Showing 108001 words to 111000 words out of 226733 words

Chapter 37 - Alkalamin Kaddara ta Complete Hausa Novel

Sajida   

11 Sep 2025

7953

shi
Su dukansu ta yiwa haka sannan ta dauka ta saka a frij wajen yin sanyi ba wajen yin kankara ba ta rufe ta koma wajen dankalin turawanta

Ba ita ta waiga wajen naman nan ba sai da ta gama bare dankalin turawan nan tass sannan ta yanyanka shi dukanshi, zuwa lokacin ta dauki kusan minti talatin ta zuba dankakin turawan a cikin babar roba mai tiloli dan ya tsane ruwansa shima gaba daya sannan ta koma ta ciro naman nan
Anfanin saka naman da ka shafawa jajagen nan a frij shine kayan zasu ratsa shi sosai ta yadda dandannonsa zai fi fitowa sannan zai fi gasuwa komai taurinsa domin hadin nan na saka namaa ya yi laushi ya yi gagawar gasuwa

Abin gashinta ta ajiye ta dauko takardar da ake siyarwa ta gashin nama ko cake t yanka ta saka a cikin abin hashin sannan ta dauki mai ta shafa sosai ta dora yanka biyu ta koma wajen foor dinta da ya gama daukan zafi a 250 wutar sama da ta kasa ta bude shi ta saka naman ta rufe sannan ta rage karfin wutar zuwa 200 dan kar naman ya dauki hanyar konewa bai gasu da kyau ba sannan ta komawarta wajen dankalin nan ta kunna wuta ta dora kasko ta zuba isashen mai sannan ta juya wajen kayan tea dinsa ta shiga harhadowa dasauri da sauri dan ta dora shi gefe shima ya dafa kansa a kan lokaci
Man nan na yin zafi ta yanka albasa karama ta jefa cikin man suyar, hakan na saka dankalin turawan bada wani kanshi mai dadi da dandano
Zuba mai yawa ta yi tana tsaye a gabansa har ya fara ja ta juya shi ta yadda dayan barinma ya dauko jan sannan ta rage wutar ta kwashe shi cikin abin tsanewa, da gagawa kuwa sai ta kawo gishiri na cikin kwanko garin nan ta dan yayafa da zafinsa ta juya shi ta yadda gishirin zai gamu a jikinsa gaba daya sannan ta zube sauran a man ta bar wanda ta kwashe din ya idasa tsane mansa bayan ta yafa kyale mai tiloli gudun wani abu ya fada kafin ta kawo abin zubawa

Nan da nan ta gama aikinta, a awa biyu danma aikin hannu daya ne kuma sai da ta bari ya gasu sosai , zuwa lokacin har ya dawo daga sallar isha'i yana mamakin aikin da yayarta ke sha ba ji ba gani falon ya dauki kanshi an gyara ko'ina masha Allah ya haye sama yana dan dafe cikinsa domin har ga Allah shi baya wasa da cikinsa sam

A hankali take tafia da kayan da ta jera tana adu'ar Allah kaita dinern lafia har ta fito suka hade da Nahidt
A nutse ta ce" Wauh, Masha Allah......Shuwwa wadinnan plat din fa da kayan shayin?"

SHUWWA ta ce" rufa min asiri na ajiye kafin na barar sai na kaiki ki gansu, kulun su ke sake sakani yin sabon girki da su walahi"

Nahidt ta ajiye turaren wutar da take yawo da shi ta kama mata gaban tana fadin " ki rage kayan mana kar garin hawa ki zubar"

SHUWWAR ta ce" Hawa ina kuma? "

Nahidt ta dubeta a tsanake ta ce" saman mana, ko ba dakinsa zaki kai masa ba?"

