Showing 9001 words to 12000 words out of 226733 words

Chapter 4 - Alkalamin Kaddara ta Complete Hausa Novel

Sajida   

11 Sep 2025

7976

ya sa ta rintse ido tana dahe rai tana son gane sunna ganninsa suma ?, Kai jama'a yau ta ga halita a gabanta

Tun daga kasa har sama ya kare mata kallo a yan sekwani kama daga shigarta, da gashin kanta dake barbaje kafin ya budi bakinsa a hade ya ce" Kin yi shaye shaye ne?"

Da sauri ta girgiza kanta tana fadin" Aa walahi "

"Ur name?" Ya fada a kausashe

SHUWAR ta ce" SHUWWAR , SHUWWAR ne sunnana Yalabai"

Gilas din idannuwansa ya cire yana fadin" Bamu takardar shedar yar kasa ce ke"

Da sauri ta juya daga wajen nan da take ta saka kanta cikin motar hakkan ya sa ta bado bayanta gabansa ta yadda duwawunta ya gogi kafarsa ta hagu da ta fi kusa da ita a lokacin da bai aune ba

Kansa ya sada dan ganin meye ya taba masa kafa a wajen da hakan ya faru ya dago da sauri daidai ta sake fitowa daga motar da jakarta ta ciro katinta ta miko masa hannayenta har dan rawa suke dan so take ta zauna ta fahimci wannan bawan Allahn mutun ne ko ba mutun ba?

Takardar ya amsa ya dan matsa yana dubawa ya dago yana tsatsareta da kakausan kallo ya ce" A nan an rubuta *IBTISAM*, kin ce sunnanki *SHUWWAR*, "

Hannayenta ta shiga hadawa tana son yin magana a kausashe ya ce" Saurara, ki tabatar abinda zaki fada gaskiyarki kennan domin tsagera na fito kamawa kuma na fara haduwa da ke, kin ga gaba dayanki kama kikai min da wada ta sha giya, sannan kikai min kama da barauniya, da kuma wace bata jin magana, so ki dan saukaka min kama ki mana? Idan kika wahalar da ni zan wahalar da ke ne"

SHUWWAR ta matse fuska sosai tana kikifta ido, a kasan zuciyarta a yau harta da bakon ashar ta hada ta laulayawa wannan gabjejen abin dake gabanta a tsaye, da ya san kudurinta a kan sojoji da bai tsayar da ita ba, wai yar shaye shaye, barauniya, marar jin magana, aka kai ikon kasar nan sata? Aka kaisu yin mankas? Bale wannan aba wai ita magana ai basu san inda aka rawaito jinta ba, shine shi zai tsaya mata a ka ya yi maganar nan?
Sai dai ta san a yanzu a nan da take tsakiyar kartin nan idan ta yi wasa sunnanta nama, babu abinda zai raba shi da ita kuma sai Allah
Iya gaskiyar lamari a kan maganar sunnanta ta budi baki tana sheda masa ta ce" Walahi sunnan IBTISAM shine asalin sunnan da iyayena suka saka min a garin Riyad, na cenza sunnan nan ne sakamakon sakina da mijina na biyu ya yi a lokacin da na tare a gidana yana sona ina sonsa aka raba auren, Yalabai ba zan manta ranar da Salisu ya mikon takardar nan fara ba mai bakin rubutuuuuuuu......" Sai kawai ta fashe da kuka tana fadin" Yalabai yana kiran IBTINA, ki yafe min, ina maimaita haba habiby kar ka sakeni ka tonan asiri yar bindin uwar babarsa ta saka ya yankan tikitin wahala nake yawo a titi ........Shin Yalabai tsakani da Allah wannan abin adalci ne??????"

