Showing 192001 words to 195000 words out of 226733 words

Chapter 65 - Alkalamin Kaddara ta Complete Hausa Novel

Sajida   

11 Sep 2025

7985

sha ua sakar mata murmushin da ya sakata sake kafe shi da ido

A hankali ya ce" Wai me ya cinye bakin, ki min magana mana"

Ita dai ta dawo daga rakiyar kililin kasau macijin kumbarsa, sani ne bai yi ta gama gane cewa shi din nan idan ya samu makararen waje zai karta ne kawai, dan haka zata fuskance shi su fuskanci junna , dama ta jima da sannin ba kaunarta yake yi ba, ya jima burinsa ya saketa, yanzun kam ta dangana da auren, ta hakura haka, ta yarda aure ya fi karfinta ita ke masa shishigi, ta hakura duniya da kiyama ta kamanta ai sosai ta kamanta

Bed din da yake nuna mata ta bi da kallo, ta sake kallonsa kafin ta girgiza kanta a hankali tana sake matse idannuwanta

A sanyaye ya ce" Oh sorru Ebti, kin san dai nima ba zan karra ba bayan na ga kin ji ciwo ko, saima da safe na kaiki wajen su Mama su fada mana me zaki sha ki warke, plz zo na kwontar da ke ki huta kin ji?"

Bakinta ta bude muryarta a shake ta ce" Ni dakina zan je, ni ni ba zan iya ba, ba sai mun je tare wajen su maman ba, daga nanma ka bani takardata sai na je da kaina wayo Allahna zafi nake ji da ina magana wayo nan dina....."
Ta idasa da nuna Wajen tana neman durkushewa

Du irin yadda maganar ya bata takardarta ta soke shi gannin zata kai kasa a durfafe ya durfafeta ya kuma dauketa a hankali ya kaita saman gadon ya shinfidata kafin ya haye ya sakata a kirjinsa a hankali ya ringa dan shafa bayanta ta yadda du irin yadda ta kai fa kokowar ya barta har ta yu laushi ta yi shiru tana sauraron yadda zuciyarsa ke dokawa, kafin a hankali idannuwanta su ringa yi mata nauyin gaske har maganin nan ya ci karfinta barcin ya yi awon gaba da ita

Sai da numfashinta ya tabatar masa ta yi barci mai karfi sannan ya cireta a jikinsa a hankali ya zubawa fuskarta ido

Dan murmushi ya yi a hankali ya manawa lebenta kiss a kasan zuciyarsa yana ayana' Na dauki maganar na sake ki a matsayin zafin ciwo da kika samu a tare da ke, domin an ce dukan macen da bata tabaa sannin da namiji ba ko yar karamar yatsa aka zo da niyar saka mata a jiki sai ta ji zafin haka balatana jikin namiji ginane, tabas nan din gonata ce, ke din kuma Allah ne ya bani, ko ba komai ai da kunya yarana su ji matar da suka aura min da gumin aljihunsu na saka itama?, IBTISAM kece sirrina, kuma yadda Allah ya tsaftace min ke, ya karre min ke du irin gwagwarmayar da kika ganni ta rayuwa na yarda cewa Allah ne ya ajiye min uwar y'ayana a kilace da irin kilacewarsa, Allah ya yi maki albarka ya karre min ke My Princess'

Da wannan ya sake komawa ya tofeta da adu'a shima ya yi ya shafa sannan ya kwonta ya sakata a jikinsa ya shiga neman barci

_____________________________________

Abinda ke sake yi mata yawo a jiki har ya haye ya nufo kunnenta ta saka hannunta ta kuma dokewa tana korewa sannan ta yi mika kadan da niyar kuyawa hadi da jan bargon da take lulube da shi tun bayan sallar asubahi da ta yi ta koma ta nade tanama tunanin du inda al'adarta take a wunin yau ko wayewar gobe zata ganta ta kuma shan maganin ciwon nan da ya bata domin sarai ta ji dadinsa hakama da ta sake shiga ruwan dumin sosai ta ji dama dama a kan abinda take ji, dan kuwa barta dadewar da wajen ya yi ya mutu murus in ba motsawa ta yi da karfi ba bata jin zafin, hakan ya sa ta smau wani lafiyayen barcin da yinwa bata samu damar tashinta ba

Dan murmushi ya yi ya sake anfani da gashin dawisun da ya zagaya ya dauko a wajen da aka zuba masa su dan kiwonsu da yake sha'awa bayan fitarsa ya jibgo mata gasasun kajin harma da wasu abubuwan na marmari,, ya kuma je gida wajen mahaifiyarsa ya bukaci a fada masa abinda ta fi so a rayuwa, irin annurin dake fita a fuskarsa ya saka mahaifiyarsa gagawar dago maganar dake dankare a zuciyarta, harma ta yi gagawar saka Nahidt hada mata abinda take so ta hada masa taa yi masa rakiya har wajen mota tana ta so a kan dole sai ta yi tambayar da zai fito mata fili, aman dukan tambayoyin da take masa sai dai ya saki lalausan murmushin dake sakata a mamaki ya bata takaitaciyar amsa har ya tada ya tafi gidan da fatan Allah ya sa bata farka ba