SHUWWAR ta girgiza kanta
Nahidt ta yi Murmushi tana fadin" mu ai a nan zamu ci ko? Muna so muci cikin sakewa ko? Ki kai masa Kawai mu sai mu baje a nan , domin kanshin gashin nan na halaka min yawu"

Yar dariya ta yi ta gyada kanta ta juya hanyar hawan a hankali tana hawa tana adu'ar Allah ya kaita lafiya da tunanin ko ya ci? Har ta haye sannan NAHIDT ta yi murmushi tana girgiza kai a ranta tana ayana'gidan rigima kennan, da ban yi mata dabarar ba, ba zata Kai ba"

A hankali ta samu ta bude ba tare da ta nemi izini ba domin kayan dake hannunta ko budewar Allah ne ya taimaketa ta iya budewar

A hankali ta shiga da salama a saman lebenta kasa kasa ba tun karfi ba dan kar ta saki farantin

Idannuwanta suka sauka a saman kansa yana zaune saman wata lalausar kujera ya mike kafafuwansa da alkur'ani mai girma a hannunsa yana karatu cen cikin kirjinsa

Samun kanta ta yi da zuba masa ido , ga wani sansanyan kanshi na tashi a dakin wanda ga dukan alamu turaren ruwa ne ya saka mai sanyin kanshi dan yaa ji dadin zaman

A hankali ta karasa ta samu ta ajiye masa a gefensa ta sake zuba idannuwanta a saman gashin da ya lulube kafafuwansa
Haka kawai ta ringa bin jikinsa da kallo dan neman rigima har sukai ido hudu da shi, wanda hakan ya sakata dan hade fuska tana basarwar nan kamar kallonsa ba dan wata niya ta kalleshi ba ta yatsina fuska tana cije lebenta na kasa hadi da juyawa gaba daya ta mike da niyar tafiyarta dan ta kula kallon nan nasa kamar yanai mata kallon kyama ne!

Ajiyar Zuciya ya sauke yana girgiza kansa kasa kasa ya ce" My bed 🛏️"




Turus ta yi ta juyo ta kale shi na yan sekwani sannan ta cire kanta ta nufi wajen gadon

Yayewa ta yi ta yi mashine wash da su , sai da ta gama wanke su ta fitar ta fito ta bude dayar kofar da igiyoyin shanyan suke ta je ta shanya su
Har ta juyo zata filo ta samu kanta da kurawa wajen abin fitila ido
Abin ta sake kurawa ido sosai tana kallonsa kafin ta juya ta fito falon daidai ya dasa aya yana rufe alkur'anin ya mike ya nufi wajen ajiyarsa ya ajiye sannan ya juyo yana fuskantarta domin ya tabata tsayuwar nan da ta yi magana ce a bakinta

Ajiyar Zuciya ta sauke tana kawar da kanta gefe ciki ciki ta ce" Am, am, am .............."

Kasa karasawa ta yi, shi kuma ya tsaya ya zuba mata ido har zuwa gaban goshinta da gargasar gashin wajen ke bashi mamaki
Idannuwanta ta dago ta dube shi sai kuma ta dubi hanyar da ta fito da hannunta ta dan nuna kafin ta kale shi ta dan shagwaba fuskarta tana sirintar da dubanta ta sake daukan duban nata ta sauke a hanyar da ta fito, hakan ya saka shi gane da abinda take nuna masa

A nutse ya taka ya zo ya gitata ya shige ciki, ya hara mata sansanyan kanshin turaransa da ya sakata lumshe idannuwanta ta bude ta raka bayansa da kallo sannan ta iya cira kafafuwanta da kyar ta bi bayansa

Wajen da ya fi dauke mata hankali ta yi ta nuna masa da idannuwanta har ya ga wajen shima
Tsakani da Allah zuwa yanzu ya amshi gayatar wannan neman fitina, zai kuma nunawa mai yi cewar ba sani bane bai yi ba so ya yi ya sirinta, aman tunda wulakancin ya kai haka zai kwatanta masa shi riga yake da ita wace ta bashi damar taka wulakantace!

Da idannuwansa ya mata alamun ta wuce

Wucewar ta yi sumui sumui ta fito a dakin gaba daya

Gannin yana biye da ita ya sakata dan yin sauri ta sauka ta nufi dakin Nahidt domin ta gama komai ta zuba abincinta ta yi shigewarta dan dama babu abinda zata yi jira ai, da gangan ta cewa Shuwwa a nan zasu ci, aman me zasu wani ci a nan? Ai du abinta ta san daidai ta san akasin daidan

A nutse ya bude ya biyo bayanta bayan ta shige

Salama ya yi a saman lebensa sannan ya daga kansa ya shiga bin dakin da kallo kafin ya dawo da dubansa kansu sun yi tsuru tsuru sunna kallonsa gaba dayansu a tsaitsaye

Dan gyaran murya ya yi ya ce" Ku shirya mu tafi"

Daga haka ya so ya juya, sai fai tambayar da SHUWWA ta masa da sauri tana kallonsa cewar ina zasu tafi? ya saka shi juyowa a hankali ya ce" Capital "


A tare suka maimaita Capital?, Yana nufin garin iyayensa kennan fa?, Sai kuma Shuwwar ta ce" Aman yaushe?, Kuma da wa da wa? sannan a me? sai nake gannin dare ya yi ai yanzun?"