A daidai likacin da MUHYIDEEN ke sake kallon wannan yarinyar sannan yana sake yarda da maganar da akai masa cewar garin nan gari ne na tsagera, yana jin sha'awar yarda da zama a garin na shiga zuciyarsa wata motar ta sake kawo kanta wajen wada ba shi ba da ya mutu da mamaki da rashin kunyar wannan mai shige da yan wiwi din ba, harta sauran sojojin da suka saki baki da hanci sunna mamakin wannan yarinya da ta budi baki take magana kanta sake hankalinta kwonce tana yiwa ogansu hira tana bashi labarin abinda ya faru da ita kamar bata san waye MUHYIDEEN ba? Suka juya sunna gannin fitowar Abdul Mutalab dake nuna takardar wuyansa yana gaishe su da girmamawa har ya samu kansa a inda take din da gaskata abinda aka fada masa na wajen da take ya ja da sauri gannin wanda ke tsaye a gaban SHUWWAR din

Wani dunkulelen yawu ya hadiye yana hado jarumta irin tasa ta d'a namiji yana hanna kafafuwansa yin rawa a gaban SIR LIEUTENANT GANARAL MUHYIDEEN ya ja daga dan nesa jikinsa bai boye rawar da kafafuwansa ke yi ba ya ce" Allah ya kara maka lafia Sir wannan din matata ce, fushi ta yi na biyota dan na bata hakuri , dan Allah a yi hakuri a bani ita mu tafi gida ita batama san da dokar da aka dora na kar a yi yawo a cikin gari yau da gobe har sai an gama taron nan ba"

SHUWAR da zuciyarta ke dukan casa'in ta raba bayanta da jikin motar da dan sauri ta yi bayan MUHYIDEEN dake son fuskantar bayanan Abdul Mutalab tana zarro ido tana sake leko dan gidan Elhaj mai shinkafa da mugun mamakin irin gileliyar karyar da ya gila wace ko wuka za'a dora mata a wuyanta a yanzu zata iya fadin cewa babansa ne ya turo shi ya kasheta ya amshe kudin da ta karbo, Au ya kai masa ita
hakan ya sa daga bayan MUHYIDEEN take danna zuciyarta dake neman balowa ta fito ta bakinta ta kasheta dan tsoro da firgici

Bayan MUHYIDEEN ya karanta sunnan dake saman bage din Abdul Mutalab dake tabatar da shi din cikaken likita ne a asibitin gwamnatin kasar ya dago ya sake kallonsa da mamakin jin wai wannan matarsa ce,
Sai a lokacin ya fahimci yarinyar nan a bayansa ta labe hakan ya sa ya dan ja baya yana bata damar bayana a filin Allah ya ce" Meye shedar da zata tabatar min da iyalinka ce wannan?"

Da sauri Abdul Mutalab ya ce" Akoy shedar kudinta dake cikin bak'ar jakarta Million goma sha uku , Code din jakar kuwa shine 098526, ga kuma dan kwalinta dake hannunna da ta bara min ta fito, ka yi hakuri Sir zamu koma gida mu sasanta kanmu"

Da karfi ta ce" Da wa?, Ka koma gida da wa? Ka ga ba inda zan je yanzun, zan biyoka Daga baya ka je kawai ka fara tafiya kawai"

Tsitttt wajen ya dauka yan kwararin mutanen dake wajen masu kakin soja suke kallon kallo hakama Abdul Mutalab ya gama sarewa cewar idan har ta yi yadda aka fahimci tafiyarsu ba daya ba zata ja da farar rigar tasa ta likita MUHYIDEEN ya karkata masa kai, me yasa zata yi haka ne?

Motar MUHYIDEEN ya karasa ya saka hannunsa ya bude ya ciro jakar yana ajiyewa a saman motar ya shiga saka numbobin da ya fada ya bude jakar

Da mamaki ya kale shi yana fadin" Wani abu kuke yi a kasar nan da yake kawo maku kudi irin haka da har matarka zata malaki irin kudin nan ya kasance har tana yawo da su a sake cikin kasa?....." Ya maida dubansa kanta yana fadin" Menene sana'arki?"

Tsakani da Allah ta yi dana sannin fitowarta a yau din nan, idan sau dari zai budi baki ya yi magana sai ta ji kamar zata saki fitsari , haka kuma gabanta idan ya yanke ya ruguje ya fadi sai ta matse kafafuwanta dan kar ta rubta kasa, watau yadda yake a tsaye haka muryarsa take bawan Allah, ta yiwu bashi da lafiyar makogwaro ne kau?