Ko da ya dawo kuwa tana barcin shine ya saka komai yadda ya dace ya rage karfin ACn sannan ya je ya dauko gashin nan ya dawo ya cire rigar dake sama ya bar ta ciki mai dogwayen hannu fara mai botira sannan ya dan bale sama saman kwaya ukun ya bar sauran

Kuma dokewa ta yi da fada fada ta ce" Nahidt in ban hannaki fira da ubana ba ki ce min ni ba yar babana bace!"

Dan murmushi ya sake yi a karro na hudu ya sake Kai abin wajen wuyanta dake ta sheki ya sake shafa shi

Raf ta yi da shi tana wartsakewa hadi da sakin kukan shagwaba, sai kuma ta yi tsittt tana wawara ido da tino cewa bafa a gida take tare da yayarta ba, hakan ya sa ta zabura da dan karfi ta mike zaune, sai dai zafin ya sakata saurin rintse ido tana furta" aushhhhh wayo Allahna nan dina......."

Da sauri ya yarda abin dawisun ya idasa hayewa saman gadon gaba daya yana fadin" Oh sorry, I'm sorry an mata , in ga wajen in ga nan din naki.......?"

Matse kafar ta yi tana zarro ido tana kallonsa hadi da turo bakinta ta sake matse kafafuwan tana fadin" Me zaka gani? Allah sawaka"

Wani murmushin ya yi yana duba agogon hannunsa ya ce" Kin ga, karfe goma ce ta gota kina ta barci, bayan na ji tsare tsarem dake gabanki na aurar da babar yaya, me zai hanna a matsayinki na matar soja ki murje ki ba marada kunya ki ci kazarki gatanan tana kallonki sannan mu shiga rubuta abinda ya dace mu yi a bikin nan? Nine fa baban amarya......" Ya karashe yana kanne mata ido daya

Hannunta ta dora a saman bakinta da mamaki ta ce" Muhamadu rasululahi sallalahu alaihi wa salam, a ina aka taba yi kai mijin kanwarta kuma ka zama baban amarya? Hana dai "

Idasa zama ya yi gannin ta fara sakewa da magana ya sake rike damar ya ce" kin ga, ko dai ranki ya kiya ne da Allah ya daukaka ni? Nine baban amarya baki ga Abanki a bayana yake buya bane?"

Ai kam tino ranar da abanta ya yi wuf ya boye a bayansa ya sakata kyalkyalewa da dariyar da bata shirya bashi a kwana kusa ba, har tana dan dafe cikinta da ya tuna mata yinwa take ji matsananciyar gaske kuwa sannan ta dan girgiza yatsarta a hankali ta ce" Nahidt bata da kirki, a bainar nasi ki saka ubana gudu kuma ki ce ke ba haka kika zo yi ba?, Allah shirya min ita......."

Ita na dariyar Nahidt ne, shi kuma yama kallon fuskarta da yadda take yi din, har ta dire ayar maganarta sannan ya saki lalausan murmushi ya juya ya dauko kwanon wajen mama da kuma ledar kazar ya sake dawowa yana bubudewa a hankali yana ajiyewa a gabanta

Tukakiyar tebar da ta sha miyar markadadiyar gyada ta zubawa ido yawunta na tsinkewa, sai kuma ga kaza wace tana yin ido hudu da ita jiya ne ya fado mata a rai
Cike da kula da yannayinta da dan sigar tsokana ya ce" Kumama ai akoy ta frij ta jiya ko ita zamu ci mu adana wannan?"

Da sauri ta kalle shi tana zarro ido a zuciyarta kuwa ta shiga ayana' waye babana, ai daya ake yi da Allah in ji kuturu, ni na ci kazarka kai kuma ka kasheni? Ka je ka ci abinka Allah zai bani nima'

A bayane kuma sai ta kiya ta ja tebar tana sake kallon kazar a hankali ta saka cokali hadi da yin Bismillah ta dan diba ta fara kaiwa bakinta
Ai kam ta sha hadi yadda take sonta hakan ya sa ta sake kaiwa bakinta still tana hankalce da lamari na leda mai dauke da kaza, shi kuma yana kallonta kamar ya samu wata TV har sai da ta masa alamu na abin jika makoshi kafin ya mike a sanyaye ya dauko ya sake ajiye mata ya kuma zuba mata ido yana kallon dukkan motsinta har wayarta ta kuma daukan vibration din da ta yi ta yi a dazu aman bata sani ba