Nahidt ta gyada kai domin itama so take ta san amsoshin nan har ga Allah

Dubansu ya yi daya bayan daya
Ko dan kwali yarinyar nan bata da shi a kanta, kuma abayar tata daga sama fa ta riketa sosai walahi

Kai ya girgiza yana sake kallonsu ya dubi agogon bangon dakin ya sake dubansu a kausashe ya ce" Now "

Daga haka ya juya ya fice a dakin, hakan ya sa suka kalli junna Shuwwar ta ce" Na ga annabi in na yi hali na gari, ke kuma me yakr nufi? "

Nahidt ta yi sakalau ta ce" Shuwwa ni na sani ne? Kin ga cewa ya yi Now, to yana nufin yanzun yanzu wai zamu yi doguwar tafiyar nan? Ko dai mutuwa aka yi ?"

Rai a hargitse SHUWWA ta💔❤‍🔥💔❤‍🔥💔❤‍🔥💔❤‍🔥💔❤‍🔥
*ALK'ALAMIN K'ADDARA TA*
‍💔❤‍🔥💔❤‍🔥💔❤‍🔥💔❤‍🔥💔❤‍🔥


*The Hero writer*


*SAJIDA*


_Bismillahir rahamanir rahim_


PAGE:. 3️⃣7️⃣



*P͓̽R͓̽E͓̽S͓̽E͓̽N͓̽T͓̽*






*S̉T̉ỎR̉Ỷ ẢN̉D̉ W̉R̉ỈT̉ỈN̉G̉ B̉Ỷ*


*S͞͞A͞͞J͞͞I͞͞D͞͞A͞͞*



*T͞͞H͞͞E͞͞ H͞͞E͞͞R͞͞O͞͞ W͞͞R͞͞I͞͞T͞͞E͞͞R͞͞'S͞͞ 👇🏻*

1 *yar mahaukaciya*
2 *Banida zabi*
3 *Duk karyar kada*
4 *Baka ce*
5 *Daga tafiya daukar soja*
6 *Kutkale*
7 *Makauniya ce*
8 *Mage mai kwanciyar daukar rai*
9 *Duk nisan jifa*
10 *Dutse*
11 *Idan Ka Raina Inda Kake*.
12 *Neman Na Kaina*
13 *WATA KOKOWAR*



*The Latest Qualitative New Book ALKALAMIN KADARRATA*


*WANNAN BOOK NA KUDI NE BA FREE BANE, IDAN KINA DA RA'AYIN KARANTASHI KI GARZAYO KI BIYA KUDINKI YAR UWA ZAKI SAMU BONUS NA DUKAN LITATAFAINA CIKI HARDA NA KUDIN DA NA GAMA KWANAN NAN, KI GANE................ALKALAMI NA DORA, NA ZUBA RUBUTU......IN SHA ALLAH ZAKI NISHADANTU SANNAN KI KARU💓💓💓*

Zaku biya kuɗin ku ta wannan account numbern 0225962748
Amina Maikudi Abdullahi
GTBank Naira 300 ne kacal zaku biya anyi araha an hana bashi.

Ko ku turo Recharge card ta wannan numbern wayar
08038856944 banda vtu hoton katin zaki ɗauka ki turo.

Sannan Sai ku tura shaidar biya ta wannan no din +22793811618


Ga ƴan Niger zaku biya kuɗin ku ta wannan layin +22793811618 katin sahelcom ko AIRTEL ta dala DARI ne ( 500 francs cefa) sai ku tura shaidar ta layin nawa sannan na saka ku a grup din