Da sauri ta ce" Shi ya min kyautarsu jiya, jiya da dare dan na ce sai ya sake ni"

Yanzun sai Abdul Mutalab ya ga kawai yau sai sun ja an masu dukan kawo wuka a yanka ko a rufe su su saka kansu a uku

Yana inda inda ya ce" Eh Sir haka ne, ni kuma na same su ne daga wajen Mahaifina mai sunna Elhaj Mustafa Mai shinkafa"

Har ga Allah daria lamarin ya bashi, sai dai ko a alamu bai nuna ba ya mayar da jakar cikin motar yana rufewa ya ce" Ku koma gida , SERGENT ka basu takardar da zasu ringa nunawa har su koma gida dan kar a rike su"

Ba Sergent din ba, su da kansu sai suka samu zukatansu da dar din barinsu da ya yi haka kai tsaye bayan bai yi kama da sakarai ba bale a ce ai sakarai ne dole ya hadiye magana irin haka tamkar ta tatsuniya
Haka yarensa suka cika da mugun mamakinsa wanda karara ya kasa boyuwa a saman fuskokinsu

Amsar takardar suka yi ya mata alamun ta shiga mana, a lokacin da ta saki baki da hanci a kasan zuciyarta tana ayana' Wayo bawan Allah, dama dan adam tara ne ba goma ba, shi wannan gashi da tsayin, da kyan, da mulkin, sai dai ba ilimi, kai tsaye mun masa wayo haka?, To bara na samu na tserewa wannan mahaukacin tun kafin ya rike ni'

Motar ta shige tana ja da sauri ta dauki hanyarta shima ya shige yana bin bayanta da saurin balaki dan kar ta bace masa

Tunda suka fara aikin yanzu ne kadai ya yi wani alamu da ya nuna kamar murmushi ya yi yana raka tseran gudun motocin nasu da kallo yana maida dubansa wajen yarensa a lokacin da LIEUTENANT maman sani cikin ladabi yake fadin" Sir sai na ga kamar karya fa suke yi su dukansu?"

Gaba ya yi kadan hannunsa daya a saman kafadar Lieutenant Maman Sani ya ce" Ka san menene? Ban taba sannin garin nan zai bani sha'awa irin haka ba, ashe haka yake cike da tsagera?"

Lieutenant Maman Sani duda bai fahimci me yasa Sir ya fadi haka ba sai ya yi murmushi yana fadin" Sir a garin nan namu sai mu"

Muhyideen a rarabe ya furta" SAI KUMA NI, Ai wannan ba matarsa bace, sannan kudin nan ba nasu bane su dukansu"

Da mamaki ya ce" Sir aman yaya aka yi ya san code din jakar kuma me yasa muka barsu suka tafi?"

Kafadunsa ya daga yana fadin" Jakar ba tasa bace aman tana da alaka da shi haka kuma ko ta waye mai ita shi ya turo ya amsar masa, idan da ba haka ba da tuni an sanar mana da batan kudi Million goma sha uku ba fa kadan bane in dai ba ba muguwar hanya bane dole mai su zai nemi hukuma, sannan ka takardarta ta bari tsabar a kidime take, ga dukan alamu barauniya ce yarinyar cen! Lieutenant ka gane ko meye a tsakaninsu su duka a tsakaninsu yake kuma a tsakaninsu yake yawo, aman zan gane idan na koma na dawo zaman garin kwata kwata, domin zan shedawa SHIRP OF ARMY cewar na amince zan zo na yi shekara biyar a garin nan kamar yadda ya bukata na kiya a da, Lieutenant ina fatan kunna maraba da bako?"

Sosai gaban Lieutenant ya fadi, harma ya shiga hali na tsoro da jin furucin Lieutenant Ganaral cewar zai sauka a garinsa gaba daya har na shekara biyar? Ai da an yi tashin hankali domin ba ga yayan ba ba ga iyayen ba kan mai uwa da wabi lamarin zai sauka, aman da fara'a a fuskarsa sai ya ce" Da mun kasance masu baban sa'a My GANARAL!"
__________________________________


A haukace ta parka motar a kofar gidansu tana waigen bayanta
Gannin ya karaso yana shirin tsayar da tashi motar ta sake ruko idannuwanta waje tana furta" Kutumar uban cen har gidan ka biyo ni?"

