Showing 216001 words to 219000 words out of 226733 words
ta ce💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥
*ALK'ALAMIN K'ADDARA TA*
💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥
*The Hero writer*
*SAJIDA*
_Bismillahir rahamanir rahim_
PAGE:. 7️⃣7️⃣
*P͓̽R͓̽E͓̽S͓̽E͓̽N͓̽T͓̽*
*S̉T̉ỎR̉Ỷ ẢN̉D̉ W̉R̉ỈT̉ỈN̉G̉ B̉Ỷ*
*S͞͞A͞͞J͞͞I͞͞D͞͞A͞͞*
*T͞͞H͞͞E͞͞ H͞͞E͞͞R͞͞O͞͞ W͞͞R͞͞I͞͞T͞͞E͞͞R͞͞'S͞͞ 👇🏻*
1 *yar mahaukaciya*
2 *Banida zabi*
3 *Duk karyar kada*
4 *Baka ce*
5 *Daga tafiya daukar soja*
6 *Kutkale*
7 *Makauniya ce*
8 *Mage mai kwanciyar daukar rai*
9 *Duk nisan jifa*
10 *Dutse*
11 *Idan Ka Raina Inda Kake*.
12 *Neman Na Kaina*
13 *WATA KOKOWAR*
*The Latest Qualitative New Book ALKALAMIN KADARRATA*
*WANNAN BOOK NA KUDI NE BA FREE BANE, IDAN KINA DA RA'AYIN KARANTASHI KI GARZAYO KI BIYA KUDINKI YAR UWA ZAKI SAMU BONUS NA DUKAN LITATAFAINA CIKI HARDA NA KUDIN DA NA GAMA KWANAN NAN, KI GANE................ALKALAMI NA DORA, NA ZUBA RUBUTU......IN SHA ALLAH ZAKI NISHADANTU SANNAN KI KARU💓💓💓*
Zaku biya kuɗin ku ta wannan account numbern 0225962748
Amina Maikudi Abdullahi
GTBank Naira 300 ne kacal zaku biya anyi araha an hana bashi.
Ko ku turo Recharge card ta wannan numbern wayar
08038856944 banda vtu hoton katin zaki ɗauka ki turo.
Sannan Sai ku tura shaidar biya ta wannan no din +22793811618
Ga ƴan Niger zaku biya kuɗin ku ta wannan layin +22793811618 katin sahelcom ko AIRTEL ta dala DARI ne ( 500 francs cefa) sai ku tura shaidar ta layin nawa sannan na saka ku a grup din
Sai kun zo🥰🥰🥰🥰🥰
Jikin hajia ne ya kwashi bari, ta dora hannunta a saman kai harshenta na rawa ta ce" Dan Allah dan annabi ku bari, Innalilahi NAHIDt saketa mu je saketa, dan Allah saketa mu tafi"
Nahidt ta kalli hannunta da Hajiar ta rike tana ja ta yi wani yannayi da fuskarta ta ce" Hajia bari mana kema, baki ga tun dazun so take ki kauce ta dakeni ba? Hajia Duka? La'ila ha ilalahu ai yanzun kuma sai dai na ruwan sama ba dai na dan Adam ba!, Idan takamarta miji ni sai na rantse na fita son Aban shuwwa, Kuma ke furera bara na zube maki zance irin na mahaukata nima kishinki nake ji, abinda kike kishin nan nima ina yinsa kamar na yi hauka, da so samu ne kawai ya daina taba ki kwata kwatama ni ba abinda ya shafeni , Sai dai na san cewa na makaro kuma ko wata zai karro bani da yadda zan yi, ko ba komai gayen da kudinsa da lafiyarsa kayan aiki na amsawa da zarar sun ga nama shikenan sai mu yo son kai mu dane shi? Ki rike da kyau a kunnenki NAHIDt ta yi bariki, ta kuma ajiye bariki ba yau ba, aman tama tare da dabi'u irin na bariki a jinninta , bale an zo kan gabar da idan na buga tsuguni Malan ya dana lada zan samu? Me ya fi raina ga lada ga mando!, Ki zage damtse iya karfinki ki amshi kaya a lokacin da ya dace, bayan wannan baki da yadda zaki yi da ni, idan kuma kin nace bismillah, na baki dama daga yanzu gar mu mutu ki bi dukkan hanyar da zaki bi dan kasheni, na tabata dukkan abinda zai sameni mukadari ne, babu wanda ya isa ya hanna, aman fa kika kuma nuna zaki taba lafiyar jikina sai na zane ki da belt!"