Shine ya dauki wayar da sauri, hakan ya sa ta zuna masa ido a lokacin da ya daga kiran ya saka a handsfree bai ce komai ba

"Wayo Allahna kanwata, fada min fada min Shuwwan Abanta shafa min an yi ko? Shikenan Shuwwan Abantama ta san abin? Fada min sumanki nawa"
Zuuuuu haka Nahidt ke maganarta tana kyakyata dariya, a lokacin da suka yi ido hudu ita da shi suka kumakin cire dubansu wajunnansu

A hankali ta fashe da kukan tabarar da ya saka shi lumshe idannuwansa ya dauki wayar ya karra a kunnensa a hankali ya ce" Bana tunanin zaki iya biyan kukanta gaskiya, sai dai ko mijin ki!" Yana gamawa ya katse kiran ya janyo matarsa jikinsa ya shiga dan rarashinta yana aukin maimaita Nahidt ce ko? Ta yi shiru zai yi tafiya mai digi tata ta kanta ya bata abinda ta nema! A haka ta lafe a jikinsa ta idasa zuba tabararta tamkar ba ita ba, tana zile zile ana tarota tamkar wata yar goye.................................

Ita kam Nahidt wayar ta cila da ihu ta ringa kwaso shokiiii tana aukin fadin ta aurar da y'arta ta kai daki, y'arta ta kai dakinta............ (🥺😔), Sai kuma ta idasa da silalewa tana zama bakin gadon a lokacin da ta tuna jibi i war haka fa ta yiwu har an daura nata auren itama da nata mijin, shin me ta tamadar masa wanda zai saka shi nishadi harma ya gasata? Ita fa tausaya masama take yi, anya malan zai iya wani katabus kuwa??????takan ji tausayinsa a zuciyarta sosai, yana cen ya kasa zaune ya kasa tsaye sai shiri yake abin har mamaki yake bata, sai dai kuma idan ta tuna Allahu gafurun rahim ne sai ta sake rike carbinta ta kuma sake kadaice kanta wa bauta masa da fatan ya sanyaya kaurin rubutun ALK'ALAMIN KADARARTA

A wannan rana Shuwwa ta ga tatali irin na soja, bama a wannan rana kadai ba har dare ya shigo idan ya matsa to fa dan ya leka masalaci ne, a nan a tare da ita ko kiransa aka yi yake amsawa, a nan a tare da ita ya baje ya ringa sakata magana da yawan nuna mata kular da ta sakata sake baje kolin tabararta, baci take yi da shagwaba son ranta kai da za'a bartama sai tace a sabata a baya Tunda dai Allah ne ya yi abinshi ta samu mai tarota ai sai yi............


_____________________________________


A gidan Malam

Karfe shida na yama

Dago kansa ya yi yace..................ALK'ALAMIN KADARATAH





Na

*Sajida*


Page


6️⃣8️⃣




Dago kansa ya yi daga ware hular da zai hadawa dinkin shadar da aka watsa masa fari kalll wanda ya sha zubi gari da yar ciki ya zunawa rigar da ta ajiye ido yana kallo sannan ya sake maida kansa dan cire abin balawa a hannun rigar da kuma safar da Matarsa uwar gidansa watau Malama ta ce ita ta fi dacewa da hawa dinkin ba tare da ya furta mata ci kanki ba

A harzuke ta sake kaiwa saman kujerar tana zama ta ce" Ka rasa wace zaka kawo ka jera ni kishi da ita Malan sai warce ba'a san asalinta ba? Y'ar ina ce ita su waye iyayenta?, Malan du irin yadda nake zuba maka karya tabaya a abincinka kana ci dan kar munafukar nan ta cin maka sai da ta cin maka ashe? Du tarin azhkar dinka da adu'o'in neman kariyar da kake yi ba dare ba rana sai da har dandi ta cin maka? Malan yau kaine kake murnar zaka je daurin aurenka da yar barikin da ta tare a gidan kanwarta har ka yi mana dinkunnan shada ka ce sai mun je? Da ni za'a tafi daurin auren yar iskar y'ar ? Malan ai ya dace ka yi min adalci ko dan zaune da nake da kai a hali na rashin jin kukan yan jarirai da yawon yan dagwai dagwai a gefena, Malan haka zaka wulakantani a anguwa a ce du abina ka kare da auren karu........"

