi ƙarfin yin kishi da ita, bandama rashin mutunci da raini irin naka Jawaad, bakaji kunyar zuwa a gaban idanunmuba kace mu haɗa maka ƴar cikinmu da wadda mukema alfarma mu aura maka”. Sosai zuciyar Jawaad take sake hasala,