Sai kun zo🥰🥰🥰🥰🥰

*AUNTY SAJIDA NI FARA CE, MATSALATA BAYA KYALI, HAKA KUMA INA DA YARINYA DA NA HAIFA ITA KUMA TANA DA DAN DUHU KASANCEWAR MAHAIFINTA BAKI NE, DU IRIN SANYIN AC DA CIMA MAI KYAU BAMA KYALKYALI IRIN NA YAN GAYU, GAMU A GARI KUSA DA SHUGABAN KASA.......*
😂.............................................................................
Amsa " Dan gwada shafa madarar ruwa peak a fuskarki idan da hali har hannayenki, sannan itama ki gwada shafa mata kadan ba da yawa ba, da zarar kin bude ki saka a frij bata komai, idan kun shafa ku barta ta bushe sai ku wanke da ruwa kadai marar sanyi karara sannan marar dumi...........kyalin fata kike so? Zaki bani bayani yar uwa🥰🥰🥰🥰🥰🥰



Rai a hargitse Shuwwar ta ce" Koma menene ai sai a yi hakurin gannin safiya ko? Ni tsorona Allah tsorona kar cen zai kaini ya kashe ya birne ba tare da aj masa komai ba, kin ga tunda Allah ya hada hanyata da shi nake haye masa nake nemansa da fitina, ta yiwu na kaishi bango ne"......... Ta idasa da yannayi na son ta fashe da kuka , dukkan tsoron tafiyar na bayana a tatare da ita

Nahidt da ta juya ta fara harhada yan kayayakinta ta juyo ta ce" ki yiwa Allah ki daina fadin haka, yo idan ya kasheni ban auri Malan ba ina zan saka raina, kin kuwa san yadda nake tunanin gani gashi a matsayin mata da miji? Ki rufan asiri na mutu maza su kaini ba mata ba"

Kai Shuwwar ta girgiza tana tsaki tare da bala mata harara ta juya ta bara mata dakin ta nufi dakinta tana gunaguni

Cikin jerin akwatunnanta ta janyo wata galeliya ta ajiye ta bude ta firfitar da kayan ciki sannan ta shiga bude sauran akwatunnan tana duduba kayan da take gannin su suka dace da zaman cen, watau rantsatsu yan kasa da kasa wa'inda zata iya zama a kusa da kishiya da su

Haka kawai ta samu kanta da tunanin wai yanzu wajen da yake da wata matar zasu je su zauna?
Sai kuma ta yatsina baki tana ayana 'dadin abin ba damuwata bace , Allah ya sa uku zan tarda matsalarku ce kai da su'

Da gudu ta fada bayi ta yi wanka a gagauce, ta dauko brosh da su sabulu da maclean ta hado da tawul, da su abin busar da gashinta, kai su kayan kwaliyarta, su turarenta, ita dai abubuwan da ta tsaya yi sun dauketa lokaci mai yawan gaske domin sai da ta kusan awa biyu a ciki hakan ya sa dare ya karra yi, harma tana tunanin tabas an fasa tafiyar domin sun yi dare ai

Wando dogo ta saka ta dora farar riga mai dan dogon hannu sannan ta saka abaya mai botira a gaba marar kyalkyali ta dauko mayafinta ta yafa bata nada ba ta shiga wanke jikinta da sansanyen turarenta sannan ta dauki su cazarta, da turaran da take shafawa lokaci zuwa lokaci du ta zuba a jakar sannan ta shiga kiriniyar janyo sauran akwatunnan biyu ta fitar ta koma ta tofe dakin da adu'a ta janyo ta rufe ruffff da ky dinta ta jefa a jaka ta dakata tana kallon dakinsa
Gannin Ky dinsa a jiki sai ta bar akwatunnanta ta je da dan gudu gudu ta bude ta leka kanta
Gannin ba kowa ciki sai ta samu kanta da shigewa tana lelekawa
Ba kowa, ga abincin da ta kawo kamar an zuba tea din aman abincin ba'a ci komai ba

Leda ta shiga nema ko Allah zai sa ta samu
Ai kam ta ga irin ledojin nan na kampani wada ya sayi wani agogo a wani kampani ko agogon bai cire a ciki ba, hakan ya sa ta saka agogon a jakarta ta zo da ledar ta juye gashin nan tsaf da soyayen dankalin turawan nan sannan ta juyo da sauri ta fito bayan ta kule ta cusa a jakarta suma ta fito ta kuma janyo akwatunnan giri giri dadin abin daya ne takalmin da ta saka kafa ciki ne mai dan karamin tallon sosai, kuma ya yiwa kafar tata cif da cif hakan ya sa bata shan wahalar tafia da shi ta ringa saukowa da dan sauri ta juya ta janyo jaka daya sannan ta janyo daya da haka har ta idasa saukowa dana nishi ta janyo su ta nufo falon da take jin muryar NAHIDT na yar daria