Tana gama fada ta cikata da karfin balaki hakan ya sa ta kai kasa du irin jikinta kuwa sai gata tana haki kamar wace ta yi tsere, dama Furera ba wani karfin ne da ita ba kawai kaifin bakin ne, gashi bata tauna maganarta da zarar ranta ya bace komaima fadi take yi dan ta huce
Hajia kam yau ta ga abu gannin idannuwanta kuma kunnayenta sun jiye mata abu iyakar jinsu
Jikinta na rawa ta rasa inda zata yi, da sauri ta juya ta bi bayan Nahidt din bayan ta ba Furera hakuri
Tana zuwa ta tarda Nahidt din na kokarin bude falonta, tana budewa ta shige da Bismillah a bayane hakan ya sa Hajiarma bin bayanta a sanyaye ta ce" Nahidt ?"
Nahidt ta dakata ta juyo a hankali tana kallonta
Hajia ta ce" Dan Allah ki yi hakuri kin ji? Kar ki ringa biye mata dan Allah, kin san ita Furera wani sa'in tana da irin haka, aman da zarar an kyaleta shikenan komai sai ya wuce, dan Allah kar ki biye mata ku ringa kishi irin na jahiliya kin ji?"
Nahidt ta yi murmushi tana nuna hajia wajen zama
Hajia ta je ta zauna itama ta zo ta zauna a gefe a nutse tamkar ba ita ba ta ce" Hajia, ki yi hakuri, kula shirmen yade yaden magana daban, taba mutunci daban....."
Ta furzar da iska ta ci gana da fadin" Wani lokacin marar kunya na ci gaba da yada rashin kunya ne da tunanin ya zama dole a yi hakuri da halinsa a saurareshi, baya sasauci a rashin mutuncinsa baya tunanin idan shi aka yiwa yaya zai ji a zuciyarsa ne? Sai ki ga har ya zamto abin tsoro a waje bayan mayar da shi wata tsiya da aka yi ya sa yake daukan kansa a haka, da watsi aka yi da shi aka nuna masa shima mutun ne irin na kowa da ya maida kansa mutun irin na kowa din!"
A hankali ta riko hannun Hajiar ta ce" Hajia ban zo gidanku dan mu ringa raba hali da kowa ba, haka kuma ban zo gidanku da wani ya ringa ci min mutunci ba, idan takamarta na yi bariki inaga wannan rayuwata ce da makomata, yau tunda har na yi aure ana iya yi min uzurin zama da ni da ido koda ba'a bini da fatan alkhairi ba, Hajia ta jima tana wulakantani a anguwar nan, ta wulakanta min gudan jinina da nake da a lokacin wace a kanta babu abinda ba zan iya yi ba dan na kareta, dimin nice mamanta, nice babanta, nice komanta..........Hajia haka take shiga tana takawa aman dalilin mai mutunci da ya rabe mu sai na kawar da kaina na kyaleta, aman yanzun bana tunanin zan iya kyaketa ta ringa min haka du haduwarmu, Idan haka ya ci gaba tana iya yi min a gaban jama'a, haka kuma tana iya mayar da ni tamkar mahaukaciya, ....... hajia ni na rayu ne da kwatar yancina da kuma soyayar makusantana, sannan na rayi ne da yakar mai yakina......................ba zan ce maki komai a kan zamantakewata da ku ba, abinda na sani shine zan zauna zuciya daya da kowananku hajia, mu'amalata da kowanenku kuwa zai danganta ne da yadda ya mu'amalanceni, ni ba makiyiyarta bace, ni kishiyarta ce, dole akoy kishi a zukatanmu mu dukanmu.....aman idan har bata iya gyara nata halin ba lalle zamu kwasheta da ita!"