A guje ta bude motar tana warto jakarta ta arta a dubu ta bankada kofar ta afka ciki tana ihun kiran💔❤‍🔥💔❤‍🔥💔❤‍🔥💔❤‍🔥💔❤‍🔥
*ALK'ALAMIN K'ADDARA TA*
‍💔❤‍🔥💔❤‍🔥💔❤‍🔥💔❤‍🔥💔❤‍🔥


*The Hero writer*


*SAJIDA*


_Bismillahir rahamanir rahim_


PAGE:. 5️⃣



*P͓̽R͓̽E͓̽S͓̽E͓̽N͓̽T͓̽*






*S̉T̉ỎR̉Ỷ ẢN̉D̉ W̉R̉ỈT̉ỈN̉G̉ B̉Ỷ*


*S͞͞A͞͞J͞͞I͞͞D͞͞A͞͞*



*T͞͞H͞͞E͞͞ H͞͞E͞͞R͞͞O͞͞ W͞͞R͞͞I͞͞T͞͞E͞͞R͞͞'S͞͞ 👇🏻*

1 *yar mahaukaciya*
2 *Banida zabi*
3 *Duk karyar kada*
4 *Baka ce*
5 *Daga tafiya daukar soja*
6 *Kutkale*
7 *Makauniya ce*
8 *Mage mai kwanciyar daukar rai*
9 *Duk nisan jifa*
10 *Dutse*
11 *Idan Ka Raina Inda Kake*.
12 *Neman Na Kaina*
13 *WATA KOKOWAR*



*The Latest Qualitative New Book ALKALAMIN KADARRATA*





Idan ana dara fidda uwa ake ina gwanin wata ga nawa, duk inda kaji wane ba banza ba, Shin kunsan banbancin zaƙin suger dana zuma kuwa? idan baku sani ba kuzo na banbance muku, shi sugar zaƙi ne cau dashi bashi da ɗanɗanon zuma domin kuwa ita zuma tana wanke ƙwaƙwalwa, misalin Zaƙin hannun Rubutun wannan fasihiyar marubuciyar taku, Duk wanda yasan labaranta ya karanta littattafanta ba sai na basa labari ba, domin kuwa bata rubutun shirme rubutu take mai cike da nutsuwa da kuma fasaha, ingantaccen labari ne mai cike da ƙalubalen rayuwa, tsantsar Soyayya yaudara cin amana munafurci, ƙulla ƙulla, gami da Izza, *ALKALAMIN KADARRATA* labarine mai cike da sarƙaƙiya gami da wahalar warwara, zaren labarin a duƙunƙune yake gashi da kaifin gaske kaifin yankan zaren munafuki yafi kaifin reza da almakashi muni, zarene na zana mai yankar mutuwa, shin kun fahimci zaurencen kuwa? Idan baku fahimta ba ku kasance da ni *SAJIDA NIGER* a cikin wannan sarƙaƙƙen labarin mai cike da ƘIYAYYA labari ne mai jan hankali gami da nishaɗantarwa kun san alƙalamina baya rubuta shirme, ku biyoni cikin wannan labarin domin jin ya ɗanɗanon yake.


*Wannan labarin ba Free bane na kuɗi ne zaku samesa a cikin farashi mai sauƙi, Yar uwa karki sake a baki labari Hajia da abaki gara ki bayar karki manta da marubuciyar BAƘA CE, MAGE MAI KWANCIYAR ƊAUKAR RAI, KUTKALE, WATA KOKOWAR nasan kun san waɗannan littattafan da daɗin su, ku hanzarta biya ko da kuɗinka sai da rabon ka.*

Zaku biya kuɗin ku ta wannan account numbern 0225962748
Amina Maikudi Abdullahi
GTBank Naira 300 ne kacal zaku biya anyi araha an hana bashi.

Ko ku turo Recharge card ta wannan numbern wayar
08038856944 banda vtu hoton katin zaki ɗauka ki turo.

Sannan Sai ku tura shaidar biya ta wannan no din +22793811618


Ga ƴan Niger zaku biya kuɗin ku ta wannan layin +22793811618 katin sahelcom ko AIRTEL ta dala DARI ne ( 500 francs cefa) sai ku tura shaidar ta layin nawa sannan na saka ku a grup din

Sai kun zo🥰🥰🥰🥰🥰


Ta arta a dubu ta bankada kofar gidan ta afka ciki tana ihun kiran " Aunty?, Faufiya na shiga uku ya biyo ni, ya biyo ni har gida zai tonan asiri"

Daidai lokacin da ya shigo balbalin gidan yana fadin" Kin ga SHUWAR, ki tsaya, ki dakata ba abinda kike tunani bane ya kawo ni wajenki tsaya ki ji mana SHUWWAR?"