Turus ta yi gannin Nahidt zaune saman kujera tana labari tana daria abinta shi kuma kamar ya samu TV sauraronta yake yana kuma kallonta sai a ransa da yake fasara dukan kalamanta

Nahidt ta yi dan murmushi ta ce" Ai yalabai wannan dalilin ya sa zaka ga wani lokacin sai a hankali, ai marayu ne mu bamu da uwa bale uba , lamarin sai gyaran Allah, daidaiku suka san hakin maraya, daidaiku suka san Allah baya so a taba maraya, daidaiku suka san shafa kanmuma alkhairi ne, yanzu haka dai kwanaki aka ce ko da danginmu a nan wajen? Shi kuma wanda ya zo din nan yayanmu ne shi dinma shine nake fadawa Shuwwa kulun cewar du inda zamu je in sha Allah ba za'a kashemu ba a duniya Allah zai saka tausayinmu a zukatan jama'a wannan ai lamari ne na ubangiji ko Yalabai?"

Kai SHUWWA ta girgiza tana dane dariyar Nahidt a ranta tana ayana' Da ace sunna da tausayi sojoji ai da ba zasunna kashe mutane ba, in zaki tashi ki tashi Allah ya sa mutuwa hutu ce a garemu kawai!'

A hankali ya maida dubansa saman kanta , sannan ya sauke idannuwansa a saman akwatunnan da take janye da su maka maka biyu masu kala daban daban, irin gata mai kala kala din nan

Bakinsa ya tabe yana gannin yadda wandon dake ciki shima fari kal ke bayanar da kansa hakan ya sa ake gannin girman cinyoyinta ta cikin abayar dake jikinta sannan ya dan juya cikin dabara yana satar kallon camerar dake boye wajen jerin fitilun dake lake ya sake juyowa yana kallonta da karra bin yafawar mayafin abayar da ta yi da kallo ya kuma samu kansa da ayana magana kamar haka ' Shi kuma turaran ko na meye? '

Bakinsa ya tabe ya mike tsaye yana duban agogon hannunsa hakan ya sa su dukansu suka kalli hannun nasa suma

Nahidt ta yi wani murmushin tana fadin" Ga dukan alama dare ya yi Yalabai tafiyar ko sai Ido na gani?"

Dan sake kallonta ya yi ya girgiza kansa ya yi wajen kicin da karkashe dukan abinda ya dace a ransa yana ayana' Ita bata gajiya da surutu ne? '

Da ido suka raka shi, kasa kasa Nahidt ta ce" Shuwwar koda kashe mun ya yi da daren nan babu mai sani, Allah mun gode maka haka rayuwa zata yi da mu ashe"

SHUWWAR ta zauna itama tana rafka tagumi tana kallonta
Wayarta ta bude ta shiga dora numbobin Aban Shuwwa ta zauna a gefenta tana sauraro

Wayar na fara ringin ya daga kiran da doguwar salamarsa

Da hausa ta ce" Kaima ya tabata a gareka amincin Allah, Aban Shuwwa kana ji?"

Malan ya gyada kansa yana sauraronta
A sanyaye ta koma yaren larabci sak ta ce" Ina sonka, (ana ahbuk ya habiby), inta amri ya hayati, inta amry ya nurry.........."

Fitowar MUHAY ya yi dan turus yana kallonsu da larabcin da take shekawa,
Da dan gagawa ta ce" Kai dai ka ringa gwada kirana lokaci zuwa lokaci idan Allah ya sa na kai gobe na yarda a daura auren nan, Aban SHUWWAR ina sonka sosai ka ji?".....................kit ta kashe tana kallon SHUWWAR da kikifta ido

SHUWWA ta yi yar dariya tana mikewa ta kara rungumar akwatunnanta da niyar bin bayansa

Juyowa ya yi yana kallonta a hankali ya ce" Barsu ".......................

Yana gama fada ya fice a dakin gaba daya
Sake juyowaa ta yi a haukace ta ce" In barsu?"

Nahidt ta daki kafadarta tana fadin" Ke banza yana nufin mu barsu yarensa su dauko mana,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login