Hular da ya dauko ce ta kubce a hannunsa ta fadi lokaci daya kuma ya sake zuba mata ido da idannuwansa da suka fara daukan launin ja dan bacin rai

A cen kasan zuciyarsa ya ringa astgfari da hailala dan samun sasaucin bacin ran dake tuko shi

A sanyaye ya karasa wajen da take zaune yana kallonta ya ce" Furera, ai ke kin san cewa an auna kwayoyin haihuwata an kuma aunawa likita dai bai ga matsalar da ta hanna ni baki ciki ba, kuma ke kin san wanene ni a saman shinfidarki wanda koda baki zauna da ni dan komai ba na gabata dan hakin da nake ba gaban jikinki kamar yadda na karanta a koyarwar adinina kadai na isa ki zauna da ni, bale ban san abinda Allah ya boye a hanna min haihuwa ba, Furera a kulun kece mai tino min cewa ban ajiye ba kuma hakan damuwa ce a tare da rayuwata, kin ga na hakura na kuma barawa Allah shi yasa nake burin ajiye wace zuciyataa ta yabama, Allah fa ya halata min shikenan ke sai ki fitineni?, Ki sani idan takamarki baki haihu ba y'arki ba zata kasance cikin jarabtar furucinki ba ki kiyaye lamarin ubangiji a kan hannin da ya yi, domin bawa baya tinkaho da halitarsa da yannayin tukin rayuwarsa har sai ya jishi a kabari, hakan na nufin ke din nan hakita ce da Alllah ke iya juyawa lokacin da ya so, kar ki manta sai idan ya so zaki shiryu idan ya ki ba zaki taba shiryuwa ba, in ba abinki ba meye riba a cikin zubar da mutunci ne? Ba zaki yi koyi da yar uwarki bane? Nan fa aka kawo mata ke ta kuma amsa ta yi min biyaya, kina tunanin akoy matar da zan yi ta tureta a kima d adaraja a cikin zuciyata ne? Furera Zuciya na son mai kyautata mata, ba kuma zan karra aure dan na tsane ku ko kun gaza min bane, zan karro ne dan halin hakan ya kama, shin ke bakya tsoron Allah ne? Kuma da kike magana a kan wai rashin asali ki wanke idannuwanki ki kuma nemi majinginin bayanki, domin ina tsoron ki tsinci keyarki a kasa a lokacin da kika ji cewar kadara ce ta rigayi fata har kika sameta a bagas kike son wulakantata, ki sani ba'a wulakanta dan Adam ko waanene domin yanzunta na iya kasancewa gabanki, ita kuma yanzunki ya dawo nata, ko a yanzu gaskiya du wanda bai yiwa NAHIDT dina adalci ya yabeta ba bana jin zamu shirya, tunda ai ta yi kokari ta zubar da komai ba tare da an saka mata wuka a wuyanta ba, sai dan mai shiryawar ya shiryeta ne, sauran kuwa zan tayata da daga hannuna na hada da kama kafa da fiyayen halita kan aya kar ta kasance a kanta , kunya da soyayar maaiki ta sa Allah ya karra yafe mata sannan ya saka Matar malan a gidan aljannah, zuwa kuwa da ki dauki shadar nan ki saka ki je da ita, ko kar ki saka ki saka wace ta maki dama so na yi mu yi ankon farin kaya tunda murna muke, ni dai na san sai kin halarci daurin aurena tare da yar uwarki, idan kuwa ba haka ba......Furera idan kuwa ba haka ba ina tsoton kanki ya kasa rike asalin wanene ni!"
Yana dasa aya ya juya ya fice a falon nasa yana ta karra tausar kansa da magangannun cewa wannan ba ranar bacin ransa bane, dan haka ya nufi bangaren da aka gama gyara komai da irin dukiyar da aka zuba mata wadda daga MUHAY ne ya bada wannan mamakin , kaya fa an zuba ko yar waye kaya kuma sun yi ko a gaban waye, shi da kansa sai da wajen ya ringa bashi sha'awa

Murmushi ya yi yana girgiza kansa da tunanin wai da gaske Shima goben nan zai kilaceta kamar yadda ya jima yana fata?, Tabas bawa kar ya cire rai da rahamar ubangijinsa duk rintsi, komai nisan dare gari zai waye ne, mai hakuri kuwa shi ke dafa dutse.



Tunda ya fice ta mike da gudu ta yi bangarenta, tana zuwa ta dauki wayarta ta kile bangaren nata ta shiga dokawa

Ta jima tana ringin ba'a daga ba hakan ya sa ta yi wurgi da wayar ta fashe da wani kukan mai tsananin gaske a bayane tana fadin" Walahi walahi walahi ba zai yiwu ba, ina ji ima gani na san kana sonta na yarda ka aurota ka kawota gidana ta yada zata idasa janye min kai daga duniyata? Malam idan taa rabani da kai na shiga ina da raina? Walahi ba zan yarda ba , uwar gidanka ai dole zuciyarta ta mace ita din kanta shekararta hamsin ne ta girmeka da shekaru bila adadin, me ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login