Idasa shigewa falon ta yi tana sake ihun kiran auntynta dake bayi a irin wannan lokacin tana fadin" ku bani tabarya ko ice, ku daukon gatari ko wani katon katako na sauke masa kai walahi talahi ya biyo ni ni kuma ba zan bada kudin nan ba, wayo na shiga uku tayani danewa Aunty zai bude ya fi karfina"

A rikice auntyn tata ta kama mata tana tayata dannawa tana fadin" Yau na shiga uku da wata jarabar, ke kudin waye kika amso kike rantsuwar ba zaki bayar ba, meye a katuwar jakar nan SHUWWAR?"

SHUWWAR na haki zata yi magana ya daga murya yana fadin" Na rantse da girman Allah ba kudin nan ne ya saka ni biyo ki gidan nan ba, kar ki manta a hatsari na gama saka kaina yanzun nan kin san dai saboda kudin nan ba zan aikata haka a gaban MUHYIDEEN ba ko?, domin kin san a dazun nan da ace ya gane ni ba mijinki bane yana iya daure mu da igiyar dake jikinmu wace sai mun tsufa a gidan yari ba wanda ya isa ya fitar da mu aman na jajirce na ce ke matata ce domin idan na bari ya tafi da ke na shiga ukuna"

Turawar da suke yana turowa ta fara sasautawa tana kallon yayarta da kuma kofar jin furucin bakinsa

Yayarta ta rage murya kasa kasa sosai ta ce" Kudinsa kika sato ne yau kuma SHUWWAR ? Waye shi mahaukaci kika janyo mana cikin gidan bayan kin san jiya na kori baba mai gadi?"

Kai ta girgiza itama ta rage murya sosai tana fadin" Ba mahaukaci bane, kudin kuma ba nasa bane na babansa ne, dan gidan mai shinkafa ne fa, na je gidan ne na masa barazana ya ban jakar kudin nan shine ya turon yaronsa ya kwace bayan inaga million goma sha uku ce a cikin jakar cen aunty"

Ido yayar tata ta zarro tana furta" Million nawa?"

Ta sake maimaita mata adadin kudin, hakan ya saka yayarta gannin a kan kudin nan ko trela ce tana iya tarba, kai a kan kudin nan ko karo ne da jirgi zata iya yi
Wata zuciya ta ciyota ta samu kanta da dakatar da Zahra'u dake sake dannewa kar ya shigo ta ja SHUWWAR ta mayar da ita bayanta da jakar suka bashi dama ya bude kofar suka bayana a gabansa sun yi cirko cirko da su

NAHIDT ta sake aro fuska irin ta rashin mutunci ta ce" Kai me kake so a nan ne? Nice nan uwarta idan wani abin ne bismillah ina sauraronka ka fara da ni!"

Wace ta kirayi kanta da maman SHUWWAR ya karewa kallo yana fadin" Mamanta kuma?"

Ta sake hade girar sama da ta kasa tana fadin" Eh da matsala ne a haka?"

Tsaki SHUWAR ta ja tana fadin" Dan Allah ki daina cewa mamana ce ke duba fa ki ga kalar gashin da kike da a saman kanki wa kike so ya yarda ? Ka ga yayata ce fada mata me na maka kake biye da ni !"

Murmushi ya sake yana kallon yadda suke shirin kaurewa da wani fada a tsakaninsu ya budi baki yana fadin" Kun ga, dan Allah ku yi hakuri ba maganar kudi ba ya kawo ni nan, haka kuma ba wani aiken babana da zan yi, abinda nake son sani, abinda ya fi daga min hankali a kan SHUWWAR , dan Allah SHUWWAR a shagon babanmu ake maganar budurwarsa harma aka jadadan an daura masa aure da wata mai sunna irin haka jiya, dan Allah, dan annabi shine nake so ki fadan cewa ba ke bace , domin idan kece na shiga uku na lalace"

Fauziya ce ta iya budar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login