Hajia ta ringa sauke ajiyar zuciya a sanyaye ta ce" Allah ya sanyaya, Allah ya kashe fitinar komai kankantarta, in sha Allah babu abinda zai ci gaba da faruwa sai alkhairi......................, Nahidt dakinki ya yi kyau sosai masha Allah, Allah ya sa a mora lafiya "
Nahidt ta daga kanta tana murmushi tana bin dakin da kallo ta amsa da amen ya Allah, ita kanta ta yi godiya da Allah da ya nuna mata wannan daula a matsayin tata, ta kuma jinjinawa mijin Shuwwa dinta, asge har haka ya yi bajinta? Lalle kanwarta ta samu miji sai fatan zaman lafiya......ai kam zata kirayesu yau ta ce da shi Aba ko zai yi dariya, shi kansa da kafarsa shi babanta ne kkai jama'a.........
Yar hira suka ci gaba da dan tabatawa da hajiar kafin take mikewa ta mata salama ta tafi cike da son tambayarta me take anfani da shi wa hannayenta suke da laushi haka ne? Zata so sannin abin itama ta nema ta jaraba, domin kuwa ita kam ta san darajar gyara, shekarunta a hamsin kadan ne babu aman a duniya idan ka ga Hajia na gyaran jiki sai ka sarra mata, takan je saloon a wanke mata kanta a busar da shi a mata kitso duk sati uku, sannan ta kirayi mai kunshi ta zo ta yanyara mata kunshinta bale na salatif, haka kuma bata wasa da gyaran jiki irin na lalle, ga kuma uwa uba tsafta da kanshi, bata iya hada turaren wuta ba aman fa bata jin ciwon cire kudinta ta sayi turarukan wuta da na humura masu daraja ta shafa ta kuma turara a dakinta.......wannan dalilin na daya daga cikin abinda ke saka Malan manta cewar wai Hajia ta girme shi, to gaskiya ta san darajar kanta ta kuma san tasaa haka kuma tana aiki da sunna, tana kamantawa sosai da sosai shi yasa yake karba yake kuma godiya da yabawa, ga ladabi da biyaya bata taba daga maganarsa ko mecece, ta fa gama da Malan shi yada NAHIDt ta yiwa Allah godiya da ba da Hajiar zasu goga ba, irin kishi da hajia irinsa ne ke saka mutun kuka da idannuwansa, ba zaka iya ba abin mai girma ne, sai jajirtaciyar mace zata iya
Bayan salarr isha'i
Tunda take maganar tana hawaye yake sauraronta da mamaki kafin ya Kalli Hajia sai kuma ya kalli NAHIDt dake zaune Idannuwanta a kasa tana ayana' Zuki kai Furera an iya sherata, wai na zaneta ni? Wai kuma muka yi mata taraya da hajia'
A nutse ya furta" Asha, Subahannalah subahannalah, me nake ji haka duka kuma? Kuma taraya? Me ya faru ne Nana Maryama?"
Hajia ta hadiye yawun bakinta a sanyaye ta ce" Aya Akaramalahu Allah ya huci zuciyarka, eh an dan samu matsala ne aman kuma bai kai ga dukan bama, aka kuma kashe wutar"
"Wace wutar aka kashe Hajia bayan kun min taron dangi?" Ta fada tana kallonta da sake fashewa da kuka ta dora da fadin" Cewa ta yi haduwa goma cin uwa goma Malan"
NAHIDt ta wangale baki da mamaki tana ta tuna anya a maganarta ta fadi haka kuwa? Sai kuma ta boye murmushinta tana ayana' Dama na ce maki haka walahi, maganar ta min dadi'
Malan ya kai dubansa kan NAHIDt da ta masa mugun kyau cikin yahiga ta atampa ta sha dauri da sarka da dankunnayenta masu kyau abinta
Ya dan tsatsareta da ido a sanyaye cikin wani salo mai saka zirya a cikin jiki bayan ya ji ta tsirga masa har kwakwaluwa ta tada kwadayinsa tare da jin son gagauta kasancewa da ita a daka dan ta kuma ba sahiba kula irin ta kulun ya furta" Sayadah "
A hankali ta dago idannuwan nata ta sauke a saman fuskarsa, haka itama Furera ta sauke a saman fuskarta dan ta ji wani sabon salo wai Sayadah yanzun yar barikin ce ta koma sayada a duniyar Malan?
Malan ya dan yi gyaran murya ya ce" Wai kin daki yar uwarki?"
Hajia ta gumtse bakinta dan har ga Allah daria abin ya bata, yo Furerar ta yi trela kawai sai tace an daketa? Da ita watace ko dukan nata aka yi sai ta boge dan kar a yi mata daria, hakan ya sa ta sada kanta daga dubansu tana ta hanna kanta fashewa da daria
A hankali Nahidt ta lumshe masa idannuwanta sannan ta bude , ta dan dantse lebenta na kasa tana wanna idannuwan nata a hankali sai kuma ta ciro harshenta kadan ta dan lashe saman lebenta da yannayi irin na baban lamari, sannan ta hade lebunnnan nata ta tura masa kisss lokaci daya ta yi kamar zata dan duka da idannuwan nata ta masa nuninda wajen da Sahiba take kilace sai kuma ta dora hannunta na dama a kan mamanta dake cikin rigarta ta atampa ta dan matsa wajen tana yatsine fuskarta sannan ta shagwabe bakinta bata ce komai ba
Sai da ya ja numfashi ya yi saurin matse kafarsa a birkice ya sake kallonta sai kuma ya kai dubansa kan Furera da ta kusa suma da gannin barikin da take fada tsagwaronta
Baakinsa na rawa ya ce" Ba'a kyauta ba, Allah ya baki hakuri ba za'a kuma ba Kin ji Furera? Ku tashi ku je yau barci nake ji da wuri Allah ya baku hakuri gaba dayanku ku je ma karasa maganar da safe in sha Allah"
A nan ne ta gabatar masa da abinda take so a dora, bayan furera ta wuce fuuuuu
Ido ya tsatsareta da shi na dan lokaci , ta cikin idannuwan nasa kuwa yake aika mata da sakwanin dake cikin zuciyarsa
A hankali kuma ya janye ya maida kan hajia a nutse ya furta" Wai haka Nananah?"
Hajia ta gyada kanta tana tabatar masa hakan NAHIDT din ta yanke
Ajiyar zuciya ya sake saukewa a nutse ya furta" Allah ya kara mana fahimtar junna da zama lafiya a tsakaninmu ya kauce dukkan fitina, Allah ya sa hakan ya fi zama alkhairi
Haka yana ji yana ganni NAHIDt ta mike ta masu salama ta fice a falon
Yana zaunen idannuwansa na Kan Hajia dake ta kokarin zuba masa abinci
A hankali ya saka hannunsa ya kamota ya dorata saman cinyarsa a sanyaye ya ce" Maryam ni yinwa nake ji"
Abincin ta kalla ta kuma kalle shi da mamaki ta ce" Yah Ustaz to bara na zuba maka....."
Kansa ya girgiza a hankali yana sake kashe ido ya ce" Ai mai gari ya cikan cikina sosai harda guzurin fura, shi yasa Sahiba ke ta neman abincinta............."
Kanta ta sada tana Murmushin jin kunya da kuma mamakin yadda Malan ya dubeta bayan ya samu daleliyar diya irin NAHIDt? Sai dai tuna cewa mijinta kai adalci ne, samun wace ta fita kyau ba yana nufin zai wulakantata ba, dan haka ta aniya bashi hadin kai da iyakar iyawarta domin Malan baya rabo da bada darasi kala daban daban.....yakan ce baya so a tashi daga zikiri da cutarwa ta kowani gefe........ 😍
______________________________________
Kwana uku tsakani ya kasance Nahidt ta rufe sati a gidan Malan, hakan ya sa yau yana anguwa sunna mesage take fada masa tana son zuwa gida ta kai ziyara , sun yi zasu hadu da Shuwa su wunni a cen gobe idan har ba damuwa
Hakan ya sa ya yi mata tambayar ita daje fama da barcin nan na gajiya ba lokaci ba zata yi hakuri ta karra hutawa ba kuwa?
A nan take sheda masa ita fa ta fara tsorata da barcin nan, domin Allah bata tare da gajiyar komai, shi yasa take son zuwa ta fadawa Mamansu ita kanta abinnan na damunta, yanzu ana hira da ita kana iya juyowa ka ga barci ya yi awon gaba da ita, abu kamar sammu? Kar aje a matsayinta na babar yar sarki an samu wani zai mata aiki da cikawa.....kai da ta shiga uku cutar barci ai cuta ce mai girman gaske sosai da sosai😌 (😂 toh fa)
Ya dai bar maganar kan har ya dawo
Da dare da ya shigo ya samu Furera an gayu a bangarensa, tuni ta gama shiryawa zuwansa domin yanzun fa su Madame Furera abin ya karra daukaka, daraja take kankarowa kanta ba ji ba gani, shi yasa ake shafa jan baki a kamanta barikin nan, tunda dai ai rami ne kowa nada shi a jikinsa itama zata iya sarafa nata tunda ta kula maza yan cin amana ne (🥺 kashhhhhhh)
Kamar yadda aka saba zuwa a gaishe shi hakan ne, sai dia Hajia kadai ce ta zo yau
Har dare na neman tsalwa shiru ba NAHIDt, hakan ua fara daga masa hankali, dan haka ya fadawa Furera zai lekata, du kuwa da ta nuna a kan me ai lafiyarta kalau ya nuna mata hakinta ne ya san ta wuni lafiya sannan ya san ya barta lafiya wajen barci, tama shirya gobe kowace ta je ta ziyarci gida
Da wannan ya samu ya fito ya nufi bangarenta
Tunda ya kama kofar ya bude ya ji ta budu ya ji hankalinsa na Neman tashi
Da sauri ya shige yana waige waige da salama a bakinsa sannan yana kiran sunnanta
Gabansa ne ya yanke ya fadi ganninta kwonce saman kafet, ga dukkan alamu barcin nan tun na sallah da ta yi ne ta kudundune sai yinsa take tamkar wace ta mutu
Da sauri ya dagota yana juyota dan gannin jikinta lokaci daya kuma ya ce" Nahidt, NAHIDt ?"
Luuuu ta yi d idannuwanta tana kallonsa sia Kuma ta maida ruf bayan ta masa murmushi hadi da fara ambaton sunnansa barcin ya kuma yin awon gaba da ita
Hankalinsa ya sake tashi ya cire mata hijab din ya dauketa ya yi ciki da ita
Saman gadonta ya dorata ya aniya damunta da tambayoyi yana ta damukarta dan ta farka
A fuzge ta saka dan kukan shagwaba tana ture shi ta ce" Muhamad barcinma ba za'a barni na yi ba sai an saka min ido, haba ina yanci na dan kasa ne wai a gidan nan?"
Ta idashe tana juyawa hadi da jan bargo ta sake rufawa a jikinta
To fah malan ya rikice, lokaci daya ya shiga karatu irin na rukiya, ayoyin karya sihiri kai babu adu'ar da bai kamo ba yana mata tofi aman ko gezau , barcinta take tamkar wace ta sheka, kuma ga dukkan alamu barcin ya yi nisa kuma tana jin dadinsa
A kan dole ya mike ya sake rurufeta ya kuma yi mata adu'a ya fice bayan ya sake shafa fiskarta ya rufe ya tafi da ky din
Da asuba shi ya budeta ko barcin kirki bai samu ba ya tasheta dan ta yi sallah
Tana layi sai da ta shige bayin sannan ya iya sauke ajiyar zuciya yana tsaye gudun kar ta yi barcin a bayin har sai da ta fito sannan ya wuce masalaci
Koda ya dawo sai da ya kuma lekata, yanzun kam ya gama yarda zai kaita gidan da kansa idan aka ce a je asibiti sai a je, idan kuma wani aikin sihiri ne sai a dauki mataki mai karfi, shi kam ya fara tsorata da wannan barci tamkar an sauko mata da shi? Kafin ya fita sai da ya fada mata ta shirya fa zai kaita gidan da kansa, sanann ya fice
Sai da ta shirya din sannan ta koma ta kwonta ta sake yin barcinta a falo domin ko kari bata